Sashe 11
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gabanta ya dawo yace " Me kike tunani kuma?"
Kai ta girgiza tace "ba komai."
Ya dan canza fuska yace " inata farin ciki zamu hadu yau amma ke naga kamar har yanzu hankalinki baya kaina."
Jalila ta sunkuyar da kanta kasa tace "Uncle wlh ba haka bane."
Yace " to menene?"
Murmushi ta shiga yi tana sunkuyar da kanta, yace "Murmushi?"
Tace " a'a."
Yace "ni to gaskiya a sanar dani"
Kasa ta kara yi dakai tana wasa da hannunta, yace "Ahhh na kula dai dan ina malaminki ne yasa ake kunyata haka, gaskiya zansa a canzamin gun service yanda zanzo har gida kinga lokacin sai a cire kunyar."
D'agowa tai ta kalleshi tace "a'a gaskiya."
Yace " bakyasan in canza?"
Tace "eh."
Ya da n yi kasa da murya yace " kinfisan ki dinga ganina kullum?"
Kunya ce ta kamata dan kuwa abinda take nufi kenan, bata kula ba ashe motarsu har tazo, horn taji anyi, kallan motar tai sannan ta kalleshi tace "Uncle zan tafi."
Ta fada cikin sauri tare da fara tafiya, juyowa yai yana kallanta dan kar ga farga har ta bude mota.
Safeena tunda ta hangosu a tsaye ta hade fuska, Jalila na shigowa ta kara kallan Sagir wanda har a lokacin idansa na kallan motar sai da suka wuce.
Safeena ta kalleta tace "na fada nace iskanci kike zama yi a makaranta kin nemi karyatani yanzu me zakice? Zance da mai mata?"
Jalila tace "Zance kikace ai ba a d'aki kika ganmu ba, a iya sanina kuma shine mijin auren ba ni ba."
Safeena ta kulu tai kwafa tace "wlh zaki fadama Mumy uban me kikeyi a makaranta."
Jalila ta juya kai tanama Yasmeen wasa.
Suna shiga gida da gudu Safeena ta je tana kaima Mumy gulma, Mumy ta ce "ya isheni menene damuwarki dan tayi zance a makaranta?"
Safeena tace "Mumy?"
"Banasan gulma, karki kuskura ki kara kawon gulmar Jalila ba yayarki bace?"
Mamaki ya kama Safeena, me Mumy take nufi?
Ita kuwa Jalila tana cire kaya tana leke ko za'azo a mata duka ko aci mutuncinta, sai dai har ta gama cire kaya bataga Mumy ba.
Goggo ce ta fito daga bandaki ta zauna da kyar tace "Jalila kin dawo?"
Jalila tace "na dawo kina bandaki."
"Wlh cikina ke mirdamin tun jiya, da alama yanayin cin abincin da muka samu ne yasa cikina ya hargitse."
Jalila cikin kulawa tace "Goggo in anso miki magani ne?"
Goggo tace "barshi kawai."
Hijab ta zara tadau dari biyun da Mumy tabata dazu tai waje da sauri.
Tana zuwa ta sai mata magani ta fito, a hanya taga mai d'ata shima ta siyi na hamsin, tana shiga gida Dady na shigowa.
Sai data jira yai parking ta karasa ta gaisheshi.
Leda taga ya miko mata yace "Gashi."
Kallan mamaki tamai tace "ciki za'a shiga dashi?"
Yace "a'a naki ne."
Kallan mamaki ta mai tace "nawa?"
Baice komai ba ya fito yai ciki.
Mamaki ne ya kamata ta bude ledar, doguwar rigace a ciki da mayafinta, sai kayan kwalliya da turare.
Kallan Dady ta sakeyi wanda yai nisa, mamaki ya kara kamata, me kenan?
Haka ta shiga bangarensu tana mamaki, tana shiga ta mikama Goggo magani sannan ta ce kinga.
Kayan Goggo ta amsa tace "daga ina?"
Jalila tace "Dady ne ya bani."
Shiru Goggo tai tana tunani, tabbas tafi kowa sanin halin mutumin nan, tunda aka haifi yarinyar nan ya bata dan kayan jarirai daga nan bai sake bata ko da da falan atamfa ba, sai sallah ne Mumy zata jefeta da atamfa mai arha, sai kuma wani sa'in in kayan Safeena sun tsufa sai a bata, meke faruwa?"
Yanda Jalila taga Mumy ta nustu tana tunani yasa tace " Goggo in maida?"
"Ba haka bane Jalila, kawai dai ina mamaki ne."
Jalila tace "Goggo ni kaina mamaki abinda ke faruwa nakeyi, kinga an hanani yin aikin gida, sannan jiya Mumy tace wai tabada dinkuna a dinkamin, sannan Inna ma yanzu sakemin fuska take, yanzu kuma Dady, bansan me hakan yake nufi ba"
Goggo dan kar Jalila ta damu sai tace mata "kila sun duba sunga yanda kike musu ne yasa suka sauko."
Jalila tace "ko?"
Tace "sosai ma."
Murmushi sukai Jalila ta mike ta wanko musu d'ata suka fara ci, basu gama cinyewa ba aka kawomusu abinci mai rai da lafiya.
Wannan sabbabin al'amari haka sukai ta faruwa a kwanan nan, Mumy da kanta tasa aka kwashe tsofaffin kayan Jalila aka sa mata sababbi, sannan tace ta dinga zuwa cikin gida tana kallo, sannan kafin su nemi abu an aiko musu.
Itakam Goggo haryanzu bata daina mamakin wannan al'amarin ba, itakuwa Jalila hankalinta a kwance sai soyayya mai karfi da take kara shiga tsakaninta da Sagir.
Kullum da daddare sai ta ba Goggo labarinsa.
Shikansa Sagir ji yake a yanzu babban burinsa bai wuce ya ganshi da Jalila ba.
**********
Yau Juma'a tun safe Mumy ta aika Jalila tazo, tare sukaje gun wanke kai aka wanke mata, sannan suka taho a hanya sai wani janta da hira takeyi, cikin hirar ne ta riko mata hannu tace "Jalila!"
Jalila ta maida hankalinta kan Mumy.
Mumy tace "Jalila kiyi hakuri abubuwan da muka muku a baya, bamu kyauta ba na nuna banbanci tsakaninki da Safeena da mukeyi, ke ce babba sai dai zuciya tasa mun tauye miki hakkinki, mun maidake kamar mai aikin gida."
Ta kara raunana murya tace "kiyi hakuri Jalila."
Jalila jikinta ne yai sanyi tace "ba komai Mumy sannan ni bakumin komai ba, Goggo itace za'a ba hakuri, ni dama 'yace a gunku kome kuka min dama hakkinane na 'ya inyi abinda kuka sa ni."
A ran mumy tace 'Ya?
Amma a fili tace "Nagode Jalila, sannan zan ba Goggon hakuri itama, inaso ki cigaba da nuna matsayinki na babba a gidan nan, karki nunama kowa ke din ba 'yata bace, da ke da Safeena duk daya kuke a gurina."
Jalila tace "nagode Mumy."
Haka suka isa gida cikin farin ciki.
Goggo kuwa bayan sun fita ta fito da kanta ta kwankwasa kofar falon cikin gida, Yasmeen ce ta bude kofar.
Goggo tana dan dingisa kafarta da take mata ciwo, tace "Yasmeen Dadynku na nan?"
Tace eh, sannan tai ciki da gudu tana kwallamai kira, dady ne yadan fito ba da dadewa ba.
Goggo ta kalleshi sannan ta gaisheshi.
Mamaki tai dataga ya amsa, tace magana nakesan muyi.
Yace ina jinki.
Sai datai dan shiru kafin tace "meke faruwa?"
Yace "name fa?"
Tace "na canzama Jalila da kukai kai da zuri'arka, nasanka nasan bazaka taba canzawa dan kanka ba sai dai in dakwai abinda kake nufi damu, domin kai da kanka kasanar dani hakan." Yace "ban ganeba?"
Tace "ka manta da bakinka kacemi kai a rayuwarka ba so, in har kuwa naga kanasan abu to lalai akwai abinda zai kareka ne."
Dady yace " kema kinsan wannan zancene na da, sannan me ya kawo wannan maganar da yar cikina?"
Kallan zargi tamai tace" tuni nazo na maka dan baxan taba tafema ba in har ka cutarmin da 'ya ta."
Ta juya ba tare da ta nemi amsarsa ba, ko ajikinsa ya juyawarsa ciki.
********
Yau tun safe ake hidima a cikin gida,Mumy ta aika aka kira mata Jalila, tare dukansu suka hadu a kitchen sukai ta aiki, Safeena kuwa tana gidan Kanin Inna a cikin gari, suna gamawa Mumy tace ma Jalila tace tai wanka a toilet din Safeena.
Wani had'ad'en material ta dauko mata ta saka, Jalila kam yau tayi mamakin kyan da tai, dan tayi kyau sosai, Mumy da kanta ta daura mata dankwali sannan ta sa mata turare.
Wajen azahar motar Taura tai parking a gida.
Ummy ce ta fara futowa sannan shikuma ya kashe motar ya fito.
Kallo d'aya zakama Ummy kasan macece mai class ba wani shigar karya tai ba sai dai kana ganinta kasan matar manya ce.
Taura ya matso sannan ya nuna mata hanyar.
Dady ne ya fito ya shigar dasu falon baki, sai wani washe baki yakeyi, Inna ta sauko suka gaisa, nan suka dan tattaba magana akan harkar business, Mumy ta mike ta shigo dakin Safeena inda Jalila take a zaune,tace "Jalila zo ki kai musu abinsha."
Jalila ta mike tana cewa "Mumy kunya nake."
Mumy ta yafa mata mayafi tana cewa "abokana Dadynki ne gaisawa kawai zakuyi."
Haka ta fito ta amshi tiren ta nufi falon, ta rasa me yasa gabanta ke faduwa, yaye labulen tai ta shiga da sallama.
Ummy tana shigowa ta kura mata ido, haka kawai taji yarinyar ta shiga ranta, yanayin nutsuwarta ne ya kara burgeta, Jalila ta ajiye tiren kanta na kasa dan ji take kamar kallanta akeyi.
Kanta na kasa ta gaishesu, Ummy ta fara amsawa sannan Taura ya amsa ya daura da cewa " Ya karatu?"
Tace "Alhamdulila."
Yace "ance kun kusa fara jarabawa sai a dage ko?"
Tace "insha Allah."
Ganin yanda take tsugunne a gun yasa Ummy tace "tashi kije."
Nan Jalila ta mike ta fita.
Inna ta kalli Ummy tace "kun ganta?"
Ummy tace " Mun ganta sai fatan Allah ya kaimu lokacin, sannan muna fatan bazaku mata maganar auren ba har sai ta gama karatunta kamar yanda aka tsara."
Inna tace "dama hakan shine daidai."
Ummy tai shiru kafin can tace "sai dai ni banasan auren dole, a matsayina na mace banasan tauye hakkin mace yar uwata, kar muje akwai wanda takeso."
Mumy tace "in dai wannan ne ba matsala dan Jalila ba ruwanta da kula kowa, ita kunya ma bazata barta ta kula saurayi ba."
Ummy ta jinjina kai na gamsuwa, haka suka sa hannu a takarda na yarjejeniya.......
Sannan sukai sallama.
Nace uhm hmm..........
[07/10, 21:28] +234 803 222 1758: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*NO 11*
Kai ta girgiza tace "ba komai."
Ya dan canza fuska yace " inata farin ciki zamu hadu yau amma ke naga kamar har yanzu hankalinki baya kaina."
Jalila ta sunkuyar da kanta kasa tace "Uncle wlh ba haka bane."
Yace " to menene?"
Murmushi ta shiga yi tana sunkuyar da kanta, yace "Murmushi?"
Tace " a'a."
Yace "ni to gaskiya a sanar dani"
Kasa ta kara yi dakai tana wasa da hannunta, yace "Ahhh na kula dai dan ina malaminki ne yasa ake kunyata haka, gaskiya zansa a canzamin gun service yanda zanzo har gida kinga lokacin sai a cire kunyar."
D'agowa tai ta kalleshi tace "a'a gaskiya."
Yace " bakyasan in canza?"
Tace "eh."
Ya da n yi kasa da murya yace " kinfisan ki dinga ganina kullum?"
Kunya ce ta kamata dan kuwa abinda take nufi kenan, bata kula ba ashe motarsu har tazo, horn taji anyi, kallan motar tai sannan ta kalleshi tace "Uncle zan tafi."
Ta fada cikin sauri tare da fara tafiya, juyowa yai yana kallanta dan kar ga farga har ta bude mota.
Safeena tunda ta hangosu a tsaye ta hade fuska, Jalila na shigowa ta kara kallan Sagir wanda har a lokacin idansa na kallan motar sai da suka wuce.
Safeena ta kalleta tace "na fada nace iskanci kike zama yi a makaranta kin nemi karyatani yanzu me zakice? Zance da mai mata?"
Jalila tace "Zance kikace ai ba a d'aki kika ganmu ba, a iya sanina kuma shine mijin auren ba ni ba."
Safeena ta kulu tai kwafa tace "wlh zaki fadama Mumy uban me kikeyi a makaranta."
Jalila ta juya kai tanama Yasmeen wasa.
Suna shiga gida da gudu Safeena ta je tana kaima Mumy gulma, Mumy ta ce "ya isheni menene damuwarki dan tayi zance a makaranta?"
Safeena tace "Mumy?"
"Banasan gulma, karki kuskura ki kara kawon gulmar Jalila ba yayarki bace?"
Mamaki ya kama Safeena, me Mumy take nufi?
Ita kuwa Jalila tana cire kaya tana leke ko za'azo a mata duka ko aci mutuncinta, sai dai har ta gama cire kaya bataga Mumy ba.
Goggo ce ta fito daga bandaki ta zauna da kyar tace "Jalila kin dawo?"
Jalila tace "na dawo kina bandaki."
"Wlh cikina ke mirdamin tun jiya, da alama yanayin cin abincin da muka samu ne yasa cikina ya hargitse."
Jalila cikin kulawa tace "Goggo in anso miki magani ne?"
Goggo tace "barshi kawai."
Hijab ta zara tadau dari biyun da Mumy tabata dazu tai waje da sauri.
Tana zuwa ta sai mata magani ta fito, a hanya taga mai d'ata shima ta siyi na hamsin, tana shiga gida Dady na shigowa.
Sai data jira yai parking ta karasa ta gaisheshi.
Leda taga ya miko mata yace "Gashi."
Kallan mamaki tamai tace "ciki za'a shiga dashi?"
Yace "a'a naki ne."
Kallan mamaki ta mai tace "nawa?"
Baice komai ba ya fito yai ciki.
Mamaki ne ya kamata ta bude ledar, doguwar rigace a ciki da mayafinta, sai kayan kwalliya da turare.
Kallan Dady ta sakeyi wanda yai nisa, mamaki ya kara kamata, me kenan?
Haka ta shiga bangarensu tana mamaki, tana shiga ta mikama Goggo magani sannan ta ce kinga.
Kayan Goggo ta amsa tace "daga ina?"
Jalila tace "Dady ne ya bani."
Shiru Goggo tai tana tunani, tabbas tafi kowa sanin halin mutumin nan, tunda aka haifi yarinyar nan ya bata dan kayan jarirai daga nan bai sake bata ko da da falan atamfa ba, sai sallah ne Mumy zata jefeta da atamfa mai arha, sai kuma wani sa'in in kayan Safeena sun tsufa sai a bata, meke faruwa?"
Yanda Jalila taga Mumy ta nustu tana tunani yasa tace " Goggo in maida?"
"Ba haka bane Jalila, kawai dai ina mamaki ne."
Jalila tace "Goggo ni kaina mamaki abinda ke faruwa nakeyi, kinga an hanani yin aikin gida, sannan jiya Mumy tace wai tabada dinkuna a dinkamin, sannan Inna ma yanzu sakemin fuska take, yanzu kuma Dady, bansan me hakan yake nufi ba"
Goggo dan kar Jalila ta damu sai tace mata "kila sun duba sunga yanda kike musu ne yasa suka sauko."
Jalila tace "ko?"
Tace "sosai ma."
Murmushi sukai Jalila ta mike ta wanko musu d'ata suka fara ci, basu gama cinyewa ba aka kawomusu abinci mai rai da lafiya.
Wannan sabbabin al'amari haka sukai ta faruwa a kwanan nan, Mumy da kanta tasa aka kwashe tsofaffin kayan Jalila aka sa mata sababbi, sannan tace ta dinga zuwa cikin gida tana kallo, sannan kafin su nemi abu an aiko musu.
Itakam Goggo haryanzu bata daina mamakin wannan al'amarin ba, itakuwa Jalila hankalinta a kwance sai soyayya mai karfi da take kara shiga tsakaninta da Sagir.
Kullum da daddare sai ta ba Goggo labarinsa.
Shikansa Sagir ji yake a yanzu babban burinsa bai wuce ya ganshi da Jalila ba.
**********
Yau Juma'a tun safe Mumy ta aika Jalila tazo, tare sukaje gun wanke kai aka wanke mata, sannan suka taho a hanya sai wani janta da hira takeyi, cikin hirar ne ta riko mata hannu tace "Jalila!"
Jalila ta maida hankalinta kan Mumy.
Mumy tace "Jalila kiyi hakuri abubuwan da muka muku a baya, bamu kyauta ba na nuna banbanci tsakaninki da Safeena da mukeyi, ke ce babba sai dai zuciya tasa mun tauye miki hakkinki, mun maidake kamar mai aikin gida."
Ta kara raunana murya tace "kiyi hakuri Jalila."
Jalila jikinta ne yai sanyi tace "ba komai Mumy sannan ni bakumin komai ba, Goggo itace za'a ba hakuri, ni dama 'yace a gunku kome kuka min dama hakkinane na 'ya inyi abinda kuka sa ni."
A ran mumy tace 'Ya?
Amma a fili tace "Nagode Jalila, sannan zan ba Goggon hakuri itama, inaso ki cigaba da nuna matsayinki na babba a gidan nan, karki nunama kowa ke din ba 'yata bace, da ke da Safeena duk daya kuke a gurina."
Jalila tace "nagode Mumy."
Haka suka isa gida cikin farin ciki.
Goggo kuwa bayan sun fita ta fito da kanta ta kwankwasa kofar falon cikin gida, Yasmeen ce ta bude kofar.
Goggo tana dan dingisa kafarta da take mata ciwo, tace "Yasmeen Dadynku na nan?"
Tace eh, sannan tai ciki da gudu tana kwallamai kira, dady ne yadan fito ba da dadewa ba.
Goggo ta kalleshi sannan ta gaisheshi.
Mamaki tai dataga ya amsa, tace magana nakesan muyi.
Yace ina jinki.
Sai datai dan shiru kafin tace "meke faruwa?"
Yace "name fa?"
Tace "na canzama Jalila da kukai kai da zuri'arka, nasanka nasan bazaka taba canzawa dan kanka ba sai dai in dakwai abinda kake nufi damu, domin kai da kanka kasanar dani hakan." Yace "ban ganeba?"
Tace "ka manta da bakinka kacemi kai a rayuwarka ba so, in har kuwa naga kanasan abu to lalai akwai abinda zai kareka ne."
Dady yace " kema kinsan wannan zancene na da, sannan me ya kawo wannan maganar da yar cikina?"
Kallan zargi tamai tace" tuni nazo na maka dan baxan taba tafema ba in har ka cutarmin da 'ya ta."
Ta juya ba tare da ta nemi amsarsa ba, ko ajikinsa ya juyawarsa ciki.
********
Yau tun safe ake hidima a cikin gida,Mumy ta aika aka kira mata Jalila, tare dukansu suka hadu a kitchen sukai ta aiki, Safeena kuwa tana gidan Kanin Inna a cikin gari, suna gamawa Mumy tace ma Jalila tace tai wanka a toilet din Safeena.
Wani had'ad'en material ta dauko mata ta saka, Jalila kam yau tayi mamakin kyan da tai, dan tayi kyau sosai, Mumy da kanta ta daura mata dankwali sannan ta sa mata turare.
Wajen azahar motar Taura tai parking a gida.
Ummy ce ta fara futowa sannan shikuma ya kashe motar ya fito.
Kallo d'aya zakama Ummy kasan macece mai class ba wani shigar karya tai ba sai dai kana ganinta kasan matar manya ce.
Taura ya matso sannan ya nuna mata hanyar.
Dady ne ya fito ya shigar dasu falon baki, sai wani washe baki yakeyi, Inna ta sauko suka gaisa, nan suka dan tattaba magana akan harkar business, Mumy ta mike ta shigo dakin Safeena inda Jalila take a zaune,tace "Jalila zo ki kai musu abinsha."
Jalila ta mike tana cewa "Mumy kunya nake."
Mumy ta yafa mata mayafi tana cewa "abokana Dadynki ne gaisawa kawai zakuyi."
Haka ta fito ta amshi tiren ta nufi falon, ta rasa me yasa gabanta ke faduwa, yaye labulen tai ta shiga da sallama.
Ummy tana shigowa ta kura mata ido, haka kawai taji yarinyar ta shiga ranta, yanayin nutsuwarta ne ya kara burgeta, Jalila ta ajiye tiren kanta na kasa dan ji take kamar kallanta akeyi.
Kanta na kasa ta gaishesu, Ummy ta fara amsawa sannan Taura ya amsa ya daura da cewa " Ya karatu?"
Tace "Alhamdulila."
Yace "ance kun kusa fara jarabawa sai a dage ko?"
Tace "insha Allah."
Ganin yanda take tsugunne a gun yasa Ummy tace "tashi kije."
Nan Jalila ta mike ta fita.
Inna ta kalli Ummy tace "kun ganta?"
Ummy tace " Mun ganta sai fatan Allah ya kaimu lokacin, sannan muna fatan bazaku mata maganar auren ba har sai ta gama karatunta kamar yanda aka tsara."
Inna tace "dama hakan shine daidai."
Ummy tai shiru kafin can tace "sai dai ni banasan auren dole, a matsayina na mace banasan tauye hakkin mace yar uwata, kar muje akwai wanda takeso."
Mumy tace "in dai wannan ne ba matsala dan Jalila ba ruwanta da kula kowa, ita kunya ma bazata barta ta kula saurayi ba."
Ummy ta jinjina kai na gamsuwa, haka suka sa hannu a takarda na yarjejeniya.......
Sannan sukai sallama.
Nace uhm hmm..........
[07/10, 21:28] +234 803 222 1758: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*NO 11*