← Book details Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 50 OF 53

Sashe 50

Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hassan ya bude motar ya shiga dya rufota da karfi yaja motar da gudu suka bar gun.

Shiru motar tai ba wanda yake magana, sai sanyin Ac dake ratsa cikin motar.

Jalila ta kalleshi taga ba alamar wargi, tai gum.

Can ta sake kallansa nan ma taga ba alama tai gum.

Sunyi nisa sosai sai tace “Yaya kashanye yoghurt dinka?”

Bai tanka mata ba sai dai yasa hannu ya miko mata ledar, ba haka taso ba, ta daure ta sake cewa “kasan yaya sai da muka shiga cikin store din nan naji cikina yana wani kara?”

Nan ma baiko tanka mata ba, ta amshi ledar ta ajiye a kusa da ita sannan ta kalli Ameera datai shiru tana danna wayarta.

Itama jan bakinta tai bata sake cewa komai ba.

Suna isa gida Ameera ta fito da sauri saboda tsoron kar reshe ya juye da ita.

Jalila ta zauna ba alamar fita, kallanta yai yace “me kikeyi?”

Tace “Yaya kaima kasan ba kaifina bane, tuntube nai sannan wlh bawai kula bane banayi”

Yace “kinji nace wani abun?”
Tace “bakace ba amma......”
Ya katseta “sauka inkuma bazaki shiga ciki ba sai ki kulle motar inkin gama zaman.”

Kallansa tai ranta yadan sosu ta fito daga ciki ta duba boot ta dauko ragowar ledojin sannan tai ciki.

Kallanta yai harta shiga ciki sannan ya dan saki huci yace “ ba saboda ke raina ya baci ba saboda kaina ne.”

Idanunsa yadan rufe da hannunsa kafin ya fito daga motar.

Ummy najin motsin shigowarsu ta fito daga dakinta tana cewa “Jalila kun dawo?”

Ameera ce ta taho da gudu ta rungumeta, Ummy tai dariya tace “Auta saukar yaushe?”

Ameera ta kalli Jalila tace “tare muke dasu Yaya Jalilah.”

Ummy ta kalli Jalila wacce ta karaso tana cewa “da ita muka je ai Ummy.”

Ameera ta kalli Ummy cikin zumudi tace “Ummy kinsan waye ya kaimu?”
Ummy ta kalleta, Ameera ta kara matsowa tace “Ummy karkiyi mamaki.........”

“Hassan kun dawo?” Abinda Ummy tace ne yasa Ameera saurin boyewa abayanta, Hassan yace “eh Ummy.”
sannan yace “Abba fa?”
Ta nunamai falo tana kallan Jalila wacce tana tsaye yazo ya wuce kamar baiganta ba.

Hassan ya wuce falo, Ameera ta kalli Ummy da sauri tace “Ummy kingani? Ummy yaya ne yake magana haka.”

Ummy ta kalleta tace “naji hajiyar magana, akwai baki a dakinki kije ku gaisa.”

Ameera tace “baki? Su waye?”

Ummy bata tanka mata ba ta matso kusa da Jalila tace “Jalila wani abun ya faru ne?”

Jalila tai yake tace “bakomai Ummy, Kinga kayan da Yaya ya sai mata.”

Ummy ta kalli ledar tace “basai kin ciro ba, angode Allah ya saka masa da alkairi.”

Jalila tace “Ameen.”

Muryar Abba sukaji yana kiran Ummy.
Ummy ta falo, Jalila kuma ta dau leda tai dakin Ameera.

Hassan na zaune kusa da Abba ta shigo, ta zauna sannan ta kallesu tace “d’a da uba ne suke hirar yaushe gamo?”

Abba yai murmushi yace “nikaina ina jiran wannan lokaci, lokacin da Hassan zai zauna dani muyi hirar duniya.”

Hassan bai tanka musu ba, Ummy tace “wani abun ya faru ne?”
Yace “a’a kawai dai sirikarsa ce ta nemi mu barta ta tafi tana kunyar zama gida daya da sirikinta da mu.”

Ummy tace “hakane munyi laifi da bamuyi wannan tunanin ba, sannan bamu tambayeta ra’ayinta ba.”

Hassan ya kalli Ummy yace “Ummy ita so take takoma kauye nikuma ina ganin hakan ba solution bane.”

Tace “mekake tunani?”
Yace “gwara a nemarmata gida anan ta zauna karami, can yayi nisa.”

Murmushi tai ta kalli Abba tace “gaskiya kam yama Jalila nisa wanda zai sata damuwa.”

Kare tsuke fuska yai yace “Ummy me kike.....”
Katseshi tai tace “ ni ba da komai nake nufi ba.”
Abba ya kalleta yace “wani abun kike tunani?”

Tace “a’a shawararce naga tayi, me zai hana a gidan da ka siya kwananan wanda ke tarauni a maidata can? Naga gidan karami ne sannan ga yarinya ma mai kula da ita.”

Abba ya jinjina kai yace “hakan ma shawara ce, kinga Allah ne yasa bamu sa haya ba dan har an fara tambaya, Hassan sai ka dau Jalila kunduba gidan sai a sai abunda ya kamata.”

Yace “to.”

Bai jira wani abu ba ya mike, yanasan yama Abba godiya sai dai bakinsa bazai iya furatawa ba, harya kai kofa ya juyo yace “Ummy na hau sama.”
Tace “to Hassan.”

Ya juya ya fita, Ummy ta kalli Abba tace “ Ya kagani?”

Murmushi yai yace “ tunda na dawo kullum Hassan sai ya bani mamaki, lalai dolene muje muyina doctor godiya ba shakka shawararsa itace babban magani a tattare dashi.”

Ummy ta sake yin murmushi.....

Jalila kuwa tana shiga daki inda Goggo take ta hau nuna mata kaya, Ameera kam tana gefe tana mamaki, kenan mahaifiyarta ce ta asibitin nan? Me yasa a lokacin bata nuna mata itace mahaifiyarta ba? Goggo ta kalli Jalila tace “Jalila garin yaya kika barshi ya kwaso kaya haka? Kudi fa aka sa aka siya.”

Ameera tai dariya tace “Goggo ashe ke tayo, shiyasa takasa bari na dau kaya ko daya wai tsada, sai da yaya yazo.”

Goggo ta kalli Ameera tace “ke kuwa yar nan ina zan kai kayan nan?”

Jalila ta kalli Goggo wani abu ya tsirga mata na tausayi, tunda Goggo take bata saka kaya masu tsada haka ba, ba ta tana samun kaya kwatan yawan wannan ba, gaba daya kayanta.......”
Idanunta ne suka ciciko ta kalli Goggo tace “yaya ya fadamin abinda kikace.”

Tace “ya sanar dake?”

Jalila ta daga kai, Goggo ta riko hannunta, Ameera tai saurin fitowa daga dakin.

Goggo ta kalli Jalila tace “Jalila kiyi hakuri, nasan burinki ma shirme nasan ganin mun zauna tare bayan kinyi aure sai dai ko a da can jinki nakeyi dan bazan iya zama da sirikina ba.”

Jalila ta daga kai alamar ta fahimta dan batasan tai kuka.
Goggo ta kalleta tace “shiyasa a koda yaushe ake cewa Allah ba azallumin bawansa bane, Jalila ban taba tunanin zakiyi aure cikin gata irin wannan ba, gaba daya mutanen gidan nan zuri’ace ta albarka, dolene mu gode ma Allah akan baiwar daya miki ta samun dangin miji irin wannan.”

Jalila ta kalleta idanunta suka zubo da kwalla, Goggo tai murmushi tace “nikam wannan yaran kanin mijinki.....”

Da sauri Jalila tace “oh Ya Sageer? Oh Goggo kinsanshi ne?”

Kallanta tai taga ba wani alama ta wani abun tace “a’a na dai ganshi a asibiti.”
Jalila tace “oh haka ne.”

Sundanyi hira kafin ta mike ta fito.

Tunda ta shiga daki taganshi a kwance ta fito ya dawo falo ta zauna, yunwa ce ta sata shiga dakin a hankali ta dauko tiren abinci ta fito falo taci ta zauna tana danne danne a waya, daga baya ma ta sauko kasa sukai girki ta koma gun Goggo sukai hira da Ameera.

Abincin ranarsu ma data kai taga yana kwance ta diba ta fito falo taci ta koma kasa sai da suka gama abincin dare ita da Ameera sannan ta dauko nasu ta hawo sama.

Yanzu kam a kasa ta ganshi kan sallaya yana karatu, gefe ta koma ta zauna tana sauraran kartun nashi, tana lumshe ido saboda dadi, tana bala’in sha’awar taga tana rera karatunn qur’ani haka.

Hassan na nan zaune har aka kira isha’i sannan yai sallah, itama tai.

Sai binshi take da kallo tanasan tamai magana amma ba fuska.

Mikewa tai ta zubo mai abinci tace “Yaya ka sauko kaci abinci.”

Kallanta yai yace “ban dade dacin na rana ba.”

Ta mike daga zaman datai a kasa ta matso kusa dashi jikin gado tace “Yaya dan Allah menene? In laifi na maka dan Allah kayi hakuri.”

Idanunya kura mata, a ransa yace “me kika min? Haushin kaina nakeji da duk abinda zanyi tun dazu sai naji kina raina, haushin kaina nakeji nasan na ganki kusa dani, haushin kaina nakeji na rashin sanin abinda ke damuna a kanki.”

Jalila ta kalli yanda ya kafe ta da ido kana gani kasan tunani yakeyi, tace “Yaya?”

Littafinsa ya dauka baice mata komai ba.

Tsayawa tai shiru kafin ta zauna taci abincin nasa data zuba, kadan ta iyaci dan ya mata yawa.

Har dare Hassan bai kula ta ba, itama haushi yasa ta dauke kai daga kansa tai kwanciyarta, kankace me bacci yayi gaba da ita.

Kwanciya yai ta saitinta yanda yana hangota daga kan gado, ya kura mata ido, what are u to me?

Gani yai tayi juyi ta juya mai baya.
Mikewa na ga yayi ya dau pillow dinsa ya kwanta akan kujera yanda zai ganta dan kusa da kujerar take shimfida.

Ajiyar zuciya yai ya kalli bargon data shimfida yace “wannan bazai sata ciwon baya ba? Kullum kwana a kasa? Gata ba jiki ba?”

(Nikuwa nace waye ya sata🤨)

Ya dade a haka yana kallanta har bacci ya daukeshi.

Yauma Alhamdulila bai farka da ciwo ba, wajen asuba ya farka, da sauri ya mike yana mamakin kansa anan ya kwana? Ahh wai Hassan hankalinka daya kuwa?

Alwala yai sannan yazo kusa da ita, ya saba sa kafa ya tasheta yau sai gani nai ya sunkuyo yasa hannu yadan bugi kafadarta tare da cewa “Jalila?”

Idanu ta bude cikin bacci ta kalleshi, mikewa yai.

Ta mike itama tai alwala...........

Tunda ta tashi take jinta ba dadi, ba sabon abu bane tasan period dinta ne ya kusa, ita kuma gashi duk sanda zatai al’ada sai tasha azaba na ciwon mara, a gida Goggo sai ta sata tasha dauri, ko ta siyo panadol......

***********

Inna ce tasa aka kira mata dady, yana zama mumy ta shigo taja ta zauna.
Inna tace “Fatima meye hakan? Magana zamuyi.”

Mumy tace “kome zakuyi kuyi agabana, sannan nima magana nazo fadamiki.”

Inna ta kalleta tace “maganar me?”
Tace “kiba Abubakar mukamin Chairman na company ke kiyi resigning, dama ai kin dade kina cewa zaki bani ke kuma ki sauka.”

Inna ta kalleta cikin tashin hankali sannan ta kalli Dady wanda shima yai alamar wai mamaki, tace “Abakar kai ka zigata?”

Da sauri Dady ya kalleta yace “Menene hakan? Ce miki nai inasan shugabanci na company din? Meyasa kike neman sa Inna taga kamar nine nake saki abu? Banasan irin wannan abun.”
Chapter 50 · 0% Book details