Sashe 34
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bazai iya shiga ciki ba dan shikadai yasan memory din da yake dawomai in ya shiga cikin asibiti gun marasa lafiya.
Jalila ta juya jiki a sanyaye, tana shiga nurse din ta tareta tace “ina yayan naki?”
Jalila ta kalleta tace “a ina Goggon take?”
Nan tai gaba Jalila ta bita a baya.
Goggo na zaune akan gado, ba laifi kafar tata ta samu sauki sosai, tana shiga tai gunta da gudu ta rungumeta ta saki wani irin kuka.
Ita ma Goggon kuka ta saka, sun dade a haka kafin Goggon ta daure tace “Jalila ina kika shiga?”
Jalila ta dago ta zauna kusa da ita tace Goggo na.
Goggo tasa hannu ta share mata kwalla tace “ kukan ya isa hakanan, me ya faru? Ko jikin naki ne?”
Jalila ta kalleta tana girgiza kai tace “ba komai Goggo na, ya jikin naki?”
Goggo ta kalleta kallon tuhuma tace “Jalila kin tabbatar? Dan nikam tsoron mutanen nan nakeyi.”
Hassan har ya fara tafiya naga yayi kwana da motarsa ya dawo asibitin, bude kofar motarsa yai ya fito sannan ya nufi asibitin.
Nurse din tana ganinshi ta taho inda yake, tace “ ka dawo?”
Hassan yace tana ina? Nan Nurse din ta fara tafiya yana binta a baya.
Suna taka steps din gaba daya kawai takawa yake, suna zuwa second floor yaji kansa ya fara juyawa, da sauri ya rike bango, sannan ya tsaya ya rike gefen zuciyarsa.
Wani irin numfashi yake fitarwa, juyawa yai da sauri ya sauka kasa, nurse din ta juyo kawai taga bayanan.
Hassan ya sauka da sauri ya shiga mota ya ja ya rufe ya fita da gudu.
Sai da yai nisa sannan yai parkin ya kifa kansa akan sityarin motar yana maida numfashi.
Jalila tai murmushi tace “Allah Goggo ba komai, kawai dai ina bakin cikin laifin dana miki ne.”
Goggo tace “laifi?”
Jalila ta kwantar da kanta akan cinyarta tace “ ni dai ki yafemin Goggo na.”
Goggo ta shafi kanta tace “ba abinda kika min Jalila, na tabbatar ko da kin min ba daidai ba sai dai a rashin saninki ko kuma tirsasaki akai, kawai dai inaso kisan ke kadai ce dani a duniya”
Jalila ta share kwallar data gangaro mata tace “ tsoron sanar dake nakeyi.”
Goggo tace “ko menene ki fadamin.”
Jalila tai shiru can tace “zan fada miki amma sai kin warke an sallameki.”
Goggo tai murmushi tace “ shikenan, da alama akan Sagir ne.”
Jalila tai murmushin yake batace komai ba.
Haka ta zauna makale da Goggonta, Lantana na gefe tana kallansu gwanin sha’awa.
*************
Su Hassan na fita Inna ta matso kusa da Dady ta daga hannu ta sharara mai wani wawan mari, da sauri ya kalleta dan sam baiyi zatan abinda zatamai ba kenan.
Mumy ta matso da sauri ta tsaya agan Inna tace “ Inna menene hakan?”
Inna cikin takaici tace “Uban wa yace ka fadi inda take?”
Dady ya kalleta ransa a bace takaicinsa agaban Yasmeen dan wulakanci.
Mumy ta kalleta tace “Ta ya bazai fada ba bayan yaran yasan komai, da alama Jalila ta gama sanar dashi duk abinda ke faruwa?”
Inna cikin kunar rai ta zauna akan kujera tace “Akace bashi da hankali?”
Mumy ta zauna kusa da ita tace “dama
Bakiyi bincike ba?”
Inna tai shiru kafin tace “ muna cikin tashin hankali, idanun yaran nan ba tsoro ko fargaba a ciki sannan da alama baya ragama wanda ya tabashi, me kuke tunanin zai faru in yasan abinda akama matarsa? Sannan canjen da mukai muka bashi Jalila a maimakon Safeena?”
Mumy ta kalli Dady tace “Dadyn Yasmeen!”
Dady ya kalli Inna wacce ke kallansa yace “ hakan bazai faru ba, ni da kaina zan sanar da ita karta kuskura ta sanar dashi komai, kuskuren sanar dashi Mahaifiyarta datai ya isa.”
Inna ta jinjina kai tace “u have to take care of her, in ba haka ba ni zan bulo mata ta bayan gida, zan sata dana sanin da bata gaba yi ba daga ita har uwarta.”
Dady yace “insha Allahu baza’a sake ba.”
Mikewa tai ta hau sama.
Tana tafiya ya mike a zuciyd ya shiga dakinsu.
Mumy ta bishi da sauri tare da rungumeshi ta baya tace “Darling.”
Hannunsa ya zare yace “meye hakan? Kina abu kamar yarinya?”
Ta kara kankameshi tace “Dadyn Yasmeen am sry.......”
Kallanta yai kamar zaiyi fada, da sauri ta sumbaceshi...........
*************
Ummy ce ta kalleshi tace “ ina zakaje da har kake san in wakilceka akan taron da yake da mahimmanci?”
Yace “Abuja zan koma dan akwai abu mai mahimmanci da nake sanyi.”
Ummy ta kalleshi tace “yafi wannan mahimmanci?”
Abba yai shiru yana duba abu a computer sa.
Ummy tace “ ni na kasa gane abinda bazaka iya fadamin ba”
Cikin zafin rai yace “wai meke damunki ne? Dolene ko wani abu na rayuwarta sai na sanar miki?”
Da karfi ya budo kofar wanda ya sa suka kalli kofar a tare, kallan Abba ya shiga yi idanunsa sun canza sosai.
Yanda yake kallan Abban ne yasa Ummy ta matso da sauri ta sa hannu ta riko hannunsa tace “Hassan meye hakan? Taya zaka banko kofa haka bako sallama?”
Idanunsa na kan Abba haryanzu wanda gaba daya Abba ya gama shan jinin jikinsa.
Hassan ya daure yace “mekenan?”
Ummy tace “ mekenan kamar ya?”
Hassan bai kalli Ummy ba idanunsa nakan Abba yace “me Ummy tai da har kake mata fada haka?”
Ummy tasa hannu da karfi ta turashi waje sannan ta fito itama, ta rufo kofar sannan ta kalleshi tace “muje.”
Ta fada tana jan hannunsa, dakyar ya hau saman sannan ya kalleta cikin takaici yace “Ummy me kika mai yake fada haka?”
Tace “ ba abinda yamin nice namai lefi shiyasa yakemin fada akan abinda nai.”
Kallan ta yai dan shikam bai yarda ba, to ko laifin ma tamai taya zai hauta da fada haka? Ummy ta kalleshi tace “Ina Jalilan?”
Yace “Ummy kin tabbatar ba abinda ya miki?”
Tace “sau nawa kake so na fada ne? Ina tambayarka Jalila, badai ajiye ta kai a hanya ba?”
Yace “Tana nan, kawai ya wuce dakinsa.”
Zama yai a bakin gado yana tunani, dolene ko wani abu na rayuwata sai na sanar miki?
Kallaman Abba ne ya sake dawo mai, meke faruwa?
Ummy tana sauka ta koma dakin, Abba ya kalleta yace “me kika cemai? Tace “ kome nacemai bana tunanin nima ya zama dole in sanar dakai.”
Abba ya matso kusa da ita yace “Ciwon sa fa? Ya tashi?”
Ummy ta kalleshi tace “ kaje ka duba.”
Ta matsa daga kusa dashi.
Abba yai shiru yana tunani sannan ya koma ya zauna agefen gado.
***********
Bayan magrib yana zaune yana karatu, naga ya rufe littafin ya sauko zuwa mota.
Kallo daya zakamai ka fahimci yana cikin bacin rai tsantsa.
A asibitin yai parking sannan ya fito, duk yanda yaso ya duba Nurse din a reception din bai ganta ba.
Kawai komawa yai mota ya zauna, ya kwantar da kansa akan kujera.
Jalila kam sunata hira da Goggo taga isha’i tayi.
Wayarta ta dauko tana dubawa ko zai kirata, ta ina zai kirata? Bayan bashi da numberta? Itama haka.
Ajiyar zuciya tai sannan ta ajiye wayar.
Goggo ta dau wayar tana kara kallo tace “gaskiya wayar nan tayi kyau ta birgeni, mahaifiyar Sagir ce?”
Tace “Hmm.”
Goggo tai murmushi tace “ karki damu ina warkewa zansa ya turo ai auran.”
Wani film akeyi a tv dake dakin, saurayin ta na waje yana ta jiranta ita kuma bata sani ba tana cikin gida suna ta hirar su
Mikewa tai ta dau hijab dinta tace “Goggo ina zuwa.”
Ta fito, tana tafe tana cewa kai inaa.... ta ya zai zauna jirana? Au ko bai san inda nake ba na tabbatar zai sa a nemi ni.
Tana fitowa kawai ta hango motarsa, mamakinne ya kamata ta karaso gun motar a ranta tana cewa “ kai.... ba shi bane, kanta tasa tana leka motar.”
Hassan na kwance ya bude idanunsa, gani yai ana leko cikin motar, tunda akwai haske fitulun waje.
Hassan ya zuge glass din motar yace “ meye hakan?”
Tace “kai!!!! Kaine da gaske, me kake anan?”
Yace “ me nake kuwa, bakisan wannan shine hubby dina ba?”
Tace “zama a mota?”
Bai tanka mata ba yace “ muje?”
Tace “bari nama Goggo salama, Yaya bazaka shiga ba?”
Kansa ya kawar gefe.
Ta fita ta ma su Goggon salama, goggo ta bita da kallo tana tunanin tabbas akwai wani abun, Jalila bazata taba zuwa ta tafi a aranar ba.
Jalila ta shiga mota ya tada suka fara tafiya, yanda taga yanayin fuskarsa ne yasa tai shiru dan taga ba alamar wasa.
Can ta kasa daurewa tace “Yaya nagode.”
Bai kalleta ba yace “ 4 wat?”
Tace “ taimakon da kamin.”
Shiru sukai sai tafiya kawai da yakeyi, can tai murmushi cikin sanyin murya tace “ at first tsoronka nakeyi, later sai na fara fahimtar ka, yau kuma na ga wani side naka na daban.”
Hassan bai kulata ba sai da aka dade yace “ kina tunanin adan karamin kwanakin da mukai ne kike tunanin kin fara sanina?”
Tai murmushi tace “a’a bansanka ba, sai dai na fahimci abu daya.”
Juyowa yai ya kalleta, yana jiran abinda zatace.
A ranta tace u are kind, amma a fili dariya tai tace “na fahimci kana matukar san Ummynka.”
Kansa ya dauke daga inda take ya cigaba da tukinsa.
Tana san sanar dashi matsalar Ummy sai dai tana tsoro.......
#Oneluv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*34*
Yana tafe yana tunanin kalaman Abba har suka iso gida, parking yai sannan ya maida kansa ya kwantar a jikin motar.
Jalila ta fita daga cikin motar, sannan ta juyo ta kalleshi, ganinsa tai bashida alamar ma fita.
Komawa tai cikin motar ta zauna tace "Yaya! Bazaka shiga ba?"
Bai kalleta ba bashi kuma da alamar bata amsa, Jalila ta kalleshi tace "Yaya?"
Idanunsa ya bude ya kalleta yace "Nikam bakinki baya shiru ne?"
Kallansa tai ta rufe bakinta da labanta, yace " jeki, ko dole sai tare zamu shiga?"
Jalila ta juya jiki a sanyaye, tana shiga nurse din ta tareta tace “ina yayan naki?”
Jalila ta kalleta tace “a ina Goggon take?”
Nan tai gaba Jalila ta bita a baya.
Goggo na zaune akan gado, ba laifi kafar tata ta samu sauki sosai, tana shiga tai gunta da gudu ta rungumeta ta saki wani irin kuka.
Ita ma Goggon kuka ta saka, sun dade a haka kafin Goggon ta daure tace “Jalila ina kika shiga?”
Jalila ta dago ta zauna kusa da ita tace Goggo na.
Goggo tasa hannu ta share mata kwalla tace “ kukan ya isa hakanan, me ya faru? Ko jikin naki ne?”
Jalila ta kalleta tana girgiza kai tace “ba komai Goggo na, ya jikin naki?”
Goggo ta kalleta kallon tuhuma tace “Jalila kin tabbatar? Dan nikam tsoron mutanen nan nakeyi.”
Hassan har ya fara tafiya naga yayi kwana da motarsa ya dawo asibitin, bude kofar motarsa yai ya fito sannan ya nufi asibitin.
Nurse din tana ganinshi ta taho inda yake, tace “ ka dawo?”
Hassan yace tana ina? Nan Nurse din ta fara tafiya yana binta a baya.
Suna taka steps din gaba daya kawai takawa yake, suna zuwa second floor yaji kansa ya fara juyawa, da sauri ya rike bango, sannan ya tsaya ya rike gefen zuciyarsa.
Wani irin numfashi yake fitarwa, juyawa yai da sauri ya sauka kasa, nurse din ta juyo kawai taga bayanan.
Hassan ya sauka da sauri ya shiga mota ya ja ya rufe ya fita da gudu.
Sai da yai nisa sannan yai parkin ya kifa kansa akan sityarin motar yana maida numfashi.
Jalila tai murmushi tace “Allah Goggo ba komai, kawai dai ina bakin cikin laifin dana miki ne.”
Goggo tace “laifi?”
Jalila ta kwantar da kanta akan cinyarta tace “ ni dai ki yafemin Goggo na.”
Goggo ta shafi kanta tace “ba abinda kika min Jalila, na tabbatar ko da kin min ba daidai ba sai dai a rashin saninki ko kuma tirsasaki akai, kawai dai inaso kisan ke kadai ce dani a duniya”
Jalila ta share kwallar data gangaro mata tace “ tsoron sanar dake nakeyi.”
Goggo tace “ko menene ki fadamin.”
Jalila tai shiru can tace “zan fada miki amma sai kin warke an sallameki.”
Goggo tai murmushi tace “ shikenan, da alama akan Sagir ne.”
Jalila tai murmushin yake batace komai ba.
Haka ta zauna makale da Goggonta, Lantana na gefe tana kallansu gwanin sha’awa.
*************
Su Hassan na fita Inna ta matso kusa da Dady ta daga hannu ta sharara mai wani wawan mari, da sauri ya kalleta dan sam baiyi zatan abinda zatamai ba kenan.
Mumy ta matso da sauri ta tsaya agan Inna tace “ Inna menene hakan?”
Inna cikin takaici tace “Uban wa yace ka fadi inda take?”
Dady ya kalleta ransa a bace takaicinsa agaban Yasmeen dan wulakanci.
Mumy ta kalleta tace “Ta ya bazai fada ba bayan yaran yasan komai, da alama Jalila ta gama sanar dashi duk abinda ke faruwa?”
Inna cikin kunar rai ta zauna akan kujera tace “Akace bashi da hankali?”
Mumy ta zauna kusa da ita tace “dama
Bakiyi bincike ba?”
Inna tai shiru kafin tace “ muna cikin tashin hankali, idanun yaran nan ba tsoro ko fargaba a ciki sannan da alama baya ragama wanda ya tabashi, me kuke tunanin zai faru in yasan abinda akama matarsa? Sannan canjen da mukai muka bashi Jalila a maimakon Safeena?”
Mumy ta kalli Dady tace “Dadyn Yasmeen!”
Dady ya kalli Inna wacce ke kallansa yace “ hakan bazai faru ba, ni da kaina zan sanar da ita karta kuskura ta sanar dashi komai, kuskuren sanar dashi Mahaifiyarta datai ya isa.”
Inna ta jinjina kai tace “u have to take care of her, in ba haka ba ni zan bulo mata ta bayan gida, zan sata dana sanin da bata gaba yi ba daga ita har uwarta.”
Dady yace “insha Allahu baza’a sake ba.”
Mikewa tai ta hau sama.
Tana tafiya ya mike a zuciyd ya shiga dakinsu.
Mumy ta bishi da sauri tare da rungumeshi ta baya tace “Darling.”
Hannunsa ya zare yace “meye hakan? Kina abu kamar yarinya?”
Ta kara kankameshi tace “Dadyn Yasmeen am sry.......”
Kallanta yai kamar zaiyi fada, da sauri ta sumbaceshi...........
*************
Ummy ce ta kalleshi tace “ ina zakaje da har kake san in wakilceka akan taron da yake da mahimmanci?”
Yace “Abuja zan koma dan akwai abu mai mahimmanci da nake sanyi.”
Ummy ta kalleshi tace “yafi wannan mahimmanci?”
Abba yai shiru yana duba abu a computer sa.
Ummy tace “ ni na kasa gane abinda bazaka iya fadamin ba”
Cikin zafin rai yace “wai meke damunki ne? Dolene ko wani abu na rayuwarta sai na sanar miki?”
Da karfi ya budo kofar wanda ya sa suka kalli kofar a tare, kallan Abba ya shiga yi idanunsa sun canza sosai.
Yanda yake kallan Abban ne yasa Ummy ta matso da sauri ta sa hannu ta riko hannunsa tace “Hassan meye hakan? Taya zaka banko kofa haka bako sallama?”
Idanunsa na kan Abba haryanzu wanda gaba daya Abba ya gama shan jinin jikinsa.
Hassan ya daure yace “mekenan?”
Ummy tace “ mekenan kamar ya?”
Hassan bai kalli Ummy ba idanunsa nakan Abba yace “me Ummy tai da har kake mata fada haka?”
Ummy tasa hannu da karfi ta turashi waje sannan ta fito itama, ta rufo kofar sannan ta kalleshi tace “muje.”
Ta fada tana jan hannunsa, dakyar ya hau saman sannan ya kalleta cikin takaici yace “Ummy me kika mai yake fada haka?”
Tace “ ba abinda yamin nice namai lefi shiyasa yakemin fada akan abinda nai.”
Kallan ta yai dan shikam bai yarda ba, to ko laifin ma tamai taya zai hauta da fada haka? Ummy ta kalleshi tace “Ina Jalilan?”
Yace “Ummy kin tabbatar ba abinda ya miki?”
Tace “sau nawa kake so na fada ne? Ina tambayarka Jalila, badai ajiye ta kai a hanya ba?”
Yace “Tana nan, kawai ya wuce dakinsa.”
Zama yai a bakin gado yana tunani, dolene ko wani abu na rayuwata sai na sanar miki?
Kallaman Abba ne ya sake dawo mai, meke faruwa?
Ummy tana sauka ta koma dakin, Abba ya kalleta yace “me kika cemai? Tace “ kome nacemai bana tunanin nima ya zama dole in sanar dakai.”
Abba ya matso kusa da ita yace “Ciwon sa fa? Ya tashi?”
Ummy ta kalleshi tace “ kaje ka duba.”
Ta matsa daga kusa dashi.
Abba yai shiru yana tunani sannan ya koma ya zauna agefen gado.
***********
Bayan magrib yana zaune yana karatu, naga ya rufe littafin ya sauko zuwa mota.
Kallo daya zakamai ka fahimci yana cikin bacin rai tsantsa.
A asibitin yai parking sannan ya fito, duk yanda yaso ya duba Nurse din a reception din bai ganta ba.
Kawai komawa yai mota ya zauna, ya kwantar da kansa akan kujera.
Jalila kam sunata hira da Goggo taga isha’i tayi.
Wayarta ta dauko tana dubawa ko zai kirata, ta ina zai kirata? Bayan bashi da numberta? Itama haka.
Ajiyar zuciya tai sannan ta ajiye wayar.
Goggo ta dau wayar tana kara kallo tace “gaskiya wayar nan tayi kyau ta birgeni, mahaifiyar Sagir ce?”
Tace “Hmm.”
Goggo tai murmushi tace “ karki damu ina warkewa zansa ya turo ai auran.”
Wani film akeyi a tv dake dakin, saurayin ta na waje yana ta jiranta ita kuma bata sani ba tana cikin gida suna ta hirar su
Mikewa tai ta dau hijab dinta tace “Goggo ina zuwa.”
Ta fito, tana tafe tana cewa kai inaa.... ta ya zai zauna jirana? Au ko bai san inda nake ba na tabbatar zai sa a nemi ni.
Tana fitowa kawai ta hango motarsa, mamakinne ya kamata ta karaso gun motar a ranta tana cewa “ kai.... ba shi bane, kanta tasa tana leka motar.”
Hassan na kwance ya bude idanunsa, gani yai ana leko cikin motar, tunda akwai haske fitulun waje.
Hassan ya zuge glass din motar yace “ meye hakan?”
Tace “kai!!!! Kaine da gaske, me kake anan?”
Yace “ me nake kuwa, bakisan wannan shine hubby dina ba?”
Tace “zama a mota?”
Bai tanka mata ba yace “ muje?”
Tace “bari nama Goggo salama, Yaya bazaka shiga ba?”
Kansa ya kawar gefe.
Ta fita ta ma su Goggon salama, goggo ta bita da kallo tana tunanin tabbas akwai wani abun, Jalila bazata taba zuwa ta tafi a aranar ba.
Jalila ta shiga mota ya tada suka fara tafiya, yanda taga yanayin fuskarsa ne yasa tai shiru dan taga ba alamar wasa.
Can ta kasa daurewa tace “Yaya nagode.”
Bai kalleta ba yace “ 4 wat?”
Tace “ taimakon da kamin.”
Shiru sukai sai tafiya kawai da yakeyi, can tai murmushi cikin sanyin murya tace “ at first tsoronka nakeyi, later sai na fara fahimtar ka, yau kuma na ga wani side naka na daban.”
Hassan bai kulata ba sai da aka dade yace “ kina tunanin adan karamin kwanakin da mukai ne kike tunanin kin fara sanina?”
Tai murmushi tace “a’a bansanka ba, sai dai na fahimci abu daya.”
Juyowa yai ya kalleta, yana jiran abinda zatace.
A ranta tace u are kind, amma a fili dariya tai tace “na fahimci kana matukar san Ummynka.”
Kansa ya dauke daga inda take ya cigaba da tukinsa.
Tana san sanar dashi matsalar Ummy sai dai tana tsoro.......
#Oneluv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*34*
Yana tafe yana tunanin kalaman Abba har suka iso gida, parking yai sannan ya maida kansa ya kwantar a jikin motar.
Jalila ta fita daga cikin motar, sannan ta juyo ta kalleshi, ganinsa tai bashida alamar ma fita.
Komawa tai cikin motar ta zauna tace "Yaya! Bazaka shiga ba?"
Bai kalleta ba bashi kuma da alamar bata amsa, Jalila ta kalleshi tace "Yaya?"
Idanunsa ya bude ya kalleta yace "Nikam bakinki baya shiru ne?"
Kallansa tai ta rufe bakinta da labanta, yace " jeki, ko dole sai tare zamu shiga?"