Sashe 14
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A rayuwar Jalila indai tana gaban Goggo jinta takeyi kamar yarinyar goye, shiyasa duk wata tabata da shirme juyema Goggo takeyi, suna kwance zasuyi bacci duk ta isheta da neman sanin asalin labarinta.
Goggo tace "to ya isheni haka nan yanzu sai ki kwanta ko kin manta gobe kunada taro a makaranta?"
Jalila ta juyo inda Goggo take tace "Goggo kinsan yanzu addu'ar da nake yi yanzu?"
Goggo tace "ya wuce shirmen soyayyarki?"
Jalila ta girgiza kai tace "A'a addu'a nake Allah ya kara miki lafiya da tsawan kwana muyi rayuwa tare, banaji zan iya kwana d'aya a duniya in bakyanan."
Goggo ta hade rai tace "Jalila nikam sai yaushe ne zaki girma? Na dauka in mutum ya tashi cikin wahala yana hankali amma wani sa'in in kikai wani abun sai inta mamakin ki."
Jalila tai murmushi tace "Goggo a koda yaushe in ina tare dake ji na nake kamar yarinyar goye, kece kawata, mahaifiyata, mahaifina, sannan kuma yar uwata, Goggo yanda bana boye miki komai dan Allah kema kidinga sanar dani komai na rayuwarki."
Kallan tausayawa ta mata dan tabbas tana ji a jikinta wani babban ciwo na cinta domin wasu sababbin canjin da take fuskata a jikinta tasan da matsala,, sai dai fatan Allah yasa abin ba babba bane.
Jalila tace "Goggo!"
Goggo tace "shikenan Jalila na miki alkawari a daren gobe zan sanar dake komai na kafin a haifeki, yanzu dai ki kwanta."
Tace "yauwa Goggona, saida safe."
Goggo ta daga kai, sannan ta zuba mata ido, kankace me Jalila ta tafi bacci.
Goggo a dade tana kallanta har batasan sanda hawaye suka gangaro mata ba, hannu tasa ta share sannan ta gyara mata bargo ta juya ta fara bacci.
Da safe bayan ta gama gyara bangarensu ta fada wanka, an dade ana saba jiki kai kace fatar tata zata canza, ta fito ta bude drawer dinta ta saka kayan makaranta sannan ta shiga duba sababbin dinkin da aka mata, nan ta zabi wani lace mai an karan kyau yasha duwatsu, ta fara kokarin sawa a jakar hannunta da aka sai mata.
Goggo ta bude labule tana kokarin shigowa, kallan Jalila tai tace "ke da zaki makaranta me zakiyi da kayan gida?"
Ta karasa shigowa da kyar ta samu ta zauna.
Jalila tai murmushi tace "Goggo yau fa ake yaye mu."
Tace "to sai akai ya?"
Jalila tace "Ana gama taran ai zamu kwabe mu shiga kayan gida ai shagali."
Goggo ta tabe baki cikin rashin gamsuwa tace " Wai yaushe aka fara haka a makarantar Gomnati ma?"
Jalila tai dariya tace " ina kike fita balle ki sani?"
Goggo tace "Hmm amma ai kyaci abinci ko?"
Jalila tace " Ni bana jin yunwa sannan za'a kawo abin saidawa a makaran........."
Kallan da Goggo ta matane yasa ta zauna da sauri tare da bude kular abincin, tea ne da bread da
farfesun naman kai."
Jalila ta dade kafin ta bude bread din, har goggo tace "menene?"
Jalila tai yake tace "rayuwa kawai nake tunani Goggo, wai yanzu mune ake bamu abinci ba tare da munyi musu aiki ba, Goggo kin manta sanda muke musu wanki? Mu musu komai na gidan?"
Goggo tace " rayuwa kenan Jalila, insha Allah wahala ta kare miki a rayuwa."
Jalila tai murmushi sannan ta fara cin abincin, bazata cemata iyaye suna zuwa ba dan ta tabbbar zataji ba dadi, gashi ita ba lafiyar kafa ba."
Tana gamaci ta fito, Sultan ta gani yana kokarin shiga mota, tace "Sultan?"
Tsayawa yai har ta iso, tace "ina zaka?" Ta dauka cemai akai ya rakata saboda gama makaranta da zasuyi.
Jitai Yace "In an kaiki makaranta ne zan wuce gidan kawu in amso sako." Sakon me?
Yace " kamar wai lefe za'a kawo."
Jalila cikin mamaki tace "lefe? Lefen wa za'a kawo?"
Yace "ina na sani?"
Ya fada tare da shiga motar.
Jalila ta shiga tana mamaki, bikin Safeena za'ai? Amma bataji labari ba, to ko amsar kayan za'ai kawai a gidan?"
Ganin batada amsa yasa ta share.
Yau yan mate dinsu Jalila ansha uban kwalliya, sai iyayi akeyi.
Haka aka fara programs kowa iyayensa da yan uwansa sai zuwa sukeyi, Jalila tana zaune dan tasan ba wanda zata gani.
Zarah ce ta tabata tace "Jalila Yaya yazo dasu Umma."
Nan sukaje suka gaishesu, Jalila tana zaune daga inda take tana hango Uncle Sagir, insuka hada ido sai suyi ma juna murmushi.
Ganin Uncle ne ma yasa ta cire komai a ranta har aka gama programs.
Nan sukaje suka canza kaya kowa yasa kayan gida suka dau kwalliya, masu waya sunata yin hotuna, Zahra ma ta zo musu da waya sai hoto ake tayi.
Wata monitor din Jss3 ce ta shigo ajin nasu, nan ta nemi inda Jalila take ta tabata.
Jalila ta kalleta tace " Hadiza ya akai?"
Mika mata wata yar karamar jaka ta kwalli tai tace "gashi inji Uncle Sagir."
Jalila ta amsa tana bude jakar.
Kwalli ta gani ta jawo,Zahrace ta matso ta fizgi kwallin tana cewa " me muka sa......"
Ganin waya yasa ta kalli Jalila tace " yeee!"
Jalila ta harareta sannan ta fizge wayar tace " muga."
Ganin Wayar ne ya sa ta kallan Zahra, hannu tasa cikin jakar ta zaro wani karamin card.
Bude shi tai taga ansa
_To u my dear!_
_Congratulation on your graduation, here is my small gift, hope you will accept it._
Zarah ce ta kara amsar wayar ta bude ta, wayace mai tsananin kyau Sumsung Note 5 ce.
Kan kice me Zarah ta fara haska Jalila wacce tai tsuru tana kallan ikon Allah.
Fitowa tai daga ajin ta shiga nemanshi, can ta hangoshi cikin mutane.
Tsayuwa tai dan bata san ya zatai ba, juyowa yai kawai sai hangota yai daga nesa.
Yaune rana ta farko da ya ganta cikin shiga haka mai kyau dauke da kwalliya, sannan wannan ne rana ta biyu daya ganta ma da kayan gida a iya zamansu, na farko sanda ya fara ganinta sai kuwa yau.
Kasa dauke ido yai daga kanta wanda har hakan yasata tsarguwa.
Juyawa tai da sauri ta shiga class din.
Zahra ta matso tana nuna mata hotunan da ta mata.
Jalila kam bata kula taba dan hankalinta nakan Uncle dake waje.
Daina hangoshi tai hakan yasa ta fito daga class din tana lekensa.
Zarah ce ta miko mata wayar da sauri tace "Zarah Yours na kiranki."
Jalila aji abin banbarakwai, kallan wayar tai a jiki an saka MINE dariya tai sannan ta kalli zahra tace ya ake daga wa?"
Mamaki ya kama Zahra sai dai kafin ta farga Jalila tana gwadawa kawai taga yaja hakan yasa Zahra tai tunanin iskanci take mata.
Jitai yace "Banga kwalliyar nan ba, tunda ba'a ganni ba sai a taimaka azo inda muke haduwa."
Murmushi tai sannan tace "to."
Kallan Zahra tai sannan tace "ina zuwa."
Nan ta fara tafiya.
Yau a kan mota ta ganshi, karasawa tai fuskarta dauke da murmushi da kuma kunya.
Tana isa ta gaisheshi, yace "Irin wannan kyau haka ai sai kisa in rasa gane hanya."
Kallansa tai tace "Uncle wannan gift din yayi yawa, bana tunanin zan iya amsa, Goggo ma fada zatamin"
Yace " to Jalila ya kikeso muyi? Kingama skul nima na gama service a ina kikeso indinga jinki? Ke ba waya ba? Sannan ko zuwa zan dinga yi kina tunanin za'a barni nazo kullum?"
Jalila tace kullum? Yace sosai in har bazaki amshi wayar ba sai dai ki amince kullum nazo muyi awa uku tare.
Da sauri ta zaro ido dan tasan wannan inaa bazai yiwu ba.
Ji tai yace "bazai yiwu ba ko? To kinga kawai ki hakura."
Jalila tace "Amma....."
Yace "mu bar maganar nan please."
Kallansa tai dan batasan me zata ce ba..........
Hira suka shiga yi ta masoya masu tashen soyayya, Kiran wayarsa da akai ne yasa ya kalli wayar mamaki yai dayaga Mine a jiki dan number Jalila ce.
Nan ya daga yana cewa wayarki na gun wa?
Tace Zahra
Zahra na dagawa tace "Uncle wai Jalila tazo anzo daukarta."
Uncle ya kalleta yace "wai anzo daukarki."
Mamaki ya kamata tace "amma nace sai bayan azahar, gabanta ne ya fadi badai wani abun bane ya samu Goggon ta?"
Kallan Uncle tai a tsorace tace "Uncle bari naje gida."
Zahra na tsaye kusa da motarsu, wayarta ta mika mata ta bata jakarta, nan Jalila ta sa a cikin jakar ta shiga ciki sukai gaba, addu'a kawai take Allah yasa ba wani abun bane ya samu Goggonta.
*£*£*********
Goggo tana zaune wajen karfe 12 Yasmeen tazo da gudu wai tazo inji Inna.
Tayi mamaki sosai dan tanaji tunda take a gidan Inna bata taba nemanta ba haka kawai.
Samun kanta tai da faduwar gaba.
Haka ta taso da kyar saboda ciwon kafa ta karasa.
Tana shiga falon taga Inna, Dady da Mumy a zaune.
Faduwar da gabanta ya shiga yi ne kawai ya sa ta shiga yin addu'a dan ta tabbatar ba lafiya ba, shiga tai a hankali.
Mumy ta mata nuni da kujerar dake gefe tace "ki zauna anan."
Goggo ta zauna sannan ta gaida Inna ta gaida Dady da Mumy.
Bayan sun amsa ne falon yai dan shiru.
Goggo tace "lafiya?"
Inna tace "Gobe za'a kawo kayan lefen Jalila."
Abin yazoma Goggo a ba zata wanda yasa tace "lefen Jalila kamar ya kenan? Dan banaji ta taba sanar dani tanada miji."
Inna tace " ba sai ta sanar dake tana da saurayi ba, dan kuwa hakkin mahaifi ne ya zaba mata mijin da yaga ya dace da ita, sannan shi Abbakar ya fitar da nasa hakkin na yi mata miji yanzu hakkin 'ya ne tabi umarnin mahaifinta."
Goggo ta kalli Dady da sauri tace " Abbakar me kenan?"
Yace "hakan da kikaji shine."
Cikin daga murya tace "da tunda aka haifeta bakasan da hakkin ta akanka ba sai yanzu? Dama wlh ni jikina yaban mutuncin da kuke mata da wani abin a kasa, ashe aurar da ita zakuyi? Mijin mahaukaci ne ko dan shaye shaye? Ko kuwa barawo ne? Ko kuma nakasasshe? Ko kuma dan fashi ne?"
Mumy tace "ya zaki fadi haka, Abbakar fa ubanta ne ta ya za........."
Goggo cikin tsawa tace "Ba dake nake ba."
Yanda tai maganar ne yasa Mumy tsorata dan bata taba ganin Goggo na fada haka ba.
Goggo tace "to ya isheni haka nan yanzu sai ki kwanta ko kin manta gobe kunada taro a makaranta?"
Jalila ta juyo inda Goggo take tace "Goggo kinsan yanzu addu'ar da nake yi yanzu?"
Goggo tace "ya wuce shirmen soyayyarki?"
Jalila ta girgiza kai tace "A'a addu'a nake Allah ya kara miki lafiya da tsawan kwana muyi rayuwa tare, banaji zan iya kwana d'aya a duniya in bakyanan."
Goggo ta hade rai tace "Jalila nikam sai yaushe ne zaki girma? Na dauka in mutum ya tashi cikin wahala yana hankali amma wani sa'in in kikai wani abun sai inta mamakin ki."
Jalila tai murmushi tace "Goggo a koda yaushe in ina tare dake ji na nake kamar yarinyar goye, kece kawata, mahaifiyata, mahaifina, sannan kuma yar uwata, Goggo yanda bana boye miki komai dan Allah kema kidinga sanar dani komai na rayuwarki."
Kallan tausayawa ta mata dan tabbas tana ji a jikinta wani babban ciwo na cinta domin wasu sababbin canjin da take fuskata a jikinta tasan da matsala,, sai dai fatan Allah yasa abin ba babba bane.
Jalila tace "Goggo!"
Goggo tace "shikenan Jalila na miki alkawari a daren gobe zan sanar dake komai na kafin a haifeki, yanzu dai ki kwanta."
Tace "yauwa Goggona, saida safe."
Goggo ta daga kai, sannan ta zuba mata ido, kankace me Jalila ta tafi bacci.
Goggo a dade tana kallanta har batasan sanda hawaye suka gangaro mata ba, hannu tasa ta share sannan ta gyara mata bargo ta juya ta fara bacci.
Da safe bayan ta gama gyara bangarensu ta fada wanka, an dade ana saba jiki kai kace fatar tata zata canza, ta fito ta bude drawer dinta ta saka kayan makaranta sannan ta shiga duba sababbin dinkin da aka mata, nan ta zabi wani lace mai an karan kyau yasha duwatsu, ta fara kokarin sawa a jakar hannunta da aka sai mata.
Goggo ta bude labule tana kokarin shigowa, kallan Jalila tai tace "ke da zaki makaranta me zakiyi da kayan gida?"
Ta karasa shigowa da kyar ta samu ta zauna.
Jalila tai murmushi tace "Goggo yau fa ake yaye mu."
Tace "to sai akai ya?"
Jalila tace "Ana gama taran ai zamu kwabe mu shiga kayan gida ai shagali."
Goggo ta tabe baki cikin rashin gamsuwa tace " Wai yaushe aka fara haka a makarantar Gomnati ma?"
Jalila tai dariya tace " ina kike fita balle ki sani?"
Goggo tace "Hmm amma ai kyaci abinci ko?"
Jalila tace " Ni bana jin yunwa sannan za'a kawo abin saidawa a makaran........."
Kallan da Goggo ta matane yasa ta zauna da sauri tare da bude kular abincin, tea ne da bread da
farfesun naman kai."
Jalila ta dade kafin ta bude bread din, har goggo tace "menene?"
Jalila tai yake tace "rayuwa kawai nake tunani Goggo, wai yanzu mune ake bamu abinci ba tare da munyi musu aiki ba, Goggo kin manta sanda muke musu wanki? Mu musu komai na gidan?"
Goggo tace " rayuwa kenan Jalila, insha Allah wahala ta kare miki a rayuwa."
Jalila tai murmushi sannan ta fara cin abincin, bazata cemata iyaye suna zuwa ba dan ta tabbbar zataji ba dadi, gashi ita ba lafiyar kafa ba."
Tana gamaci ta fito, Sultan ta gani yana kokarin shiga mota, tace "Sultan?"
Tsayawa yai har ta iso, tace "ina zaka?" Ta dauka cemai akai ya rakata saboda gama makaranta da zasuyi.
Jitai Yace "In an kaiki makaranta ne zan wuce gidan kawu in amso sako." Sakon me?
Yace " kamar wai lefe za'a kawo."
Jalila cikin mamaki tace "lefe? Lefen wa za'a kawo?"
Yace "ina na sani?"
Ya fada tare da shiga motar.
Jalila ta shiga tana mamaki, bikin Safeena za'ai? Amma bataji labari ba, to ko amsar kayan za'ai kawai a gidan?"
Ganin batada amsa yasa ta share.
Yau yan mate dinsu Jalila ansha uban kwalliya, sai iyayi akeyi.
Haka aka fara programs kowa iyayensa da yan uwansa sai zuwa sukeyi, Jalila tana zaune dan tasan ba wanda zata gani.
Zarah ce ta tabata tace "Jalila Yaya yazo dasu Umma."
Nan sukaje suka gaishesu, Jalila tana zaune daga inda take tana hango Uncle Sagir, insuka hada ido sai suyi ma juna murmushi.
Ganin Uncle ne ma yasa ta cire komai a ranta har aka gama programs.
Nan sukaje suka canza kaya kowa yasa kayan gida suka dau kwalliya, masu waya sunata yin hotuna, Zahra ma ta zo musu da waya sai hoto ake tayi.
Wata monitor din Jss3 ce ta shigo ajin nasu, nan ta nemi inda Jalila take ta tabata.
Jalila ta kalleta tace " Hadiza ya akai?"
Mika mata wata yar karamar jaka ta kwalli tai tace "gashi inji Uncle Sagir."
Jalila ta amsa tana bude jakar.
Kwalli ta gani ta jawo,Zahrace ta matso ta fizgi kwallin tana cewa " me muka sa......"
Ganin waya yasa ta kalli Jalila tace " yeee!"
Jalila ta harareta sannan ta fizge wayar tace " muga."
Ganin Wayar ne ya sa ta kallan Zahra, hannu tasa cikin jakar ta zaro wani karamin card.
Bude shi tai taga ansa
_To u my dear!_
_Congratulation on your graduation, here is my small gift, hope you will accept it._
Zarah ce ta kara amsar wayar ta bude ta, wayace mai tsananin kyau Sumsung Note 5 ce.
Kan kice me Zarah ta fara haska Jalila wacce tai tsuru tana kallan ikon Allah.
Fitowa tai daga ajin ta shiga nemanshi, can ta hangoshi cikin mutane.
Tsayuwa tai dan bata san ya zatai ba, juyowa yai kawai sai hangota yai daga nesa.
Yaune rana ta farko da ya ganta cikin shiga haka mai kyau dauke da kwalliya, sannan wannan ne rana ta biyu daya ganta ma da kayan gida a iya zamansu, na farko sanda ya fara ganinta sai kuwa yau.
Kasa dauke ido yai daga kanta wanda har hakan yasata tsarguwa.
Juyawa tai da sauri ta shiga class din.
Zahra ta matso tana nuna mata hotunan da ta mata.
Jalila kam bata kula taba dan hankalinta nakan Uncle dake waje.
Daina hangoshi tai hakan yasa ta fito daga class din tana lekensa.
Zarah ce ta miko mata wayar da sauri tace "Zarah Yours na kiranki."
Jalila aji abin banbarakwai, kallan wayar tai a jiki an saka MINE dariya tai sannan ta kalli zahra tace ya ake daga wa?"
Mamaki ya kama Zahra sai dai kafin ta farga Jalila tana gwadawa kawai taga yaja hakan yasa Zahra tai tunanin iskanci take mata.
Jitai yace "Banga kwalliyar nan ba, tunda ba'a ganni ba sai a taimaka azo inda muke haduwa."
Murmushi tai sannan tace "to."
Kallan Zahra tai sannan tace "ina zuwa."
Nan ta fara tafiya.
Yau a kan mota ta ganshi, karasawa tai fuskarta dauke da murmushi da kuma kunya.
Tana isa ta gaisheshi, yace "Irin wannan kyau haka ai sai kisa in rasa gane hanya."
Kallansa tai tace "Uncle wannan gift din yayi yawa, bana tunanin zan iya amsa, Goggo ma fada zatamin"
Yace " to Jalila ya kikeso muyi? Kingama skul nima na gama service a ina kikeso indinga jinki? Ke ba waya ba? Sannan ko zuwa zan dinga yi kina tunanin za'a barni nazo kullum?"
Jalila tace kullum? Yace sosai in har bazaki amshi wayar ba sai dai ki amince kullum nazo muyi awa uku tare.
Da sauri ta zaro ido dan tasan wannan inaa bazai yiwu ba.
Ji tai yace "bazai yiwu ba ko? To kinga kawai ki hakura."
Jalila tace "Amma....."
Yace "mu bar maganar nan please."
Kallansa tai dan batasan me zata ce ba..........
Hira suka shiga yi ta masoya masu tashen soyayya, Kiran wayarsa da akai ne yasa ya kalli wayar mamaki yai dayaga Mine a jiki dan number Jalila ce.
Nan ya daga yana cewa wayarki na gun wa?
Tace Zahra
Zahra na dagawa tace "Uncle wai Jalila tazo anzo daukarta."
Uncle ya kalleta yace "wai anzo daukarki."
Mamaki ya kamata tace "amma nace sai bayan azahar, gabanta ne ya fadi badai wani abun bane ya samu Goggon ta?"
Kallan Uncle tai a tsorace tace "Uncle bari naje gida."
Zahra na tsaye kusa da motarsu, wayarta ta mika mata ta bata jakarta, nan Jalila ta sa a cikin jakar ta shiga ciki sukai gaba, addu'a kawai take Allah yasa ba wani abun bane ya samu Goggonta.
*£*£*********
Goggo tana zaune wajen karfe 12 Yasmeen tazo da gudu wai tazo inji Inna.
Tayi mamaki sosai dan tanaji tunda take a gidan Inna bata taba nemanta ba haka kawai.
Samun kanta tai da faduwar gaba.
Haka ta taso da kyar saboda ciwon kafa ta karasa.
Tana shiga falon taga Inna, Dady da Mumy a zaune.
Faduwar da gabanta ya shiga yi ne kawai ya sa ta shiga yin addu'a dan ta tabbatar ba lafiya ba, shiga tai a hankali.
Mumy ta mata nuni da kujerar dake gefe tace "ki zauna anan."
Goggo ta zauna sannan ta gaida Inna ta gaida Dady da Mumy.
Bayan sun amsa ne falon yai dan shiru.
Goggo tace "lafiya?"
Inna tace "Gobe za'a kawo kayan lefen Jalila."
Abin yazoma Goggo a ba zata wanda yasa tace "lefen Jalila kamar ya kenan? Dan banaji ta taba sanar dani tanada miji."
Inna tace " ba sai ta sanar dake tana da saurayi ba, dan kuwa hakkin mahaifi ne ya zaba mata mijin da yaga ya dace da ita, sannan shi Abbakar ya fitar da nasa hakkin na yi mata miji yanzu hakkin 'ya ne tabi umarnin mahaifinta."
Goggo ta kalli Dady da sauri tace " Abbakar me kenan?"
Yace "hakan da kikaji shine."
Cikin daga murya tace "da tunda aka haifeta bakasan da hakkin ta akanka ba sai yanzu? Dama wlh ni jikina yaban mutuncin da kuke mata da wani abin a kasa, ashe aurar da ita zakuyi? Mijin mahaukaci ne ko dan shaye shaye? Ko kuwa barawo ne? Ko kuma nakasasshe? Ko kuma dan fashi ne?"
Mumy tace "ya zaki fadi haka, Abbakar fa ubanta ne ta ya za........."
Goggo cikin tsawa tace "Ba dake nake ba."
Yanda tai maganar ne yasa Mumy tsorata dan bata taba ganin Goggo na fada haka ba.