← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 53

Sashe 25

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ameera tace "matar yaya."
Ummy tace "ya sunanta ita matar yayan?"
Ameera ta kalleta tace "Ja....."
Kallan da Ummy ta mata ne yasa tai saurin cewa "Yaya Jalila."
Ummy tace "me ya faru?"
Sagir ne yai saurin katseta yace "to uwar gulma, ki bari ita Ummyn ta tambayeta da kanta mana."

Ameera ta turo baki, Ummy tace "Sagir ya akai?"
Hannunsa rike da plate din da ya zubo abinci ya zauna akan dinning yana cewa "Wlh nima bansan wacece a asibitin ba Ummy, sai dai yanda hankalinta ya tashi da alama mai mahimmancice a gareta....."

Ummy tace " shikenan, zan tambayeta."

Sagir shiru yai ya kasa ko kai loma d'aya bakinsa, tunawa yai sanda suna zance da Jalila a makaranta yawanci in zatai abu zai ji tace ai Goggo kaza, ai Goggo kaza.

Kallan Ummy yai da sauri yace "Ummy wannan matar data kawo Jalila itace "Mahaifiyarta?"
Ummy tace "eh mana."
Sagir yai shiru can yace "me suke ce mata?"
Ummy tai murmushi tace "ina fa na sani? Dan jarida?"
A tare sukai dariya

^********^

Jalila tayi bacci sosai dan sai azahar ta tashi, Ameera na dakin tana sa kaya sanda Jalila ta farka.
Kallan Agoggo tai sannann ta mike da kyar ta kalli Ameera tace "Dan Allah zanyi alwala."
Ameera tace "ki shiga ga toilet."

Jalila ta mike tai alwala, Tana idar da sallah Ameera tace mata ga abinci nan kici, Jalila tace "banajin yunwa.
Bata sake mata magana ba, ta karasa kwalliyarta dan fita zatai ta fito daga d'akin.

D'akin Ummy ta shiga tana zaune tana ta kiran number Abba, tun safe take ta ringing amma no answer.
Ameera ta shigo tace "Ummy dawa zan kai sakon gidan Aunty Nanan?"
Ummy tace " dama abin gara ne, gashi ba driver a gidan, ki duba ko Sagir nanan."
Har ta juya Ummy tace " yayar taki ta tashi ne?"

Tace "eh tayi sallah ma."

Ummy ta mike ta fito tare da ajiye wayar.
Sama ta hau dan taji alamar dawowar Hassan dazu, dakin ta kwankwasa.
Yana kan sallaya rike da littafin Riyadul Salihin, ajiyewa yai ya bude kofar.
Kallansa tai tace "Hassan ya jikin matar taka?"
Kallanta yai yace "Ummy ni ai banganta ba?"
Tace " baka ganta ba? Tana ina kenan?"
Yace "ina na sani ni ai tun da suka fita ban kara ganinta ba."

Tace "ko?"
Baice komai ba sai kallan mamaki da yake mata, Ummy me take mai haka? A iya saninsa batasan abinda zai bata mai rai, sannan ko magana zatamai a cikin sanyi take mai.
Kallanta yai yace "Ummy na kasa gane me ke faruwa, kince na amince da auran nan na amince ba tare da na musa ba, yanzu kuma gaba daya kin canza."

Kallansa tai, yanayin fuskarta ya canza, abinda bataso dan ta kula in tama Hassan lago lago tabbas yarinyar nan zata kuntata a gunsa.
Tace "Hassan ko kare ne aka baka shi akace ma gashi an baka shi, baka tunanin ya zama hakkinka ka kula dashi? In har kasa hannu ka amsa a iya tunani na dolene ka bashi hakkinsa, Hassan dabba ma kenan, balle dan adam, dan adam din ma mace mai rauni, yarinya karama."

  Kallanta yai baice komai ba, tace " yanzu da ace gidanku daban kenan haka zaka barta har ciwo ya mata illa?"

Hassan ya kalleta yace "ba gaku nan ba,Ummy? Na tabbatar abinda zaku mata ni bazan mata ba."
Tace "Hassan zuciyarka ma ta fara rikidewa?"

Kallanta yai sannan ya kauda kai gefe, tace " a iya sanina yarona mutum ne mai tausayi da kula da abinda yake nasa da wanda ba nashi ba, Hassan yaushe zuciyarka ta fara rikidewa zuwa rashin tausayi?"

   Shiru yai jikinsa yai sanyi bai ce komai ba, tace " na haramta mata kwana a d'akinta, daga ranar jiya Hassan ko me zai faru in ganta a d'akin nan.

Yace "Ummy...."
Tace "zan kulle d'akinta ne ma in tafi da makullin, zan sa Ameera ta dawo da kayan sawarta nan dakin."

Ran Hassan ya baci sai dai bai iya cewa komai ba, yana ji ta juya ta sauka, da kallo ya bitaa sannan yai ajiyar zuciya, dama ba auran ba, azomai da wasu sababbin al'amura shi ya tsana, sanda sukesan yai auran ba acemai komai ba, sai yanzu da yai auran ake san a canza mai rayuwarsa, me yasa basa duba yanayin lalurarsa tana bukatar sirri da kadaicewa?

  Ameera bata samu Sagir ba, tazo ta sanar ma Ummy, ba tare da damuwa ba Ummy tace "a kai gobe, yanzu muje sama."
Tace "Sama kuma?"

Haka suka shiga d'akin Jalila tasa a kwaso kayanta, tayi mamaki sosai dataga duk an d'auke kayan lefen da suka sa mata masu tsadar ciki, sai dai bata nuna ma Ameera wani abu ba, Hassan na jin alamunsu yasan me suke shirinyi.
Fitowa yai ya sauko kasa ransa a bace zai fita.

Jalila ta fito dan neman yarinyar da batasan sunanta ba, tanaso tace mata ta nuna mata inda kayanta suke tanaso ta dauko abu (wanka take sanyi ga batasan inda inners dinta suke ba.)

  Tana fitowa ta nufo falo tana tunanin inda zata ganta, tangamemen falon ta shiga kallo, dan dazu da yake kunya take sannan ba lafiya ce da ita ba ko kai bata daga ba, haka gidan yake? Kallan gidan ta shiga yi shi kuma ya sauko daga sama, san bata kuka dashi ba, shi kuma ransa a bace yake yana san fita.

  Tana tafe shi kuma ya taho da karfinsa ya bigeta, tsoron faduwa yasa ta riko rigarsa suka fadi a tare.

  Zafin faduwar ne yasa tai dan kara kadan, dagowa yai ya kalleta, itama kallansa tai.
Idanunta ne suka fito dan ta ganeshi shine na jiya, wato shine angon nata kenan, kura mata ido yai sosai wanda yasa ta tsarguwa.

A ina ya santa? Kallanta ya sakeyi, sannan ya mike tsaye.
  Haushi ya kamata duk da batajin dadi ai yaci ace ya mata sannu dan ta tabbatar yasan ta bige sosai.
Hararsa tai wanda shi kuma daidai lokacin ya juyo da fuskarsa, hada ido sukai tana harararsa da sauri ta wayance tace "yaji ne ya shigarmin ido?" Wai ita adole bata ma kula dashi ba, magana take da kanta.

  Hassan kallanta yai sannan ya tuno harararnan an masa ita sau biyu, har ya juya sai kuma ya kara juyowa yai ya kalleta dan ya fahimceta sosai, itace takan hanyarnan da wacce ta harareshi a adaidaita.
Oh, a ransa yace mai kuka?

Jalila ma shiru tai tana tunanin faduwarnan, bashakka ta tuno, da sauri ta d'ago ta kalleshi.
Mikewa tai tsaye, tana kokarin mai magana shikuma yai waje.

Da sauri tace " ba kai bane?"
Bai tsaya ba balle tasa ran tanka mata, kara kankance ido tai tana tunani, tabbas shine, wanda ya fadi akan titin nan.
Zata kara magana taga harya fita, da kallo ta bishi sannan ta dan tabe baki tace "ba dai sanda ya kusa kadeni ya sanni ba?"

  Ganin batada amsar tambayarta yasa ta juya tana neman Ameera tare da rike bayanta, dan ta bugu sosai.

  Ummy tasa aka matsar da kayansa bangare guda, sannan aka jerama Jalila nata, hatta kan madubi sai da aka matsar da kayansa akasa nata.

Ameera ta kalleta tace "Ummy kina tunanin Yaya zai  barta kuwa?"

Ummy tai shiru, meye amfanin yi masa auran in basa tare?

Haka suka gama sannan suka sauko.

Jalila kam ganin ba alamar kowa yasa ta koma dakin ta zauna.

**********

  A can gidansu Mumy kuwa, Dady na kwance yayi shiru, Mumy ta shigo dakin, kusa dashi ta zauna ta sakalo hannu ta gefen cikinsa ta rungumeshi tace "Dadyn Yasmeen tunanin me kake?"

  Fuskarta ya shafa yace " Tunanin ki?"
Tace "ban yarda ba, tunanin Jalila kake?"

Yace "A'a why should i?"
Tace "karka boyemin komai plx, sannan kaima kaga gidan Taura ai, kasan daidai mata ne zasu samu zama a irin wannan gidan."

Yai murmushi, tace "yaushe za'a fadawa Goggonta?"

Yace "karki damu, ko ta sani yanzu ba abinda zata iyayi, macece mai hakuri, indai taga yarta cikin farinciki bazata iya cewa komai ba."

Mumy ta jinjina kai, yace "ya gun Safeena?"
Tace "suna Abujan, wai sai gobe zasuje ayi visa din."

Yace "okay."

#OneLuv💕
[08/10, 04:14] ‪+234 803 380 9216‬: 🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

(_D home of expert and perfect writer's_💡)

*25*

Tana zama bata dade ba taji anyi knocking din kofar sannan taji ance "Ameera!"
Gabanta ne ya fadi jin muryar Uncle, wai nan fa gidansu ne ko? Sunanta Ameera dama?
A hankali tace "batanan."
Shiru yai shima kafin yace "Jalila dan bude."

Mikewa tai ta bude kofar ba tare da ta bari idanunsu sun hadu ba.
Sagir ya miko mata ledar dake hannunsa, kallansa tai bata amsa ba sannan batace komai ba.
Kallanta shima yake sannan yace " test din ya fito, shine sukaban magunguna, dama kinada typoid ne?"

Bata amsa mai ba ta amshi ledar ta bude, bayan magani taga yoghurt da exotic a kasa, zare ledar maganin tai sannan ta mikamai ledar kasan wanda ke dauke da yoghurt din.
Kallanta ya sake yi sannan yace "kinsan wasu basa san shan magani da ruwa shiyasa....."

Kallansa tai kamar zatai magana sai ta fasa, tace " Ameeran bansan inda tai ba."

  Juyawa tai tana neman rufe kofar, hannu yasa da sauri ya rike kofar, juyowa tai ta kalleshi idanunta sun canza suna neman yin kuka.
Yace "Jalila wacece dazu a asibiti?"
Tace " me kake so ka sani?"
Yace "Kina nufin haka zamu zauna ko magana bakyasan ta hadamu?"
Kallansa tai zuciyarta na kuna, sannan ta juya da sauri ta banko kofar.
Hannu tasa ta rufe fuskarta saboda bakin ciki, wasu hawaye ne suka gangaro mata, ba santa yake ba, ta tabbatar yanzu kila kawai tausayin halin da ya ganta yakeyi.

  Sagir tsayawa yai ajikin kofar tare da kurama kofar ido kamar tana gun, sannan ya juya jiki a sanyaye.
Yana neman fita yaji Ameera nacewa "Ya Sagir!"
Chapter 25 · 0% Book details