← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 53

Sashe 38

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kai ta daga cikin jin dadi tace “nagode Ummy.”
Sannan ta ce “ina zuwa.”
Da gudu tabar kitchen din ta haw sama, tana hakki ta shiga cikinn dakin, yana kwance kamar me bacci ta shiga.

Kai ya girgiza kawai ba tare da ya kalleta ba, dan yasan in ba ita ba waye zai banko mai kofa haka?
Jalila ta isa kusa dashi tana hakki tace “Yaya!”
Idanunsa a rufe sai dai yadan yi motsi da hannunsa daya yake kan goshinsa, ta kara gyarawa sannan tace “Yaya dan Allah me kake nufi? Naga ni ba gida ba, ba yan uwa ba, in na dauketa in kaita ina?”
Ta karasa maganar tana hakki.

Bai bude idanunsa ba yace “ni zaki tambaya?”

Ta sa gwiwowinta a kasa sannan ta sunkuyo jikin gadon tace “ yaya tunda kai magana na tabbatar da abinda kake nufi,, shiyasa naketa tunani har Ummy ta bani amsa.”
Yanzu kam jin an anbaci Ummy yasa ya bude idanunsa ya dan kalleta, yace “tace me?”
“In tambayi wanda ya sani a duhu in har bangane ba.”

Ya gyara kwanciyarsa tare da juya mata baya yace “ ni ai banine na saki a duhun ba.”
Mikewa tai ta dawo ta bangaren daya juya tace “ Yaya kaine fa kace in dauketa kafin su dauketa.”
Yace “sosai haka nace.” Ya fada yana kallanta.

Tace “to ai shine ban gane ba.”
Yace “baki gane ba ko kwakwalwarki bata aiki yanda ya kamata?”

Baki tadan turo jin wannan bakar maganar, ya kalleta yace “na nawa kike ci a skul? Na tabbatar double number kike dauka.”

Fuskarta a dan hade tace “double din ai kala kala ne, ni na farko farko nake dauka.”

Yanzu ma bai san bakinsa ya dan murmusa ba, sai kallanta dayai yace “ what’s the difference?”
Tace “ mai daukan double number akwai yan 10’s akwai 20’s akwai 30’s har 50’s ma akwai kaga kuwa ba daya bane.”

Kai yadan jinjina kadan sannan ya sakala hannayensa tare da maida hankali kanta yace “ and?”
Tace “ mene?”
Yace “ u.”
Shiru tai tana dan kumburo baki sannan ta mike tace “Yaya ni danazo magana daban ka canza ta zuwa wani.”

Hannunsa yasa yadan bugi gefen sa wajen saitin cikinsa, kallansa tai sannan tace “in zauna?”
Da ido ya mata alamar eh, nan ta zauna tana kallanshi, ganin yanda ya kafeta da ido ne yasa tai saurin dauke nata idanun.

Hassan ya kalleta yace “ me yasa kika aureni? Bayan baki sanni ba?”

Dagowa tai ta kalleshi, yanayin idanunta suka canza, yace “am sry let me change the question, me yasa kika bari aka miki auren dole? Last time da na tambayeki baki bani amsar da ya dace ba.”

Jalila idanunta ne suka ciciko tana kallansa tana wani murmushin wanda kana gani kasan na damuwa ne ta dan rangwada kai gefe kadan tace “ ya zanyi? Bayan rayuwar mahaifiyata na hannunsu.”

Yace “ kin taba ganin rayuwar wani a hannun wani dan Adam irinsa?”

Bakinsa tasan rufe da labanta kafin ta kalleshi tanna share hawaye tace “she is too sick, wanda hakan ya tsoratani, sunce in ban aminceba bazasu taimaketa ba, how can i.......”

Hawaye ya cigaba da zubo mata, idanu ya zuba mata kafin yace “sai yaushe ne zaki gama?”

Ta kalleshi tana hawaye tace “mene?”
Da kai ya mata alama da fuskarta.

Ta share hawayenta tana cewa “ na gama.”

Gani tai ya mike ya zauna, sannan ya sa kafafunsa ta daya bangaren ya saukar kasa kamar mai shirin sauka sannan yace “ sai a fara canza mata asibiti, inda suma bazasu ganta ba kafin ta samu lafiya cikake.”

Da sauri ta kalleshi, tace “Yaya!”
Cikin wani yanayi ta kira sunan wanda kana ji kasan kira ne na jin dadi da ba zata.”

Mikewa yai tare da bude wardrobe, gaba daya ita kam ta kame a zaune tana mamakinsa, a yanda ta ganshi bata taba tunanin mutumin nan zai mata rana ba, ta dauka itace ake san ta taimakeshi batasan itace wacce za’a taimaka ba, sannan batasan zai ata rana a dan karamin zaman da sukai ba, sai gashi tana ganin side na halayensa kala kala, wanda ta tabbatar zaman taren da sukai, su kwana tare su tashi tare shine yasa ta fahimci hakan, lalai taga hallaci daga gunsa, da gun Ummy.

Batasan tayi nisa a tunani ba sai jitai yace “sai yaushe zaki fadama Ummy?”

Tace “ bansan in kara mata damuwa.......”
Da sauri tai shiru tare da juya kai, takowa yai a hankali zuwa inda take, yasa hannu ya juyo da fuskarta yace “Damuwarta?”

Yawo ta hadiya sannan ta mike da sauri ta matsa daga inda yake.
Hannu yasa a gefen cikinta ya jawota yana kallanta da idanunsa wanda suka canza.
Gabanta ne ya shiga faduwa, tana kallansa.

Dayan hannun yasa ya juyo da fuskarta saitinsa yace “ tambayarki nake.”

Jalila idanuna suka firfito tace “ hmm.”
Saketa yai yana neman fita, da sauri tasha gabansa tace “Yaya Please!”

Kallanta yai yace “ in bakyasan in tambayeta ki fadamin meke faruwa?”

Jalila ta kalleshi tace “ wlh bansani ba nima, ranan nan ne na fita naji Abba nadan fada.”

Yace “yace me?”

Jalila tace “Yaya dan Allah.....”

Cikin zafi yace “ bani hanya”

Jikinta ne yai sanyi ta kalleshi sannan ta sanar dashi abinda ya faru, ta daura da cewa “Yaya dan Allah karka nuna ka sani, dan Allah.”

Gani tai a hankali idanunsa sun rikede, a hankali tadan matsa baya kadan, tana tsoron kar ya mazge ta.
Gani tai ya dau key din mota a zuciye yayi waje.

Biyoshi tai da sauri, sai taga ya fita waje.

Komawa tai kitchen gun Ummy tana cewa “Ummy yahkuri na dade.”

Ummy tai murmushi tace “bakomai, dama kinyi zamanki, Hassan ne ya fita?”

Tace Umm kawai dan batasan me zata ce ba daga nan......

#OneLuv💕

🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)

" *Sending you smiles for every moment of your special day...Have a wonderful time and a very happy birthday!*" .......Phertyn Uwani😂 (El-Mustapha)

*37*

Haryasa key ya ta da motar sai ya kashe motar ya kwantar da kansa jikin kujera tare da rufe idanunsa.

Idanunsa ya bude wanda yanzu ya kara kadawa yai jaa sosai, wayarsa ya dauko ya kira number Abba.

Bayan sun gama yawo shi da ita yai parking din motarsa a gaban gidansu.
Zaliha ta kira number yayarta a waya tace "Aunty mun dawo."

Tace "to bari in fadamai ya fito."
Hafiz ta kalla wanda ke faman hada takardu tace mai "Taura yana waje."
Wasu takardun ya dauka ya fita, Taura na ganinshi ya kalleta yace "ki shiga ciki bari muyi magana."
Tace "a'a ku gama magana ni ina jiranka anan, banasan rabuwa dakai yanzu."

Taura yai murmushi sannan ya fita, tsayawa sukai da Hafiz suna tattauna wani abun.

Ringing din waya ne yasa ta kalli inda ya ajiye wayarsa, Eldest Son abinda taga an rubuta kenan.

Eldest? Tuno hoton maza biyun nan tai, ta tabbatar wanda ya maze din nan shine babban, murmushi naga tayi sliding ta daga wayar, a kunnenta ta kara.

  Hassan shiru yai kafin can yace "Abba?"

Zaliha tadan sake murmushi tace "Bayanan."

  Gani nai Hassan ya bude kofar motar ya fita yace "waye"

Gaban Zaliha ne ya fadi dan batasan ya akai ta tanka mai ba.
Cikin tsawa yace "waye nace?"

Bakinta ta shiga motsawa dan ta kasa magana, raban dataji tsawa ace ita akema har ta manta.
Hassan cikin tsawa da karfin gaske yace " kin fadamin ke wacece ko sai nazo nan na fasa miki baki."

Zaliha ta kalli inda Taura yake a rikice tace "Bari ba........"

Yace "ina mai wayar?"
Da sauri ta bude motar ta taho inda Taura yake jiki na rawa ta mika mai wayar.

Yana ganin sunan Hassan gabansa ya fadi, kallanta yai cikin takaici yace "Meyasa kika dagamin waya?"
Tace "bansani ba nima...."

Matsawa yai daga gun sannan ya kara wayar a kunnensa yace "Hassan!"

"Hassan? How can u call my name as if ba abinda ke faruwa"

Abba yace "Ya akai? Ina wani meeting ne Secretary gun ce ta dauka."

Hassan fuskarsa ta kara hadewa yace " Wacece wannan? Abba me kakeyi a garin Abuja? Ba dai......"

Kasa karasawa yai saboda kansa da yaji yamai nauyi, Abba a rikice yace "Hassan? Hassan jikin ne?"

  Idanunsa ya runtse cikin takaici yace " Abba ko ka manta wacece Ummy a gareka? Ta yaya zaka yi mata haka?"
Abba a rikice yace "Hassan ba haka bane ka tsaya kaji."
Cikin takaici yace " Wallahi Wallahi Abba in dai ina numfashi a doron kasa bazan taba bari ka tozarta Ummy ba, sannan kayi gaggawar gayawa wannan yarinyar dan na tabbatar muryar yarinya naji, wallahi in har bata shiga hankalinta ba har cikin gidan ubanta zanzo in lahantata, in yaso a kamani."

Ya kashe wayar cikin takaici sannan ya saki wayar kasa cikin wani irin bakin ciki ya saki wani irin kara tare da tsugunnawa.

Jalila da Ummy dake kitchen suka fito da gudu saboda karar da sukaji, da sauri Ummy ta karasa kusa dashi tace "Hassan! Menene?"

  Idanunsa na runtse bashi koma da alamar dagawa, Ummy ta kalli Jalila a rikice wacce itama gaba daya hankalinta ya tashi, tace "Jalila kira Sageer a daki."

Da gudu a juya, bata kwankwasa kofar ba saboda rikicewar da tai itama ta bude kofar.

Yana kwance daga shi sai singlet da gajerar wando, yana ganinta ya mike zaune da sauri, juyawa baya tai da sauri tace "Uncle kazo, yaya....."
Ai yanajin tace yaya ya sauko da sauri ya zari goduwar riga ta fito, shima ya fito bai ma karasa sa kaya ba sai a falon.

  Yasan nanan a tsugunne duk yanda Ummy tai ta dagashi yaki, Sageer na zuwa ya dagashi da kyar, kallan Ummy Hassan yai idanun sa jawur kai kace garwashi.

  Ummy batasan hawaye na zubo mata ba tace "Hassan lafiya?"

  Idanunya rufe kawai dan takaici, wato ita tana nan ta dauka mijinta na aiki ashe mata yake bi? Tun yaushe ya fara? Badai zina yake ba?
Chapter 38 · 0% Book details