Sashe 35
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jalila ta mike sum sum tai waje, ita kanta mamaki take, tana da surutu sai dai ba'a ko ina ba, a gaban Goggonta kadai take magana san ranta, amma ta rasa me yasa yanzu ta saki jiki da Hassan har take magana haka dashi, duk kuwa da dizgatan da yake.
Rufe masa motar tai ta tako zuwa cikin gida, tana kokarin bude kofa shi kuma ya turo kofar zai fita.
Tsayawa sukai suka kalli Juna, Jalila ta matsa ta bashi hanya.
Sagir ya kalleta yace " ki shiga."
Ya fada tare da rike da matsa mata, kallansa tai sannan ta tako ta shiga.
Har zata wuce taji yace " kinga Goggon?"
Ta kalleshi ta daga mai kai alamar eh, murmushi yai tare da cewa "Alhamdulila."
Bata amsa mai ba ta wuce ciki, dakin Ummy ta nufa ta kwankwasa mata kofa.
Ummy na kwance dan zazzabi ke neman rufeta tace "shigo."
Jalila ta murda kofar dakin ta shiga, Ummy na kishingide akan gado Jalila ta shiga.
Tace "Ummy ina wuni?"
Ummy ta kalleta tace "kun dawo?"
Jalila ta matso tace "eh, amma Ummy lafiya dai ko na ganki a kwance"
Kallanta tai tace "kai na kemin ciwo."
Da sauri Jalila ta matso tace "Sannu Ummy, kinsha magani?"
Murmushi ta sakar mata tace "kar ki damu daga nayi bacci zai ware."
Jalila ta tsaya tana kallanta cikin tausayawa, tabbas abinda ya faru jiya ne kila yake damunta.
Daurewa tai tace "Abba fa?"
Ummy tace "dazu ya tafi Abuja."
Jalila tace "Ummy ko dai in kira Yaya akaiki asibiti?"
Hannunta ta kamo tace "Jalila karki fadama Hassan banajin dadi."
Jalila cikin mamaki tace "Ummy me yasa?"
Tai murmushi tace "Tun yana karami bayasan yaga ko ya ya ne banda lafiya, in kuwa ya sani to ya dinga kuka kenan, yanzu kuwa da ba lafiya gareshi ba inya sani abin nashi karuwa yake."
Jalila tace "to a kira Ya Sagir."
Ummy tace "Jalila karki damu, daga na kwanta shikenan."
Jalila tai shiru kafin tace "bari nai sallah."
Nan ta fito zuwa sama, baya dakin nan tai alwala tai sallar isha'i sannan ta sauko zuwa kitchen.
Duk da batajin dadi Ummy sai data musu jollof din taliya wacce tasha kayan ciki.
Jalila ta dau nasu takai sama sannan ta dawo gun Ummy.
Hassan kam ya dade a mota kafin ya fito, kofar dakin Ummy ya murda dan yana san ya tabbatar da gaske Abban yayi tafiyar?
Ummy na kwance da alama bacci take, ita kuma Jalila na zaune a kasan carpet ta daura kanta akan gado, itama da alama bacci ya fara dan daukarta.
Tsayawa yai yana kallansu, yanayin kallan da yake musu ba irin kallan daya saba bane, yau kallo ne yake na jin dadin ganin Ummy da Jalila.
Yana neman juyawa yaji Ummy tace "Hassan!"
Juyowa yai ya kalleta, tace "zo ka dauki matarka ku tafi."
Yace "in dauketa kamar ya?"
Tace " Badai dan rashin tausayi tashinta zakayi ba?"
Yace "Ummy tanada kafa fa?"
Ummy ta mai alama da hannu akan yai shiru sannan ta mai alama da dayan hannun akan ya shigo.
Shigowa yai fuskarsa a daure, a hankali tace "dauketa, da alama baccin yanzu ya dauketa, kuma da karfi ya dauketa."
Hassan ya kalli Ummy sannan ya kalli Jalila dake bacci, ta karamai alama da hannu akan ya dauketa.
Cikin takaici yasa hannu ya dauketa kamar yarinya.
Jalila kam yana daukanta taji alama sai dai muryar Ummy dataji tace "to sai da safenku."
Yasa ta fahimci Hassan ne sai ta kara rufe ido dan batasan ta ina zata fara kallansa ba.
Hassan ya juya ya fita, Ummy ta kallesu cikin farinciki sannan ta kalli gefen gado, Abinci Jalila ta ajiye mata da ruwa da paracetamol wanda ta tabbatar a cikin magungunanta ta dauko mata.
Murmushi tai sannan ta hadiye maganin kawai ta kishingida.
Hassan haka ya hau da ita steps din har yaje kofarsu, kallanta yai yaga tana kif kif da ido, hannu yasa ya bude kofar sannan ya shiga ciki.
Gani nai yayi hanyar toilet da ita ya bude kofar, yana neman shiga, Jalila kam jin ya sake bude kofa yasa ta bude ido ta kalleshi.
Ganinshi tai yana neman shiga toilet da ita, da sauri tace "Yaya ina zaka kaini?"
Yace "au kin tashi?"
Tace "ina zaka kaini?"
Yace "kamar Ummy cewa tai in kaiki bandaki in taimaka miki kiyi wanka."
Da sauri ta fara kokarin kwace kanta tana cewa "wlh banji tace haka ba.
Sauke ta yai a ciki sannan yace " me tace to?" Yafada tare da tare hanyar toilet din.
Jalila ta kalleshi tace " cewa tai sai da safenku."
Hassan yace "hmmm bakiji farkon ba kenan, ni kuma na ji."
Kallansa tai batace komai ba, fitowa yai yasa hannu yana neman rufe kofar.
Da sauri ta rike tana cewa "yaya menai? Naga lafiya muka dawo."
Yace " idanki biyu kikasa ma daukeki?"
Tace " ba idona biyu ba Allah daga baya na farka."
Yace " da kika farka fa?"
Tace "yahkuri wlh ni kunya naji."
Kallanta ya tsaya yanayi.
Kanta ta maida kasa tana kara rike kofar, can ta saki dan kara ta rike hannunta tace "wayyo hanuna."
Kallanta yai yace "hannu?"
Jinginna tai da bango tana dan murza hannun, sakin kofar yai ya shigo yana cewa "menene?"
Da sauri tai waje da gudu tana dariya.
Tsayawa yai kawai yana kallan ta, lalai yarinyar nan.
Dariya ta shiga yi tana cewa "yaya wai harka shiga?"
Hassan ya hade rai ya fara nufo ta, ganin yanda idanunsa suka canza yasa ta tsaya cikin tsoro tanayin baya.
Sai dayaje daf da ita sannan ya zauna akan gado bai ce mata komai ba ya dau littafinsa.
Kallansa tai jiki a sanyaye tace " Yaya bakai dinner ba."
Kallanta yai yanzu ma baice komai ba, tai shiru ta zauna a gefen gado daga karshe.
Shiru ne ya ratsa dakin kafin can yace "Jalilah!"
Kallansa tai da sauri, yauce rana ta farko da ya kirata da sunanta cikin wannan muryar, murya ba mai dauke da zafi ko fada ba.
Idanunta na kansa yace " Jalilah Please take care of Ummy."
Idanunta na kansa tana kallansa ta daga mai kai alamar fahimta sannan tace " Insha Allah."
Haryanzu idanunsa na kanta yace " Nagode."
Kanta ta sunkuyar sannan tace "nima na gode Yaya da taimakon da kamin."
Yace " me kika ce ma Goggon taki?"
Ta kalleshi da raunanan ido tace " ban iya cemata komai ba, bansan ta ina zan bulo ba, bansan me zan ce mata ba."
Ta karasa magana tana share kwalla, kallanta yai yanasan lalashinta sai dai bai san ta ina zai fara bama.
Kansa ya dauke daga gunta, wayarsa ya dauka ya dubo sunan Abba.
Rabon daya kirashi harya manta, sai dai shi Abban ya nemi shi.
Dialing yai yana kallan agoggo, goma saura.
Yanajin wayar har ta gama ringing bai dauka ba, idanunsa ne suka kara canzawa ya sake kira, tana daf da katsewa Abba ya daga cikin mamaki da shakka.
Kallan Abokinsa yai sannan ya mike daga falon ya fito waje.
Ya daga yana cewa "Hassan!"
"Abba kana ina?"
Jalila ce ta kalleshi da sauri, Abba yace "nayi tafiya ne, baka tambayi Ummynka ba?"
Hassan yace " na dauka akan tafiyarne kukai fada?"
Abba cikin mamaki yace "Haka tacem?" Yana mamakin kiran da Hassan yamai da kuma mamakin yanda yake tambayarsa, duk da Hassan na tsananin san Ummy bai taba shiga maganarsu ba, me ke faruwa?"
Hassan harzai sake magana sai kuma ya kashe ya cillar dawayar gefen gadon.
Jalila tai shiru tana kallansa, mikewa tai tai shimfida dan yanda ta ganshi tasan da matsala.
Bata dade da kwanciya ba bacci yai gaba da ita.
Hassan kam ya dade kafin ya mike ya sauko kasa.
Sai daya leka Ummy yaga tana bacci sannan ya juya ya koma sama.
Jalila ya kalla wacce ke bacci, daga gefen gado ya kwanta har bacci ya daukeshi.
Yanda jikinsa ke kadawa da yanda yake abu kamar maiyin kuka yasa cikin baccinta ta farka.
Da sauri ta kunna wayarta sannan ta kunna fitilar dakin.
Bakinsa sai kakkarwa yakeyi, da sauri ta karasa kusa dashi ta kamo hannunsa.
Ganin yana neman fadowa daga kan gadon yasa ta rungumeshi tana hawaye tana kiran sunansa.
Idanunta a runtse, hawaye kawai ke zuba.
Ta kankameshi, sun dade a haka kafin nimfashinsa ya fara daidaituwa.
A hankali ya bude idanunsa ya zubasu akanta, hawaye kawai take tana kiransa.
Yanda ta rungumeshi ne yasa ya kara kallanta sannan yace "Jalila!"
Idanunta ta bude ta kalleshi, bakinta na rawa tace "Yaya?"
Yace "wannan rikon fa?"
Sakeshi tai tana kallansa, ya kalleta yace "baki iya addu'a bane sai kuka da kiran sunana?"
A hankali tace "banyi islamiya ba."
Kallan mamaki ya mata da tausayawa, sannan yace " kukan fa? Are u worried about me? Or are u scared?"
Kallansa tai bata iya cewa komai ba.
Agoggo ya kalla, karfe biyar saura, mikewa yai ya nufi toilet har zai shiga sai yace " forget what I just said."
Sannan ya shiga, ajiyar zuciya tai sannan ta sa hannunta shafi fuskarta.
**********
A abuja kuwa, Abba ya kalli Abokinsa Hafiz yace " sry muna magana yarona ne ya kira."
Hafiz yace " to yaya? In sanar da ita ne ko ka fasa?"
Abba yai shiru kafin can yace "bari dai sai zuwa gobe, in na sake yin nazari."
Hafiz yai dariya yace "nazarin me? Bayan abinda ranka ke so ne sannan ba haramun bane?"
Abba yai shiru yana tunanin yanda idanun Hassan sukai alokacin daya shigo, can yace "sai dai goben."
Hafiz yace shikenan Allah ya kaimu.
Nan Abba ya fito, yana neman fita gate yaji muryarta tace "Ba gaisuwa?"
Juyowa yai da sauri ya kalleta, gani nai ya hadiye wani yawo, Zaliha tayi kyau iya kyau kamar mai shirin zuwa dinner doguwar riga ce a jikinta ba dankwalli balle mayafi.
Gashin kanta kawai ta saukar wanda yasa gyara.
Bakinsa na rawa yace "Zaliha ko?"
Ta dan kashe mai ido sannan ta matso inda yace tace "badai sunan ma an manta ba?"
Yai dariya yace " ina zan manta?"
Tace "muje ciki mu gaisa, bana iya jurar tsayuwa."
Nan yaga ya juya tana gabe yana binta a baya, komai na jikinta motsi yakeyi.
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Rufe masa motar tai ta tako zuwa cikin gida, tana kokarin bude kofa shi kuma ya turo kofar zai fita.
Tsayawa sukai suka kalli Juna, Jalila ta matsa ta bashi hanya.
Sagir ya kalleta yace " ki shiga."
Ya fada tare da rike da matsa mata, kallansa tai sannan ta tako ta shiga.
Har zata wuce taji yace " kinga Goggon?"
Ta kalleshi ta daga mai kai alamar eh, murmushi yai tare da cewa "Alhamdulila."
Bata amsa mai ba ta wuce ciki, dakin Ummy ta nufa ta kwankwasa mata kofa.
Ummy na kwance dan zazzabi ke neman rufeta tace "shigo."
Jalila ta murda kofar dakin ta shiga, Ummy na kishingide akan gado Jalila ta shiga.
Tace "Ummy ina wuni?"
Ummy ta kalleta tace "kun dawo?"
Jalila ta matso tace "eh, amma Ummy lafiya dai ko na ganki a kwance"
Kallanta tai tace "kai na kemin ciwo."
Da sauri Jalila ta matso tace "Sannu Ummy, kinsha magani?"
Murmushi ta sakar mata tace "kar ki damu daga nayi bacci zai ware."
Jalila ta tsaya tana kallanta cikin tausayawa, tabbas abinda ya faru jiya ne kila yake damunta.
Daurewa tai tace "Abba fa?"
Ummy tace "dazu ya tafi Abuja."
Jalila tace "Ummy ko dai in kira Yaya akaiki asibiti?"
Hannunta ta kamo tace "Jalila karki fadama Hassan banajin dadi."
Jalila cikin mamaki tace "Ummy me yasa?"
Tai murmushi tace "Tun yana karami bayasan yaga ko ya ya ne banda lafiya, in kuwa ya sani to ya dinga kuka kenan, yanzu kuwa da ba lafiya gareshi ba inya sani abin nashi karuwa yake."
Jalila tace "to a kira Ya Sagir."
Ummy tace "Jalila karki damu, daga na kwanta shikenan."
Jalila tai shiru kafin tace "bari nai sallah."
Nan ta fito zuwa sama, baya dakin nan tai alwala tai sallar isha'i sannan ta sauko zuwa kitchen.
Duk da batajin dadi Ummy sai data musu jollof din taliya wacce tasha kayan ciki.
Jalila ta dau nasu takai sama sannan ta dawo gun Ummy.
Hassan kam ya dade a mota kafin ya fito, kofar dakin Ummy ya murda dan yana san ya tabbatar da gaske Abban yayi tafiyar?
Ummy na kwance da alama bacci take, ita kuma Jalila na zaune a kasan carpet ta daura kanta akan gado, itama da alama bacci ya fara dan daukarta.
Tsayawa yai yana kallansu, yanayin kallan da yake musu ba irin kallan daya saba bane, yau kallo ne yake na jin dadin ganin Ummy da Jalila.
Yana neman juyawa yaji Ummy tace "Hassan!"
Juyowa yai ya kalleta, tace "zo ka dauki matarka ku tafi."
Yace "in dauketa kamar ya?"
Tace " Badai dan rashin tausayi tashinta zakayi ba?"
Yace "Ummy tanada kafa fa?"
Ummy ta mai alama da hannu akan yai shiru sannan ta mai alama da dayan hannun akan ya shigo.
Shigowa yai fuskarsa a daure, a hankali tace "dauketa, da alama baccin yanzu ya dauketa, kuma da karfi ya dauketa."
Hassan ya kalli Ummy sannan ya kalli Jalila dake bacci, ta karamai alama da hannu akan ya dauketa.
Cikin takaici yasa hannu ya dauketa kamar yarinya.
Jalila kam yana daukanta taji alama sai dai muryar Ummy dataji tace "to sai da safenku."
Yasa ta fahimci Hassan ne sai ta kara rufe ido dan batasan ta ina zata fara kallansa ba.
Hassan ya juya ya fita, Ummy ta kallesu cikin farinciki sannan ta kalli gefen gado, Abinci Jalila ta ajiye mata da ruwa da paracetamol wanda ta tabbatar a cikin magungunanta ta dauko mata.
Murmushi tai sannan ta hadiye maganin kawai ta kishingida.
Hassan haka ya hau da ita steps din har yaje kofarsu, kallanta yai yaga tana kif kif da ido, hannu yasa ya bude kofar sannan ya shiga ciki.
Gani nai yayi hanyar toilet da ita ya bude kofar, yana neman shiga, Jalila kam jin ya sake bude kofa yasa ta bude ido ta kalleshi.
Ganinshi tai yana neman shiga toilet da ita, da sauri tace "Yaya ina zaka kaini?"
Yace "au kin tashi?"
Tace "ina zaka kaini?"
Yace "kamar Ummy cewa tai in kaiki bandaki in taimaka miki kiyi wanka."
Da sauri ta fara kokarin kwace kanta tana cewa "wlh banji tace haka ba.
Sauke ta yai a ciki sannan yace " me tace to?" Yafada tare da tare hanyar toilet din.
Jalila ta kalleshi tace " cewa tai sai da safenku."
Hassan yace "hmmm bakiji farkon ba kenan, ni kuma na ji."
Kallansa tai batace komai ba, fitowa yai yasa hannu yana neman rufe kofar.
Da sauri ta rike tana cewa "yaya menai? Naga lafiya muka dawo."
Yace " idanki biyu kikasa ma daukeki?"
Tace " ba idona biyu ba Allah daga baya na farka."
Yace " da kika farka fa?"
Tace "yahkuri wlh ni kunya naji."
Kallanta ya tsaya yanayi.
Kanta ta maida kasa tana kara rike kofar, can ta saki dan kara ta rike hannunta tace "wayyo hanuna."
Kallanta yai yace "hannu?"
Jinginna tai da bango tana dan murza hannun, sakin kofar yai ya shigo yana cewa "menene?"
Da sauri tai waje da gudu tana dariya.
Tsayawa yai kawai yana kallan ta, lalai yarinyar nan.
Dariya ta shiga yi tana cewa "yaya wai harka shiga?"
Hassan ya hade rai ya fara nufo ta, ganin yanda idanunsa suka canza yasa ta tsaya cikin tsoro tanayin baya.
Sai dayaje daf da ita sannan ya zauna akan gado bai ce mata komai ba ya dau littafinsa.
Kallansa tai jiki a sanyaye tace " Yaya bakai dinner ba."
Kallanta yai yanzu ma baice komai ba, tai shiru ta zauna a gefen gado daga karshe.
Shiru ne ya ratsa dakin kafin can yace "Jalilah!"
Kallansa tai da sauri, yauce rana ta farko da ya kirata da sunanta cikin wannan muryar, murya ba mai dauke da zafi ko fada ba.
Idanunta na kansa yace " Jalilah Please take care of Ummy."
Idanunta na kansa tana kallansa ta daga mai kai alamar fahimta sannan tace " Insha Allah."
Haryanzu idanunsa na kanta yace " Nagode."
Kanta ta sunkuyar sannan tace "nima na gode Yaya da taimakon da kamin."
Yace " me kika ce ma Goggon taki?"
Ta kalleshi da raunanan ido tace " ban iya cemata komai ba, bansan ta ina zan bulo ba, bansan me zan ce mata ba."
Ta karasa magana tana share kwalla, kallanta yai yanasan lalashinta sai dai bai san ta ina zai fara bama.
Kansa ya dauke daga gunta, wayarsa ya dauka ya dubo sunan Abba.
Rabon daya kirashi harya manta, sai dai shi Abban ya nemi shi.
Dialing yai yana kallan agoggo, goma saura.
Yanajin wayar har ta gama ringing bai dauka ba, idanunsa ne suka kara canzawa ya sake kira, tana daf da katsewa Abba ya daga cikin mamaki da shakka.
Kallan Abokinsa yai sannan ya mike daga falon ya fito waje.
Ya daga yana cewa "Hassan!"
"Abba kana ina?"
Jalila ce ta kalleshi da sauri, Abba yace "nayi tafiya ne, baka tambayi Ummynka ba?"
Hassan yace " na dauka akan tafiyarne kukai fada?"
Abba cikin mamaki yace "Haka tacem?" Yana mamakin kiran da Hassan yamai da kuma mamakin yanda yake tambayarsa, duk da Hassan na tsananin san Ummy bai taba shiga maganarsu ba, me ke faruwa?"
Hassan harzai sake magana sai kuma ya kashe ya cillar dawayar gefen gadon.
Jalila tai shiru tana kallansa, mikewa tai tai shimfida dan yanda ta ganshi tasan da matsala.
Bata dade da kwanciya ba bacci yai gaba da ita.
Hassan kam ya dade kafin ya mike ya sauko kasa.
Sai daya leka Ummy yaga tana bacci sannan ya juya ya koma sama.
Jalila ya kalla wacce ke bacci, daga gefen gado ya kwanta har bacci ya daukeshi.
Yanda jikinsa ke kadawa da yanda yake abu kamar maiyin kuka yasa cikin baccinta ta farka.
Da sauri ta kunna wayarta sannan ta kunna fitilar dakin.
Bakinsa sai kakkarwa yakeyi, da sauri ta karasa kusa dashi ta kamo hannunsa.
Ganin yana neman fadowa daga kan gadon yasa ta rungumeshi tana hawaye tana kiran sunansa.
Idanunta a runtse, hawaye kawai ke zuba.
Ta kankameshi, sun dade a haka kafin nimfashinsa ya fara daidaituwa.
A hankali ya bude idanunsa ya zubasu akanta, hawaye kawai take tana kiransa.
Yanda ta rungumeshi ne yasa ya kara kallanta sannan yace "Jalila!"
Idanunta ta bude ta kalleshi, bakinta na rawa tace "Yaya?"
Yace "wannan rikon fa?"
Sakeshi tai tana kallansa, ya kalleta yace "baki iya addu'a bane sai kuka da kiran sunana?"
A hankali tace "banyi islamiya ba."
Kallan mamaki ya mata da tausayawa, sannan yace " kukan fa? Are u worried about me? Or are u scared?"
Kallansa tai bata iya cewa komai ba.
Agoggo ya kalla, karfe biyar saura, mikewa yai ya nufi toilet har zai shiga sai yace " forget what I just said."
Sannan ya shiga, ajiyar zuciya tai sannan ta sa hannunta shafi fuskarta.
**********
A abuja kuwa, Abba ya kalli Abokinsa Hafiz yace " sry muna magana yarona ne ya kira."
Hafiz yace " to yaya? In sanar da ita ne ko ka fasa?"
Abba yai shiru kafin can yace "bari dai sai zuwa gobe, in na sake yin nazari."
Hafiz yai dariya yace "nazarin me? Bayan abinda ranka ke so ne sannan ba haramun bane?"
Abba yai shiru yana tunanin yanda idanun Hassan sukai alokacin daya shigo, can yace "sai dai goben."
Hafiz yace shikenan Allah ya kaimu.
Nan Abba ya fito, yana neman fita gate yaji muryarta tace "Ba gaisuwa?"
Juyowa yai da sauri ya kalleta, gani nai ya hadiye wani yawo, Zaliha tayi kyau iya kyau kamar mai shirin zuwa dinner doguwar riga ce a jikinta ba dankwalli balle mayafi.
Gashin kanta kawai ta saukar wanda yasa gyara.
Bakinsa na rawa yace "Zaliha ko?"
Ta dan kashe mai ido sannan ta matso inda yace tace "badai sunan ma an manta ba?"
Yai dariya yace " ina zan manta?"
Tace "muje ciki mu gaisa, bana iya jurar tsayuwa."
Nan yaga ya juya tana gabe yana binta a baya, komai na jikinta motsi yakeyi.
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯