Sashe 53
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 11 min read
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔️ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*49*
Goggo tana zaune tana kara bin gidan da kallo, hawayenta yaki tsayawa, ashe alheri ne a dukulle a tattare da sharrin da aka jefesu dashi.
Ba wani katon gida bane, falo daya ne babba sai 2bedrooms a cikin falon da toilet daya.
Sai tsakar gida kato wanda za'a iya ajiye motoci kananan guda biyu.
Ameera da Lantana dake sa labule ta kalla tama rasa ta ina zata fara, ashe a rayuwa akwai rana irin wannan? Shiyasa mutane ke cewa Allah yasa muci darajar 'ya'yan mu, a da bata fahimtar abinda ake nufi da hakan amma yanzu ta gane dalilin fadan hakan, in kai a rayuwa bakai sa'ar abokin zama ko iyaye ba sai ka nemi sa'a akan 'ya'yanka.
Hawayenta ta share, ko mahaifiyarta da mahaifinta nada rai?
Haka su kai ta aiki, itama tana tayasu, sai yamma su Ummy suka dawo, sun siyo abin kitchen, tv set, toilet, abinci da sauransu, dama zuwan farko aka siyo kujeru, gado da labulaye.
Haka suka taho musu da gashashiyar hanta da juice suka ci suka sha, Ummy ta nunama Goggo kawai komai ta samu tayi. Hamdalla bawai taita kuka ba, hakan yasa ta saki jiki sukaci abinci tanata godiya.
Sai wajen Magrib suka kammala komai, Ummy tace su tafi, sai asa ranar tarewarta.
Goggo tai shiru tana tunani, Ummy ta matso tace "lafiya? Ko kina tunanin zama ne gaba daya?"
Goggo tace " indai hakan zai samu nafisan hakan, dan maganar gaskiya kunyar gidan nakeyi.
Ummy tace "shikenan ai ba wani abu bane, in har hakan yafi kwanta miki a rai, sai dai kamar ba'a gama jan wutar gidan ba, sannan bamu siyo generator ba."
Goggo da sauri tace "hakan ma ya isa, ba sai anja wutar ba dan acan gidan ma bamu samu wannan darajar ba ni har na rasa ta inda zan soma yi muku godiya."
Ummy tace "dan Allah ki bari, yanzu bari mu barku anan, sai nasa yanzu Sageer ya samo katuwar fitila kafin a gyara wutar gidan, kayanki kuma gobe in Jalila zata zo sai na bada a kawo miki."
Goggo ta kamo hannun Ummy cikin wani irin yanayi na farinciki tace " nagode nagode, sai dai dan Allah ina da alfarma daya dazan nema."
Ummu tace "menene?"
Goggo tace "Jalila tana bala'in san makarantar addini ta islamiyya, bansani ba ko da yanda zakuyi ku taimaka mata."
Ummy tace "basu sata a makaranta ba?"
Tace "basu sata ba, karatun da nake dashi kadan shi na koya mata."
Ummy tai shiru tana tunanin wannan muguntar kafin tace "shikenan zan sanar ma mijinta, hafizi ne na karatu dan da wuri ya sauke alqur'ani zan ji shawarar da zai yanke."
Goggo tace "nagode sosai."
Haka suka fito sukabar Goggo da Lantana a gidan, sai da suka sai katuwar fitila suka kai musu sannan suka fito.
Ummy a hanya ta kalli Sageer tace "Sageer akwai iyayenda in basuyi wasa ba alhakin 'ya'yansu shine dalilin da zaisa su shiga wuta."
Sageer yace "Ummy nikam haryanzu kwakwalwata na mamakin irin wannan mahaifin, wanda san kansa yamai yawa da har baya damuwa da halin da 'ya'yansa suke ciki."
Ameera ta kalli Ummy tace "Ummy nikam dan Allah kumin bayani, wai ya akai Goggo ta zama mahaifiyar Jalila, Mumy fa? Nifa gaba daya na rasa meke faruwa tun jiya nakesan yin tambaya."
Ummy tasa yatsa ta ta tura goshita tace "gulmar me kike sanji? Magana daya dai wannan ce mahaifiyarta me kike nemanji bayan wannan?"
Sageer ya sa dariya yace "Ummy in Ameera batai gulma ba ai ba Ameeran bace."Cikin shagwaba tace "Yaya Sageer haka zakace? Harda wani in banyi gulma ba?"
Ya kara sa dariya yace "To yahkuri ba gulma ba."
Ummy ta kalleta tace "ba wani tayi hakuri, ai dama uwar gulma ce da san jin komai."
Ameera ta kara shagwabewa tace "Ummy Allah ni abubuwan da nakeso in tambaya dayawa fa amma tun yanzu kunsa na kasa."
Ummy tace "sai ki hadiye gulmarki inkin samu Abbanki sai ki tambayeshi."
Tace "shikenan ai nasan Abbana bazai min haka ba..."
Haka sukai ta zolayarta suna dariya cikin farinciki har suka isa gida.
********
A can gida kuwa Hassan tunda ya shiga daki ya zauna a bakin gado yai shiru yana tunani, tabbas gaba daya rayuwarsa ta canza a 'yan kwanakin nan, gaba daya yarinyar nan taki barin zuciyarsa.
Abu daya ne ya fara zuwa♀️😘😏😘🤺😘🤺😛😘😘 mai badai santa kake ba?
Da sauri ya girgiza kai yace "so? Ni? Yarinyar nan?"
Kai ya sake girgizawa alamar ba haka ba yace "tausayine."
Tausayi akan me? Ka tabbatar shi kadai ne? Damuwar da kakeyi fa in abu ya sameta?
Tambayar dake tamai yawo a zuciya kenan, shiyasa ma gaba daya daga ta shigo sai yai gamar yana bacci, ko ya dau littafi wai a dole karatu hakeyi ko ya dau wayarsa....
Ita kuwa daga baya ta sauka falon kasa ta zauna.
Bayan tayi sallar isha'i ne Abba ya dawo, ta gaisheshi ya amsa fuska a sake bai dade da dawowa ba su Ummy suka dawo.
Tanajin dawowarsu ta tashi da sauri tazo taryarsu.
Ummy ta kalleta cikin kulawa tace "Jalila jikin ne?"
Tace "na warke Ummy gashi banyi abinci ba."
Tace "nina hana kiyi, bakida lafiya wake ta abinci?"
Sunkuyar da kanta tai, Ummy ta amshi ledar hannun Sageer tace "ga shi kije kuci da Hassan muma munyo namu tsarabar."
Jalila ta amsa tace "angode."
Ta fada sannan ta leka bayan Ummy, Ummy tace "tana can."
Jalila ta sunkuyar da kai tace "tam."
Ameera ta matso tace "ya jikin?"
Jalila tace da sauki.
Ummu tai gaba Ameera ma tabita, ta kalli Sageer tace "Sannu da zuwa."
Kallanta yai yace "ya jiki?"
Tace "na ware ba wani serious bane dama."
Ya kalleta cikin kulawa yace "Sannu Allah ya kara sauki."
Tace Ameen ta juya, da kallo ya bita.
Kowa daki ya shiga da ledarsa dan duk sun gaji.
Jalila ta wuce sama.
Tana shiga ta sameshi a zaune, yana ganinta ya dau littafi wai karatu yake.
A ranta tace ko gajiya bayayi.
Ta matso dan dama ta dauko plate daga kasa, ta bude tace "yaya sauko Ummy ta kawo mana abin dadi."
Kallanta yai yace "menene abin dadin?"
Ta bude kedar ta ciro ledar juice sannan ta ciro foil paper ta bude, kaza ce da kuma daurin kundu wanda yasha hadi na musamman.
Juyowa tai ta kalleshi, kallanta yai sannan ya sauko fuska ya zauna, dandai yunwa yakeji amma da cewa zaiyi bazaici ba.
Kallansa tai batasan yanda zata raba musu ba gashi plate daya ta dauko, kallansa tai shima kallanta yai tace bari na dauko wani plate din.
Ta fada tana kokarin mikewa, hannu yasa akan hannunta data dafa kasa zata tashi, kallansa tai, yace "muci tare."
Tace "naam?"
Yace "me? Dama ba haka kikeso ba?"
Tace "nakeso kamar ya kenan?"
Yace "duba ki gani, kinsan mu biyu ne a dakin nan kika dauko plate daya, yimin bayani meyasa kikai hakan to?"Jalila ta kalleshi kamar zatai magana kawai sai tasa dariya tace "lalai Yaya, yanzu nace zan dauko plate ka hanani sannan kace nice nakeso."
Yace "to ba hakan bane?"
Tace "wlh ba haka bane, ni na....."
Yanda ya mata da fuskarsa ne yasata ta kasa magana alamar bayarda zaiyi da duk abinda ta ce ba.
Bismilla tai tasa hannu tana cewa "shikenan tunda an dakeni an hanani kuka."
Bai tanka mata ba yasa hannunsa, a tare suka fara ci, itadai kunya take, shikam wani irin sanyi yakeji a ransa, yana kallanta yasa hannu cikin plate din, a kann hannunta yasa hannunsa.
Dagowa tai ta kalleshi, kallanta yai sannan ya kalli hannunsa, yace "yanzu nine nasa hannuna ko kece?"
Tai dariya sannan ta kalli hannun nashi tace "to hannun waye a sama?"
Ya kalla yace "nawa ne sai dai me yasa nakeji a jikina kamar dauramin akai?"
Tace "me? Daurama?"
Dariya ta fara yi tana kallansa, samun kansa yak da shagala gun kallanta, wanda har bai san ganin yanda take dariya yasashi sakar murmushi ba.
Tsayawa tai da dariya tace "Yaya! Kasan kayi murmushi yanzu?"
Fuska ya hade tare da zare hannunsa da sauri yace " a ina nai murmushin?"
Tace "wallahi kayi yanzu, baka san kayi ba?"
Juya kansa gefe yai yace "u are mistaken."
Tai shiru tana kallansa kafin tace " mistake nai? Amma na tabbatar naga kayi murmushi."
Yace "are u sure ba hakan kike san gani ba?"
Tace"wannan karan bazan musa ba, dan ina san inga ka yi murmushi kullum fuskarka a daure take."
Ya kalleta tare da daukan cup din juice yasha.
Haka sukaci abinci tare sannan ta mike ta wanke hannu ta sauka kasa dan kai plate.
Tana fita ya saki ajiyar zuciya yace "Hassan?"
Gaban madubi ya koma ya kalli kansa, a hankali naga yanayin fuskarsa ya canza zuwa tashin hankali, yasa hannu ya bude drawer karshe ta jikin madubi.
Wani littafi ya dauko ya bude tsakiyar hoto be ya bayyana, kallan hoton yai cikin wani yanayi sannan yamaida hoton ya rufe ya runtse idanunsa, bancancanci farinciki ba, ban kuma cancanci inso ko a so ni ba.
Mikewa yai ya dafa kansa dake sarawa........
Gaba daya ranar bai sake magana ba har ta gaji ta kwanta dan ba alamar fuska.
Washegari ma da Ummy tace ya kaita gidan Goggo bai musa ba ya jira ta suka fita tare, yana kaita kofar gidan baijira me zatace ba yai gaba.
Da kallo tabi motar tana mamakin abinda ya faru, ko a mota duk yanda taso suyi magana kin yarda yai.
Shikuwa yana ajiyeta yaja mota yana tunani.
Jalila kam tana shiga gidan Goggo ta saki baki tana kallan iko Allah, ta shigar da kayan data taho dashi, nan suka zauna suka hau hira cikin farin ciki.
Lantana ma ta zauna sukaita hira.
Goggo cikin hira ne take tambayarta wanda ya kawota.
Jalila tace driver dinsu ne ya kawoni, Yaya ya fita ne.
Goggo tace "Allah sarki, na dauka shine ince bai shigo mun gaisa ba na mai godiya."
Jalila tace "zaizo shima."
Haka sukai ta hira suna tuno rayuwar baya da yanda sukasha wahala, Goggo tanata kara nuna mata ta kula da mutanen nan dan tabbas sun musu hallacin da basu taba tunani ba.
Jalila jefi jefi tana tuno abinda yaya ya mata yanzu da zata sauko, ta fito ta kalleshi tace "Yaya baza......"
Gano tai ya dauke kai yana neman wucewa.
Tsayawa tai dagalo tana kallan ikon Allah kafin ta shigo.
Meya sameshi?
Sai bayan magrib yaro ya turo ta fito, tana fitowa taga Mamman, jikinta ne yai sanyi ta bude bayan mota ta shiga tayima Lantana da Goggo sallama akan sai ta dawo.
Haka suka hau hanya, ta kasa daurewa tace "Mamman ina Yayan?"
Yace "wlh Hajiya bansani ba, waya yamin yace in daukoki."
Tace "okay."
Haka suka isa gida taitama Ummy godiya da Abba.
Kafin ta hau sama.
A daki ta sameshi yana karatu, sallamarta kawai ya amsa shima baiko kalleta ba, Jalila ta daure tace "Yaya na dawo."
Yace "naganki."
Shiru tai a tsaye kafin ta nufi toilet, tai wanka ta sa kayan bacci sannan ta fito ta dau bargo ta shimfida tana cewa "Yaya bacci nakeji, yau da alama na zama kasa, ko dan banyi baccin safe bane? Ina ta zumudi?"
Bai tanka mata ba, tai dariya tace "hmm basa banba, ni fa da agida bansan ma wani baccin safe ba amma yanzu jin dadi yasa har in banyi ba sai naji wani iri."
Bai tanka mata ba hakan yasata yin shiru, ta sa bargo ta kwanta, bata dade ba bacci ya dauketa.
Juyowa yai ya ajiye littafin ya kura mata ido, idanunsa ne suka canza kala a fili yace " Jalilah! Jalilah!"
Sannan yai shiru, mikewa yai ya shiga toilet ya watsa ruwan zafi sannan ya zura riga, harzai wuceta ya tsaya, sai kuma ya koma ya zauna kusa da ita.
Hannu yasa a gefen fuskarta yana kallanta cikin wani yanayi.
Cikin wata raunaniyar murya yace " nasan i am hurting u, sai dai kafin kiji zafin abinda nake miki ni na ji zafi, duk sanda na wulakantaki inaji a jikina sai dai bansan ya zanyi ba, Jalilah bansan ya zanyi ba banasan naga na dawwama a koda yaushe a cikin kuntata miki."
Shiru yai yanajin wani abu a kirjinsa kafin yace "Jalila Husain......."
Ya runtse ido a hankali wasu hawaye naga sun zubomai masu zafi, hannunsa yakai kan labanta.
Idanunsa ya sake rufewa a hankali ya shiga matso da kansa ya sumbashi bakinta, bakinsa ya bari a kan labanta.
Idanunta ta bude, me zata gani?
Shima idanu ya bude suka kalli juna, da sauri tasa hannu ta tureshi, ya mike tsaye da sauri.
Tace "Yaya!"
Yace "bargona nakesan dauka sanyi nakeji."
Tace "bargo?"
Bargo a.......
Ta kasa karasawa, yace "bargo a me?"
Tace "bakomai, nagane tun jiya kaki kulani, yanzu kuma gashi kanamin magana."
Yace "yanzun ma bakiji me nace miki ba? Bargona zaki bani."
Tace "to in na baka in shimfida me?"
Ya kalleta taya zaiyi yace mata shi kwanan kasan ne bayaso?
Ya hade fuska yace "sai ki kwanta akan gado ni sam laushin katifa samin ciwon baya take."
Da sauri tace "haba? Da gaske na kwanta?"
Ya kalleta sannan ya dau bargonsa ya kwanta akasa.
Murmushi tai sannan ta hau kan gado tana dariya jin dadi.
Can kuma tace "yaya badai barmin kai ba?"
Yace "barmiki? Bakiji me nace ba?"
Tace "oh naji."
Ta kwanta tare da juya baya.
Shiru tai kamar mai bacci tana tunanin abinda ya faru yanzu, hannunta takai kan labanta ta shafasu, shima kwanciya yai yana tuno abinda ya faru, me yakai shi? Baisan ya akai yaji a lokacin sumbatarta yakesan yi ba.
Ahhh kansa ya shafa yace "Hassan!"
#OneLuv💕
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔️ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*49*
Goggo tana zaune tana kara bin gidan da kallo, hawayenta yaki tsayawa, ashe alheri ne a dukulle a tattare da sharrin da aka jefesu dashi.
Ba wani katon gida bane, falo daya ne babba sai 2bedrooms a cikin falon da toilet daya.
Sai tsakar gida kato wanda za'a iya ajiye motoci kananan guda biyu.
Ameera da Lantana dake sa labule ta kalla tama rasa ta ina zata fara, ashe a rayuwa akwai rana irin wannan? Shiyasa mutane ke cewa Allah yasa muci darajar 'ya'yan mu, a da bata fahimtar abinda ake nufi da hakan amma yanzu ta gane dalilin fadan hakan, in kai a rayuwa bakai sa'ar abokin zama ko iyaye ba sai ka nemi sa'a akan 'ya'yanka.
Hawayenta ta share, ko mahaifiyarta da mahaifinta nada rai?
Haka su kai ta aiki, itama tana tayasu, sai yamma su Ummy suka dawo, sun siyo abin kitchen, tv set, toilet, abinci da sauransu, dama zuwan farko aka siyo kujeru, gado da labulaye.
Haka suka taho musu da gashashiyar hanta da juice suka ci suka sha, Ummy ta nunama Goggo kawai komai ta samu tayi. Hamdalla bawai taita kuka ba, hakan yasa ta saki jiki sukaci abinci tanata godiya.
Sai wajen Magrib suka kammala komai, Ummy tace su tafi, sai asa ranar tarewarta.
Goggo tai shiru tana tunani, Ummy ta matso tace "lafiya? Ko kina tunanin zama ne gaba daya?"
Goggo tace " indai hakan zai samu nafisan hakan, dan maganar gaskiya kunyar gidan nakeyi.
Ummy tace "shikenan ai ba wani abu bane, in har hakan yafi kwanta miki a rai, sai dai kamar ba'a gama jan wutar gidan ba, sannan bamu siyo generator ba."
Goggo da sauri tace "hakan ma ya isa, ba sai anja wutar ba dan acan gidan ma bamu samu wannan darajar ba ni har na rasa ta inda zan soma yi muku godiya."
Ummy tace "dan Allah ki bari, yanzu bari mu barku anan, sai nasa yanzu Sageer ya samo katuwar fitila kafin a gyara wutar gidan, kayanki kuma gobe in Jalila zata zo sai na bada a kawo miki."
Goggo ta kamo hannun Ummy cikin wani irin yanayi na farinciki tace " nagode nagode, sai dai dan Allah ina da alfarma daya dazan nema."
Ummu tace "menene?"
Goggo tace "Jalila tana bala'in san makarantar addini ta islamiyya, bansani ba ko da yanda zakuyi ku taimaka mata."
Ummy tace "basu sata a makaranta ba?"
Tace "basu sata ba, karatun da nake dashi kadan shi na koya mata."
Ummy tai shiru tana tunanin wannan muguntar kafin tace "shikenan zan sanar ma mijinta, hafizi ne na karatu dan da wuri ya sauke alqur'ani zan ji shawarar da zai yanke."
Goggo tace "nagode sosai."
Haka suka fito sukabar Goggo da Lantana a gidan, sai da suka sai katuwar fitila suka kai musu sannan suka fito.
Ummy a hanya ta kalli Sageer tace "Sageer akwai iyayenda in basuyi wasa ba alhakin 'ya'yansu shine dalilin da zaisa su shiga wuta."
Sageer yace "Ummy nikam haryanzu kwakwalwata na mamakin irin wannan mahaifin, wanda san kansa yamai yawa da har baya damuwa da halin da 'ya'yansa suke ciki."
Ameera ta kalli Ummy tace "Ummy nikam dan Allah kumin bayani, wai ya akai Goggo ta zama mahaifiyar Jalila, Mumy fa? Nifa gaba daya na rasa meke faruwa tun jiya nakesan yin tambaya."
Ummy tasa yatsa ta ta tura goshita tace "gulmar me kike sanji? Magana daya dai wannan ce mahaifiyarta me kike nemanji bayan wannan?"
Sageer ya sa dariya yace "Ummy in Ameera batai gulma ba ai ba Ameeran bace."Cikin shagwaba tace "Yaya Sageer haka zakace? Harda wani in banyi gulma ba?"
Ya kara sa dariya yace "To yahkuri ba gulma ba."
Ummy ta kalleta tace "ba wani tayi hakuri, ai dama uwar gulma ce da san jin komai."
Ameera ta kara shagwabewa tace "Ummy Allah ni abubuwan da nakeso in tambaya dayawa fa amma tun yanzu kunsa na kasa."
Ummy tace "sai ki hadiye gulmarki inkin samu Abbanki sai ki tambayeshi."
Tace "shikenan ai nasan Abbana bazai min haka ba..."
Haka sukai ta zolayarta suna dariya cikin farinciki har suka isa gida.
********
A can gida kuwa Hassan tunda ya shiga daki ya zauna a bakin gado yai shiru yana tunani, tabbas gaba daya rayuwarsa ta canza a 'yan kwanakin nan, gaba daya yarinyar nan taki barin zuciyarsa.
Abu daya ne ya fara zuwa♀️😘😏😘🤺😘🤺😛😘😘 mai badai santa kake ba?
Da sauri ya girgiza kai yace "so? Ni? Yarinyar nan?"
Kai ya sake girgizawa alamar ba haka ba yace "tausayine."
Tausayi akan me? Ka tabbatar shi kadai ne? Damuwar da kakeyi fa in abu ya sameta?
Tambayar dake tamai yawo a zuciya kenan, shiyasa ma gaba daya daga ta shigo sai yai gamar yana bacci, ko ya dau littafi wai a dole karatu hakeyi ko ya dau wayarsa....
Ita kuwa daga baya ta sauka falon kasa ta zauna.
Bayan tayi sallar isha'i ne Abba ya dawo, ta gaisheshi ya amsa fuska a sake bai dade da dawowa ba su Ummy suka dawo.
Tanajin dawowarsu ta tashi da sauri tazo taryarsu.
Ummy ta kalleta cikin kulawa tace "Jalila jikin ne?"
Tace "na warke Ummy gashi banyi abinci ba."
Tace "nina hana kiyi, bakida lafiya wake ta abinci?"
Sunkuyar da kanta tai, Ummy ta amshi ledar hannun Sageer tace "ga shi kije kuci da Hassan muma munyo namu tsarabar."
Jalila ta amsa tace "angode."
Ta fada sannan ta leka bayan Ummy, Ummy tace "tana can."
Jalila ta sunkuyar da kai tace "tam."
Ameera ta matso tace "ya jikin?"
Jalila tace da sauki.
Ummu tai gaba Ameera ma tabita, ta kalli Sageer tace "Sannu da zuwa."
Kallanta yai yace "ya jiki?"
Tace "na ware ba wani serious bane dama."
Ya kalleta cikin kulawa yace "Sannu Allah ya kara sauki."
Tace Ameen ta juya, da kallo ya bita.
Kowa daki ya shiga da ledarsa dan duk sun gaji.
Jalila ta wuce sama.
Tana shiga ta sameshi a zaune, yana ganinta ya dau littafi wai karatu yake.
A ranta tace ko gajiya bayayi.
Ta matso dan dama ta dauko plate daga kasa, ta bude tace "yaya sauko Ummy ta kawo mana abin dadi."
Kallanta yai yace "menene abin dadin?"
Ta bude kedar ta ciro ledar juice sannan ta ciro foil paper ta bude, kaza ce da kuma daurin kundu wanda yasha hadi na musamman.
Juyowa tai ta kalleshi, kallanta yai sannan ya sauko fuska ya zauna, dandai yunwa yakeji amma da cewa zaiyi bazaici ba.
Kallansa tai batasan yanda zata raba musu ba gashi plate daya ta dauko, kallansa tai shima kallanta yai tace bari na dauko wani plate din.
Ta fada tana kokarin mikewa, hannu yasa akan hannunta data dafa kasa zata tashi, kallansa tai, yace "muci tare."
Tace "naam?"
Yace "me? Dama ba haka kikeso ba?"
Tace "nakeso kamar ya kenan?"
Yace "duba ki gani, kinsan mu biyu ne a dakin nan kika dauko plate daya, yimin bayani meyasa kikai hakan to?"Jalila ta kalleshi kamar zatai magana kawai sai tasa dariya tace "lalai Yaya, yanzu nace zan dauko plate ka hanani sannan kace nice nakeso."
Yace "to ba hakan bane?"
Tace "wlh ba haka bane, ni na....."
Yanda ya mata da fuskarsa ne yasata ta kasa magana alamar bayarda zaiyi da duk abinda ta ce ba.
Bismilla tai tasa hannu tana cewa "shikenan tunda an dakeni an hanani kuka."
Bai tanka mata ba yasa hannunsa, a tare suka fara ci, itadai kunya take, shikam wani irin sanyi yakeji a ransa, yana kallanta yasa hannu cikin plate din, a kann hannunta yasa hannunsa.
Dagowa tai ta kalleshi, kallanta yai sannan ya kalli hannunsa, yace "yanzu nine nasa hannuna ko kece?"
Tai dariya sannan ta kalli hannun nashi tace "to hannun waye a sama?"
Ya kalla yace "nawa ne sai dai me yasa nakeji a jikina kamar dauramin akai?"
Tace "me? Daurama?"
Dariya ta fara yi tana kallansa, samun kansa yak da shagala gun kallanta, wanda har bai san ganin yanda take dariya yasashi sakar murmushi ba.
Tsayawa tai da dariya tace "Yaya! Kasan kayi murmushi yanzu?"
Fuska ya hade tare da zare hannunsa da sauri yace " a ina nai murmushin?"
Tace "wallahi kayi yanzu, baka san kayi ba?"
Juya kansa gefe yai yace "u are mistaken."
Tai shiru tana kallansa kafin tace " mistake nai? Amma na tabbatar naga kayi murmushi."
Yace "are u sure ba hakan kike san gani ba?"
Tace"wannan karan bazan musa ba, dan ina san inga ka yi murmushi kullum fuskarka a daure take."
Ya kalleta tare da daukan cup din juice yasha.
Haka sukaci abinci tare sannan ta mike ta wanke hannu ta sauka kasa dan kai plate.
Tana fita ya saki ajiyar zuciya yace "Hassan?"
Gaban madubi ya koma ya kalli kansa, a hankali naga yanayin fuskarsa ya canza zuwa tashin hankali, yasa hannu ya bude drawer karshe ta jikin madubi.
Wani littafi ya dauko ya bude tsakiyar hoto be ya bayyana, kallan hoton yai cikin wani yanayi sannan yamaida hoton ya rufe ya runtse idanunsa, bancancanci farinciki ba, ban kuma cancanci inso ko a so ni ba.
Mikewa yai ya dafa kansa dake sarawa........
Gaba daya ranar bai sake magana ba har ta gaji ta kwanta dan ba alamar fuska.
Washegari ma da Ummy tace ya kaita gidan Goggo bai musa ba ya jira ta suka fita tare, yana kaita kofar gidan baijira me zatace ba yai gaba.
Da kallo tabi motar tana mamakin abinda ya faru, ko a mota duk yanda taso suyi magana kin yarda yai.
Shikuwa yana ajiyeta yaja mota yana tunani.
Jalila kam tana shiga gidan Goggo ta saki baki tana kallan iko Allah, ta shigar da kayan data taho dashi, nan suka zauna suka hau hira cikin farin ciki.
Lantana ma ta zauna sukaita hira.
Goggo cikin hira ne take tambayarta wanda ya kawota.
Jalila tace driver dinsu ne ya kawoni, Yaya ya fita ne.
Goggo tace "Allah sarki, na dauka shine ince bai shigo mun gaisa ba na mai godiya."
Jalila tace "zaizo shima."
Haka sukai ta hira suna tuno rayuwar baya da yanda sukasha wahala, Goggo tanata kara nuna mata ta kula da mutanen nan dan tabbas sun musu hallacin da basu taba tunani ba.
Jalila jefi jefi tana tuno abinda yaya ya mata yanzu da zata sauko, ta fito ta kalleshi tace "Yaya baza......"
Gano tai ya dauke kai yana neman wucewa.
Tsayawa tai dagalo tana kallan ikon Allah kafin ta shigo.
Meya sameshi?
Sai bayan magrib yaro ya turo ta fito, tana fitowa taga Mamman, jikinta ne yai sanyi ta bude bayan mota ta shiga tayima Lantana da Goggo sallama akan sai ta dawo.
Haka suka hau hanya, ta kasa daurewa tace "Mamman ina Yayan?"
Yace "wlh Hajiya bansani ba, waya yamin yace in daukoki."
Tace "okay."
Haka suka isa gida taitama Ummy godiya da Abba.
Kafin ta hau sama.
A daki ta sameshi yana karatu, sallamarta kawai ya amsa shima baiko kalleta ba, Jalila ta daure tace "Yaya na dawo."
Yace "naganki."
Shiru tai a tsaye kafin ta nufi toilet, tai wanka ta sa kayan bacci sannan ta fito ta dau bargo ta shimfida tana cewa "Yaya bacci nakeji, yau da alama na zama kasa, ko dan banyi baccin safe bane? Ina ta zumudi?"
Bai tanka mata ba, tai dariya tace "hmm basa banba, ni fa da agida bansan ma wani baccin safe ba amma yanzu jin dadi yasa har in banyi ba sai naji wani iri."
Bai tanka mata ba hakan yasata yin shiru, ta sa bargo ta kwanta, bata dade ba bacci ya dauketa.
Juyowa yai ya ajiye littafin ya kura mata ido, idanunsa ne suka canza kala a fili yace " Jalilah! Jalilah!"
Sannan yai shiru, mikewa yai ya shiga toilet ya watsa ruwan zafi sannan ya zura riga, harzai wuceta ya tsaya, sai kuma ya koma ya zauna kusa da ita.
Hannu yasa a gefen fuskarta yana kallanta cikin wani yanayi.
Cikin wata raunaniyar murya yace " nasan i am hurting u, sai dai kafin kiji zafin abinda nake miki ni na ji zafi, duk sanda na wulakantaki inaji a jikina sai dai bansan ya zanyi ba, Jalilah bansan ya zanyi ba banasan naga na dawwama a koda yaushe a cikin kuntata miki."
Shiru yai yanajin wani abu a kirjinsa kafin yace "Jalila Husain......."
Ya runtse ido a hankali wasu hawaye naga sun zubomai masu zafi, hannunsa yakai kan labanta.
Idanunsa ya sake rufewa a hankali ya shiga matso da kansa ya sumbashi bakinta, bakinsa ya bari a kan labanta.
Idanunta ta bude, me zata gani?
Shima idanu ya bude suka kalli juna, da sauri tasa hannu ta tureshi, ya mike tsaye da sauri.
Tace "Yaya!"
Yace "bargona nakesan dauka sanyi nakeji."
Tace "bargo?"
Bargo a.......
Ta kasa karasawa, yace "bargo a me?"
Tace "bakomai, nagane tun jiya kaki kulani, yanzu kuma gashi kanamin magana."
Yace "yanzun ma bakiji me nace miki ba? Bargona zaki bani."
Tace "to in na baka in shimfida me?"
Ya kalleta taya zaiyi yace mata shi kwanan kasan ne bayaso?
Ya hade fuska yace "sai ki kwanta akan gado ni sam laushin katifa samin ciwon baya take."
Da sauri tace "haba? Da gaske na kwanta?"
Ya kalleta sannan ya dau bargonsa ya kwanta akasa.
Murmushi tai sannan ta hau kan gado tana dariya jin dadi.
Can kuma tace "yaya badai barmin kai ba?"
Yace "barmiki? Bakiji me nace ba?"
Tace "oh naji."
Ta kwanta tare da juya baya.
Shiru tai kamar mai bacci tana tunanin abinda ya faru yanzu, hannunta takai kan labanta ta shafasu, shima kwanciya yai yana tuno abinda ya faru, me yakai shi? Baisan ya akai yaji a lokacin sumbatarta yakesan yi ba.
Ahhh kansa ya shafa yace "Hassan!"
#OneLuv💕