← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 53

Sashe 17

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

#Oneluv💕
[08/10, 02:07] ‪+234 803 222 1758‬: 🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

(_D home of expert and perfect writer's_💡)

*No 16*

Kallansa Inna tai sannan ta zare tabaron dake manne a fuskarta, ta ajiye magazine din da take dubawa tace "Me kace?"
Abubakar ya kalleta cikin jin shakarta yace "Inna abinda akai dazu bai daceba, bana tunanin ya kamata a sa rayuwar mahaifiyarta a tsakiya saboda neman abinda mukeso."
Inna tai murmushi sannan tace " a yau ne ka fara damuwa da yar taka? Ko kuwa yau ne kake neman kula da matarka?"
Yace "Inna kinsan ba haka nake nufiba."
Tace "ya isheni haka nan, sannan daga wannan lokacin ba ruwanka akan duk abinda na sharada akan harkar bikin nan, na dauka kaine ka sanar damu da matar da abinda ke cikinta duk baka sansu? Na dauka kaine ka nuna mana Fatima da 'ya'yanta ne kadai abinda kake so?"
Yace "Inna......"
Tace "ya isheni haka nan."

Mumy cikin rashin jin dadi tace "Inna me yasa kike san canza maganar mutunci zuwa rashinsa? Kinfi kowa sanin Abban Yasmin ba haka yake nufi ba, ko ni banji dadin abinda kika aikata ba dazu, yanzu da tsautsayi yazo da mutuwa fa?"

  Inna tace "kin min shiru ke kuma ko kuwa?"
Mumy tai shiru, Inna ta kalli Abubakar tace "zanyima tambaya ta farko kuma ta karshe akan harkar Jalila, da ita da company dinmu wanne kake ganin yafi cancanta a ceta?"
Dady ya kalleta jiki a sanyaye, tace "ina jinka."
Yace " ba dogon nazari Inna kinsan company yafi, sai dai......."
Tace "magana ta kare, daga yanzu kuma  daga kai har Fatima sai ku bar komai a hanuna, yarinyar nan dai ba gidan yankan kai zamu kaita ba, ba gidan yan shaye shaye ko talakawa zata ba, mezaisa kudinga haka?"

  Dady da Mumy sukai shiru, can tace "ina takardar asibitin?"
Dady ya zaro a aljihu ya mika mata, nan suka fito.

Dady na shiga daki ya zauna a bakin gado ya shafi fuskarsa sannan yai wani irin ajiyar zuciya.
Kusa dashi Mumy taje kusa dashi ta zauna, tasa hannunta a kafarsa.
Hannunsa ya sa ya zare hannunta daga jikinsa yace "Fatima duk yanda naso nai tunani akan abin nan i think this is not right."
Hannunsa ta kamo tace " let us save the company first, in komai ya daidaita sai musan ya zamuyi da Jalila, karka damu."

  Kai ya daga alamar gamsuwa, sannan ta jawoshi jikinta ta rungume.
Shiru yai yana tunani, tabbas company dinsu shine darajarsu sai dai idanun Jalila sun tsaya mai a rai.

*********

  Yau duk yanda taso tai bacci ta kasa, juyi kawai take tana kara karanto rayuwar mahaifiyarta, tabbas dolene yanzu ta dau damarar taimakon mahaifiyarta, insha Allahu yau ne rana ta karshe da Mahaifiyarta zata zubar da hawaye, tunda a tsawon rayuwarta ta kula rabi na bakinciki da zubar da kwalla ne, sai dai ta yaya zata temaki mahaifiyarta?

  Hawayenta ta share, kalaman Inna ne suka sake dawo mata, haka tai ta juyi har batasan sanda bacci yai gaba da ita ba.

******

Washegari Ummy bayan anyi sallar azahar ta fito da lefe dan kara dubawa ita da yan uwanta, Ameera na ta zungurin Aina'u dan tasan Aina'u na san Hassan.
Aina'u tai murmushi kawai ta mike tai ciki.
Hassan kam dama tunda ya fara jin hayaniyar mutane ya bar gidan, da Sagir akai ta hidimomin.

Bayan la'asar aka kawo lefe gidansu Jalila, yan uwan Mumy me suka karbi lefen, ganin uban kayan da aka kawo, dan akwati set biyu aka kawo masu dan karen kyau da tsada, sannan kayan dake ciki, ba'a magana, yan uwan Mumy sukai ta mata fada akan ta bark dan masu kudi yaso yar da ke zaune a gidansu a maimakon yarta, in taji haka murmushi kawai take sai tace wai ai so ba ayi masa dole.

  Haka yan kawo lefe suka tafi bayan an tsaida biki sati biyu.
Ameera ce ta sanar ma Mumy cewa Ummy tace angon zai zo gobe dan yaga Amarya.
Ana watsewa Mumy ta hau sama da sauri ta sanarma Inna.
Ganin abin bai damu Inna ba tace "Inna kina tunanin Jalilan zata yarda taje?
Inna tace " ki tura mota a daukomin Jalila zanyi magana da ita."
Mumy tace "me zakice mata?"
Inna tace "ba ruwanki, ke dai ki yi abinda nace."

  Mumy ta mike ta fita.
Jalila na zaune duba dan karatun da Goggo ta d'ora mata na islamiya, dan itama Goggon ba wani nisa karatun nata yai ba.
Goggo na kwance tana bacci, dan da safe sai da aka tsaga kafarta akai mata aiki, aka daye fatar gun aka wanke.
  Amsa sallama tai sannan ta kalli kofar, Sultan ne ya shigo ya ajiye kular abinci sannan ya kalleta yace "ya mai jikin?"
Tace da sauki Sultan.
Yace "Inna na san ganinki."
Tace "akan me?"
Ta fada tana kallan Goggo, ganin tana motsi yasa ta mike da sauri ta kamo Sultan suka fito, tace "akan me?"
Yace "ban sani ba wlh, amma jiya dai naga mata sunzo da akwatuna, naji kuma ana cewa naki ne."
  Tace "Mene?"
Shiru yai ganin yanda tai, yace " menene? Baki sani ba?"
Idanunta ne ya ciciko tace "Sultan zaka iya zama agun Goggo naje na dawo?"
Yace " ba matsala."
Tace"nagode Sultan, dan Allah ko ta tambaya kace mata naje gida dauko kaya ne."

Ya daga ai.
Mota ta shiga drivern ya ja, tunda ta shiga jikinta ke rawa har suka isa.
Haka ta fito da kyar ta shiga cikin gidan.
Yasmeen na falo ita da Mumy, gaishesu kawai tai ta wuce.

  Inna na zaune ta shiga, sai da ta zauna sannan ta gaisheta.
Bata amsa ba ta ajiye mata farar takarda a gabanta.
Jalilata kalleta tace "Na menene?"
Inna tace " duba ki gani."

Jalila ta sa hannu ta dauka, receipt ne da aka bada a cashier, ga kuma tambarin asibitin Standard a jiki.
Kallan Inna ta sake yi, Inna tace " Bakiyi makaranta bane?"
Jalila ta kara kallan takardar, kudi ne zunzurutu wanda aka biya, na daki da kuma na aikin da aka mata da na treatment, sa dai bataji su a gunsu kudi ne mai yawa.

Kallan Inna ta sakeyi dan bata fahimci me takesan nuna mata ba.
Inna tace takardar kudin da muka kashema Mahaifiyarki ne.
Jalila tace "na gani angode Allah ya saka....."
Inna tace " Biya zakiyi."
Jalila cikin rashin fahimta tace "bangane ba."

Inna tace "kina tunanin kina zaune a gidan mu, mun saki a makaranta, mun kula dake da mahaifiyarki, mun biya mata wannan kudin, sannan kice ba zakibi umarnin mu ba?"

  Jalila tace "Inna......."
Inna ta katseta tace "yaya? Kina da kudin da zaki biya mu dai ko?"

Idanunta ne suka kara firfitowa ta fara zubarda hawaye, Inna tace " in har kinfi karfin bin umarninmu sai mu zare hannunmu daga rayuwarku sai inga yanda zakuyi, ina fatan kinada inda zaku zauna da kuma kudin da zaki cigaba da kula da mahaifiyarki harta warke."

  Jalila tasa kuka tace "Inna dan Allah kiyi hakuri, Goggo tana neman kulawarku dan Allah ki yafemin."
Inna ta mike tace " tashi ki fita, na baki daga yau zuwa gobe da safe inhar baki bi umarnin mu ba, zansa a koreta daga asibitin, sannan kubar gidan mu bayan kin biya kudin."

  Jalila ta zauna tana wani irin kuka mai ban tausayi, Inna tace "tashi ki fita."
Mikewa tai tana hawaye ta sauko.
Yasmeen na mata magana ko kallanta batai ba ta fito tana hawaye.
Bangarensu ta nufa kawai ta zube akasa tana kuka, ya zatai? Uncle ne ya fado mata, da sauri ta janyo jakarta ta zaro wayar nan.
Ganin irin kiran da yai mata yasa ta saurin danna kira, ringing take ta yi ba'a daga ba.

Shikuwa a lokacin Ummy ta nemi ya rakata store, sai daya shiga mota ya tuna yabar wayarsa a gida.
Sai dai ganin ba wani dadewa zasuyi ba yasa ya fita kawai.

   Kuka ta shiga yi sosai da taga bai daga ba, kira take tayi ba kakkautawa.
Ganin ba dama ta cila wayar kan gado ta fito rike da jakarta.

Tana tafe tana kuka, drivern na mata magana ko bi takansa batai ba tai waje.
Tana tafe tana wani irin kuka.

  Sai da ta mike layinsu sosai, taje tsalakawa ta titi shi kuma ya taho saura kiris ya bugeta, wani irin burki yaja da karfi sannan ya kifa kansa da sitiyari.

Jikinsa ne ya shiga karkarwa, Jalila kuwa ta dauka karshen rayuwarta yazo har ta tsugunna, ganin bai kade ta ba kawai sai taji wani irin kuka yazo mata.

  Tsananin tsoro yasa zufa ta shiga keto mai, da kyar ya iya fitowa daga motar, kusa da ita yazo yanda yaji tana kuka yasa yaji kansa na wani irin juyawa, dan tabbas ya dauka ya mata illa, dan uwansa ya hango alokacin da matsalar da bazai taba mantawa ba ta faru, numfashinsa ne ya shiga sarkewa, hannunsa yasa a wuyansa yana wani irin abu.

Jalila ta dago, ganin mutum na neman zubewa yasa hankalinta ya tashi.
Da sauri ta shiga yin ihun neman taimako.
Mikewa tai zata nemo mutane, hannu yasa ya riko siket dinta.
Juyowa tai da sauri tare da tsorata.
Da kyar yace " ba bige nai ba?"

  Gaba daya ta tsorata dan ta dauka shi aka bige.

Siket dinta ta fizge ta tsaya tana kallan sa.
Mikewa yai sannan ya matso kusa da ita, matsawa ta dan yi.
Ya kara matsowa fuskarsa a hade, kara matsawa tai cikin tsoro.
Yace " meye dalilinki na tsugunnawa akasan motata da sa mun kuka?"
Jalila ta kalleshi tace " motarka ce?"
Yace "tambayarki nake?"
Ta kara kallan motar sannan ta tuno abinda ya faru da irin mai motar, da alama duk masu irin motar nan basuda mutunci.
Tace " na dauka ma hakuri zaka bani, tunda kasan na tsorata."

Baya san magana amma yanda tai maganar yasa ransa ya baci yace " me? Hakuri?"
Ta daga kai, kallanta yai, harzai sake magana sai kuma naga ya fasa, motarsa ya koma ya shiga ya fizgeta da gudu.

  Jalila ta harari motar, ta cigaba da tafiyarta tana matsar kwallarta.
Da alama yau gaba daya ranar bakin ciki ce a gareta.
Chapter 17 · 0% Book details