← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 53

Sashe 15

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

  Goggo cikin fada tacigaba " me ka mata a matsayinka na ubanta? Me ka mata?"
Dady shim ya kasa magana dan bai taba ganin tana fada haka ba.

  Goggo fa mike da kyar idanunta sun canza tace " duk abinda kuke ma tunanin ku ajiye dan wlh ba wanda ya isa ya yima Jalila auren dole."

  Juyawar da zatai taji wani jiri na debanta, kan kace me tayi baya luuuu jikake tim ta fadi a kasa.

  Da sauri suka mike suna jijigata.

Jalila wacce ta shiga bangarensu da gudu taga ba Goggo jakarta ta cilar a dakin sannani ta fito ta nufi bangarensu Mumy dan tambayarsu,ganin Goggo a kasa su Dady da Mumy na kanta yasa ta karasa da gudu jikinta na bari.

#ONELUV💕
[08/10, 02:02] ‪+234 803 222 1758‬: 🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

(_D home of expert and perfect writer's_💡)

*No 14*

  Dady a rikice ya nufi daki ya dauko key din mota ganin yanda Goggo take a kwance ga Jalila sai wani irin kuka takeyi.
Jiyai ance "ABUBAKAR."
Tsayawa yai sannan ya juyo ya kalli Inna, kallansa tai tace "ina zaka?"
Yace "Asibiti."
Tace "dawo ka zauna."
Tsayawa yai yana kallan Goggo sannan ya kalli Inna.

Mumy ce ta kalli Inna tace "Inna kingafa......"
Kallan data mata ne yasa ta yin shiru, Jalila a rikice ta jawo gwiwarta ta iso inda Inna take tace "Inna dan Allah ki bar Dady ya kai Goggo asibiti, duk da bansan me ya hadaku da Goggo ba har take nan bangaren sai dai na rokeki da ki yi hakuri."
Hannunta ta hada guri daga tana ta murzasu tana kuka alamar tsantsar neman taimako.

Ganin Inna batada niyyar kulata yasa ta ja gwiwa zuwa gun Dady ta rike kafaraa tace "Dady ka taimaka dan Allah, karka manta Goggo matarka ce, sannan mahaifiyatace."

  Gani tai Dady ya kalli Inna, hankalin Jalila ne ya kara tashi ta matso kusa da Mumy ta rike gwiwowinta tace "Mumy ki taimaka min, bazan sake yima Safeena laifi ba, sannan zan cigaba da yi muku aiki, dan Allah ku taimakeni ku kai Goggo Asibiti."

  Muryar Inna ce ta katseta da cewa " kinaso a ceci ran mahaifiyarki?"
Jalila a rikice tana kuka shabe shabe ta shiga daga kai ba kakautawa, Inna tace " akwai hanya daya mafi sauki, wanda in kika amince da ita bama kaita asibiti ba hatta kula da ita zamu samo wanda zai dinga yi, sannan asibiti duk tsadarsa zamu kaita indai zata samu lafiya."

  Jalila a rikice tace "ko me kukeso ku fada zanyi dan Allah."

Inna tace "ki amince da auran da Mahaifinki zai miki."

Gabanta ne ya fadi ta kalli Dady idanunta jagab da hawaye, yana ganin sun hada ido ya juyar da kansa gefe.
Jalila tace "ban gane ba Inna."
Inna tace "in baki gane ba sai ki bar Goggon taki ta karasa rayuwarta anan."

  Wani irin fitar da numfashi da Goggo tai shi yasa Jalila rikicewa ta karasa gunta da gudu tana kuka.
  Inna tace "kina tunani ne akan maganar? Ashe baki dauki ran mahaifiyarki da daraja ba kenan tunda kina tunanin yanda zakiyi tsakanin lafiyarta da farincikin ki."

  Jalila ta kalleta tana kuka tace "ko ma dawa zaku hadani na amince ni dai dan Allah ku kai Goggo asibiti."
Inna tace "yanzu kikai magana, Abbakar kai Mahaifiyarta asibiti, sannan ki sani gobe za'a kawo lefenki da sa rana."

  Jalila kam kuka kawai takeyi, haka Dady da Mumy sukasa Goggo a mota Jalila ta shiga baya suka fita.

Asibitin Standard sukai parking, Jalila kam banda kuka ba abinda takeyi, ana shiga da Goggo nurse ta nufi office din likita dan sanar da ita halin da Goggo take ciki.

  Jalila na zaune a kasan beni kuka kawai takeyi tana addu'ar samun lafiya ga mahaifiyarta.

Dady na zaune shida Mumy, sunyi shiru suma.
Sai da suka samu da taimakon Allah numfashinta ya daidaita sannan suka shiga yi mata gwaje gwaje.

  Sai da suka gama sannan suka fito aka kira Dady.
Likitan ce kalleshi tace "wani maganin hypertension take amfani dashi?"
Yace "hypertension?"
Tace "kanaso kacemin bakusan tanada shi ba?"
Dady ya girgiza kai alamar rashin sani, tace "diabetes fa?"
Dady yai shiru nan ma.

Tace " menene tsakaninka da ita?"
Kunya tasa yace "yar uwatace."
Cikin rashin jin dadi tace "wannan wani irin abu ne? Batada miji ne? Ko kuwa neman kasheta yakeyi?"

  Dady yai shiru, tamai bayanin ciwon ta wanda ya riga ya ci jikinta sosai, tace " ta ya za'ayi ku bari diabetes har yai nisa ya ci kafarta?"
Dady yace "ai mun dauka ciwon kafa ne na girma."
Tace "ko ciwon kafa ne na girma ai kwa gwada zuwa asibiti, da kunzo da wuri ai za'a sanar daku ba shi bane." Sosai ta nuna masa laifinsu sannan ta bashi takardar magunguna tace yaje pharmacy dinsu.

  Jalila na zaune kusa da Goggo tana kuka, ko mayafi babu a jikinta dan kwalli ne kawai a kanta.

  Dady sai da ya gama biyan kudin komai sannan ya shigo dakin, Jalila ce ta kalleshi batace komai ba.
Dady yace "ya jikin nata?"
Kasa amsa mai tai dan gaba daya yau tana tir da kasancewa  uba a gareta.
Duk wani mutum mai imani bataji zai yiwa matarsa abinda dady ya ma Goggo yau.

  Dady ganin yanda Jalila ta dauke kai daga kansa yasa ya fito.
Mumy ya tadda a zaune yace " mu tafi."
Tace ya jikin nata?"
Bai bata amsa ba ya wuce mota.
Suna shiga ya kalli Mumy yace " yanzu abinda Inna tai dazu ta kyauta?"
Mumy ta riko hannunsa tace "nima banji dadi ba sai dai kafi kowa sanin duk abinda Inna takeyi tanayinsa ne saboda mu, na tabbatar ba a san ranta itama tai haka ba."

Shiru yai baice komai ba yaja motar sukai gaba.

  ******

  Ummy ce take ta buga mai kofar yanaji sai dai ya kasa mikewa ya bude, yana takure a gefen bandaki ya matse kansa da karfe, zufa nata karyomai, jikinsa sai rawa yakeyi.

  Ummy ganin ba alamar budewa yasa ta sauka kasa da sauri tana kwallama Sagir kira.
Sagir na kwance a falon kasa yasa waya a gaba sai gwada number Jalila yakeyi sai dai tai ringing har ta gaji ba'a daukaba.
Jin yanda Ummy ke kiransa yasa ya mike da sauri yana tambayarta Ummy lafiya?

Ummy a rikece ta karaso tace "Hassan."
Yana jin haka ya hau sama da gudu.
Aina'u da Ameera dake zaune suna hira suma suka taso da sauri.

  Ganin buga kofar bazata kara mai komai ba yasa ya shiga dakinsa da sauri ya dauko spire key ya bude.

  Hassan na takure jikinsa sai rawa yakeyi ga wani azabbaben ciwon kai dayake damunsa, Sagir ya karasa da sauri ya rungumeshi, Ummy kam zubewa tai a kasa tana maida nimfashi dan ta tsorata ganin yanzu abin da dan sauki zakaga in ka kwankwasa yana budewa, Aina'u da sauri ta karasa kusa da ita.

  Sagir ya dade yana mai addu'oi samun nutsuwa sannan shima Hassan din ya fara kokarin yi a zuciyarsa.

  Ameera kam kuka kawai takeyi.

  Hassan ya kalli Sagir idansa yai ja, kallan Ummy yai da Ameera dake kuka gaba daya tausayinsu ne ya kamashi sai dai bai nuna a fuskarsa ba, mikewa yai ya zari key din motarsa zai fita.

Ummy ce ta riko hanunsa dayazo wucewa ta kusa da ita, sannan ta kalli su Ameera ta musu alama da su fita.
Suna fita ta kalleshi tace "ina zaka?"
Yace "fita kawai zanyi."
Tace "Hassan sai yaushene zaka dainafita haka kawai?"
Kallanta yai cikin takaicin rayuwarsa yace "To Ummy ya kikeso nai? Nace zan bar garin kin hanani? Sannan ba tun yanzu ba kukasan matsalata sai yaushene zaku daina damuwa in kuka gan ni cikin halin nan? Sai yaushe ne zaku cire abin a ranku ku saba da ganina haka?"

Ummy tace "taya kuwa zamu cire abin a ranmu bayan kaidin jinin mu ne? Damuwar ka itace damuwarmu? Rashin lafiyarka itace tamu?"
Cikin akaici yace "Ummy please, Please na rokeki da ki cire ni a ranki, Please ki manta dani kiyi rayuwarki yanda kikeyinta da."

  Tace " kana jin takaicin yanda nake shiga kunci saboda lalurarka?"
Kallanta yai baice komai ba, tace "in har kanaso inyi rayuwa yanda kakeso to ka amince da abinda na fada ma."

Kallanta yai yace "Ummy wai ta yaya zakuyi tunanin yimin aure cikin wannan halin? Wace macece zata iya zama dani?"
Tace " in har ka amince ai zaka ganta, zakaga wace macecen ce haka dazata iya zama dakai?"

Hassan yai shiru dan kansa har yanzu yana sarawa, yace "naji kiyi duk abinda kike ganin shine daidai."
Ya fada tare da fita daga dakin, da kallo ta bishi dashi cikin tausayawa, dan tasan halin zuciyar danta,  mutum ne mai saukin kai, sai dai tundaga faruwar al'amarin nan ya rikede ya koma haka.

  Hassan na fita ya fizge mota yai gaba.

Jalila kuwa da daddare Driver ya kawo musu abinci, ganin yunwa zataata lahani ne ya sa ta zuba abincin taci.
Goggo ce ta farka daga nannauyan maganin baccin da aka sa mata, kallan Jalila tai sannan ta kalli asibitin, a hankali ta budi baki tace "Jalila!"
Tsame hannunta tai da sauri ta isa guda da ita tace "Goggo! Kin ganeni?"
Da kyar ta mata murmushi tace "Jalila karki kuskura ki yarda da abinda Mahaifinki ke shirin yi miki."

  Jalila ta kalli kasa jiki a sanyaye sannan ta kalli Goggo tace "Goggo abinda kikesan cemin kenan daga farfadowarki?"
Goggo da kyar tace "Karki yarda Jalila, bazan kara bari su cutar dake ba ta hanyar da bazata kare ba, aure ai ba wasa bane."

Jalila tace "to bazan yarda ba yanzu dai ki kwantar da hankalinki kinji?"
Goggo ta daga kai a hankali, wani baccin ne ya kara yin gaba da ita.........

#ONELUV💕
[08/10, 02:05] ‪+234 803 222 1758‬: 🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

  (_D home of expert and perfect writer's_💡)

*No 15*
Chapter 15 · 0% Book details