← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 53

Sashe 19

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kasa magana tai, hankalinsa ne ya tashi.
Ya shiga tambayarta, can ta daure tace "Uncle yaushe zamu hadu? Akwai maganar da zamuyi dakai."
Yace " ko yanzu ma in kinaso."
Tace "a'a banda yau."
Yace "nima na manta yau zan raka yayana wani gun, gobe fa?"
Tace " to, Allah ya kaimu, zan kiraka goben."
Haka kawai tace ta kashe wayar saboda yanda taji zuciyarta ta karye.
Tana kashewa kuwa tasa kuka.
Shikenan Uncle, soyayyar da muke ma juna ashe anan zata tsaya.........

Sagir na kashe wayar shima yai shiru, tabbas akwai abinda ke damunta......

#Oneluv💕
[08/10, 02:09] ‪+234 803 222 1758‬: 🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

  (_D home of expert and perfect writer's_💡)

*No 18*

   Sake kwanciya tai, ta kwantar da kanta akan katifa, itada take burin auren soyayya? Yanzu me kenan?
Idanunta ta bude a hankali, tana kallan dakinsu, rayuwarsu da mahaifiyarta ne ta shiga dawo mata, rayuwace wacce sukai ta talauci da tsana, sai dai a tsakaninsu rayuwace mai cike da dinbin kewar juna da shakuwa, zata iya rayuwa ba tare da Goggonta ba?
Haka tai ta saka da warwara har bacci yai gaba da ita.

  Sai wajen karfe uku ta farka, shima mafarki ne ya tasheta wanda ya sata razana da sauri, sai dai me? Duk yanda taso ta tuno wani mafarkin tai ta kasa sam, wayarta ta dauka da sauri ta yima Sagir text.
Uncle please mu hadu a makaranta ko na minti goma ne, i really want to talk to you.
Ajiye wayar tai ta mike, gaskiya dole ta sanar ma Uncle abinda ke faruwa taji me zaice.

  Mikewa tai ta kalli kayan da aka kawo mata ta saka, nan tai wanka ta saka ta fito sidif sidif tai waje.
*****

A can gidansu Hassan kuwa, Sai da Ummy ta mai magana ya kimtsa, da kananan kaya ya saka tasashi ya koma ya sako manya kaya.
Fitowa yai daga dakinsa sanye da dakakiyar shad, cyan color wanda mukafi sani da bluegreen, shadar ta mai kyau sosai, dan shi dama bai fiya sa manyan kaya ba, daga kanana sai jallabiya, Abba ne baya gajiya da dinkamai.
Ameera da kanta ta d'aukomai hula ta mikamai.
Hassan kallansu kawai yake dan bayasan magana ya amsa.
Takalmi ya saka sannan ya sauko kasan, Sagir sai janshi yake da tsokana wai kai Yaya gaskiya wannan kyan kamar ranar auranka.

Hassan ko kallansa baiyi ba bare ya tankamai, shima Sagir din manyan kaya ya saka.
Ummy ta jawo Sagir tace "Sagir ka taimaka kar a samu matsala, kasan halin yayan naka."
Sagir ya daga kai yace "Karki damu Ummyna, ki bar komai a wuyana."

Murmushi tai tace "godiya nake dan lele na."
Haka suka fito kowa yana farinciki, Ummy ta mikama Sagir gift din da zasu kai mata.

Aina'u na jikin dakin Ameera tana kallansu, komawa tai cikin dakin ta kwanta ranta ba dadi.

  Motar Hassan suka nufa, Hassan na shiga ya rufo kofa, Sagir ya zagawa ta bangaren kusa da driver yana cew "Yaya na dauka da Mamman zamuje saboda shi yasan gidan.

Jiyai kofar a rufe, cikin mamaki yace "Yaya me kenan?"
Hassan ya zuge glass dinsa yace " ka shiga motar ka Mamman ya jaka, ni daga can wani guri zanje."
Sagir ba tare da tunanin komai ba ya juya ya shiga motar sa shida Mamman.

   Haka suka fita da motoci biyu, su Sagir na baya shi yana gaba.
Suna tafe suna hira sam hankalinsa baikai kan wayarsa ba domin yanzu harkar yayansa ce a gabansa baya tunanin akwai wani abu da zai ratsa wanda zaiyi distracting dinsa.

  A kofar gidan Mamman yasa signal sannan aka bude mai gate ya shiga, maimakon Hassan ya shiga kawai sai yai gaba.

  suna parking Sagir ya juya baiga motar Hassan ba, mamaki ya kamashi da sauri ya fito wajen gidan yana lekawa, sai dai ba shi ba labarinsa.

Haka suma mutanen gidan, dan tun lokacin da Mumy ta aika Jalila tazo ta karasa shiryata, taki zuwa hankalinsu ya tashi, ta fito ta duba bangarensu bata ganta ba.

Hankalinsu yayi tsananin tashi dan sun duba ko ina basu ganta ba, Mumy kam kamar tai ya ya.
Nan Dady ya fito nemanta.

  Can ita kuwa tana tsaye a inda suke haduwa, tana duba agoggo, taji ance bayan la'asar zaizo shiyasa take sauri Uncle yazo suyi magana ta koma kafin hudu da rabi.

  Agoggon hannunta ta kalla, karfe 4:30jiki a sanyaye ta juya, lalai yanzu wata zuciya tana sanar da ita Uncle bai damu da ita sosai ba, wata zuciyar kuma neman yi masa uzuri takeyi.

Haka ta tako jiki a sanyaye ta tsaya akan titi dan neman adaidaita.

Tana tsaye mota tai parkin ta bayanta kadan, kallan motar tai dan ta dauka uncle ne, batai ma tunanin motar waye ba kawai ta nufi motar.
Shikuwa yanda tazo saitinsa ne yasa cikin mamaki yake kallanta.

  Sai dataje jikin kofar sannan tai tunanin ba shi bane, lalai zuciyarta a matse take da san ganin Uncle, baki ta turo sannan ta juya jiki a sanyaye.
Yana zaune a ciki yana kallanta, da yake motar tint ce itakam bata ganshi ba.

Haka ta tsaya a titi zuciyarta duk ba dadi, sai kara leka hanya take ko zata ganshi.

Yana kallanta harta samu mota ta shiga, kai ya girgiza sannan ya kashe motar, yasa kansa akan kujera yana tunani, shikam ta ina zai fara kallan mace da sunan zance? Sannan in tsautsayi yasa matsalarsa ta tashi fa?
shikam hankalinsa ya kasa kwanciya, ya san kuma Sagir zaisan me zaice mata.

  Haka ta samu adaidaita ta hau jiki a sanyaye, ajiyar zuciya taitayi a cikin adaidaitar har suka isa, tana kokarin biyan kudin adaidaitar su kuma suka fito daga cikin gidan.

Motar tabi da kallo, taga mutane biyu a zaune sai dai hankalinta ba'a kansu yake ba.

Haka ta taho a hankali ta tura gate din gidan.

  Mumy ta ganina waje itada Dady suna magana, suna ganinta suka juyo suka zuba mata idanu.

Dady a zuciye ya fara takowa, ganin haka yasata ta tsorata.
Hannu ya daga zai shara mata mari, da sauri ta runtse idanunta, tsayawa yai sannan ya kalleta rai a bace, yatsa ya nuna mata yace "ni zaki cima mutumci?"

Mumy ta matso ta sauke mai hannu tace "Dadyn Yasmeen meye hakan?"
Kallanta yai yace "yanzu da badan shima dalili ya hanashi zuwa ba fa?sannan da kanin nasa bai fahimcemu ba fa?"

Mumy ta kalleshi tace "tunda dai komai yazo da sauki ba shikenan ba?"
Yace "in Inna taji fa? Me kike tunanin za'ace?"
Mumy tace "sai muce mata ta ganshi sun gaisa harya tafi."

Dady ya kalleta cikin jin dadi, wanda baisan  a ranta ba wai damuwa da Jalilan tai ba balle tace batasan a mata fada ne, tayi hakan ne dan abin ya kara karfafa.
Jalila ta kalla sannan tace "Hassan din wani uzuri mai karfi ya tasomai a hanya bayan sun fito, dole ne yasashi kin zuwa, shiyasa ya turo kaninsa.

Jalila ta dan tabe baki kadan, dan itakam ba damuwarta bane.
Mumy ta rike hannunta tace "muje ciki ko?"

Jalila tace "A'a Mumy asibiti zan koma."
Mumy ta jinjina kai tace "bari mu kaiki."

Jalila fuskarta dama a daure take tai bangarensu.
Kayan da Goggo tace ta dauko mata ta dauko sannan ta fito.

Suna tsaye suna ta wani abu wai su a dole mata da miji, ita Mumy sai wani shagwabewa take, haushi ya kara kama Jalila a ranta tace "mutum ya girma amma jinsa yake kamar yaro."
Ta gabansu tazo ta wuce, Mumt ta riko hannunta tace "Jalila tare zamu tafi."
Jalila tai shiru tana kallan Dady.
Mumy ta bude mata baya sannan ta shiga, ita kuma ta shiga kusa da Dady.
A hanya tayi shiru tana kallan waje, wayarta ce ta fara ringing, da sauri ta zarota.

Uncle? Da sauri ta daga tace "Uncle!"

  Jalila i am............
Bata gama jin mai zai fada ba, Dady yai wani irin parking, wanda ya tsoratata, sam ta mantada mutane a motar.

Mumy ta fizgi wayar tana cewa "Jalila me kenan?"

Jalila a tsorace ta kalleta, sunan da ke jiki ta kalla MINE? Nunawa Dady tai ya kashe wayar yace "uban wa ya sai miki waya?"
Idanunta ne suka firfito tai shiru.
Mumy tace "Jalila zance kike a bayan idanun mu?"
Jalila ta kallesu sai dai ta kasa magana, cikin salo Mumy tace "shiyasa take neman bijerawa maganarka kenan? Lalai samarin zamani sun iya siyan zuciya, da har zasusa 'da ya bijirema mahaifinsa."

Dady cikin takaici yace "Uncle? Malamin ku ne kenan? Dama abinda kike a makarantar kenan?"

Jalila da hawaye suka fara zubo mata tai shiru tana kallan ikon Allah.
Dady yace "wato ina miki magana ma kinfi karfin amsawa ko?"
Jalila tace "ba haka bane Dady."
Mumy tace " Jalila yaushe kika zama haka?" 

Jalila jitai hawaye suna gudu a idanunta, wannan shine a dakeka a kuma hanaka kuka.

Haka tana kallo Dady ya zare sim din ya karyashi sannan ya cilar waje, sannan ya ajiye wayar cikin motar sa.

  Jalila tana kuka tana cewa "dan Allah dady ka barni ko magana daya muyi."
Dady ko kallanta baiyi ba ya ja motar sukai gaba.
Mumy tana cewa "lalai Jalila wato ya baki kima saurayinki magana?"

Juyawa tai tana kallan window tana wani irin kukan takaici.

#ONELUV💕
[08/10, 02:11] ‪+234 803 222 1758‬: 🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

(_D home of expert and perfect writer's_💡)

*No 19*

  A kofar asibitin Dady yai parking sannan sukai shiru a cikin motar, Jalila tasa hannu. zata bude kofar Dady yace "Jalilah!"
komawa tai ta zauna tana kallansa tare da amsawa.
Dady ya juyo yace "Fatima dan bamu guri."
kallansa tai kamar zatai magana sai naga ta fasa, kofar ta bude ta fita sannan ta nufi cikin asibitin.
Chapter 19 · 0% Book details