← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 53

Sashe 10

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Da kyar ya ja wani dogon numfashi sannan ya kallesu cikin takaicin halin da yake sa su.
Wasu zafafun hawaye ne suka zubomai yana kallan mahaifiyarsa.
Ummy jiki a sanyaye ta karaso inda yake ta rike hannunsa tace “Hassan!”
Bakinsa ne ya shiga rawa, a hankali yace “Ummy kiyi hakuri.”

Kai ta shiga girgizawa tana kuka tace “Hassan please kadaina fadar haka.”
Sagir ma jiyai hawaye ya zubo masa saboda tausayi, Abba ya sa hannu ya d’agata yace “ ku je ku barshi ya huta.”
Haka suka fito daga d’akin hankalinsu a tashe, Abba ya zauna kusa dashi yace “Hassan meyasa kake kokarin jefa rayuwarka cikin halaka? Sau nawa zamu sanar dakai abinda ya faru a baya ba laifinka bane?dan Allah ka taimakemu ka cirema zuciyarka wannan zargin da takeyi.”
Hassan ya juya kansa gefe kawai baice komai ba, Abba ya mike ya fita, tabbas ya yarda da maganar likita aure ne ya dace dashi, yanzu in tsakar dare ne abin nan ya faru ba wanda zai kula dashi me zai faru?

Ummy kam kuka tai tayi, Sagir yana zaune a kasanta ya rasa ta ina zai fara lallashinta, gaba d’aya gidan a wannan rana ba wanda yai walwala.

***********

Yau da daddare Abba ya gama yanke hukuncinsa dan a daren jiya bacci kalilan yai.
Yau da safe kuwa karfe 10 ya kira wayar Inna.
Bayan sun gaisa ne yace “Hajiya nayi dogon nazari akan al’amarin nan, sai dai ina tunanin haduwa ya kamata muyi ko in sanar dake ta nan?”
Inna tace “Taura duk yanda ka gani.”

Yai shiru kafin yace “Bari in sanar dake ta nan in yaso in kikai tunani sai mu hadu dan yanke hukunci.”
Tace “ba laifi hakan yayi.”

Sai daya danyi shiru kadan kafin yace “ me zai hana muyi yar hadin gida.”

“Yar hadin gida?kamar ya kenan?”
Yace “eh, ina nemawa d’ana babba auran babbar jikarkarki.”

Mikewa tai daga zaman da take tama kasa cewa komai, yace “Hello!”
Tace “ Taura naji, ba matsala mayi magana daga baya.”
Ta katse wayar hankalinta a tashe.
Da sauri ta danna number Dady.

Yana kwance akan gado Mumy ba kwance a kafadarsa suna hira.
Yana ganin wayar Inna ya mike tsaye yace “plm ce.”
Mumy ta turo baki tace “share ta kawai, na tabbatar maganar aiki......”
Bata karasa abinda zata fada ba taji yana cewa “To.”
Yana kashewa taga ya kalleta yace “Inna na neman mu.”

Mikewa tai suka hau sama.

Jalila na ta aiki sanda ta gansu sun hau sama, sun nutsu dan yanda suka ganta alamar ba lafiya.
Inna ta dade kafin ta kallesu tace “Taura ya kirani.”
Mumy tace “ya amince?”
Tace “eh.”
Mumy tace “lalai mutumin nan yanada kudi, wannan uban kudi da muka nema?”
Inna ta mata kallan batada hankali, sannan ta daga waya ta kira Sani a gabansu ta sa a hands free.
Bayan sun gaisa tace “ Sani me kacemin dangane da babban dan Taura?”
Sani yace “ bashida cikakiyar lafiya, dan akwai wanda yacemin ma kwakwalwarsa ba daidai take ba.”
Inna tace to nagode.
Ta kashe wayar sannan ta kallesu tace “hadin aure Taura yake neman yi damu.”
Mumy cikin halin ko in kula tace “Hadin aure da wa kenan?”
Dady kallan Inna yai cikin mamaki, Inna tace “me yasa bakya amfani da kwakwalwarki ne?”
Tace “to ai ni bangane da wa za’ai hadin aure...... “
Dady ne yai saurin tabata sannan ya kalli Inna yace “amma ai baiga Safeena ba.”

Tace “nima abinda ya ban mamaki kenan daga farko, sai daga baya nai tunanin yaransa ashe fa ancemin ba hankali gareshi ba, kaga kuwa ta ya ya zai damu da sai ya ganta? Tunda shine dai kawai burinsa yaga ya sa marmai mata ne?”

Mumy tace “hauka kenan, ta ya ya dan zai bamu kudi zai nemi hadin aure tsakanin mai hankali da mahaukaci?”

Dady ma yace “gaskiya Inna nima ban amince abama Safeena mahaukaci ba.”
Inna tace “me kuke tunani? Kuna tunanin nima a san raina ne?”
Mumy zatai magana sukaji an kwankwasa kofa.
Inna tace “waye?”
Jalila tace “nice, abinci na kawo.”

Inna tace shigo.
Shiga tai ta ajiye abincin a inda tasaba ajiyewa sannan ta gaisheta, ta gaidasu Dady sannan ta mike tai waje.

Tana rufe kofa naga idanun Mumy dana Inna sun kalli juna, Inna ta hade rai ta kalli Dady tace “ da Taura ya kira cewa yai yanasan hadin aure tsakanin babban dansa da babbar jikata.”
Dady yace “ to yazamuyi?”
Tace “baka fahimceni ba kenan?”
Yace “kamar ya kenan?”
Inna tace “a ka’ida wacece babbar yarka?”
Da sauri ya kalleta dan yanzu ya fahimce me take san fad’a, jiki a sanyaye yace “Jalilah.”
Tace “wa kake tunanin Taura na nufi?”
Dady ya kalleta sai dai bai iya cewa komai ba.

Mumy cikin kissa tace “Yanzu Inna ta ya zamu aurana Jalila mahaukaci? Gaskiya nikam ban yarda ba.”
Inna tace “ to sai shi Abbakar din ya duba ya gani, da company dinmu ya durkushe mu rasa kudin mu, da mu daure mu aurama Jalila yaran wanne yafi? Sannan yaushe kikaji ance miki mahaukaci ne?”

Dady yai shiru yama rasa me zaice, can yace “amma ai suna ganinta zasusan ba yar cikin gidan nan bace.”

Inna tace “karka damu da wannan zansa yau din nan a maga dinkuna kala kala, sannan zansa a dauko mai aiki, ai dama na dade ina tunanin cewa ta bar aikin da takeyi, kuma yaran nan tunda yana da matsalar kwakwalwa gani nake bazai zama wani abu ba, gidan kudi zata sannan in haukar ta juyo mai zai iya sakintama a ranar kaga shikenan kowa ya huta.”

Kallan mamaki ya shiga yima Inna, tabbas wannan kalaman nata sunzo da rainin hankali sai dai bayaji zai iya bijirewa domin shima ya tsani talauci a rayuwar sa, menene dan ya sadaukar da rayuwar yarinya d’aya?

Inna tace “in kuma baka yarda ba.......”
Yace “Inna waec.....”
Tace “zanyima Taura magana a barta sai ta gama karatunta, sannan a gida ma banasan kowa ya sani har sai ta kammala karatunta yanda hankalinta zai kwanta.”
Dady ya jinjina kai alamar gamsuwa.

Haka suka cigaba da tsare tsarensu shidai Dady kome sukace yarda yakeyi.

Kiran Taura Inna tai ta sanar dashi amincewarsu.
Yaji dadi sosai ya ce zaizo karshen satin nan ya kawo kudi sannan su sa hannu akan contract din da sukai.

Ummy dai batace komai ba, sai dai Abba yace “in zaije sai suje tare ta ganta.” Da haka ya rufe mata baki.

*********
Jalila tayi mamaki sosai ran lahadi da yamma da Mumy ta nuna mata wata mata a matsayin mai aikinsu, sannan tace mata daga yau karta kara yin aikin gida.
Abinci ma mai raia da lafiya aka aiko musu.
Yau kam cike da mamaki tabar gidan.

Da zata tafi har dari biyu Mumy ta bata wai kudin kashewa, yanda ake ba su Safeena.

Suna isa makaranta ta sauko tana tafiya, tunani takeyi wannan kuma wani sabon salon ne ke faruwa?

Sam bata kula dashi ba wanda missing dinta ya sashi fitowa da wuri.
Yana kallanta har ta wuce bata kula dashi ba, sai datai nisa yace “Jalilah!”
Juyowa tai ta kalleshi, jitai duk damuwar dake ranta ya tafi, wani sansanyan murmushi ne ya bayyana a fuskarta.
Tace “Uncle.”
Fuska ya daure sannan yace “ what are u thinking?”
Tace “Something suspicious.”
Ganin Zarah ta taho yasa yace “See u later.”
Sannan ya juya.
Da kallo ta bishi dashi tana murmushi.
Zarah ta daka mata duka a baya tace “Anya Jalila bakida crush akan Uncle Sagir kuwa?”
Jalila ta ture hannunta tace “to uwar sa ido, in ma inada shi laifi ne?”

Zarah tai dariya tace “in shigar dake?”
Jalila a ranta tace na shigar da kaina tuni, amma a fili tace “ ni banasan love one side.”

Haka suka tafi suna hira.

Sai da aka tashe aka watse tana tsaye, sai leken kofa take ko zataga fitowarsa, sai can ta hangoshi ya taho.
Da sauri ta juya kamar bata kallan gun, har sai daya iso.
Jitai yace “ Hajiyar tunani an cigaba ne?”
Kallansa tai tace “Uncle kaine?”
Murmushi yai sannan yace “bakima ji alamun na iso ba?”
Tace “sry na tafi tunani ne.”
Fuska ya dan canza yace “anya kuwa kinyi missing dina?”

Idanu ta rufe wai ita kunya sannan tace” sosai ma.”
Yace “ to kunyar ita kuma ta menene? Ni bude idanunki ki fadamin meke damunki?”
Idanunta ta bude tace “Uncle me zakace ingaka wanda ya tsaneka ya fara nuna maka yana sanka?”

Sagir yai shiru kafin yace “ya danganta da irin tsanar da kuma irin san.”
Tace “ da ba wanda ya damu dakai haka kawai sai kuma kaga kowa yana ma mutunci yana kula da kai.”
Yace cikin dayan biyu ne, ko sun fara santa da gaske ko kuma suna san wani abu daga gunta.”

Jalila tai shiru tana tunani, itakam bataji akwai na biyun, to ko santa sukeyi yanzu? Da sauri ta girgiza kai tace “tunda aka haifen basa sona sai yanzu?????

Nima nace gaskiya kam😝

#Oneluv💕
[07/10, 21:26] ‪+234 803 222 1758‬: 🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

  (_D home of expert and perfect writer's_💡)

*NO 10*
Chapter 10 · 0% Book details