Sashe 12
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummy har ta sa hannu zata kwankwasa kofar Hassan sai kuma naga ta sauke hannunta sannan ta bi kofar da kallo, juyawa tai jiki a sanyaye tana neman sauka.
Sagir ne ya fito daga dakinsa, kallan Ummy yai sannan ya matso gunta, yace "Ummy menene?"
Tace " Sagir ashe kana ciki?"
Ya kalli shima kofar Hassan sannan yace "Ummy in koma dakin yaya ta karfi?"
Harararsa tai na wasa tace "kana tunanin zai barka ne?"
Yace "sai in zauna ta karfi ince bazan fita ba."
Ummy tai murmushi tace "karka damu insha Allah na kusa samun mai tayashi kwana."
Cikin zumudi yace "haba?wanene?"
Ummy ta fara sauka daga matatakalar tana cewa " watace."
Sagir cikin mamaki yace " Aure?"
Nan ta shiga bashi labarin abinda ke faruwa sannan ta daura da cewa " Sagir ni na rasa me yasa tunda na ga yarinyar nan nakeji kamar akwai alamun tauye hakki acikin wannan lamarin."
Sagir yace "ba wani tauye hakki Ummy, na farko Yaya ba mahaukaci bane, ba kuma nakasashe bane, sannan a zamanin da ai mace ma ance ba sanin wanda zata aura take ba har sai anyi mata auren."
Kallansa tai tace " hakane nima dan Abbanku sai da aka gama komai na ganshi."
Tana fada tana dariya.
Yace "kinji ma ko? Wow Ummy harna kosa naga yarinyar, tunda ta kwanta miki ma tabbatar yarinyar ta gaske ce."
Ummy tace "kai sai yaushe zaka nunamin taka budurwar?"
Yace "nan gaba kadan nafisan ne sai mun rabu ta gama makaranta sai na fara zuwa gidansu a matsayin saurayinta ba malami ba, kinga sai na kawo miki ita kiganta."
Ummy tai murmushi tace "babban burina a duniyarnan bai wuce abubuwa uku ba Sagir, na farko naga yayanka ya warke ya dawo kamar da, na biyu naga ya samu macen da zata kula dashi na uku kuma na ganka kaima da matar da kakeso kuna rayuwar farin ciki."
Sagir yai murmushin jin dadi yace "insha Allah Ummy duka burikan nan naki zasu cika ba da dadewa ba."
Haka suka sauko kasa suna hira.
*****
Kansa yaji yamai gingirin gim, gaba daya dakin yamai zafi, mikewa yai ya fito daga d'akin ya sauko kasa.
Yana jin muryar Ummy dasu Ameera a kitchen, waje yai ya fada motarsa yai waje...........
Wani irin farinciki kwanan nan takeji, ga gida yanzu ana santa sosai, ga tsananin soyayya dake kara shiga tsakaninta da Sagir, jiya suka gama waec zasu fara neco, shine yau ta fita da kanta ta hau mota tace gidansu Zarah ta amso aran wasu litattafanta.
Tana zaune cikin adaidaita tana murmushi suka dan tsaya saboda dan karamin go slow dake gun, gefenta ta kalla motarsa ce a gun, kallan motar tai sannan tai dan tsaki tace " irin motar wannan dan iskan."
Kallan motar ta sakeyi sannan, da yake motar mai tint ce sannan bata ganshi ba a wancan ranar shiyasa bazata iya ganewa ba.
Sa'a akai ya juyo da fuskarsa inda take, kawai ya hangota tana murguda baki da hararar motar, mamaki ya kamashi dan ya tabbatar bata ganinsa bare tace wani abin ya mata.
Har ya dauke idanunsa sai ya kara juyawa, baki ta kara tabewa sannan ta juya kanta tana yan guna guni, kai ya girgiza sannan ya juya fuskarsa.
Jalila tana dan masifa tana cewa ai indai na kama mutumin nan ko ban mai komai ba sai na harareshi irin taimakon nan ma bai iya ba, ba kunya ranar ya mata rashin mutunci.
Hassan kam gaba yai ya tafi can inda ya saba zama, ya kashe motar sannan ya kwantar da kansa a jikin kujera tare da kunna karatun al-qur'ani, kira'ar Malam Abdullahi Abba ne ya zagaye cikin motar.
Jalila an samu jin dadi, yanzu kayanta kala kala, sannan haka zata zauna wani sa'in a falo itafa Yasmeen suyi ta kallansu, duk sanda suke kallan india in ana soyayya itada Sagir dinta kawai take hangowa, ba shakka bata san sanda san Sagir yai nisa a zuciyarta ba.
Goggo najin dadin yanda Jalila yanzu ta murmure duk da ba kiba tai ba amma inka ganta zakaga ba wahala a jikinta.
A kasan zuciyar Goggo har yau hankalinta ya kasa kwanciya da yanda su Mumy da Dady ke jan Jalila a jiki, sai dai duk sanda Goggo ta nemi Jalila data rage zuwa gunsu Jalila sai tace "Goggo Allah ba abinda sukemin sai mutunci."
Jalila an dage sosai ana ta karatun Neco saboda Sagir yace tai karatu sosai dan yanasan yaga matarsa ta cigaba da karatu.
Duk sanda yai wannan maganar sai Jalila ta sunkuyar da kai wai ita kunya, sai dai a kasan ranta wani dadi take ji.
Goggo har ta gaji da labarin Sagir dan kusan kullum sai ta mata tadin shi.
Su kuwa a bangaren su Inner company ya kara habaka saboda sun samu kudi sosai a gun Taura, yanzu company din ma yafi da karfi.
Su uku suke tsara abin biki dan har kayan daki sun fara siya, Safeena kuma suna ta shirye shiryen kaita Egypt wai ta cigaba da karatunta.
Sai dai ni nasan suna kokarin fita da ita ne dan karma a san da zamanta har sai anyi auren.
A can gidan su Ummy kuwa, suma ita da Ameera da Aina'u suna zuwa siyayyar kayan lefe, sanda Aunty nana taji zancen nan har gida tazo tacema Ummy wai tayi dabara ai gwara da suka nemarmai mata ta kudi wai sai yafi daraja.
Sanda tai maganar nan Ummy bata tanka ba dan haryau kalaman Aunty Nana na mata ciwo.
Yau suke zane paper karshe ta neco, suna fitowa suka hau ihon gama makaranta.
Jalila ma zaune itada Zarah a can gefe, Zarah tace "Jalila ni tun jiya nakesan fada miki wani abu."
Jalila tace "menene? Fada kukai da Nasir?"
Zarah ta juyo saitin Jalila sosai tace "Jalila tsoron abinda na aikata nakeyi."
Jalila ta mata kallan tuhuma.
Zarah tace "Jalila jiya Nasir ya sani yin abinda na ke ta tsoro."
Jalila tace " me ya saki yi?"
Idanun Zarah ne suka canza suka ciciko da kwalla tace "Jalila jiya muna tare da Nasir kinsan in zaizo kasan layinmu yake tsayawa sai ni kuma naje saboda tsoron kar yayana ya ganmu, jiya sai na ganshi a mota sai yake cemin motar babansa ce aka aikeshi, bayan mun gama hirarmu a cikin mota zai tafi sai cemin yai wai sai na mai kiss."
Jalila cikin tsantsar mamaki tace "kiss?"
Zarah ta runtse ido cikin dana sani tace "Jalila kinsan yanda nake tsananin san Nasir ganin ransa ya baci dana tsaya ina tunani yasa na matso kusa dashi na sumbaceshi a kunci, shine yace shi sai na mai a baki, nan na kai bakina saitin bakinsa shine ya rikoni ya dinga tsotsar leb'ena bansan sanda na bude mai cikin bakina ba, Jalila bansan ya akai ba na kasa kwacewa sai bashi hadin kai danai, dakyar na kwavi zuciyata na fizge jikina da sauri na fito daga motar nai gida da gudu........."
Kuka ne ya zo mata wanda yasa ta kasa karasa abinda takesan fada, Jalila kam sam tama kasa magana sai inalilahi kawai da take cewa........
Ganin yanda Zarah ke kuka yasa Jalila ta riko hannunta tace "Zarah it's okay! Kinyi laifi babba ma kuwa sai dai tunda harkin fahimci kinyi laifi sai ki nemi yafiya a gun Allah ki kuma kiyayi aikata makamancin abinda kika aikata."
Zarah ta rungume Jalila tana kuka, Jalila tace "Sai dai magana daya zan fada miki gaskiya ki bincike san da Nasir yake miki, so ne ko sha'awa, in so ne sai ku tuba ga Allah ku nemi kariya daga shedan in kusa sha'awa ne sai kisan zaman da zakiyi dashi."
(_Gareku 'yan mata da samari masu irin wannan soyayyar, sai kaga saurayi yazo gun budurwa in zai tafi sai yace sai ta mai kiss ko sai ya rungumeta, ko kuma ya nemi tamai abinda bai kamata ba, wanda ke da kike aikatawa kinsan haramun ne, sannan shi da yake saki shima yasan haramun ne._
_Dan Allah mu guji fadawa halaka saboda wani buri na zuciyar mu, Allah ya mana tsari ya kare mu daga sharrin zuciya_Ameen suma Ameen)
Jalila na zaune itada Zarah tana kara mata fada aka aiko tazo inji Uncle Sagir.
Kallan Zarah tai tace "Zarah ina zuwa."
Zarah tace " Ba sai kin dawo ba dan na san ba ganinki zanyi yanzu ba."
Jalila ta kalleta tace " har kin dago?"
Zarah ta harareta tace " yanda kike nunawa ta ya ya zan kasa ganewa? Ba ni ba na tabbatar yawancin mutane sun sani."
Jalila ta matso tace "da gaske? Ina nunawa a fili?"
Zarah tai dariya tace gashi nan kin rubuta a goshinki da jan biro."
Jalila ta dan daket tace "bansan iskanci."
Zarah tace "daga ke har shi ai kun gama sanar ma mutane dan ni a bakin mutane ma na fara ji."
Jalila ta dan shagwabe fuska tace " kice kowa kallona kawai yakeyi?"
Zarah tace "ah to mu ai yan kallo ne."
Jalila ta rufe fuskarta tace "bari in rufe fuska ta inje a haka."
Zarah tai dariya tana cewa " u are so Naive."
Jalila tana ta wani nuku nuku a haka har ta fita dan dama jiya ma a waje suka hadu gaban makarantarsu kadan, wani dan lungu.
Sai data dan laleka kafin ta gangara wai ita a dole batasan a ganta.
Sagir na kallanta yana murmushi har ta karaso, yace " me kike ta lekawa?"
Tace "Uncle ya zamuyi? Duk fa ansan menene tsakanin mu."
Yace "to sai akai ya?"
Tace "qx
Yace "nace sai akai ya?"
Tace "hmm hmm"
Murmushi yai yace " kin manta kin gama skul? Sannan ba yaudara ko wasa muke ba balle muce bamasan a sani, ya zakiyi in sukazo auranmu? Ko gidan mu?"
Idanu ta zaro sai kuma ta rufe idanta da sauri, yace "oh ni wai sai yaushe ne za'a daina min kunyar nan?"
Sauke hannu tai tace "ni in kai wata maganar ne sai naji kunya ta kamani."
Yace "to da alama zan tattara maganganun dake cina sai munyi aure."
Murmushi tai, sun dade tare kafin tace zata tafi, dan yau ita kadai za'azo dauka tunda Safeena tana gidan kanin Inner tun last week tacan take zuwa makaranta.
********
Sagir ne ya fito daga dakinsa, kallan Ummy yai sannan ya matso gunta, yace "Ummy menene?"
Tace " Sagir ashe kana ciki?"
Ya kalli shima kofar Hassan sannan yace "Ummy in koma dakin yaya ta karfi?"
Harararsa tai na wasa tace "kana tunanin zai barka ne?"
Yace "sai in zauna ta karfi ince bazan fita ba."
Ummy tai murmushi tace "karka damu insha Allah na kusa samun mai tayashi kwana."
Cikin zumudi yace "haba?wanene?"
Ummy ta fara sauka daga matatakalar tana cewa " watace."
Sagir cikin mamaki yace " Aure?"
Nan ta shiga bashi labarin abinda ke faruwa sannan ta daura da cewa " Sagir ni na rasa me yasa tunda na ga yarinyar nan nakeji kamar akwai alamun tauye hakki acikin wannan lamarin."
Sagir yace "ba wani tauye hakki Ummy, na farko Yaya ba mahaukaci bane, ba kuma nakasashe bane, sannan a zamanin da ai mace ma ance ba sanin wanda zata aura take ba har sai anyi mata auren."
Kallansa tai tace " hakane nima dan Abbanku sai da aka gama komai na ganshi."
Tana fada tana dariya.
Yace "kinji ma ko? Wow Ummy harna kosa naga yarinyar, tunda ta kwanta miki ma tabbatar yarinyar ta gaske ce."
Ummy tace "kai sai yaushe zaka nunamin taka budurwar?"
Yace "nan gaba kadan nafisan ne sai mun rabu ta gama makaranta sai na fara zuwa gidansu a matsayin saurayinta ba malami ba, kinga sai na kawo miki ita kiganta."
Ummy tai murmushi tace "babban burina a duniyarnan bai wuce abubuwa uku ba Sagir, na farko naga yayanka ya warke ya dawo kamar da, na biyu naga ya samu macen da zata kula dashi na uku kuma na ganka kaima da matar da kakeso kuna rayuwar farin ciki."
Sagir yai murmushin jin dadi yace "insha Allah Ummy duka burikan nan naki zasu cika ba da dadewa ba."
Haka suka sauko kasa suna hira.
*****
Kansa yaji yamai gingirin gim, gaba daya dakin yamai zafi, mikewa yai ya fito daga d'akin ya sauko kasa.
Yana jin muryar Ummy dasu Ameera a kitchen, waje yai ya fada motarsa yai waje...........
Wani irin farinciki kwanan nan takeji, ga gida yanzu ana santa sosai, ga tsananin soyayya dake kara shiga tsakaninta da Sagir, jiya suka gama waec zasu fara neco, shine yau ta fita da kanta ta hau mota tace gidansu Zarah ta amso aran wasu litattafanta.
Tana zaune cikin adaidaita tana murmushi suka dan tsaya saboda dan karamin go slow dake gun, gefenta ta kalla motarsa ce a gun, kallan motar tai sannan tai dan tsaki tace " irin motar wannan dan iskan."
Kallan motar ta sakeyi sannan, da yake motar mai tint ce sannan bata ganshi ba a wancan ranar shiyasa bazata iya ganewa ba.
Sa'a akai ya juyo da fuskarsa inda take, kawai ya hangota tana murguda baki da hararar motar, mamaki ya kamashi dan ya tabbatar bata ganinsa bare tace wani abin ya mata.
Har ya dauke idanunsa sai ya kara juyawa, baki ta kara tabewa sannan ta juya kanta tana yan guna guni, kai ya girgiza sannan ya juya fuskarsa.
Jalila tana dan masifa tana cewa ai indai na kama mutumin nan ko ban mai komai ba sai na harareshi irin taimakon nan ma bai iya ba, ba kunya ranar ya mata rashin mutunci.
Hassan kam gaba yai ya tafi can inda ya saba zama, ya kashe motar sannan ya kwantar da kansa a jikin kujera tare da kunna karatun al-qur'ani, kira'ar Malam Abdullahi Abba ne ya zagaye cikin motar.
Jalila an samu jin dadi, yanzu kayanta kala kala, sannan haka zata zauna wani sa'in a falo itafa Yasmeen suyi ta kallansu, duk sanda suke kallan india in ana soyayya itada Sagir dinta kawai take hangowa, ba shakka bata san sanda san Sagir yai nisa a zuciyarta ba.
Goggo najin dadin yanda Jalila yanzu ta murmure duk da ba kiba tai ba amma inka ganta zakaga ba wahala a jikinta.
A kasan zuciyar Goggo har yau hankalinta ya kasa kwanciya da yanda su Mumy da Dady ke jan Jalila a jiki, sai dai duk sanda Goggo ta nemi Jalila data rage zuwa gunsu Jalila sai tace "Goggo Allah ba abinda sukemin sai mutunci."
Jalila an dage sosai ana ta karatun Neco saboda Sagir yace tai karatu sosai dan yanasan yaga matarsa ta cigaba da karatu.
Duk sanda yai wannan maganar sai Jalila ta sunkuyar da kai wai ita kunya, sai dai a kasan ranta wani dadi take ji.
Goggo har ta gaji da labarin Sagir dan kusan kullum sai ta mata tadin shi.
Su kuwa a bangaren su Inner company ya kara habaka saboda sun samu kudi sosai a gun Taura, yanzu company din ma yafi da karfi.
Su uku suke tsara abin biki dan har kayan daki sun fara siya, Safeena kuma suna ta shirye shiryen kaita Egypt wai ta cigaba da karatunta.
Sai dai ni nasan suna kokarin fita da ita ne dan karma a san da zamanta har sai anyi auren.
A can gidan su Ummy kuwa, suma ita da Ameera da Aina'u suna zuwa siyayyar kayan lefe, sanda Aunty nana taji zancen nan har gida tazo tacema Ummy wai tayi dabara ai gwara da suka nemarmai mata ta kudi wai sai yafi daraja.
Sanda tai maganar nan Ummy bata tanka ba dan haryau kalaman Aunty Nana na mata ciwo.
Yau suke zane paper karshe ta neco, suna fitowa suka hau ihon gama makaranta.
Jalila ma zaune itada Zarah a can gefe, Zarah tace "Jalila ni tun jiya nakesan fada miki wani abu."
Jalila tace "menene? Fada kukai da Nasir?"
Zarah ta juyo saitin Jalila sosai tace "Jalila tsoron abinda na aikata nakeyi."
Jalila ta mata kallan tuhuma.
Zarah tace "Jalila jiya Nasir ya sani yin abinda na ke ta tsoro."
Jalila tace " me ya saki yi?"
Idanun Zarah ne suka canza suka ciciko da kwalla tace "Jalila jiya muna tare da Nasir kinsan in zaizo kasan layinmu yake tsayawa sai ni kuma naje saboda tsoron kar yayana ya ganmu, jiya sai na ganshi a mota sai yake cemin motar babansa ce aka aikeshi, bayan mun gama hirarmu a cikin mota zai tafi sai cemin yai wai sai na mai kiss."
Jalila cikin tsantsar mamaki tace "kiss?"
Zarah ta runtse ido cikin dana sani tace "Jalila kinsan yanda nake tsananin san Nasir ganin ransa ya baci dana tsaya ina tunani yasa na matso kusa dashi na sumbaceshi a kunci, shine yace shi sai na mai a baki, nan na kai bakina saitin bakinsa shine ya rikoni ya dinga tsotsar leb'ena bansan sanda na bude mai cikin bakina ba, Jalila bansan ya akai ba na kasa kwacewa sai bashi hadin kai danai, dakyar na kwavi zuciyata na fizge jikina da sauri na fito daga motar nai gida da gudu........."
Kuka ne ya zo mata wanda yasa ta kasa karasa abinda takesan fada, Jalila kam sam tama kasa magana sai inalilahi kawai da take cewa........
Ganin yanda Zarah ke kuka yasa Jalila ta riko hannunta tace "Zarah it's okay! Kinyi laifi babba ma kuwa sai dai tunda harkin fahimci kinyi laifi sai ki nemi yafiya a gun Allah ki kuma kiyayi aikata makamancin abinda kika aikata."
Zarah ta rungume Jalila tana kuka, Jalila tace "Sai dai magana daya zan fada miki gaskiya ki bincike san da Nasir yake miki, so ne ko sha'awa, in so ne sai ku tuba ga Allah ku nemi kariya daga shedan in kusa sha'awa ne sai kisan zaman da zakiyi dashi."
(_Gareku 'yan mata da samari masu irin wannan soyayyar, sai kaga saurayi yazo gun budurwa in zai tafi sai yace sai ta mai kiss ko sai ya rungumeta, ko kuma ya nemi tamai abinda bai kamata ba, wanda ke da kike aikatawa kinsan haramun ne, sannan shi da yake saki shima yasan haramun ne._
_Dan Allah mu guji fadawa halaka saboda wani buri na zuciyar mu, Allah ya mana tsari ya kare mu daga sharrin zuciya_Ameen suma Ameen)
Jalila na zaune itada Zarah tana kara mata fada aka aiko tazo inji Uncle Sagir.
Kallan Zarah tai tace "Zarah ina zuwa."
Zarah tace " Ba sai kin dawo ba dan na san ba ganinki zanyi yanzu ba."
Jalila ta kalleta tace " har kin dago?"
Zarah ta harareta tace " yanda kike nunawa ta ya ya zan kasa ganewa? Ba ni ba na tabbatar yawancin mutane sun sani."
Jalila ta matso tace "da gaske? Ina nunawa a fili?"
Zarah tai dariya tace gashi nan kin rubuta a goshinki da jan biro."
Jalila ta dan daket tace "bansan iskanci."
Zarah tace "daga ke har shi ai kun gama sanar ma mutane dan ni a bakin mutane ma na fara ji."
Jalila ta dan shagwabe fuska tace " kice kowa kallona kawai yakeyi?"
Zarah tace "ah to mu ai yan kallo ne."
Jalila ta rufe fuskarta tace "bari in rufe fuska ta inje a haka."
Zarah tai dariya tana cewa " u are so Naive."
Jalila tana ta wani nuku nuku a haka har ta fita dan dama jiya ma a waje suka hadu gaban makarantarsu kadan, wani dan lungu.
Sai data dan laleka kafin ta gangara wai ita a dole batasan a ganta.
Sagir na kallanta yana murmushi har ta karaso, yace " me kike ta lekawa?"
Tace "Uncle ya zamuyi? Duk fa ansan menene tsakanin mu."
Yace "to sai akai ya?"
Tace "qx
Yace "nace sai akai ya?"
Tace "hmm hmm"
Murmushi yai yace " kin manta kin gama skul? Sannan ba yaudara ko wasa muke ba balle muce bamasan a sani, ya zakiyi in sukazo auranmu? Ko gidan mu?"
Idanu ta zaro sai kuma ta rufe idanta da sauri, yace "oh ni wai sai yaushe ne za'a daina min kunyar nan?"
Sauke hannu tai tace "ni in kai wata maganar ne sai naji kunya ta kamani."
Yace "to da alama zan tattara maganganun dake cina sai munyi aure."
Murmushi tai, sun dade tare kafin tace zata tafi, dan yau ita kadai za'azo dauka tunda Safeena tana gidan kanin Inner tun last week tacan take zuwa makaranta.
********