Sashe 13
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abba ne ya kalli Ummy yace " ya kamata yau na sanar ma Hassan abinda ke faruwa."
Ummy tace " ni kam tsoro nake kar abin nashi ya dawo."
Abba yace " sai yaushe ne zaki bari a fadamai? Tun wancan satin kike sani nake jan lokaci ko so kike sai abin ya zo zai sani?"
Tace"shikenan ka fadamai yau."
Abba ya mike yai sama...........
#ONELUV💕
[07/10, 21:30] +234 803 222 1758: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*NO 12*
Hassan na sa kaya yaji Abba na knocking, da sauri ya karasa sa rigarsa sannan ya murda makullin ya bude dakin.
Abba ya matsawa ya shiga cikin dakin, kallan dakin Abba ya shiga yi yana jinjina kai, gashi dau duk lalurar dake damun Hassan amma bazaka taba ganin dakinsa da datti ba, yadan murmusa dan tabbas bai manta lokacin yana yaro ba kafin abin nan ya sameshi Hassan mutum ne mai tsafta da tsantsani, sai dai dakin bai musu karami ba? Ko sagir zai maida kasa? Dan dama saboda Hassan ne ya dawo nan kusa da dakinsa.
Ganin Abba na ta dubs dube yasa hassan ya koma kan sofa ya zauna.
Abba ya kalleshi sannan ya koma kusa dashi shima ya zauna.,
Matsawa kadan Hassan yai dan Abba ya zauna daf dashi.
Abba yai murmushi yace " Hassan yada matsawa?"
Bai tanka ba dan dama Abban yasan ba tankawar zaiyi ba.
Sunyi shiru sai karar fanka dake kadawa a cikin dakin, sai sanyin A.C, Abba ya rasa ta ina zai fara, can ya daure ya maida hankalinsa kan Hassan yace "Hassan!"
Kallansa yadanyi baice komai ba.
Sai daya dan kara yin shiru kafin yace "Hassan ke kake tunani game da aure?"
"Aure? Aure kamar ya?"
Abba yace "baka tunanin aure?"
Cikin rashin fahimta yace "ban fahimci aure ga mara lafiya?"
Abba ya danyi shiru kafin yace " Hassan mubar zancen lafiya da rashinsa, kafi kowa sanin halin da mahaifiyarka take ciki a kanka, ka kuma san yanda tasha wahala akan rashin dan uwan............"
Kallan sa Hassan yai idanunsa har sun kada, bakinsa ne ya fara rawa, hannunsa ya sa a wuyansa yana dan kakari, cikin lokaci kankani Hassan ya rikede, hankalin Abba ya tashi sosai rungumeshi kawai yai dan ya rasa ma mai zai mai.
Da kyar numfashinsa ya daidaita sai dai zufa da ta keto masa, Abba jikinsa ya kara yin sanyi tsananin tausayi dan nasa ya kara kamashi.
Ya dade sosai kafin ya dawo daidai, Abba ya mike zai fita, Har yakai kofa Hassan yace "Wani abu ya samu Ummy ne?"
Abba ya juyo daga inda yake a tsaye cikin raraunar murya yace " Hassan in har ka damu da halin da muke ciki ka amince ka auri yarinyar da mukesanka da ita."
Mamaki me ya kara kamashi yace" tambayar abinda ya samu Ummy......."
Yanzu Abba ya canza muryarsa daga alamar tausasawa zuwa dan bacin rai, yace " akwai wani abu dake damunta ne a duniya daya wuce matsalar da kake ciki? In har kanasan hankalinta da nawa ya kwanta ka yarda da auren da muke kokarin yi maka."
Hassan shima cikin dan zafi abinda rabon da yai magana mai tsayi haka harya manta yace " Taya zaku nemi min aure bayan kunsan halin da nake ciki? Sannan ni a rayuwata kunfi kowa sanin banasan zama inba ni kadai ba, ya zakuyi kuyi tunanin hadani da wata? Bayan kunsan daga ita har ni hakkin mu zaku shiga?"
Abba ya dan matso yace "wannan halin da kake ciki shine yasa muke tunanin ma auren kota wani hali, halin zama kai kadai, halin kin fadar in baka da lafiya, halin nunkufarci da rashin fadar matsalar ka, halin kin yima kowa magana, halin rashin kula da kanka, wannan kadan ne daga cikin dalilan dayasa mukesan ma aure."
Hassan har zaiyi magana yaji kansa yayi gingirin gim dan gaba daya dama baya iya magana mai tsayi, mikewa yai ya shige cikin toilet ya rufo kofar.
Abba ya juya ya fita, Ummy na tsaye a falo a kasa sai zagaye takeyi tana ganinsa ta matso tace ya kukai?
Yace "kema kinsan bazai yarda ba daga bugu daya ba."
Tace haka ne, yace "ke zaki mai magana gobe, dan inyaga kin damu kema kinsan zai yarda."
Tace "amfani dani da tsauyi da kaunar da yakemin zamuyi?"
Abba yace "ba haka nake nufina, hakan dai shi kadai ne haya."
Shiru tai batace komai ba.
Jalila kuwa tana zaune kusa da goggo suna dan cin abinci duk ta dameta da labarin film din India data kalla mai suna Vivah tana ta fada mata yanda saurayin ciki da budurwar ke san juna can tace "Goggo kinsan abin mamaki? Matarfa ranar auransu ta kone a jikinta amma saurayin nan dan tsabar san da yake mata ya nuna shi wannan ba komai bane, Goggo a asibitin fa ya aureta......"
Goggo tace " nikan Jalila sai yaushe ne zaki kyalemu muci abinci shiru? Bafa asan mutum na cin abinci na magana, sannan ni na rasa me yasa baki da aiki sai zancen soyayya, wani irin so kikema Sagir din nan dayasa kika koma haka?"
Jalila tai dariya tace "Goggo karki damu yanzu tunda muka gama makaranta zaki ganshi tunda kinga gobe za'ai taron yaye mu, kinga kuwa kila ma jibi ki ganshi dan bazai iya dadewa bai ganni ba."
Goggo ta girgiza kai cikin mamaki tace "yaran zamani wato ba kunya, sannan ya san gidan nan ne?"
Tace "gobe zan kwatantamai."
Goggo ta tabe baki tace " da alama dai kinfi sanshi ma."
Jalila tau dariya tace " tab Goggo ai ni bansan wayafi san wani a tsakanin mu ba."
Ya isheni haka nan.
Ta fada tare da tsame hannunta dan ta rasa me yasa takejin kirjinta na mata nauyi sosai sannan sai tafi kanta na sarawa.
Jalila tace " Goggo ki bari kawai na kusa daukeki mu koma gidan aurena."
Harararta Goggo tai tace " to sannu, nidai na fada miki ki kiyayi kanki karkije ba shine mijinki ba."
Jalila tai dariya tace "tab lalai Goggo kina tunanin zan kara san wani bayan Uncle? Ai nni har mafarki nayi na auranmu."
Goggo tace "to uwar surutu ya isheni haka nan, ba wanda yasan mijinki a duniya sai Allah sai dai a koda yaushe ina miki fatan miji na gari wanda zai soki kamar ransa ya kuma kula dake kulawar da baki samu ba a rayuwarki."
Jalila batace komai ba sai cigaba da cin abincinta datai tana murmushi dan itakam tasan mai so da kula da ita ba kowa bane sai Uncle dinta.
********
Abba ne ya kira Sagir ya tambayeshi labarin jarabawa dan shi ba sanin abinda ake ciki yai ba, nan Sagir ya sanar mai ai an gama Neco.
Yana kashe wa ya kira Inna, bayan sun gaisa ne yace mata "Inna yara sun gama jarabawa ko?"
Tace "eh sun kammala nima dama ina jiran kiranka."
Abba yace " sai mu hanzarta ko?"
Tace "ba laifi ai ku muke jira."
Yace " To Alhamdulila insha Allah jibi sai mata su kawo lefe."
Tace "hakan yayi , Allah ya kaimu."
Nan sukai sallama, kallan Mumy tai tace " yaushe kike tunanin ya kamata asanar mata?"
Mumy tace " duk sanda ya dace kinsan bata isa bijirema maganar mu ba tunda tasan Uwarta a karkashinmu take, sannan in muka mata barazana da rayuwar ta ba shiri zata aminta da duk abinda muka gindaya mata."
Inna ta jinjina kai tace " hakan yayi, yanzu mu bari sai jibinbin ankawo lefe dan na tabbatar bazai wuce sati biyu ba bikin dan da alama Taura ya kosa."
Mumy tace "mu ko yau yake so menene damuwar mu? Shiyasa ma nace Safeena ta cigaba da zama a gidan kawu daga nan ta wuce Egypt hankali a kwance."
Inna tace " da nace kibi mijinki Abuja yau kin binsa kikai ko?"
Tace "Inna dan Allah ki kyale Abbakar, sai yaushe ne zaki barshi yai aikinsa cikin nutsuwa?"
Inna ta girgiza kai tace "haryanzu baki da hankali, ke wai a naki haukar har yanzu kina tunani tsabar so ne yasa yake kula dake haka? Yake kuma wulakanta matarcan?"
Mumy tace "Hajiya."
Inna tai tsaki tace "Ke kika sani, ni dai company din ku bazan taba yarda na barmai gaba daya ba dan kina kallan idanunsa da yanda yake aiki zakisan akwai tsantsar greediness."
Mumy ta mike tace " Zan sauka."
Inna ta kalleta ta girgiza kai, tace ba da dan ina nuna mai matsayinsa ba kina tunanin zai ci. A da darajaki ne?"
Mumy tai shiru, Inna tace "jeki ke kika sani."
Mumy ta sauko ranta ba dadi.
*******
Ummy ce ta turo kofarsa dan tajita ba a kulle ba, yana zaune a kasa yayi shiru sai ma ka rasa me yakeyi shi kadai kullum a zaune, ta shiga ta ajiye tiren abincin sannan ta zauna gefensa kadan tace "tunani kake?"
Kallanta yai bai ce komai ba, tace "Dazu Abbanka yama magana ko?"
Yanzun ma baice komai ba, tace "Hassan mu iyayenka ne wandanda duk duniya duk wani mai sanka sai dai ya biyo bayanmu, ka fi kowa sanin bazamu zabama abinda zai cutar dakai ba, bazan kuma nemi takura maka ba, sai dai abu daya zan fadama wannan auran ni na fara amincewa akai sannan shine babban burina wanda nakesan ka taimaka ka cikamin shi."
Ta danyi shiru kafin ta mike tai waje.
Da kallo yabi bayanta sannan ya runtse idanunsa, Ummy ya takeso yai?
#ONELUV💕
[07/10, 22:19] +234 803 222 1758: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*Sisters Always Ask Questions, Borrow Clothes, Tell You When Your Hair Doesn't Look Good, Always Fight but Never Drawn Apart, Love You Always, Encorage You When You Are Dawn...*
_A Small Quote For My Sister Love You Always Ameenah😍_
*NO 13*
Ummy tace " ni kam tsoro nake kar abin nashi ya dawo."
Abba yace " sai yaushe ne zaki bari a fadamai? Tun wancan satin kike sani nake jan lokaci ko so kike sai abin ya zo zai sani?"
Tace"shikenan ka fadamai yau."
Abba ya mike yai sama...........
#ONELUV💕
[07/10, 21:30] +234 803 222 1758: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*NO 12*
Hassan na sa kaya yaji Abba na knocking, da sauri ya karasa sa rigarsa sannan ya murda makullin ya bude dakin.
Abba ya matsawa ya shiga cikin dakin, kallan dakin Abba ya shiga yi yana jinjina kai, gashi dau duk lalurar dake damun Hassan amma bazaka taba ganin dakinsa da datti ba, yadan murmusa dan tabbas bai manta lokacin yana yaro ba kafin abin nan ya sameshi Hassan mutum ne mai tsafta da tsantsani, sai dai dakin bai musu karami ba? Ko sagir zai maida kasa? Dan dama saboda Hassan ne ya dawo nan kusa da dakinsa.
Ganin Abba na ta dubs dube yasa hassan ya koma kan sofa ya zauna.
Abba ya kalleshi sannan ya koma kusa dashi shima ya zauna.,
Matsawa kadan Hassan yai dan Abba ya zauna daf dashi.
Abba yai murmushi yace " Hassan yada matsawa?"
Bai tanka ba dan dama Abban yasan ba tankawar zaiyi ba.
Sunyi shiru sai karar fanka dake kadawa a cikin dakin, sai sanyin A.C, Abba ya rasa ta ina zai fara, can ya daure ya maida hankalinsa kan Hassan yace "Hassan!"
Kallansa yadanyi baice komai ba.
Sai daya dan kara yin shiru kafin yace "Hassan ke kake tunani game da aure?"
"Aure? Aure kamar ya?"
Abba yace "baka tunanin aure?"
Cikin rashin fahimta yace "ban fahimci aure ga mara lafiya?"
Abba ya danyi shiru kafin yace " Hassan mubar zancen lafiya da rashinsa, kafi kowa sanin halin da mahaifiyarka take ciki a kanka, ka kuma san yanda tasha wahala akan rashin dan uwan............"
Kallan sa Hassan yai idanunsa har sun kada, bakinsa ne ya fara rawa, hannunsa ya sa a wuyansa yana dan kakari, cikin lokaci kankani Hassan ya rikede, hankalin Abba ya tashi sosai rungumeshi kawai yai dan ya rasa ma mai zai mai.
Da kyar numfashinsa ya daidaita sai dai zufa da ta keto masa, Abba jikinsa ya kara yin sanyi tsananin tausayi dan nasa ya kara kamashi.
Ya dade sosai kafin ya dawo daidai, Abba ya mike zai fita, Har yakai kofa Hassan yace "Wani abu ya samu Ummy ne?"
Abba ya juyo daga inda yake a tsaye cikin raraunar murya yace " Hassan in har ka damu da halin da muke ciki ka amince ka auri yarinyar da mukesanka da ita."
Mamaki me ya kara kamashi yace" tambayar abinda ya samu Ummy......."
Yanzu Abba ya canza muryarsa daga alamar tausasawa zuwa dan bacin rai, yace " akwai wani abu dake damunta ne a duniya daya wuce matsalar da kake ciki? In har kanasan hankalinta da nawa ya kwanta ka yarda da auren da muke kokarin yi maka."
Hassan shima cikin dan zafi abinda rabon da yai magana mai tsayi haka harya manta yace " Taya zaku nemi min aure bayan kunsan halin da nake ciki? Sannan ni a rayuwata kunfi kowa sanin banasan zama inba ni kadai ba, ya zakuyi kuyi tunanin hadani da wata? Bayan kunsan daga ita har ni hakkin mu zaku shiga?"
Abba ya dan matso yace "wannan halin da kake ciki shine yasa muke tunanin ma auren kota wani hali, halin zama kai kadai, halin kin fadar in baka da lafiya, halin nunkufarci da rashin fadar matsalar ka, halin kin yima kowa magana, halin rashin kula da kanka, wannan kadan ne daga cikin dalilan dayasa mukesan ma aure."
Hassan har zaiyi magana yaji kansa yayi gingirin gim dan gaba daya dama baya iya magana mai tsayi, mikewa yai ya shige cikin toilet ya rufo kofar.
Abba ya juya ya fita, Ummy na tsaye a falo a kasa sai zagaye takeyi tana ganinsa ta matso tace ya kukai?
Yace "kema kinsan bazai yarda ba daga bugu daya ba."
Tace haka ne, yace "ke zaki mai magana gobe, dan inyaga kin damu kema kinsan zai yarda."
Tace "amfani dani da tsauyi da kaunar da yakemin zamuyi?"
Abba yace "ba haka nake nufina, hakan dai shi kadai ne haya."
Shiru tai batace komai ba.
Jalila kuwa tana zaune kusa da goggo suna dan cin abinci duk ta dameta da labarin film din India data kalla mai suna Vivah tana ta fada mata yanda saurayin ciki da budurwar ke san juna can tace "Goggo kinsan abin mamaki? Matarfa ranar auransu ta kone a jikinta amma saurayin nan dan tsabar san da yake mata ya nuna shi wannan ba komai bane, Goggo a asibitin fa ya aureta......"
Goggo tace " nikan Jalila sai yaushe ne zaki kyalemu muci abinci shiru? Bafa asan mutum na cin abinci na magana, sannan ni na rasa me yasa baki da aiki sai zancen soyayya, wani irin so kikema Sagir din nan dayasa kika koma haka?"
Jalila tai dariya tace "Goggo karki damu yanzu tunda muka gama makaranta zaki ganshi tunda kinga gobe za'ai taron yaye mu, kinga kuwa kila ma jibi ki ganshi dan bazai iya dadewa bai ganni ba."
Goggo ta girgiza kai cikin mamaki tace "yaran zamani wato ba kunya, sannan ya san gidan nan ne?"
Tace "gobe zan kwatantamai."
Goggo ta tabe baki tace " da alama dai kinfi sanshi ma."
Jalila tau dariya tace " tab Goggo ai ni bansan wayafi san wani a tsakanin mu ba."
Ya isheni haka nan.
Ta fada tare da tsame hannunta dan ta rasa me yasa takejin kirjinta na mata nauyi sosai sannan sai tafi kanta na sarawa.
Jalila tace " Goggo ki bari kawai na kusa daukeki mu koma gidan aurena."
Harararta Goggo tai tace " to sannu, nidai na fada miki ki kiyayi kanki karkije ba shine mijinki ba."
Jalila tai dariya tace "tab lalai Goggo kina tunanin zan kara san wani bayan Uncle? Ai nni har mafarki nayi na auranmu."
Goggo tace "to uwar surutu ya isheni haka nan, ba wanda yasan mijinki a duniya sai Allah sai dai a koda yaushe ina miki fatan miji na gari wanda zai soki kamar ransa ya kuma kula dake kulawar da baki samu ba a rayuwarki."
Jalila batace komai ba sai cigaba da cin abincinta datai tana murmushi dan itakam tasan mai so da kula da ita ba kowa bane sai Uncle dinta.
********
Abba ne ya kira Sagir ya tambayeshi labarin jarabawa dan shi ba sanin abinda ake ciki yai ba, nan Sagir ya sanar mai ai an gama Neco.
Yana kashe wa ya kira Inna, bayan sun gaisa ne yace mata "Inna yara sun gama jarabawa ko?"
Tace "eh sun kammala nima dama ina jiran kiranka."
Abba yace " sai mu hanzarta ko?"
Tace "ba laifi ai ku muke jira."
Yace " To Alhamdulila insha Allah jibi sai mata su kawo lefe."
Tace "hakan yayi , Allah ya kaimu."
Nan sukai sallama, kallan Mumy tai tace " yaushe kike tunanin ya kamata asanar mata?"
Mumy tace " duk sanda ya dace kinsan bata isa bijirema maganar mu ba tunda tasan Uwarta a karkashinmu take, sannan in muka mata barazana da rayuwar ta ba shiri zata aminta da duk abinda muka gindaya mata."
Inna ta jinjina kai tace " hakan yayi, yanzu mu bari sai jibinbin ankawo lefe dan na tabbatar bazai wuce sati biyu ba bikin dan da alama Taura ya kosa."
Mumy tace "mu ko yau yake so menene damuwar mu? Shiyasa ma nace Safeena ta cigaba da zama a gidan kawu daga nan ta wuce Egypt hankali a kwance."
Inna tace " da nace kibi mijinki Abuja yau kin binsa kikai ko?"
Tace "Inna dan Allah ki kyale Abbakar, sai yaushe ne zaki barshi yai aikinsa cikin nutsuwa?"
Inna ta girgiza kai tace "haryanzu baki da hankali, ke wai a naki haukar har yanzu kina tunani tsabar so ne yasa yake kula dake haka? Yake kuma wulakanta matarcan?"
Mumy tace "Hajiya."
Inna tai tsaki tace "Ke kika sani, ni dai company din ku bazan taba yarda na barmai gaba daya ba dan kina kallan idanunsa da yanda yake aiki zakisan akwai tsantsar greediness."
Mumy ta mike tace " Zan sauka."
Inna ta kalleta ta girgiza kai, tace ba da dan ina nuna mai matsayinsa ba kina tunanin zai ci. A da darajaki ne?"
Mumy tai shiru, Inna tace "jeki ke kika sani."
Mumy ta sauko ranta ba dadi.
*******
Ummy ce ta turo kofarsa dan tajita ba a kulle ba, yana zaune a kasa yayi shiru sai ma ka rasa me yakeyi shi kadai kullum a zaune, ta shiga ta ajiye tiren abincin sannan ta zauna gefensa kadan tace "tunani kake?"
Kallanta yai bai ce komai ba, tace "Dazu Abbanka yama magana ko?"
Yanzun ma baice komai ba, tace "Hassan mu iyayenka ne wandanda duk duniya duk wani mai sanka sai dai ya biyo bayanmu, ka fi kowa sanin bazamu zabama abinda zai cutar dakai ba, bazan kuma nemi takura maka ba, sai dai abu daya zan fadama wannan auran ni na fara amincewa akai sannan shine babban burina wanda nakesan ka taimaka ka cikamin shi."
Ta danyi shiru kafin ta mike tai waje.
Da kallo yabi bayanta sannan ya runtse idanunsa, Ummy ya takeso yai?
#ONELUV💕
[07/10, 22:19] +234 803 222 1758: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*Sisters Always Ask Questions, Borrow Clothes, Tell You When Your Hair Doesn't Look Good, Always Fight but Never Drawn Apart, Love You Always, Encorage You When You Are Dawn...*
_A Small Quote For My Sister Love You Always Ameenah😍_
*NO 13*