← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 53

Sashe 26

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Juyowa yai ya kalleta, yana tsaye harta karasa gangarowa daga saman benan, ta matso gunsa tace "ina zaka?"
Leda ya mika mata yace "Gashi kiba matar Yaya."
Amsa tai tana cewa "menene ya Sagir? Sam ka canza  gaba daya yanzu bakasan magana sosai."
Murmushi yai na dole yace "Ummy fa?"
Ta nuna sama da hannu tace "tana sama" sannan ta matso kusa dashi sosai alamar rada tace "Ummy fa ta dage sai yaya ya amince da matarsa."

Sagir ya kalleta yace "bangane ba...."
Tace "tana sama tana hada musu daki daya."

Wani abu ne yaji ya harba kirjinsa me kake tunani Sagir? Abinda wata zuciyar ta tambayeshi kenan?.
kallanta yai yace "haba."
Dakyar yai maganar, tace "Ai Ummy ta dage wannan karan."
Harararta har sannan ya ture kanta yace "yaushe kika zama mara kunya? Wato harkin fassara zamansu a daki daya kena?"

Tace " ko yaro dan shekara sha biyar ai yasan me ake nufi a wannan lokacin."
Buge kafadarta yazoyi ta zille da sauri yace "Ameera? Kece kuwa?"

Dariya tasa tace "ni ba ruwana Ya Sagir."

Da kallo ya bita yana murmushi harta shige daki, tana shiga yanayin fuskarsa ya canza, daki daya? Wata zuciyarce ta kara cewa me kake tunani ne wai? Daga lokacin da aka daura aure ai kaima kasan abinda ya kamata.
Juyawa yai jiki a sanyaye ya fita.

Tana zaune tana kuka Ameera ta turo kofar, da sauri ta goge hawayenta, Ameera ta kalleta tace "jikin ne?"
Kai ta daga alamar a'a sannan tace "Sunanki Ameera ko?"
Tace eh, Jalila tace "ni sunana Jalila."
Ameera tace "na sani."
Jalila tai murmushi tace "Oh, yahkuri."
Ameera ta kalleta tace "Ummy ce ta fadamin, sannan na gani a katin daurin aure."

Jalila ta jinjina kai, Ameera ta mika mata ledar tace "gashi inji Ya Sagir, ah bakisanshi ba ko?"
Jalila ta kalleta batace komai ba, Ameera tace "shine kanin Yaya, daga shi sai ni, mu uku ne."
Jalila tace "Yaya?"

Ameera tace "Ya Hassan fa nake nufi mijinki."

Jalila batasan sanda tai wata dariya ba wace ni kaina bansan irinta ba, miji? Mijin da sai yanzu ma tasan sunansa?

  Kallanta tai a ranta tace Husainin fa? Tace Hassan sannan tace Sagir.
Kamar Ameera tasan me take tunani tace "ya rasu, dan uwan nasa."
Jalila ta kalleta tace "Ayya Allah ya jikansa."
Ameera ta ajiye ledar tana cewa Ameen.

Jalila ta dau maganin tasha.
  Jalila can tace "wanka nakesan yi kayana fa dan Allah?"

Ameera tace "muje sama."
Jalila ta mike ba tare da ta musa ba, Ummy na saukowa suna fitowa, Ummy ta kallesu murmushi tai sannan tace "Jalila kin mike?"
Kai ta daga tare da sunkuyawa, tsugunawa sukaga tayi tace "Ina wuni."

Ummy tasa hannu ta dagata sannan tace "ke da bakida lafiya?"

Jalila kanta na kasa, Ummy tai murmushi sannan ta kamo hannunta, maimakon su hau sama sai ta riketa zuwa falo.

Ameera ta kalla tace "Ameera asa mana abincin dare."
Ameera tace "Ummy yau ma nice?"
Ummy tace "ai na fada miki dama, daga kin shiga aji shida shikenan girki ya kamaki, yanzu kuwa kunyi hutun canjin aji kinga kuwa a matsayin yar aji 6 kike."

Ameera ta shagwabe fuska ta nufi kitchen ranta ba dadi, ita kam tana ganin ya kamata a samarmusu mai aikin yin abinci amma taki, mai musu aiki ma suna gama gyara gidan suke tafiya sai kuma gobe.

  Ummy ta maido da hankalinta kan Jalila ta zauna sannan ta zaunar fa ita a gefen ta.
Jalila ta zauna a darare, Ummy ta riko hannunta tace "Jalila!"
Jalila ta kalleta kadan sannan ta maida kanta kasa tana kallan yanda Ummy take rike da hannunta, Ummy tace " ya jikin naki?"
Jalila tace Da sauki.
Ummy tai shiru kafin tace "da rokonki nake san yi."
Jalila ta kalleta da sauri tana san jin menene, sai dai bazata iya dadewa tana kallanta ba, da sauri ta maida idanunta kasa.

Ummy tace "rokonki zanyi akan ki saki jikinki da mu, ki maida gidan nan kamar gidan ku koma sama da gidanku, nasan zama da iyayen miji ba abune dayake da dadi ba,  abu ne mai wahala tun balle ga yarinya, sai dai mu lalurace tasa muke sanki anan gidan, sannan bawai dan mu cutar dake bane sai dan muna ganin in kina kusa damu hankalinki da namu sai yafi kwanciya."

Lalura? Abinda yazo mata a ranta kenan sai dai batace komai ba har Ummy tace "Jalila mun miki laifi wanda nikaina nasan bamu kyauta miki ba."
Jalila ta kalleta tace "Laifin me?"
Ummy ta saki hannunta sannan jiki a sanyaye tace "mun miki laifi gun b'oyemiki larurar Hassan."

  Kallanta tai sannan ta tuno sanda ya fadi akan titin nan, aljanu? Hauka? Abinda ya fado mata arai kenan, Ummy tace "Hassan nada larura wanda mu kanmu iyayensa bamu sani ba, haka kawai tundaga mutuwar dan uwansa da dan kanin mijina Hassan ya koma haka, duk yanda mukaso musan matsalarsa mun kasa, munje asibitoci kala kala sai dai maganar daya ce, ba abinda ke damun kwakwalwarsa sai dai bamu san meke damunsa ba."

Ummy ta juyo tare da goge kwallarta tace "Jalila ki yafe mana wannan laifin da muka aikata."

  Ganin Matar da ta sani a rana d'aya tana share kwalla sai taji gaba daya hankalinta ya tashi, batasan sanda tace "Bakomai na yafe muku."

Ummy ta kalleta cikin jin dade sannan ta kara riko hannunta tace " jikina yana bani ke alhere ce a gareshi da mu kanmu, daga sanda naganki hankalina ya kwanta dake, Jalila ki daukeni a matsayin mahaifiyarki, ni kuma zan yi miki duk wani abu da uwa takema danta."

Jalila tai murmushin jin dadi, dan haka kawai taji tanasan matar, dazu kukanta kadai yasa hankalinta tashi.

Ummy ta kalleta tace "wa aka kwantar a asibiti?"

Jalila ta kalleta idanunta suka ciciko, a hankali hawaye ya fara zubo mata.
Ummy hankalinta ya tashi tace "ya isa haka nan Jalila, bazan kara tambayarki ba harsai sanda hankalinki ya kwanta da ki sanarmin."

Jalila share hawaye kawai take, Ummy ta mike tace "tashi kije dakin nasan abu zakiyi na tsayar dake."
Jalila ta dago sannan ta mike, sama ta fara hawa, Ummy taji tace "dakin kusa da wanda aka kaiki jiya zaki shiga.
Jalila tace to, nan ta tura kofar dakin, sanyin Ac dake kadawa a dakin da wani sansanyan turare ne suka bugeta, idanu ta lumshe a hankali sannan ta kalli dakin, yanayin kan madubin kadai yasa tasan dakin hade yake da namiji.
Da sauri ta fito ta nufi dakin data shiga jiya, jin dakin tai a kulle, komawa tai dakin ta bude wardrobe gefe daya kayanta ne kaf, dayan kuma na namiji.

Daki daya zasu zauna kenan?

  Inners dinta ta ciro sannan ta shiga wanka, kamar ba dakin namiji ba dan komai nashi a tsars suke, haka ta fito ta saka wata doguwar riga sannan ta kwanta agefen gadon, tana tunanin rayuwa, tabbas itakam zata fadama Ummy matsalar Goggo dan bazata iya kwana biyu ba bata ganta ba.
Ta tabbatar Ummy zata fahimceta.

  Batasan bacci yayi gaba da ita ba, dan dama in tana zazzabi ta dinga bacci kenan, tsabar bacci ya mata dadi har da kara kwanciya, sanyin Ac din yasa ta jawo bargo.
Bacci take hankalinta a kwance.

  Kofar dakin ya turo, gaba daya shi gidan ma baya san zama, tunda ya fita yana cikin mota a zaune.
Sai yanzu daya gangaro gida, ganin magrib tayi, ya tabbatar Ummy yanzu zata shiga nemansa.

Cak ya tsaya a kofar dakin yana kallan ikon Allah, tunda yake yau ne rana ta farko da wani ya taba bajemai akan gado haka, harda jan bargo?

Ransa ne ya turnuko dan shi sam bayasan yaga wani a dakinsa, kusa da ita ya matso ya sa hannu ya fizgi bargon da karfi.

  Jan bargon da yai yasa ya hado da kasan doguwar rigarta yadan kwaye ta.
Da sauri ta bude idanu, kallansa tai a zabure, shima idanunsa ne suka kai kasanta daya kwaye, da sauri ya dauke kansa, ita kuma ta mike zaune da sauri tana gyara rigarta tace "Malam me kenan?"

Kallanta yai yace "Malam? Malam me kenan?"
Bakinta na rawa tace " Umm."
Ya hade rai yace "will you get up?"
Kallansa tai cikin rashin fahimta, yace " bakyajin yaren?"
Nan ma tai shiru, yace "banasan magana please tashimin daga kan gado."

Jalila ta kalleshi tace " dan zaka ce in tashi sai ka min haka?"

Wani kallo ya buga mata wanda batasan sanda ta mike ba, yace "a haka kika gadon?"

A ranta tace "ahh yau ga wani irin mutum."

Kallanta yai sannan ya kalli gadan, Jalila ta fara gyara gadan da karfi kana gani kasan na mugunta takeyi, tana yi tana dan murguda baki.
Kallanta yai a ransa yace wannan kana gani kasan batada kunya wannan bakin sai ba fasashi wata rana.

Jalila kuwa tana gyara wa tana cewa yo matsala ma ai basai an tambaya ba, mutum ba mutunci ai babbar matsalace.

#OneLuv💕

🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

(_D home of expert and perfect writer's_💡)

*26*

Toilet ya shiga ya d'auro alwala, yana fitowa ya kalleta, tana tsaye tsuru dan itama jiransa take ya fito, ga fitsari ya matseta.
Tana gani ya fito ta shiga ciki, kallan kofar data rufo yai ransa ya kara baci dan bakin cikinsa ya ganta a dakin nan.
Tada sallah yai, bayan ya idar ya zauna ya fara addu'oinsa, itakam daga gefe ta dan rakube tai sallah, tana idarsa ta zauna agun tana yima Goggonta addu'a.

Ameera ce ta buga musu kofa tana cewa "Yaya Jalila ki fito kici abinci"

Juyowa yai ya kalleta ransa a bace, mikewa tai da sauri zata bude kofar.
Batasan ya mike ba sai gani tai ya rigata sa hannu ajikin kofar.
Kallansa tai yanda taga idanunsa sunyi yasa taji tsoro.
Da karfi ya bude kofar sannan ya kalli Ameera.

A tsorace Ameera tace "Yaya kana nan?"

Kallanta ya sakeyi,ba sai ya mata magana ba tasan me yake nufi.
Da sauri tace "Yahkuri yaya bansan kana nan ba."

Jalila ya kalla, itama kallansa tai sannan ta kalli Ameera, bata fahimceshi ba sai cewa tai "me zanyi?"
Chapter 26 · 0% Book details