Sashe 1
Jalilah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
[08/10, 19:17] +234 816 365 0557: *JALILA 1*
In the name of Allah the most Beneficent the most merciful.
Praise be to Allah lord of the words.
The beneficent the Merciful.
Master of the Day of judgement.
Alone we worship;Alone we ask for help.
Show us the straight way
The way of those on whom Thou has bestowed the Grace, those whose portion
Is not wrath, and who do not go astray.
Gaisuwa tare da jinjina da fatan alkairi gareku daukacin masoyana, ina mika sakon gaisuwa gareku, dafatan kowa yayi sallah lafiya, Allah ya maimaita mana Ameen, musulmai da suka rigamu gidan gaskiya Allah ya jikansu, mu da muke da rai Allah ya sa mu gama da duniya lafiya Ameen suma Ameen.
_Oh ina fatan me karatu yayi saurin cewa Ameen..... lol duk da nasan ke ko kai ka fada.........._
*JALILA*
*Ayusher Muhd's Novel ke dauke da shafin na 1 daga cikin littafin Jalila.*
*Dauke da tambarin Kungiyar Haske Writers Association*
***********
Da sauri ta fito daga wanka ko mai bata tsaya shafawa ba ta zura kaya, ta rataya jakarta ta dauko safarta a hannu ta nufi hanyar waje, Goggo mahaifiyarta ce tai saurin cewa "Jalila ko karyawa bakiyi bafa."
Tace tana kokarin sa sandal "Goggo share abinci nan in driver dinsu Safeenah ya tafi ni kadai nasan uban tafiyar da zansha in banyi wasa ba inci duka in naje makarantar."
Tafada tare da gama saka sa sandal din,Goggo da sauri ta miko mata naira ashirin tace " ungo to in kinje kya samu wani abin kici."
Jalilah ta amsa tare da yin waje da gudu.
Tana zuwa motar na fita daga gidan da gudu ta karasa hanyar kofar sai dai kafin ta karasa sunyi gaba.
Idanunta ne suka ciciko dan ta tabbatar anganta ko ta madubin mota ne, bayan yau aikin gidan ne ya mata yawa amma ko su tsaya ta, inda sabo ta saba sai dai tana kokarin kiyayewa dan kuwa makarantar da takeyi akwai nisa, duk da sudin makarantar kudi sukeyi ita kuma ta gomnati, sai dai ba nisa sosai tsakanin makarantun nasu.
Sauri ta shiga yi dan tasan tabbas kafin ta isa sai tayi late.
Duk hanya ba dadin tafiya sakamakon ruwan da aka sheka a daran jiya, dan ma bata sa safarta ta makaranta ba, jin yanda wata mota ta shararo da gudu yasa tai saurin matsawa, tare da bin motar da kallo, da gudu ya zo ya wuce da motarsa, wata muguwar harara ta bi mai motar dashi sannan ta ja wani tsaki juyawa tai baya taga duk yawanci mutanen baya motar suke bi da harara da alama kowa yaji haushin yanda motar ta kunno da gudu cikin layinsu, Jalila ta kara kallan motar wacce ta riga ta kule tare da kara tsaki tace " wasu dai ba kai sai na daukar kaya"
Cigaba da tafiyarta tai duk ta gaji, har sai da ta kusa isa makarantar sannan ta tsaya tare da ciro safarta ta tsaya a gefe ta saka sannan ta dan karkade jikinta, ita nufi makarantar, mamaki tai da taga kamar motar da gani dazu.
Motar ta gani tayi gaba, baki tadan tabe sannan ta karasa gate din makarantar.
Sabon Malaminsu ta gani tsaye a bakin gate da alamar shine yake tarar late comers, kanta ta sunkuyar har ta isa gun.
Shikuwa tunda ta taho yake kallanta fuskarsa a dan hade tana matsowa yace " Habiba Auwal me kenan?"
Kallansa tai da sauri tare da cewa " Good Afternoon Sir!"
Yace "Afternoon?now?"
Da sauri tace" Oh sorry sir Good Mor......."
Katseta yai yace "Dama bakya zuwa school da wuri?"
Kallansa tai tace " No sir wlh yau ma tsaytsayi ne."
Fuska ya kara had'ewa yace " Tsautsayi a ranar farko dana fara tsayawa a gate?"
Kasa tai da kanta tana wasa da yatsun hannunta, yace "sai ki dau dustbin kiyi picking."
Kallansa tai dan ta dauka dukkanta zaiyi, murmushi ne ya bayyana a fuskarta tace "Thank you sir"
Shima murmushin yai yace "Last warning in har kinaso mu shirya kenan."
Da sauri ta daga kai sannan ta dau dustbin tai gaba ta fara picking, kallansa ta juyo tai ta baya, ba shakka bata taba ganin wanda kayan Nysc sukama kyau ba irin Uncle Sagir.
Jalila na gamawa ta wuce ajinsu, ganin ba kowa a cikin ajin yasa tai saurin juyawa ta nufi lap.
Suna lap din chemistry ana musu practical, da sauri ta wuce gun groups dinsu, Zarah ta kalleta tace "Jalila kinga yarda idanunmu suka firfito muna tsoron kar a ce ya akai aka ganmu mu shida.
Tace "Kedai bari nima na dauka zai ganni."
Haka sukai ta karatu har sai da aka tashi break sannan ta samu tasai biscuit na naira goma taci ta sha ruwan fanfo sannan ta ajiye naira goman.
Ana tashi suka fito ita da Zarah suna hira, Zarah tace " Jalila kinsan jiya sai ga Ya Amud da takardar jamb!"
Jalila ta kalleta cikin jin dadi tace "Haba? Kice hankalinki ya kwanta dama kina ta tsoron kar ace za'a miki aure."
Tace " ke dai bari jiya ai baccin dadi nai, dan banaji zan iya rabuwa da Nasir dina, kuma kinga shi level 3 yake a Buk."
Jalila ta tabe baki tace " su soyayya manya, da alama kema makarantarsu zaki nema.
Tace "sai ma kin tambaya...."
Dariya sukai, Zarah tace " ni nayi gida ke nasan sai kin jira ko?"
Tace eh
Dayake gidansu Zarah ba nisa da makaranta nan ta kwana, Jalila taja gefe ta tsaya kamar yanda suka saba, minti 30 ne tsakanin lokacin tashinsu dasu Safeena, abinda zai baka mamaki shine su in har suka shirya zasu taho to fa ba ruwansu da jiranta sai dai ita bata isa a tashi ta tafi ba sai ta jirasu.
Tana nan a tsaye taji ance "baki tafi ba?
Juyowa tai ta kalli malamin nasu wanda yanzu su yan aji shida kusan dukansu matan nan in suka zauna gulmarsa sukeyi, tace " eh sir."
Ya dan daga littafin dake hannunsa kamar zai kwada mata, da sauri ta runtse idanunta, jin shiru bai dake taba yasa ta bude idanunta a hankali, kallansa tai ya harde hannayensa kawai yana kallanta cikin mamaki tace "ba dukana zakai ba?"
Yace "me kikamin da zam dakeki? Dazu da kikai laifi ban dakeki ba sai yanzu?"
Cikin mamaki tace amma naga ka daga......
Yace "sato ke bakya zuwa school da wuri sannan in an tashi kece karshe a tafiya, me hakan yake nufi?"
A ranta tace "ni kaina wannan amsar nemanta nakeyi."
A fili tace " hmmm, ai......"
Wayar da aka mai ne ta katsesu ya dau waya tare da fara tafiya, alama ya mata da hannu akan ya wuce.
Tace " Okay Sir."
Bin bayansa tai da kallo, sannan tai ajiyar zuciya, nan ta cigaba da tsayuwa har suka iso, 2017 toyota sienna ce tai parkin a kusa da ita, tura kofar motar tai ta shiga.
Sannan ta rufe kofar, Safeena ce wacce kana kallanta kasan bata wuce sa'ar Jalilan ba tace " Ashe kuma yau da kafa kika taho."
Jalila ta kalleta tace " Amma Safeena dazu tsakani da Allah baku ganni ba, sannan Malam Auwal ma bai ganni ba?"
Safeena tace " Ta ina zamu ganki? Sannan in ma munganki menene damuwarmu? Uban wa ya hanaki yin sauri?"
Jalila ta juyo ta kalleta tace "Uban wa ya hanani yin sauri? Kwata kwata fitowata daga bangarenku minti nawa ne har kuka taho?"
Tace "wannan damuwarki ce, naga kina wani hararata ni na saki aikin? Sannan in kinsan bakyasan kiyi late me zai hana ki dinga tashi karfe hudu?"
Jalila ranta ya baci ta juyo gaba dayanta tace " karfe hudu? Ku karfe nawa kuke tashi, ni daga na tashi sallar asuba me nakeyi? Bangarenku nake shigowa sai na gama muku komai har abinci sannan nake tafiya na shirya, sannan hakan ma ba birgewa nake ba har zakice indinga tashi karfe hudu?"
Sultan kanin Safeena ne ya zare earphone din dake kunnensa yace " will you please keep quiet, duk kun cika mana kunne da wani musunku."
Ya maida earphone dinsa, tare da kwantar da kansa kan kujera, Safeena tai kwafa tace " in munje gida kya maimaitawa Mumy na abinda kika fada a motar nan."
Jalila a ranta tace " yauma a kwai wani sabon shan wahalar kenan, ai wahala bata kisa."
Suna isa gida motar Dadynsu Safeena na parking, Safeena ta tashi kanwarta Yasmeen dake barci, tana ganin Dadynta ta ruga da gudu ta gunsa.
Safeena ma tai gunsa tana murmushi, daga Yasmin yai yana cewa "Baby Yasmin an dawo?"
Sultan ne ya karaso yace " sannu da zuwa Dady."
Kallansa yai yana murmushi, Safeena kusa hannayenta ta zargo cikin nashi tare da cewa " Dady kace da safe zaka dawo."
Yace " Naso dawowa da safe sai dai akwai wani meeting da nadan yi ne da suppliers dinmu.
Karasa maganar yai yana kallan Jalila wacce kullum take jiya iyau, irin yar kibar nan ko dan murmurewar nan batayi, Jalila tace " Dady sannu da zuwa."
Yace "Jalila an dawo?"
Ya fada tare da juya kai zuwa gun Safeena wacce ke harar ta, yace " muje ko?"
Nan suka nufi ciki Yasmin ma hannunsa ita kuma Safeena ta rikeshi.
Murmushinnn takaici tai tace " happy family, wazai kalleni yace mahaifinane?"
Wucewa tai can cikin gida inda aka dan musu dakinsu daya da bandaki a can karshen gidan aka katangesu kamar masu aikin gidan........
*************
A hankali ta tura kofar d’akin bayan ya amsa sallarmarta, zama tai daga gefen gadon inda yake a kwance, kallanta yai sannan ya fara kokarin mikewa zaune, a hankali cikin sanyin muryarta tace “ Hassan bazakai breakfast da mu bane?”
Yace “Ummy banajin yunwa.”
Idanunta ne suka canja yanayi cikin tsananin tausayama dan nata tace “ Hassan sai yaushe ne zakai yaki da wannan matsalar dake damunka? Mun kaika duk wani asibiti da ake ji dashi a duniya amma ba wani ci gaba, dole ance kaine zakai yaki da wannan matsalar da kanka ba wani bane zai maka.”
In the name of Allah the most Beneficent the most merciful.
Praise be to Allah lord of the words.
The beneficent the Merciful.
Master of the Day of judgement.
Alone we worship;Alone we ask for help.
Show us the straight way
The way of those on whom Thou has bestowed the Grace, those whose portion
Is not wrath, and who do not go astray.
Gaisuwa tare da jinjina da fatan alkairi gareku daukacin masoyana, ina mika sakon gaisuwa gareku, dafatan kowa yayi sallah lafiya, Allah ya maimaita mana Ameen, musulmai da suka rigamu gidan gaskiya Allah ya jikansu, mu da muke da rai Allah ya sa mu gama da duniya lafiya Ameen suma Ameen.
_Oh ina fatan me karatu yayi saurin cewa Ameen..... lol duk da nasan ke ko kai ka fada.........._
*JALILA*
*Ayusher Muhd's Novel ke dauke da shafin na 1 daga cikin littafin Jalila.*
*Dauke da tambarin Kungiyar Haske Writers Association*
***********
Da sauri ta fito daga wanka ko mai bata tsaya shafawa ba ta zura kaya, ta rataya jakarta ta dauko safarta a hannu ta nufi hanyar waje, Goggo mahaifiyarta ce tai saurin cewa "Jalila ko karyawa bakiyi bafa."
Tace tana kokarin sa sandal "Goggo share abinci nan in driver dinsu Safeenah ya tafi ni kadai nasan uban tafiyar da zansha in banyi wasa ba inci duka in naje makarantar."
Tafada tare da gama saka sa sandal din,Goggo da sauri ta miko mata naira ashirin tace " ungo to in kinje kya samu wani abin kici."
Jalilah ta amsa tare da yin waje da gudu.
Tana zuwa motar na fita daga gidan da gudu ta karasa hanyar kofar sai dai kafin ta karasa sunyi gaba.
Idanunta ne suka ciciko dan ta tabbatar anganta ko ta madubin mota ne, bayan yau aikin gidan ne ya mata yawa amma ko su tsaya ta, inda sabo ta saba sai dai tana kokarin kiyayewa dan kuwa makarantar da takeyi akwai nisa, duk da sudin makarantar kudi sukeyi ita kuma ta gomnati, sai dai ba nisa sosai tsakanin makarantun nasu.
Sauri ta shiga yi dan tasan tabbas kafin ta isa sai tayi late.
Duk hanya ba dadin tafiya sakamakon ruwan da aka sheka a daran jiya, dan ma bata sa safarta ta makaranta ba, jin yanda wata mota ta shararo da gudu yasa tai saurin matsawa, tare da bin motar da kallo, da gudu ya zo ya wuce da motarsa, wata muguwar harara ta bi mai motar dashi sannan ta ja wani tsaki juyawa tai baya taga duk yawanci mutanen baya motar suke bi da harara da alama kowa yaji haushin yanda motar ta kunno da gudu cikin layinsu, Jalila ta kara kallan motar wacce ta riga ta kule tare da kara tsaki tace " wasu dai ba kai sai na daukar kaya"
Cigaba da tafiyarta tai duk ta gaji, har sai da ta kusa isa makarantar sannan ta tsaya tare da ciro safarta ta tsaya a gefe ta saka sannan ta dan karkade jikinta, ita nufi makarantar, mamaki tai da taga kamar motar da gani dazu.
Motar ta gani tayi gaba, baki tadan tabe sannan ta karasa gate din makarantar.
Sabon Malaminsu ta gani tsaye a bakin gate da alamar shine yake tarar late comers, kanta ta sunkuyar har ta isa gun.
Shikuwa tunda ta taho yake kallanta fuskarsa a dan hade tana matsowa yace " Habiba Auwal me kenan?"
Kallansa tai da sauri tare da cewa " Good Afternoon Sir!"
Yace "Afternoon?now?"
Da sauri tace" Oh sorry sir Good Mor......."
Katseta yai yace "Dama bakya zuwa school da wuri?"
Kallansa tai tace " No sir wlh yau ma tsaytsayi ne."
Fuska ya kara had'ewa yace " Tsautsayi a ranar farko dana fara tsayawa a gate?"
Kasa tai da kanta tana wasa da yatsun hannunta, yace "sai ki dau dustbin kiyi picking."
Kallansa tai dan ta dauka dukkanta zaiyi, murmushi ne ya bayyana a fuskarta tace "Thank you sir"
Shima murmushin yai yace "Last warning in har kinaso mu shirya kenan."
Da sauri ta daga kai sannan ta dau dustbin tai gaba ta fara picking, kallansa ta juyo tai ta baya, ba shakka bata taba ganin wanda kayan Nysc sukama kyau ba irin Uncle Sagir.
Jalila na gamawa ta wuce ajinsu, ganin ba kowa a cikin ajin yasa tai saurin juyawa ta nufi lap.
Suna lap din chemistry ana musu practical, da sauri ta wuce gun groups dinsu, Zarah ta kalleta tace "Jalila kinga yarda idanunmu suka firfito muna tsoron kar a ce ya akai aka ganmu mu shida.
Tace "Kedai bari nima na dauka zai ganni."
Haka sukai ta karatu har sai da aka tashi break sannan ta samu tasai biscuit na naira goma taci ta sha ruwan fanfo sannan ta ajiye naira goman.
Ana tashi suka fito ita da Zarah suna hira, Zarah tace " Jalila kinsan jiya sai ga Ya Amud da takardar jamb!"
Jalila ta kalleta cikin jin dadi tace "Haba? Kice hankalinki ya kwanta dama kina ta tsoron kar ace za'a miki aure."
Tace " ke dai bari jiya ai baccin dadi nai, dan banaji zan iya rabuwa da Nasir dina, kuma kinga shi level 3 yake a Buk."
Jalila ta tabe baki tace " su soyayya manya, da alama kema makarantarsu zaki nema.
Tace "sai ma kin tambaya...."
Dariya sukai, Zarah tace " ni nayi gida ke nasan sai kin jira ko?"
Tace eh
Dayake gidansu Zarah ba nisa da makaranta nan ta kwana, Jalila taja gefe ta tsaya kamar yanda suka saba, minti 30 ne tsakanin lokacin tashinsu dasu Safeena, abinda zai baka mamaki shine su in har suka shirya zasu taho to fa ba ruwansu da jiranta sai dai ita bata isa a tashi ta tafi ba sai ta jirasu.
Tana nan a tsaye taji ance "baki tafi ba?
Juyowa tai ta kalli malamin nasu wanda yanzu su yan aji shida kusan dukansu matan nan in suka zauna gulmarsa sukeyi, tace " eh sir."
Ya dan daga littafin dake hannunsa kamar zai kwada mata, da sauri ta runtse idanunta, jin shiru bai dake taba yasa ta bude idanunta a hankali, kallansa tai ya harde hannayensa kawai yana kallanta cikin mamaki tace "ba dukana zakai ba?"
Yace "me kikamin da zam dakeki? Dazu da kikai laifi ban dakeki ba sai yanzu?"
Cikin mamaki tace amma naga ka daga......
Yace "sato ke bakya zuwa school da wuri sannan in an tashi kece karshe a tafiya, me hakan yake nufi?"
A ranta tace "ni kaina wannan amsar nemanta nakeyi."
A fili tace " hmmm, ai......"
Wayar da aka mai ne ta katsesu ya dau waya tare da fara tafiya, alama ya mata da hannu akan ya wuce.
Tace " Okay Sir."
Bin bayansa tai da kallo, sannan tai ajiyar zuciya, nan ta cigaba da tsayuwa har suka iso, 2017 toyota sienna ce tai parkin a kusa da ita, tura kofar motar tai ta shiga.
Sannan ta rufe kofar, Safeena ce wacce kana kallanta kasan bata wuce sa'ar Jalilan ba tace " Ashe kuma yau da kafa kika taho."
Jalila ta kalleta tace " Amma Safeena dazu tsakani da Allah baku ganni ba, sannan Malam Auwal ma bai ganni ba?"
Safeena tace " Ta ina zamu ganki? Sannan in ma munganki menene damuwarmu? Uban wa ya hanaki yin sauri?"
Jalila ta juyo ta kalleta tace "Uban wa ya hanani yin sauri? Kwata kwata fitowata daga bangarenku minti nawa ne har kuka taho?"
Tace "wannan damuwarki ce, naga kina wani hararata ni na saki aikin? Sannan in kinsan bakyasan kiyi late me zai hana ki dinga tashi karfe hudu?"
Jalila ranta ya baci ta juyo gaba dayanta tace " karfe hudu? Ku karfe nawa kuke tashi, ni daga na tashi sallar asuba me nakeyi? Bangarenku nake shigowa sai na gama muku komai har abinci sannan nake tafiya na shirya, sannan hakan ma ba birgewa nake ba har zakice indinga tashi karfe hudu?"
Sultan kanin Safeena ne ya zare earphone din dake kunnensa yace " will you please keep quiet, duk kun cika mana kunne da wani musunku."
Ya maida earphone dinsa, tare da kwantar da kansa kan kujera, Safeena tai kwafa tace " in munje gida kya maimaitawa Mumy na abinda kika fada a motar nan."
Jalila a ranta tace " yauma a kwai wani sabon shan wahalar kenan, ai wahala bata kisa."
Suna isa gida motar Dadynsu Safeena na parking, Safeena ta tashi kanwarta Yasmeen dake barci, tana ganin Dadynta ta ruga da gudu ta gunsa.
Safeena ma tai gunsa tana murmushi, daga Yasmin yai yana cewa "Baby Yasmin an dawo?"
Sultan ne ya karaso yace " sannu da zuwa Dady."
Kallansa yai yana murmushi, Safeena kusa hannayenta ta zargo cikin nashi tare da cewa " Dady kace da safe zaka dawo."
Yace " Naso dawowa da safe sai dai akwai wani meeting da nadan yi ne da suppliers dinmu.
Karasa maganar yai yana kallan Jalila wacce kullum take jiya iyau, irin yar kibar nan ko dan murmurewar nan batayi, Jalila tace " Dady sannu da zuwa."
Yace "Jalila an dawo?"
Ya fada tare da juya kai zuwa gun Safeena wacce ke harar ta, yace " muje ko?"
Nan suka nufi ciki Yasmin ma hannunsa ita kuma Safeena ta rikeshi.
Murmushinnn takaici tai tace " happy family, wazai kalleni yace mahaifinane?"
Wucewa tai can cikin gida inda aka dan musu dakinsu daya da bandaki a can karshen gidan aka katangesu kamar masu aikin gidan........
*************
A hankali ta tura kofar d’akin bayan ya amsa sallarmarta, zama tai daga gefen gadon inda yake a kwance, kallanta yai sannan ya fara kokarin mikewa zaune, a hankali cikin sanyin muryarta tace “ Hassan bazakai breakfast da mu bane?”
Yace “Ummy banajin yunwa.”
Idanunta ne suka canja yanayi cikin tsananin tausayama dan nata tace “ Hassan sai yaushe ne zakai yaki da wannan matsalar dake damunka? Mun kaika duk wani asibiti da ake ji dashi a duniya amma ba wani ci gaba, dole ance kaine zakai yaki da wannan matsalar da kanka ba wani bane zai maka.”