Sashe 29
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kasa tsayuwa tai kawai ta tsugunna agun tasa kuka, Sagir ya koma cikin asibitin ya tambayesu, yanda suka fadamai haka suka fada mai, fitowa yai gunta yace ta shiga mota tunda ai sunce wanda ya kawota shine ya dauketa.
Tanaji tace "Dady ne."
Nan suka shiga yaja motar da gudu suka nufi gidansu, basuyi nisa da fara tafiya ba wayar Sagir ta shiga kara, Sagir ya daga tare da cewa "Ummy!"
Ummy tace "Sagir kuyi sauri ku dawo iyayen Jalila da kakarta sunzo."
Yace "gamunan."
Ya juya kan motar yana cewa "jalila iyayenki suna gida."
Hawayenta ta share tace "an fadama wa nene yazo?"
Yace "kawai dai cemin tai iyayenki da ko kakarki ne?"
Jalila tai shiru sai fatan Allah yasa ba wani abin bane ya faru, suna isa gidan ta fita da sauri ko motar bata rufe ba ta nufi cikin gidan.
Da gudu ta shiga, a falo ta taradda Ameera rike da waya tana latsawa.
Jalila ta matso tace "Ameera ina Mumy?"
Kallan ta tai tace "suna sama."
Jalila tai sama da gudu, a falon sana ta taradda Inna, tsayawa tai sannan ta karaso a hankali, tsugunnawa tai ta gaida Inna kafin ta gaida Mumy.
An ajiye musu kayan ciye ciye a gaban su.
Ameera ce ta hawo saman sannan ta mika mata makullin dakinta, Jalila ta mike ta bude dakin sannan tace ku shigo.
Mumy ce ta fara mikewa, Inna kuwa sai data karema falon kallo sannan ta shiga dakin, zama tai tana kallan dakin kafin tace "ina mijin naki?"
Jalila tace "ya fita."
Inna ta kalleta tace "rufe kofar."
Jalila ta mike jiki a sanyaye ta rufe kofar, Inna ta kalleta ta mata alama data matso kusa da ita.
Jalila gabanta sai faduwa yake ta matsa a hankali, ta tsugunna.
Mumy ta kalleta tace "Jalila gun Goggo kika je?"
Ta kalleta sannan tace "eh amma bata asibitin, ance Dady ya dauketa."
Mumy ta kalli inna, Inma ta kalli Jalila tace "ni nasa ya dauketa daga asibitin."
Jalila ta kalleta tace "Inna kikace in na amince da auran nan zaki kula da Goggo?"
Inna ta kalleta tace "hakane."
Jalila tace "kuma....."
Inna tai murmushi tace " ba dai kina tunanin wani abin muka mata ba?"
Jalila a tsorace ta kalleta, Inna tace " kinsanar ma wani a gidan nan Goggo ce ta haifeki?"
Jalila jiki a sanyeye tace "a'a amma......."
Inna tace "Jalila wacece ta haifeki?"
Kallan mamaki ta mata tace "ban gane ba Inna?"
Har yaje zai shiga dakinsa yaji kamar ana magana a dakin Jalila bayan yasan Ummy ta rufe dakin, kuma yaga Ummy da Ameera a kasa.
Hannu yasa kamar zai bude kofar yaji ance "tambayarki nake sannan amsarki nake so naji."
Jalila tace "to ai Inna tambayarki gaba daya na kasa fahimtarta, bangane wanene ya haifeni ba?"
Har ya juya zai tafi dan shi mutum ne da bai damuwa da abinda bai dameshi ba.
Jiyai ance " abinda zamsanar dake inaso ya zama amsarki a duk lokacin da aka tambayeki, daga yau ko waye ya tambayeki mahaifiyarki ki tabbatar kince Mumy ce ta haifeki."
Da sauri Jalila ta kalli kofar, shima da sauri ya kalli kofar, meke faruwa? Shidai a iya saninsa bai taba ji inda ake sanar da d'a mahaifiyarsa ba.
Jalila tace "Bangane Mumy ce ta haifeni ba? Goggon tawa rasuwa tai ko me? Ina kuka boyeta? Ta fada cikin wani yanayi mai ban tausayi wanda yasa Hassan din jingina da bangon jikin kofar.
Inna tace "ko daya, ina dai sanar dake ne hakan shine kadai zaisa mu taimaki mahaifiyarki mu kuma bata rayuwa na gari."
Jalila jitai ta sa wata dariya mai tattare da bakin ciki da kuka, tana hawaye tace " A lokacin da za'amin auran nan kunce in na amince zaku kula da Goggona, sannan bayan na amince yanzu kunce kuma gaba daya ma in canza mahaifiyar datai wahala akai........"
Marin da aka kifa mata ne yasa tai shiru, Inna tace " dan kinyi aure a gidan nan ne yasa kika fara tunanin yin jayayya dani? Ina magana kina magana?"
Haryasa hannu zai bude kofar saboda ransa ya baci sai kuma naga ya tsaya, hannunsa naga ya dunkule sannan a ja baya daga jikin kofar, cikin takaici.
Saboda nine kenan? Saboda iyayena sun nemi auranta yasa har ake neman sata yin haka.
Labansa ya ciza sannan ya bude dakinsa ya shiga, ya rufo kofar da karfinsa na gaske.
Wanda yasa sukaji kara, Inna ta kalli Jalila tace "mijin naki ne?"
Jalila tana hawaye ta daga kai, Inna ta tabe baki a ranta tace hauka yake muraran irin wannan buga kofa haka? Ai kanaji kasan na marasa hankaline.
Maida kallanta tai kan Jalila tace "shawara ya rage naki, inhar kinasan kiga mahaifiyarki kiyi abinda na saki, in kuma bakyaso ki hakura da ganinta ne wannan ya rage naki."
Ta kalli Mumy tace "tashi mu tafi dan ba'a dadewa gidan surukai."
Jalila tana kallansu suka mike gaba daya inbanda hawaye ba abinda takeyi, Inna ta fita daga dakin ta juyo tace "bazaki rakamu ba?"
Jalila ta kallesu, yanda Inna take kallanta ne yasa ta mike ta fito falon.
Tana fitowa shima yana fitowa daga dakin, rufo kofa, fuskarnan tasa a daure kallo daya ya musu ya dauke kansa, yi yai kamar bai ga mutane a gun ba ya wucesu ya sauka.
Inna ta kalleshi sannan ta kalli Jalila bayan ya sauka tace "shine?"
Jalila ta daga kai, Mumy tace "amma yana ganinmi kamar yaga kashi?"
Inna tace "ki mai uzuri......"
Sai kuma tai shiru, kallanta Jalila tai badai sunsan matsalarshi ba? Ai a take tai tunani, haba itadai ta tabbatar da wani abun daga sanda ta iso gidan nan, ta tabbatar Bazasu taba ajiye Safeena su dauketa ba.
Yanda take kallan Mumy ne yasa Inna tace" me kikeyi? Na dauka cewa nai muje ki rakamu."
Zubewa akan gwiwowinta tai tana hawaye tace "Inna dan Allah na rokeki kiyi hakuri, zanyi komai amma dan Allah banda gurbin mahaifiyata."
Inna ta kalli hanyar sama tace" me kike yi hakan? Salan wani ya ganki yace cutar dake mukeyi?"
Jalila ta mike tana matse kwalla, Inna tace "muje."
Haka suka sauko kasa tana bayansu.
Ummy ta fito daga daki tace "har zaku tafi?"
Mumy tace "eh wlh."
Ummy ta kalli Jalila tace "Jalila ana kukan rabuwa ne?"
Jalila ta sunkuyar dakai, Mumy tace " Ga tanan mun barmuku amana."
Amana? Abinda ya darsuna zuciyar Jalila kenan, su basu riketa amana ba shine suke bada ita wai amana?
Ummy taji tace "ai Jalila diyace agurina, insha Allahu yanda zan rike dan cikina haka zan riketa."
Inna tace "mun gode sosai, Allah yabar zumunci, amma Taura fa?"
Ummy tace " yana Abuja yau dai muke sa ransa."
Sannan ta kalli Jalila tace "ki daina kuka dan Allah."
Jalila ta daga kai tana share hawayenta.
Haka suka fito Ummy ta mikoma Jalila leda tace " ki basu."
Jalila ta amsa tama Ummy godiya.
Sai da suka shiga mota sannan tamikama Mumy tace "tace gashi inji Ummy."
Inna ta kalleta tace " ki tabbatar kinji abinda na fada miki."
Jalila batace komai ba har motarsu, ta fita daga gidan, wasu zafafan hawaye ne suka zubo mata.
Komawa cikin gida tai, wucewa dakinta tai kawai ta zauna tana kuka.
Ummy ce ta shigo dakin, itakanta Ummy tun jiya hankalinta ba'a kwance yake ba ta nemi number Abba harta gaji, yanzu kuwa bama ta shiga gaba daya.
Hannun Jalila ta kamo, tace "ya isa haka nan, insha Allahu bazakiyi dana sanin auranki cikin zuri'ata ba, Hassan na cikin wani yanayi ne sai dai ba haka Allah ya halliceshi ba, lalurace ta afkomai shekarun baya da suka wuce wanda muke addu'ar neman mai lafiya, da taimakon ki."
Jalila ta kalli Ummy, Ummy tai murmushi tace "jiya a kasa kika kwana?"
Jalila cikin mamaki tace "ya akai ki...." sai kuma tai shiru, Ummy tai murmushi tace " ya miki magana?"
Jalila tace "hmm amma baifi sau hudu ba."
Tace "Ba laifi dan banyi tunanin ma zai kula ki ba kwata kwata."
Shiru tadanyi kafin ta kara riko hannun Jalila cikin murya mai rauni da tausayi tace "Jalila ki taimakeni."
Jalila ta kalleta jiki a sanyaye, tace "Jalila ki taimakeni gun ceto Hassan daga halin da yake ciki."
Jalila tai shiru sai kallanta da takeyi, Ummy tace "Kiyi hakuri da duk abinda zai miki ma tabbatar wata rana zakiyi mamakin shi"
Jalila ta share kwallarta tace "Insha Allahu Ummy."
Ummy ta jinjina kai cikin jin dadi tace "Jalila nagode sosai, sannan karki bari ya wulakantaki, inya miki ba daidai ba ki fito ki fadamai, hakan ne zaisa ya saki jiki dake."
Jalila tai shiru, Ummy tace "Sannan inaso duk wani abu da kikeso ko ya dameki ki sanar dani, inaso mu zama daya ni dake, yanda na dauki Ameera haka na daukeki, kema inaso ki daukeni a matsayin mahaifiyarki...."
Kalmar mahaifiya itace ta sa jikinta yin sanyi, a ranta tace Goggo kina ina????
Ummy ce ta mike sannan tace " bari naje lokacin abincin rana yayi."
Jalila ta mike da sauri tace "bari inyi abincin Ummy."
Ummy tace "ah hb? Daga yin aure sai girki?"
Jalila tace " dan Allah ki barni nayi."
Ummy tace "muje muyi tare to, dan ina tunani Abbansu yau zai dawo."
Haka suka sauko kasa abin sha'awa, sai dai zuciyar Jalila ciki take da tunani wanda take kokarin nemo ma kanta mafita."
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
_ "There are three constants in life...change, choice and principles." -Stephen Covey_
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*29*
Abba suna shigowa garin kano yacema driver dinsa su wuce gidansa na governor road, driver din yayi mamaki dan Abba ya dade bai ko leka gidan ba, ko yazoma sai dai yai abu minti kadan ya fita.
Yau kam suna isa ya shiga ciki ya kwanta a falonsa, hannunsa yasa asaman goshinsa yana tunani.
Tanaji tace "Dady ne."
Nan suka shiga yaja motar da gudu suka nufi gidansu, basuyi nisa da fara tafiya ba wayar Sagir ta shiga kara, Sagir ya daga tare da cewa "Ummy!"
Ummy tace "Sagir kuyi sauri ku dawo iyayen Jalila da kakarta sunzo."
Yace "gamunan."
Ya juya kan motar yana cewa "jalila iyayenki suna gida."
Hawayenta ta share tace "an fadama wa nene yazo?"
Yace "kawai dai cemin tai iyayenki da ko kakarki ne?"
Jalila tai shiru sai fatan Allah yasa ba wani abin bane ya faru, suna isa gidan ta fita da sauri ko motar bata rufe ba ta nufi cikin gidan.
Da gudu ta shiga, a falo ta taradda Ameera rike da waya tana latsawa.
Jalila ta matso tace "Ameera ina Mumy?"
Kallan ta tai tace "suna sama."
Jalila tai sama da gudu, a falon sana ta taradda Inna, tsayawa tai sannan ta karaso a hankali, tsugunnawa tai ta gaida Inna kafin ta gaida Mumy.
An ajiye musu kayan ciye ciye a gaban su.
Ameera ce ta hawo saman sannan ta mika mata makullin dakinta, Jalila ta mike ta bude dakin sannan tace ku shigo.
Mumy ce ta fara mikewa, Inna kuwa sai data karema falon kallo sannan ta shiga dakin, zama tai tana kallan dakin kafin tace "ina mijin naki?"
Jalila tace "ya fita."
Inna ta kalleta tace "rufe kofar."
Jalila ta mike jiki a sanyaye ta rufe kofar, Inna ta kalleta ta mata alama data matso kusa da ita.
Jalila gabanta sai faduwa yake ta matsa a hankali, ta tsugunna.
Mumy ta kalleta tace "Jalila gun Goggo kika je?"
Ta kalleta sannan tace "eh amma bata asibitin, ance Dady ya dauketa."
Mumy ta kalli inna, Inma ta kalli Jalila tace "ni nasa ya dauketa daga asibitin."
Jalila ta kalleta tace "Inna kikace in na amince da auran nan zaki kula da Goggo?"
Inna ta kalleta tace "hakane."
Jalila tace "kuma....."
Inna tai murmushi tace " ba dai kina tunanin wani abin muka mata ba?"
Jalila a tsorace ta kalleta, Inna tace " kinsanar ma wani a gidan nan Goggo ce ta haifeki?"
Jalila jiki a sanyeye tace "a'a amma......."
Inna tace "Jalila wacece ta haifeki?"
Kallan mamaki ta mata tace "ban gane ba Inna?"
Har yaje zai shiga dakinsa yaji kamar ana magana a dakin Jalila bayan yasan Ummy ta rufe dakin, kuma yaga Ummy da Ameera a kasa.
Hannu yasa kamar zai bude kofar yaji ance "tambayarki nake sannan amsarki nake so naji."
Jalila tace "to ai Inna tambayarki gaba daya na kasa fahimtarta, bangane wanene ya haifeni ba?"
Har ya juya zai tafi dan shi mutum ne da bai damuwa da abinda bai dameshi ba.
Jiyai ance " abinda zamsanar dake inaso ya zama amsarki a duk lokacin da aka tambayeki, daga yau ko waye ya tambayeki mahaifiyarki ki tabbatar kince Mumy ce ta haifeki."
Da sauri Jalila ta kalli kofar, shima da sauri ya kalli kofar, meke faruwa? Shidai a iya saninsa bai taba ji inda ake sanar da d'a mahaifiyarsa ba.
Jalila tace "Bangane Mumy ce ta haifeni ba? Goggon tawa rasuwa tai ko me? Ina kuka boyeta? Ta fada cikin wani yanayi mai ban tausayi wanda yasa Hassan din jingina da bangon jikin kofar.
Inna tace "ko daya, ina dai sanar dake ne hakan shine kadai zaisa mu taimaki mahaifiyarki mu kuma bata rayuwa na gari."
Jalila jitai ta sa wata dariya mai tattare da bakin ciki da kuka, tana hawaye tace " A lokacin da za'amin auran nan kunce in na amince zaku kula da Goggona, sannan bayan na amince yanzu kunce kuma gaba daya ma in canza mahaifiyar datai wahala akai........"
Marin da aka kifa mata ne yasa tai shiru, Inna tace " dan kinyi aure a gidan nan ne yasa kika fara tunanin yin jayayya dani? Ina magana kina magana?"
Haryasa hannu zai bude kofar saboda ransa ya baci sai kuma naga ya tsaya, hannunsa naga ya dunkule sannan a ja baya daga jikin kofar, cikin takaici.
Saboda nine kenan? Saboda iyayena sun nemi auranta yasa har ake neman sata yin haka.
Labansa ya ciza sannan ya bude dakinsa ya shiga, ya rufo kofar da karfinsa na gaske.
Wanda yasa sukaji kara, Inna ta kalli Jalila tace "mijin naki ne?"
Jalila tana hawaye ta daga kai, Inna ta tabe baki a ranta tace hauka yake muraran irin wannan buga kofa haka? Ai kanaji kasan na marasa hankaline.
Maida kallanta tai kan Jalila tace "shawara ya rage naki, inhar kinasan kiga mahaifiyarki kiyi abinda na saki, in kuma bakyaso ki hakura da ganinta ne wannan ya rage naki."
Ta kalli Mumy tace "tashi mu tafi dan ba'a dadewa gidan surukai."
Jalila tana kallansu suka mike gaba daya inbanda hawaye ba abinda takeyi, Inna ta fita daga dakin ta juyo tace "bazaki rakamu ba?"
Jalila ta kallesu, yanda Inna take kallanta ne yasa ta mike ta fito falon.
Tana fitowa shima yana fitowa daga dakin, rufo kofa, fuskarnan tasa a daure kallo daya ya musu ya dauke kansa, yi yai kamar bai ga mutane a gun ba ya wucesu ya sauka.
Inna ta kalleshi sannan ta kalli Jalila bayan ya sauka tace "shine?"
Jalila ta daga kai, Mumy tace "amma yana ganinmi kamar yaga kashi?"
Inna tace "ki mai uzuri......"
Sai kuma tai shiru, kallanta Jalila tai badai sunsan matsalarshi ba? Ai a take tai tunani, haba itadai ta tabbatar da wani abun daga sanda ta iso gidan nan, ta tabbatar Bazasu taba ajiye Safeena su dauketa ba.
Yanda take kallan Mumy ne yasa Inna tace" me kikeyi? Na dauka cewa nai muje ki rakamu."
Zubewa akan gwiwowinta tai tana hawaye tace "Inna dan Allah na rokeki kiyi hakuri, zanyi komai amma dan Allah banda gurbin mahaifiyata."
Inna ta kalli hanyar sama tace" me kike yi hakan? Salan wani ya ganki yace cutar dake mukeyi?"
Jalila ta mike tana matse kwalla, Inna tace "muje."
Haka suka sauko kasa tana bayansu.
Ummy ta fito daga daki tace "har zaku tafi?"
Mumy tace "eh wlh."
Ummy ta kalli Jalila tace "Jalila ana kukan rabuwa ne?"
Jalila ta sunkuyar dakai, Mumy tace " Ga tanan mun barmuku amana."
Amana? Abinda ya darsuna zuciyar Jalila kenan, su basu riketa amana ba shine suke bada ita wai amana?
Ummy taji tace "ai Jalila diyace agurina, insha Allahu yanda zan rike dan cikina haka zan riketa."
Inna tace "mun gode sosai, Allah yabar zumunci, amma Taura fa?"
Ummy tace " yana Abuja yau dai muke sa ransa."
Sannan ta kalli Jalila tace "ki daina kuka dan Allah."
Jalila ta daga kai tana share hawayenta.
Haka suka fito Ummy ta mikoma Jalila leda tace " ki basu."
Jalila ta amsa tama Ummy godiya.
Sai da suka shiga mota sannan tamikama Mumy tace "tace gashi inji Ummy."
Inna ta kalleta tace " ki tabbatar kinji abinda na fada miki."
Jalila batace komai ba har motarsu, ta fita daga gidan, wasu zafafan hawaye ne suka zubo mata.
Komawa cikin gida tai, wucewa dakinta tai kawai ta zauna tana kuka.
Ummy ce ta shigo dakin, itakanta Ummy tun jiya hankalinta ba'a kwance yake ba ta nemi number Abba harta gaji, yanzu kuwa bama ta shiga gaba daya.
Hannun Jalila ta kamo, tace "ya isa haka nan, insha Allahu bazakiyi dana sanin auranki cikin zuri'ata ba, Hassan na cikin wani yanayi ne sai dai ba haka Allah ya halliceshi ba, lalurace ta afkomai shekarun baya da suka wuce wanda muke addu'ar neman mai lafiya, da taimakon ki."
Jalila ta kalli Ummy, Ummy tai murmushi tace "jiya a kasa kika kwana?"
Jalila cikin mamaki tace "ya akai ki...." sai kuma tai shiru, Ummy tai murmushi tace " ya miki magana?"
Jalila tace "hmm amma baifi sau hudu ba."
Tace "Ba laifi dan banyi tunanin ma zai kula ki ba kwata kwata."
Shiru tadanyi kafin ta kara riko hannun Jalila cikin murya mai rauni da tausayi tace "Jalila ki taimakeni."
Jalila ta kalleta jiki a sanyaye, tace "Jalila ki taimakeni gun ceto Hassan daga halin da yake ciki."
Jalila tai shiru sai kallanta da takeyi, Ummy tace "Kiyi hakuri da duk abinda zai miki ma tabbatar wata rana zakiyi mamakin shi"
Jalila ta share kwallarta tace "Insha Allahu Ummy."
Ummy ta jinjina kai cikin jin dadi tace "Jalila nagode sosai, sannan karki bari ya wulakantaki, inya miki ba daidai ba ki fito ki fadamai, hakan ne zaisa ya saki jiki dake."
Jalila tai shiru, Ummy tace "Sannan inaso duk wani abu da kikeso ko ya dameki ki sanar dani, inaso mu zama daya ni dake, yanda na dauki Ameera haka na daukeki, kema inaso ki daukeni a matsayin mahaifiyarki...."
Kalmar mahaifiya itace ta sa jikinta yin sanyi, a ranta tace Goggo kina ina????
Ummy ce ta mike sannan tace " bari naje lokacin abincin rana yayi."
Jalila ta mike da sauri tace "bari inyi abincin Ummy."
Ummy tace "ah hb? Daga yin aure sai girki?"
Jalila tace " dan Allah ki barni nayi."
Ummy tace "muje muyi tare to, dan ina tunani Abbansu yau zai dawo."
Haka suka sauko kasa abin sha'awa, sai dai zuciyar Jalila ciki take da tunani wanda take kokarin nemo ma kanta mafita."
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
_ "There are three constants in life...change, choice and principles." -Stephen Covey_
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*29*
Abba suna shigowa garin kano yacema driver dinsa su wuce gidansa na governor road, driver din yayi mamaki dan Abba ya dade bai ko leka gidan ba, ko yazoma sai dai yai abu minti kadan ya fita.
Yau kam suna isa ya shiga ciki ya kwanta a falonsa, hannunsa yasa asaman goshinsa yana tunani.