Sashe 20
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jalila ta kalleshi sai dai gani take kamar shiryawa sukai, Dady ya kalleta sannan yace "Habiba, na tabbatar kina ganin kamar ban damu dake ba wanda a gaskiyar magana ba haka bane, a duk inda uba yake to lalai tabbas ne yaso abinda ya haifa, kallan mamaki tamai dan tabbas da ace Goggo ba ta bata labarin yanda tai rayuwa dashi ba tabbas zata yarda yana santa sannan zata iya tunanin wani abun akamai daya hanashi nuna mata so.
Dady ya kara kallanta yace " kinajin haushi na ko?"
kanta na kasa batace komai ba, yace " Jalila wannan auran da za'a miki ba wai rayuwar mahaifiyarki kadai zai taimaka ba, ni kaina kin ceci ni sannan kin taimaki rayuwar yan uwanki."
Dagowa tai ta kalleshi cikin rashin fahimta tace " Dady ba aure ne tsakaninku da Goggo?"
kallanta yai yace "me kike tunani?"
Tace " amsar da zaka bani ita zata bani ikon ajiye komai dake raina."
Shiru yai yana kallanta yace "Jalila yanzu ba zancen wani aure da rashinsa bane a gabanmu, inhar kinason Inna ta taimaki mahaifiyarki dolene sai kin amince da auran nan, sannan in fada miki gaskiya ko ki yarda ko karki yarda Inna sai ta aura miki yaran nan."
Idanunta ne suka fara zubar da kwalla tace "Dady kaine mahaifina ko Inna?"
Cikin fada yace "Wai meke damunki ne?yaushe kika fara gardama haka? kina tunanin lalabakin da nakeyi zai baki damar bijirema abinda mukesanki dashi ne? inhar kinasan farincikin uwar data sha wahalarki, kina neman lafiyarta to kibi abinda muka ce miki sannan karki kuskura ki fada mata zancen nan."
Kallansa kawai take tana zubarda hawaye, faduwar da Goggo tai kenan su riba suka samu da rashin lafiyarta? tunda batasan dame zasuyi threatening dinta ba.
Dady ne yace "muje."
A hankali ta tura kofar ta fito, jitai kafafunta na rawa hakan yasa ta rike kofar motar.
Haka suka shiga cikin asibitin yana gaba tana baya.
********
A cikin asibitin kuwa Goggo ce tana kwance tana tunanin Jalila da bata dawo ba,Mumy ta turo kofar dakin.
Goggo ta kalleta sannan ta gaidata, dan dama tunda sukazo gidan haka suka saba, Goggo ce ke gaidata.
Mumy ta zauna a kan kujera sannan ta kalleta tace "Ya jikin?"
Goggo tace "Da sauki, tare kuke da Jalila ne?"
Mumy tace "eh suna tare da mahaifinta ne yanzu zata shigo."
Da sauri Goggo ta canza fuska tace "me yake ce mata? ba dai zance........."
Mumy ce ta katseta tana murmushi tace "Kai maman Jalila, ba wannan zancen bane, ai wannan maganar an ajiyeta sai kin samu lafiya, mun isa mu yanke hukunci ne mahaifiyar yarinya na asibiti?"
Goggo ta mata kallan zargi, Mumy tace "duk rashin kirkirnmu ai bamu isa yi mata aure dai kina asibiti ba, sannan mahaifinta ma har fada mukai akan zancen nan, ya hana a kara tada shi."
Jin hakan ne yasa Goggo tadan saki jiki har tace "mun gode kuna ta dawainiya."
Mumy a ranta tace "Yarki dai nayi.
Amma a fili tace " Karki damu, ke dai ki kwantar da hankalinki ki samu lafiya, kinga dai irin kudin da ake narkarwa a asibitin nan."
Turo kofar da Dady yai ne yasa ta dan canza fuska wai ita a dole fishi takeyi.
Jalila ta shigo ta tafi kusa da Goggo ta zauna.
Dady fuskarnan a hade yace "Ya jiki?"
Tace "Alhamdulila."
Kusa da ita ya matso ya ajiye mata kudi sannan ya juya.
Mumy ce ta mike tace "Sai an kawo abincin dare."
Goggo tace "Angode."
Haka suka fita, Jalila ta kwanta a kafadarta.
Goggo tace "Menene?"
Jalila ta kara gyarawa tace " Kawai dumin Goggona nakesan ji."
Goggo tai murmushi tace "wani abun ya faru ne?"
Tace " me zai faru? Ni fa bangarenmu naje na kwanta, hardasu barci."
Goggo tace "kin kyauta, ki dinga zuwa kema kina hutawa, zaman asibiti ba dadi sannan na kula bakya samun barci sosai."
Jalila ta daga kai tana murmushi.
Goggo ta miko mata duka kudin da Dady ya ajiye tace "irga."
Jalila ta irga tace "ni Goggo dubu ashirinn nake gani."
Goggo cikin mamaki tace "dubu ashirin? Me zamuyi da kudi haka? Sannan ni tunda nake a rayuwata ban taba rike kudi mai yawa haka ba."
Jalila a ranta tace " gashi kin rike yau tunda suna san saida farincikin yarki."
Goggo tai shiru aranta tana mamaki........
***********
A can gidansu Hassan kuwa, Sagir sai karya yai akan sunje sannan shima yayan ya ganta.
Ummy duk ta matso dasan jin labari tace "Sagir kana tunanin ta mai?"
Yace "kinsan halin yaya baice komai ba amma ga dukan alamu ta kwantamai."
Ummy tai murmushi tace "ni kaina nasan zata kwantamai dan wannan inaji a jikina alheri ne atattare da ita."
Abba yai dariya yace "Ah Alhamdulila lalai yau hankalinmu ya kwanta."
Hassan sai wajen magrib ya dawo, yana shigowa Ummy ta fito cikin farinciki tace "Hassan ka dawo?"
Kai ya daga kawai ya nufi sama.
Yana shiga daki, kafin kofar ta rufo Sagir ya shigo, yace "Yaya dan Allah me ka aikata dazu? Ta ya zaka tafi ka barmu a gidan yarinya?"
Hassan bai tanka mai ba sai rigarsa da ya cire dan dama ya gaji da ita.
Sagir yace "Amma Yaya wlh ba dadi, bakaji yanda na ji kunya ba, gashi an hada maka abinci kala kala.
Hassan ya juyo ya kalleshi, Sagir yace "Ya Hassan."
Hassan ya matso kusa dashi yace " Sry." Ya juya yaja towel ya shiga toilet.
Sagir ya bishi da kallo sannan yai ajiyar zuciya.
Juyawa yai ya koma d'aki, dan shi yau abin duniya shima ya dameshi.
Baiga Jalila a makaranta ba daya koma sannan duk yanda ya sake kiranta a waya sai acemai a kashe take.
*£*£*£££**
Ta kowani bangare shirin aure sukeyi, Sagir ya dawo kasa an kara gyara musu saman, sai dai duk yanda ake shirin auren nan Amarya da Ango ko a tsikar jikinsu, dan ita tana asibiti gun mahaifiyarta, yanzu ko gidan ma bata zuwa, kayanta kala uku data taho dasu shi take ta sawa.
Sam batasan auran sati biyu aka saba itadai kawai tasan batasan zuwa gidan ne ma bare a mata zancen.
Kudin da Dady ya basu shi suke dan kwalam dinsu, sai abinci da ake aiko musu, kaf gidan ba wanda ya sake zuwa duba Goggo sai Sultan da yake zuwa duk bayan kwana biyu, sannan ita ko lefen ma da aka kawo basu nuna mata ba, ita kuwa dama ba wannan bane a gabanta, bakincikinta inda zataga Ya Sagir.
Zuwanta makarantarsu uku amma ba ta taba dakar sa'ar ganinsa ba, har ta hakura.
A yau da yazone wanda kwananta 10 kenan da zuwa gida wanda yai daidai da kwana 11 da kawo lefe.
Yau saura kwana uku kenan bikin ta amma bata sani ba.
Tana zaune bayan sunci abincin safe Sultan yazo shi da wata yarinya wacce batakai Jalila ba, gaida Goggo yai.
Jalila ta kalleshi tace "Sultan wannan fa?"
Yace "itace zata dinga tayaki zama, mai kula da Goggo."
Gabanta ne ya fadi dan tabbas ta fahimci me hakan yake nufi, yace "sannan Dady yanasan ganinki yanzu."
Jalila tai yake tana kallan Goggo, Goggo cikin mamaki tace "Allah sarki angode, kinga yanzu sai ki taimaka inkinje gida ki huta ki bari sai gobe ko jibi kya dawo tunda kinga jikin nawa ai da sauki sosai, ni da zasu sallamemu ma da naji dadi."
Jalila ta mike jiki a sanyaye, yarinyar ta gaida Goggo, Goggo ta amsa fuska a sake tace "ya sunanki?"
Zulai yarinyar ta fada.
Jalila ta matso kusa da Goggo ta rike hannunnta idanunta suna neman canzawa tace "Goggo sai na dawo."
Goggo ta jinjina kai tace "ki bari sai gobe ko jibi."
Tace to.
Haka suka fito ta shiga mota.
Suna fara tafiya ta kalli Sultan tace "Sultan wani abin ya faru ne?"
Yace "ban sani ba sai dai na tabbatar an kusa auranki tunda yanzu ma gidan da mutane, sannan naji Mumy na cewa an turo wai yau kanin Ango zaizo dan kuyi magana, tun jiya yaso zuwa to sai sukai tafiya, bandai san maganar da zakuyi ba."
Gaban Jalila ne ya shiga faduwa, a hankali hawaye suka fara zubo mata, kanin ango? Zancen me? Ankusa bikinta? Da wa? Wad'an nan sune suka sake ingizata ta shiga zubar da hawaye.
#Oneluv💕
[08/10, 02:12] +234 803 222 1758: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*No 20*
Suna isa gidan ta fara gaida bakin dake gidan, duk yan uwan Mumy ne dan dama a iya tsayin rayuwarta bata taba ganin dangin mahaifiyarta ba, dan duk yawansu ba mai nemansu, sannan shima Dadyn baya kuma san su nemeshin.
Shikuwa danginsa dama Mahaifinsa ya dade da rasuwa, sai mahaifiyarsa wacce dama ita kam bata san auransa da Goggo sai Mumy, takanzo lokaci zuwa lokaci, abinda zai baka mamaki shine, ita kadai take zuwa sai kanwarsa wacce dama ita fitsarariyace.
Ko sau d'aya Mahaifiyarsa bata taba cewa Innan Goggo tazo suje muhalin yarta ba, Jalila na shekara 10 Allah ya d'auki ran mahaifiyar Dadyn.
Shikadai yaje, dan sai daya dawo daga gaisuwa ya aiko mata da tsintsiya, kuka da gyada wai inji babarta sannan tasan yaje, sai Jalila data jiyo gun Safeena akan mahaifiyar Dady ta rasu.
Kaf gidan yan uwan Mumy ne, sai ita kanwar Dadyn ita kadai.
Abin mamaki shine taya akai tasan ana taro? Kuma me yasa itama in zata zo sai dai ta taho ita kadai? Kana ganin hakan kasan Dady ne ke sanar da ita.
Jalila itakam gaishesu kawai takeyi, tana gamawa ta mike zatai gun Mumy wacce ta leko tana mata alama da hannu akan tazo.
Jalila ta mike zata wuce taji an tawo mata hijab saura kadan ta fadi, kallanta tai zatai magana sai kuma ta fasa tace "Aunty?"
Kanwar Dady wato Aunty Adama tace "Ke dama bakida tarbiya, in ba haka ba ki gaida kowa baki ko kalleni ba?"
Jalila ta tsuguna tace "Aunty kema kinsan ban ganki bane."
Tace "eh ni da nake a kauye ai bazaki ganni ba, tunda kaf falon nan akaina idan naki ya makance."
Jalila zatai magana, Mumy tace "Jalila!"
Dady ya kara kallanta yace " kinajin haushi na ko?"
kanta na kasa batace komai ba, yace " Jalila wannan auran da za'a miki ba wai rayuwar mahaifiyarki kadai zai taimaka ba, ni kaina kin ceci ni sannan kin taimaki rayuwar yan uwanki."
Dagowa tai ta kalleshi cikin rashin fahimta tace " Dady ba aure ne tsakaninku da Goggo?"
kallanta yai yace "me kike tunani?"
Tace " amsar da zaka bani ita zata bani ikon ajiye komai dake raina."
Shiru yai yana kallanta yace "Jalila yanzu ba zancen wani aure da rashinsa bane a gabanmu, inhar kinason Inna ta taimaki mahaifiyarki dolene sai kin amince da auran nan, sannan in fada miki gaskiya ko ki yarda ko karki yarda Inna sai ta aura miki yaran nan."
Idanunta ne suka fara zubar da kwalla tace "Dady kaine mahaifina ko Inna?"
Cikin fada yace "Wai meke damunki ne?yaushe kika fara gardama haka? kina tunanin lalabakin da nakeyi zai baki damar bijirema abinda mukesanki dashi ne? inhar kinasan farincikin uwar data sha wahalarki, kina neman lafiyarta to kibi abinda muka ce miki sannan karki kuskura ki fada mata zancen nan."
Kallansa kawai take tana zubarda hawaye, faduwar da Goggo tai kenan su riba suka samu da rashin lafiyarta? tunda batasan dame zasuyi threatening dinta ba.
Dady ne yace "muje."
A hankali ta tura kofar ta fito, jitai kafafunta na rawa hakan yasa ta rike kofar motar.
Haka suka shiga cikin asibitin yana gaba tana baya.
********
A cikin asibitin kuwa Goggo ce tana kwance tana tunanin Jalila da bata dawo ba,Mumy ta turo kofar dakin.
Goggo ta kalleta sannan ta gaidata, dan dama tunda sukazo gidan haka suka saba, Goggo ce ke gaidata.
Mumy ta zauna a kan kujera sannan ta kalleta tace "Ya jikin?"
Goggo tace "Da sauki, tare kuke da Jalila ne?"
Mumy tace "eh suna tare da mahaifinta ne yanzu zata shigo."
Da sauri Goggo ta canza fuska tace "me yake ce mata? ba dai zance........."
Mumy ce ta katseta tana murmushi tace "Kai maman Jalila, ba wannan zancen bane, ai wannan maganar an ajiyeta sai kin samu lafiya, mun isa mu yanke hukunci ne mahaifiyar yarinya na asibiti?"
Goggo ta mata kallan zargi, Mumy tace "duk rashin kirkirnmu ai bamu isa yi mata aure dai kina asibiti ba, sannan mahaifinta ma har fada mukai akan zancen nan, ya hana a kara tada shi."
Jin hakan ne yasa Goggo tadan saki jiki har tace "mun gode kuna ta dawainiya."
Mumy a ranta tace "Yarki dai nayi.
Amma a fili tace " Karki damu, ke dai ki kwantar da hankalinki ki samu lafiya, kinga dai irin kudin da ake narkarwa a asibitin nan."
Turo kofar da Dady yai ne yasa ta dan canza fuska wai ita a dole fishi takeyi.
Jalila ta shigo ta tafi kusa da Goggo ta zauna.
Dady fuskarnan a hade yace "Ya jiki?"
Tace "Alhamdulila."
Kusa da ita ya matso ya ajiye mata kudi sannan ya juya.
Mumy ce ta mike tace "Sai an kawo abincin dare."
Goggo tace "Angode."
Haka suka fita, Jalila ta kwanta a kafadarta.
Goggo tace "Menene?"
Jalila ta kara gyarawa tace " Kawai dumin Goggona nakesan ji."
Goggo tai murmushi tace "wani abun ya faru ne?"
Tace " me zai faru? Ni fa bangarenmu naje na kwanta, hardasu barci."
Goggo tace "kin kyauta, ki dinga zuwa kema kina hutawa, zaman asibiti ba dadi sannan na kula bakya samun barci sosai."
Jalila ta daga kai tana murmushi.
Goggo ta miko mata duka kudin da Dady ya ajiye tace "irga."
Jalila ta irga tace "ni Goggo dubu ashirinn nake gani."
Goggo cikin mamaki tace "dubu ashirin? Me zamuyi da kudi haka? Sannan ni tunda nake a rayuwata ban taba rike kudi mai yawa haka ba."
Jalila a ranta tace " gashi kin rike yau tunda suna san saida farincikin yarki."
Goggo tai shiru aranta tana mamaki........
***********
A can gidansu Hassan kuwa, Sagir sai karya yai akan sunje sannan shima yayan ya ganta.
Ummy duk ta matso dasan jin labari tace "Sagir kana tunanin ta mai?"
Yace "kinsan halin yaya baice komai ba amma ga dukan alamu ta kwantamai."
Ummy tai murmushi tace "ni kaina nasan zata kwantamai dan wannan inaji a jikina alheri ne atattare da ita."
Abba yai dariya yace "Ah Alhamdulila lalai yau hankalinmu ya kwanta."
Hassan sai wajen magrib ya dawo, yana shigowa Ummy ta fito cikin farinciki tace "Hassan ka dawo?"
Kai ya daga kawai ya nufi sama.
Yana shiga daki, kafin kofar ta rufo Sagir ya shigo, yace "Yaya dan Allah me ka aikata dazu? Ta ya zaka tafi ka barmu a gidan yarinya?"
Hassan bai tanka mai ba sai rigarsa da ya cire dan dama ya gaji da ita.
Sagir yace "Amma Yaya wlh ba dadi, bakaji yanda na ji kunya ba, gashi an hada maka abinci kala kala.
Hassan ya juyo ya kalleshi, Sagir yace "Ya Hassan."
Hassan ya matso kusa dashi yace " Sry." Ya juya yaja towel ya shiga toilet.
Sagir ya bishi da kallo sannan yai ajiyar zuciya.
Juyawa yai ya koma d'aki, dan shi yau abin duniya shima ya dameshi.
Baiga Jalila a makaranta ba daya koma sannan duk yanda ya sake kiranta a waya sai acemai a kashe take.
*£*£*£££**
Ta kowani bangare shirin aure sukeyi, Sagir ya dawo kasa an kara gyara musu saman, sai dai duk yanda ake shirin auren nan Amarya da Ango ko a tsikar jikinsu, dan ita tana asibiti gun mahaifiyarta, yanzu ko gidan ma bata zuwa, kayanta kala uku data taho dasu shi take ta sawa.
Sam batasan auran sati biyu aka saba itadai kawai tasan batasan zuwa gidan ne ma bare a mata zancen.
Kudin da Dady ya basu shi suke dan kwalam dinsu, sai abinci da ake aiko musu, kaf gidan ba wanda ya sake zuwa duba Goggo sai Sultan da yake zuwa duk bayan kwana biyu, sannan ita ko lefen ma da aka kawo basu nuna mata ba, ita kuwa dama ba wannan bane a gabanta, bakincikinta inda zataga Ya Sagir.
Zuwanta makarantarsu uku amma ba ta taba dakar sa'ar ganinsa ba, har ta hakura.
A yau da yazone wanda kwananta 10 kenan da zuwa gida wanda yai daidai da kwana 11 da kawo lefe.
Yau saura kwana uku kenan bikin ta amma bata sani ba.
Tana zaune bayan sunci abincin safe Sultan yazo shi da wata yarinya wacce batakai Jalila ba, gaida Goggo yai.
Jalila ta kalleshi tace "Sultan wannan fa?"
Yace "itace zata dinga tayaki zama, mai kula da Goggo."
Gabanta ne ya fadi dan tabbas ta fahimci me hakan yake nufi, yace "sannan Dady yanasan ganinki yanzu."
Jalila tai yake tana kallan Goggo, Goggo cikin mamaki tace "Allah sarki angode, kinga yanzu sai ki taimaka inkinje gida ki huta ki bari sai gobe ko jibi kya dawo tunda kinga jikin nawa ai da sauki sosai, ni da zasu sallamemu ma da naji dadi."
Jalila ta mike jiki a sanyaye, yarinyar ta gaida Goggo, Goggo ta amsa fuska a sake tace "ya sunanki?"
Zulai yarinyar ta fada.
Jalila ta matso kusa da Goggo ta rike hannunnta idanunta suna neman canzawa tace "Goggo sai na dawo."
Goggo ta jinjina kai tace "ki bari sai gobe ko jibi."
Tace to.
Haka suka fito ta shiga mota.
Suna fara tafiya ta kalli Sultan tace "Sultan wani abin ya faru ne?"
Yace "ban sani ba sai dai na tabbatar an kusa auranki tunda yanzu ma gidan da mutane, sannan naji Mumy na cewa an turo wai yau kanin Ango zaizo dan kuyi magana, tun jiya yaso zuwa to sai sukai tafiya, bandai san maganar da zakuyi ba."
Gaban Jalila ne ya shiga faduwa, a hankali hawaye suka fara zubo mata, kanin ango? Zancen me? Ankusa bikinta? Da wa? Wad'an nan sune suka sake ingizata ta shiga zubar da hawaye.
#Oneluv💕
[08/10, 02:12] +234 803 222 1758: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*No 20*
Suna isa gidan ta fara gaida bakin dake gidan, duk yan uwan Mumy ne dan dama a iya tsayin rayuwarta bata taba ganin dangin mahaifiyarta ba, dan duk yawansu ba mai nemansu, sannan shima Dadyn baya kuma san su nemeshin.
Shikuwa danginsa dama Mahaifinsa ya dade da rasuwa, sai mahaifiyarsa wacce dama ita kam bata san auransa da Goggo sai Mumy, takanzo lokaci zuwa lokaci, abinda zai baka mamaki shine, ita kadai take zuwa sai kanwarsa wacce dama ita fitsarariyace.
Ko sau d'aya Mahaifiyarsa bata taba cewa Innan Goggo tazo suje muhalin yarta ba, Jalila na shekara 10 Allah ya d'auki ran mahaifiyar Dadyn.
Shikadai yaje, dan sai daya dawo daga gaisuwa ya aiko mata da tsintsiya, kuka da gyada wai inji babarta sannan tasan yaje, sai Jalila data jiyo gun Safeena akan mahaifiyar Dady ta rasu.
Kaf gidan yan uwan Mumy ne, sai ita kanwar Dadyn ita kadai.
Abin mamaki shine taya akai tasan ana taro? Kuma me yasa itama in zata zo sai dai ta taho ita kadai? Kana ganin hakan kasan Dady ne ke sanar da ita.
Jalila itakam gaishesu kawai takeyi, tana gamawa ta mike zatai gun Mumy wacce ta leko tana mata alama da hannu akan tazo.
Jalila ta mike zata wuce taji an tawo mata hijab saura kadan ta fadi, kallanta tai zatai magana sai kuma ta fasa tace "Aunty?"
Kanwar Dady wato Aunty Adama tace "Ke dama bakida tarbiya, in ba haka ba ki gaida kowa baki ko kalleni ba?"
Jalila ta tsuguna tace "Aunty kema kinsan ban ganki bane."
Tace "eh ni da nake a kauye ai bazaki ganni ba, tunda kaf falon nan akaina idan naki ya makance."
Jalila zatai magana, Mumy tace "Jalila!"