← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 53

Sashe 33

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

  Kallansa tai bayan ta fito cikin zumudi tace "Yaya na fito ka shiga wanka."
Yace "in nayi wanka me zan miki? Ko dama ke kike sani yin wanka?"

A ranta tace "hmm wannan mutumin?"
Amma a fili tace " a'a gani nai zamu fita."
Yace "zuwa inafa?" Ya fada yana gyara gadan daya kwanta dan shi kam badai gyara muhalinsa ba."
Jalila da sauri ta fara tayashi ta dayan bangaren tana cewa "jiya fa kace yau zamu."
Yace "yau din ta kare ne?"

Baki tadan turo mai mutumin nan yake da ita?
Hassan ya matso kusa da inda take a tsaye, hannu yasa ta bayanta ya dauko wani littafi sannan ya koma kan kujera ya zauna.
Jalila ta tsaka sakato tana kallan ikon Allah, amma mutumin nan....
Cikin takaici ta fita waje tana wata irin tafiya, bugo kofar tai sannan tabi kofar da kallo, dama ita tasan ba lalai ya taimaketa ba.
Da alama Uncle kawai zata fadama, haka ta zauna a kujera ta kuna Tv.
Shikuwa tunda ta fara cika tana batsewa yake kallanta ta gefe ido, da ta fara wata irin tafiya kuwa tsayawa yai yana kallanta harya banko kofar.
Mai zan gani? Hassan naga ya murmusa sannan ya girgiza kai.
Shikansa bai fahimci murmushin yai ba saboda rabansa dayai murmushi ko dariya har ya manta.
Amma tabas yau kam da saninsa ya kular da ita, dan ya fahimci wani sabon zumudi da takeyi.

Ajiye littafin yai sannan ya mike ya shiga toilet, yana fitowa ya dauko jeans da shirt yana shirin sawa, baisan msi ya tuna ba sai naga ya cire ya dauko farin yadi mai shara shara ya sa.
Bayasa hula dan haka ko dubata ma baiyi ba.
Zama yai ya bude tiren data ajiye.
Kallan plate biyun dake gun yai, kenan bataci abinci ba?

A falo taji yunwa ta kamata ta turo kofar daki fuskarta a hade, kallanta yai sannan ya dauke kai kamar bai ganta ba.
Ganinsa a gaban abinci yasa ta tsaya turus tana kallansa.

Kallanta yai yace " Kin fasa zuwa ne?"
Da sauri tace "zamu?"
Kallan abinci yai sannan ya kalleta, da sauri ta matso tana dariya, duk yanda taso ta boye farin cikinta ta kasa.

Shikam ya hade rai yana kallan ikon Allah, shi ta fara zubama sannan ta zuba nata.
Dan kadan taci ta fara neman mikewa, kallansa tai taga shima kallanta yai fuskarsa a daure.
Da sauri ta koma ta zauna tana kara cin abincin.

Yana mikewa kuwa itama ta mike, gani tai ya koma ya zauna akan gado.
Tace "Yaya na......"
Kasa karasawa tai sai ta wayance tace "Yaya naga bakasha tea din ba, ko na kawoma ruwa?"

Yace "later."
Juyawa tai ta fita, kallanta yai sannan ya mike ya dau key din mota ya dau wayarsa.

  Sannan ya sauka, bata falon sama shiyasa ya wuce kasa.

A kitchen ya hangota, ita da Ummy da alama wanke wanke suke.
Tsayawa yai yana kallansu, bai san me take cewa ba yaga Ummy na dariya.

Matsowa yai yana san yi mata magana, kuma bazai iya ba.
Juyawa kawai yai yana neman komawa sama, Sagir yace "Yaya kaine a falo?"

Hassan ya kalleshi sannan ya juya zai hau sama, Jalila najin ance Yaya ta juyo da sauri tana hangoshi ta tsame hannunta a ruwan dauraya tai gunsa da sauri.
Ko bi takan Sagir batai ba tasha gaban Hassan tace "Yaya ina zaka?"
Kallanta yai yace " fita ma inzanyi sai an tambayen?"

Tace "au yahkuri, in fito?"

Juyawa yai ya fita waje bai bata amsa ba, da  gudu ta haura sama ta dauko hijabinta, da wayarta.
  Da gudu ta fito ta sauko, Sagir kallanta kawai yake, Ummy da mamaki ya sa ta tsaya tana kallansu, Jalila ta karaso gunta tace "Ummy zamu fita, na tafi karya fasa."

  Ummy mamaki yasa ta kasa ma magana, yau Hassan ne zai kai wani unguwa?
Kallan Sagir tai da sauri wanda yai shiru yana kallan Jalila wace yaga ko kallansa batai ba tana zumudin fita da miji.

  Ummy tace "Sagir ka ga Hassan?"
Kallanta yai ya kakaro murmushi yace "naganshi Ummy, ni kaina mamaki nake."
Ummy ta fadada murmushinta tace " Sagir da alama Hassan ya fara canzawa, ko?"
Sagir ya jinjina kai yace "sosai Ummy."

Ummy ta juya cikin tsananin farin ciki.

Jalila kam da sauri ta bude gaban mota inda yake ta shiga.

Tana hakki, Hassan ya kalleta yace "meye hakan? Gudu kikai?"

Tace " tsoro nake karkai zuciya."

Hassan ya tada mota ya ja, suna tafi motar shiru ba komai sai sanyin AC din da ya kunna, ita ta dinga nuna mai hanya da suka shiga unguwar.

Suna zuwa kofar gidan tace "nan ne, amma yaya kana tunanin zasu nuna mana inda Goggon take?"

Bai kula taba yai  horn, mai gadin gidan ya fito da sauri ya leka ganin Jalila yasa ya koma ya bude.

  Shiga sukai yai parking, sannan ya kashe motar ya kalleta yace "ki shiga."
Juyowa tai ta kalleshi tace "in shiga?"
Yace "ko ni zan shiga?"
Tace "a'a ban dai fahimceka bane, ba tare zamu ba?"
Yace " a yaushe mukai hakan dake?"

Jalila ta tsaya tana kallanshi tace "Yaya kaifa kace zaka taimaken."
Yace "a yaushe kenan?"
Jalila yanayin fuskarta ya canza tace "Amma....."
Yace " ki shiga ku gaisa, in kuka bakida niyya mu juya."

Kallansa tai tama rasa me zatace " Hassan ya dau wayarsa yana duba abu."
Idanunta ne suka ciciko ta bude motar ta fita, ta nufi gidan zuciyarta a dagule.
Amma mutumin nan anyi mara mutunci.

Shikuwa yana kallanta har ta shiga.

Dady na zaune yana hada wasu takardu yana waya ta tura kofar tare da yin sallama.

Dady ya juyo jin muryar Jalila.
A daidai lokacin Mumy ta fito ita da Yasmeen, Mumy na rike da plate dake dauke da kayan marmari.
Da yake yau asabar ba aiki.

Kallanta sukai sai suka zubo mata ido, Yasmeen ta rugo da gudu ta rungumeta tana mata oyoyo.
Jalila ta kalleta tace "My Yasmeen ya makaranta?"

Yasmeen ta rike hannunta tana zuba mata shagwaba, nan Jalila ta dauketa.

Dady ya kalleta yace "Jalila! Kece?"

Mumy ma tace "Jalila shigo mana."
Jalila ta shigo jiki a darare ta zauna a kasa, tana gaidasu.

Mumy ta amsa sannan tace "banyi tunanin ganinki ba daga aure."
Jalila ta kalleta sannan tai kasa dakai ita duk ta rasama me tazo yi.

Knocking din kofa sukaji, Dady ya kalleta yace " bake kadai bace?"
Kallan kofar tai da sauri tana cewa "eh tare muke."

Mamaki tai dataga Dady ya mike da sauri yana kallan Mumy yace "yi maza kinsanar ma Inna."
Mumy tai sama da gudu.

Jalila ta tsaya kallan ikon Allah, Dady ya bude mai kofa.
Hassan ya kalleshi sannan yace "sannu."
Dady ya washe baki yace "shigo mana."
Hassan ya shigo tare da zama akan kujera.

Dady ha zauna a dayar kujerar yana cewa "ai bamu san tare kuke ba, ke kam Jalila bakyaji akan me da kika shigo baki sanar mana ba?"
Hassan ya kalleshi sannan ya kalli sama wanda yaji alamar saukowar mutane.

Matan biyu daya gani a gidan su yau ma su ya gani.
Kallan Dady yai yace " tanata damuwa akan rashin lafiyar mahaifiyarta shiyasa nace bari muzu."

Turus Inna da Mumy sukai akan kasan beni, Jalila ma da sauri ta kalleshi, Dady yace "naam? Me kake nufi?"

Hassan ya zubawa su Inna ido yace " Jalila a ina Goggon take? Dan nasan bata cikin su."
Ya fada yana nuna su Mumy da kai.

Inna wace ranta yakai koluwa gun baci, ta kalli Jalila tana jiran me zatace, Jalila kuwa tayi mamakin kalamansa dan bata taba tunanin haka zai bulo musu gatse gatse ba.

Hassan ya kallesu yace " Ina wuni?"

Inna bakinta na dan rawa tace "Lafiya."
Hassan ya mike ya kalli Dady yace " dan Allah a ina take? Ina sauri ne."

Dady baki na rawa ya kalli Mumy da Inna yace "tana primer."
Yace "wani dakin?"
Dady ya kalli Mumy yace "wani dakin ne ma?"
Tace "hmm...."
Hassan ya kalli Jalila yace "muje ko?."

Jalila tai sakato tana kallan ikon Allah.
Ganin yana neman fita yasa ta mike da sauri kar a rufeta da duka tai waje.

Suna shiga mota ya ja yai gaba.

Jalila ta zubamai ido tana nazari akansa, can tasa wata dariya tace "Yaya kaga idon Inna kuwa?"
Kallanta yai yace "wacee hakan?"

Jalila tace "kaka ta? Ahh ba kakata ba kakar su Yasmeen."

Hassan bai kula ta ba ya juya yana tuki, ita kuwa in ta tuno yanda sukai sai ta kara sa dariya.
A haka har suka isa, suna shiga ya nemi a duba musu sunan Goggo.

Nan wata nurse ta wuce dan nuna musu dakin, Hassan ya kalleta yace "ina mota."
Da sauri ta riko rigarsa ta kasa tace "mota?"
Kallanta yai, tace "dan Allah kuje ka gaidata. Batasan anmin aure ba fa?" Ta fada tare da canza fuska xuwa tausayi......

#Oneluv💕

🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*

     *HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
  (_D home of expert and perfect writer's_💡)

*33*

Hassan ya kara kallanta yace “kina nufin in shiga ciki?”
Ta daga kai, ya kara kallan asibitin, batasan nan ma dakyar ya shigo ba?
Jalila ta kalleshi tace “Yaya!”

Kallanta yai sannan ya fizge rigarsa ya juya.
Binshi tai har jikin motar ta tsaya a jikin kofar inda yake tace “Dan Allah yaya kazo muje.”
Kallanta yai yace “ wai meke damunki? Ana abu dole ne?”

Tace “i am really scared”
Kallanta ya sakeyi, tace “bansan a wani hali zan sameta ba, bansan me zance mata ba in ta tambayeni, Yaya dan Allah kazo muje.”

Oh God! Wannan wace irin yarinya ce? Yace “to in naje ta tambayeki wanene ni me zaki ce?”

Kallansa tai sannan tai shiru, yace “ki je ki fito in kuma in barki anan ne sai ki zauna sai dare.”

Jalila ta kalleshi tace “zan zauna anan din.”
Yace “ ur choice.”
Sannan ya kalleta yace” zan rufe kofa.”

Jiki a sanyaye ta matsa daga jikin motar, ya ja yai gaba, ta glass din mota ya hangota tana tsaye inda ya barta.
Chapter 33 · 0% Book details