Sashe 37
Idan An Ciza Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Madiha ba ta zo ba sai ranar suna, Asma'u ma Mommy ta turo ta dag anan za ta tsaya gida ta yi hutu, Madiha ba ta san an daidaita har Mimi ta sauko ba sai da ta ga zuwan Hibba ana cewa matar ƙanin Mijin Mimi sai kuma da ta ganta sai ta tuna ta taɓa ganinta a wannan gidan da aka kai Mimi, Tun anan ta nuna ba ta ji daɗi ba Mimi ba ta ma san tana yi ba ta riƙa ina ta saka da bakuwarta Hibba ta na nan har dare har riga ta kawo ma Bby Girl da ta ci sunan Mahaifiyar Jawahir mai suna Hadiza, Sai bayan da Mu'azzam ya zo ya ɗauketa ne da daddare suna ɗakin Dr su huɗun gabaɗaya Madiha ta tada zencen da cewa"Ke Mimi me ya haɗa ki da dangi wancan matsiyacin?
Ba Mimi kaɗai ba harta Khadi sai ta ji wani iri, Dr ya kalleta cikin ɓacin rai kafin ya ce" Haba Madiha, ko an rabu ai bai kamata ki kira shi da wannan sunan ba, Ballantana har gobe a matsayin mijin Mimi yake."
Madiha cikin halin ko in kula, ta ce"To sai me? Ai sai ya sake ta wlh in ya yi taurin kai a maka shi a kotu,"
Khadi ta yi Saurin cewa"Ke, to tana son mijinta, yanzu hakama ya je ya samu Daddy kuma ya ce ya ba shi bikon ta, tana komawa Gombe sai shirin tarewa daman Yajin barazana ta yi ko Mimin Abi?
Mimi ta kasa mgana Idanuwanta har sun kawo kwallah, Dr ne ya tsawarta ma Madiha da cewa" Ki daina shiga hurumin da ba na ki ba don Allah, Mimi ba za ta ji daÉ—i ba."
Madiha ta kalle su cikin mamaki kafin ta ce" Mi ye illar mgana ta? Na ga ita da kanta ta ce ba ta son auran domin na taimaka mata komai ya kare laifi ne?
Sai kawai Mmi ta miƙe tana kallon Dr kafin tace" Dr gobe ko jibi zam koma Gombe."
Ta na gama faÉ—in haka ta bar musu É—akin.
Khadi ta kai duban ta kan Madiha kafin ta ce"Gaskiya Sisto ba ki kyauta ba, kamar ni ne fa ki zagi Muhammad"
Madiha ta taɓe baki kafin ta ce"Muhammad dabam wannan talakan dabam, ki daina ma haɗa su."
Khadi na dariya shi kuma Dr ya haÉ—e rai yana mata faÉ—an abin da ta yi na ta kyauta ba sai kawai ta ce"Au don nace matsiya ci? Karya na yi? To shike nan na cire bakina."
Ba za ta daina ba halin su ɗaya da Abi shigen kafiya aiko har washegari Mimi ba ta ƙara yi ma Madiha mgana ba sai ta nemi ma jirgin Komawa Gombe ta samu na yamma.
Dr bai hana ta tafiya ba, an kulla mata Naman suna da yaji na ta da na Hajiya, Jirgin karfe biyar ta bi zuwa Gombe Dr. da Khadi su ka kaita filin Jirgi sai da za ta tafi sannan ta yi ma Madiha sallama ta amsa a daƙune ita gani take yi ina laifi domin ta faɗi gaskiya.
Sai dai Hajiya ta ga Mimi sarkin Ya ji kamar daga sama kuma ba domin mganar Daddy ba, hutun ta ya ƙare ya zama dole ta dawo.
Hajiya ta yi murna Baaba Uwani ta ce daman gidan shuru da ba ta nan, ta kira Daddy ta ce masa ta dawo kila anan Mama taji ta gayama Jaheed daman tun da ya ji ta Dawo gida ya addabeta da waya yana gaya mata yana kan bakan shi ta ce ba shi ma da hankali da auranta ai ba ya mutu ba ne.
Sai da ya ji ta dawo wai zai biyo jirgi gobe su yi mgana. Daman a gidan Madiha zuwan sa uku wajenta yana mata magiya ta faɗa masa Mijinta bai saketa ba amman ya na ce wai zai taya ta karɓan sakin daman ai ba su da ce da juna ba, shi a tunanin shi Madiha na goyon bayan shi, shike nan ya same ta ya gama. Tun da ya ce mata zai zo washegari ta ce masa ka da ya zo, domin ita ta san abin da take yi da auranta ba za ta zo tana haɗuwa da shi ba.
Washegari hutawa ta yi a gida, shi kuma Jaheed bai samu dama a wajen aiki ba Shi ya sa bai zo ba, Aji kuma Daddy da kansa ya kira shi ya faɗa masa Mimi ta dawo daman ranar sun karɓi lambar wayar juna sai ya ce zai shigo gidan ko a ranar da daddare ko washegari da yammah.
Bai samu zuwa a daran ba sai washegari bayan la'sar daga gida yake ya je ya gaida Inna sai da ta kara masa mganan Mimi ya ce daga nan wajen ta zai nufa.
A motarsa ya je yana sanye da ƙananun kaya, megadi na buɗe masa get ya shiga motarsa Mimi na fitowa tare da Rukky da ta zo ta rakota sun tsaya suna mgana sai ganin Aji suka yi ya fito daga motarsa duk da ya saka hula P. cap ta rufe rabin fuskar shi ba zai hana taƙi gane shi ba.
*Janafty*
[9/8, 19:53] Auntyna: *INZB3008*
*INZ IS A PAID BOOK PAY N500 FOR REGULAR OR 1K FOR VIP SECTION. VIA 0007468217 ZAINAB INUWA TAJ BANK,*
*09069067488*
https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC
No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba.
Mansor na tsaye a tsakiyar falon gidan tsohon Sanata Alhaji Hamza sulaiman Dabo. Hannayensa harɗe a kirjinsa, lokaci ɗaya yana nazarin falon, ya taɓa shigowa falon kusan sau biyu wani lokacin a can baya Mimi ta matsa masa ya shiga suka gaisa na farko rashin lafiyan Hajiya na biyu ya manta falilin.
A haka Daddy ya zo ya same shi yana tsaye bai zauna ba, yana ƙarisowa ya miƙa masa hannu suka yi masabaha.
Sannan Daddy ya nuna masa kujera ya ce ya zauna amman sai bai zauna ba sai ya zauna a saman tattausan cafet É—in da ya malale fallon gabaÉ—aya saboda ya tuna wayar su da Mu'azzam yana hanyar tahowa nan ya yi ta hadadda masa ya je neman sulhu ne kuma surukinsa ne ya kamata ya nuna masa girma da daraja.
"Haba ka tashi ka zauna saman kujera mana."
Kan Mansoor na ƙasa ya ce"A aa nan ma ya isa Alhaji."
Sai Daddy bai ja ba kawai sai ya gyara zama suka gaisa yana tambayan shi wajen iyayanshi a sanyaye ya ce Alhamdulillah, shuru na wani lokaci ba daɗewa sai ga Anty ta shigo da farantin ruwa da lemu ta sauke nan saman center table ɗin dake falon, Itama Mansoor ya gaisheta ta amsa cikin sakewa kafin ta ce"Ah yallaɓai ya ka bar surukin namu ya zauna a ƙasa kuma?
Daddy ya yi mirmishi kafin ya ce" Biko ya zo shi ya sa ya ninka biyayyarsa." Tare suka yi dariya shi da Anty sannan ta fice shi ko Mansoor kansa na ƙasa domin sai ya ji Daddy ya yi masa kwarjini ya kuma rasa ta ina zai fara ma mganar, In hr Mimi ta faɗa musu dukkan abin da ya aikata mata ai da Kunya, Shi kuma Daddy nazarinsa yake yi ta gefen ido amman bai nuna ba, wata Jarida ma ya ja anan gefe yana karantawa kamar yadda Daddy ya yi masa kwarjini haka shima Daddy ya ga ƙwarjinin Mansoor ya cika falon gabaɗaya.
"Ka sha ruwan mana."
Daddy ya katse shi lokaci ɗaya yana kallon sa, sai Mansoor ya muskuta ya ɗan mike ya isa ga wajen ruwa ya saka kofi ya tsiyaya Kaɗan ya sha sannan ya ijiye kofin sannan ya koma in da ya tashi ya zauna. Shuru ya sake wanzuwa na wani lokaci kafin Daddy ya sake katse shurun da cewa" Ya wajen aikin na ku? Kwanaki abokanka da ƙaninka suka zo sun ce wasa gare ku masu yawa baka samun lokaci."
Sai ya samu kansa da amsawa da E, shi kuma Daddy sai ya jinjina kai kafin yac e"Good! Allah ya saka albarka," Aji ya amsa da Amin cikin yanayin maganarsa amman muryansa ta yi kasa sosai.
Gani ya yi Daddy ya yi kamar bai san dalilin zuwanshi ba, ya ma cigaba da karatun Jaridarsa lokaci É—aya kuma ya na amsa waya in an kira shi.
Mansoor kuma na duke ya rasa ta in da zai fara dakyar ya iya kundunbalan É—agowa ya na kallon Daddy kafin lokaci É—aya ya fara da faÉ—in.
"Alhaji dama kan mganar Fatima ne.."
Sai ya dakata shi kuma Daddy sai ya kalle shi kafin ya ce"E, ina jin ka, Mimi ba ai ta dawo mana nan cikin kuka, ta ce ka ce ba ka sonta sannan ta ce za ta tafi ka ce is better da ta tafi É—in, ni kuma da na ji haka sai na ce ai ba dole a cikin aure kuma in ka ga alaqa ta fara lalacewa gwara rabuwar shi ya fi alheri."
Mansoor ya yi shuru kafin yac e" Alhaji ni ban ce ta tafin da gaske ba"
"To me ya sa bayan ta taho a daran ko washegari ba ka biyo sahun ta ba, in ba ka nufin ta tafin ba?
Kai tsaye Mansoor ya gyara zama yana faɗin" Ina da dalilina Alhaji, saboda ka san su mata wani lokacin in ransu ya ɓaci gwara ka yi nesa da su su huce, na ga ranta ya ɓaci a lokaci to ba laifi ba ne domin ta dawo gida ta huta amman ba na nufin wai ta tafi saboda ba na sonta, in ba na sonta ai ba zan yarda na aureta ba. Kawai na bata lokaci ne ta huta sannan ta huce daga ɓacin ran da take ciki."
Ba Mimi kaɗai ba harta Khadi sai ta ji wani iri, Dr ya kalleta cikin ɓacin rai kafin ya ce" Haba Madiha, ko an rabu ai bai kamata ki kira shi da wannan sunan ba, Ballantana har gobe a matsayin mijin Mimi yake."
Madiha cikin halin ko in kula, ta ce"To sai me? Ai sai ya sake ta wlh in ya yi taurin kai a maka shi a kotu,"
Khadi ta yi Saurin cewa"Ke, to tana son mijinta, yanzu hakama ya je ya samu Daddy kuma ya ce ya ba shi bikon ta, tana komawa Gombe sai shirin tarewa daman Yajin barazana ta yi ko Mimin Abi?
Mimi ta kasa mgana Idanuwanta har sun kawo kwallah, Dr ne ya tsawarta ma Madiha da cewa" Ki daina shiga hurumin da ba na ki ba don Allah, Mimi ba za ta ji daÉ—i ba."
Madiha ta kalle su cikin mamaki kafin ta ce" Mi ye illar mgana ta? Na ga ita da kanta ta ce ba ta son auran domin na taimaka mata komai ya kare laifi ne?
Sai kawai Mmi ta miƙe tana kallon Dr kafin tace" Dr gobe ko jibi zam koma Gombe."
Ta na gama faÉ—in haka ta bar musu É—akin.
Khadi ta kai duban ta kan Madiha kafin ta ce"Gaskiya Sisto ba ki kyauta ba, kamar ni ne fa ki zagi Muhammad"
Madiha ta taɓe baki kafin ta ce"Muhammad dabam wannan talakan dabam, ki daina ma haɗa su."
Khadi na dariya shi kuma Dr ya haÉ—e rai yana mata faÉ—an abin da ta yi na ta kyauta ba sai kawai ta ce"Au don nace matsiya ci? Karya na yi? To shike nan na cire bakina."
Ba za ta daina ba halin su ɗaya da Abi shigen kafiya aiko har washegari Mimi ba ta ƙara yi ma Madiha mgana ba sai ta nemi ma jirgin Komawa Gombe ta samu na yamma.
Dr bai hana ta tafiya ba, an kulla mata Naman suna da yaji na ta da na Hajiya, Jirgin karfe biyar ta bi zuwa Gombe Dr. da Khadi su ka kaita filin Jirgi sai da za ta tafi sannan ta yi ma Madiha sallama ta amsa a daƙune ita gani take yi ina laifi domin ta faɗi gaskiya.
Sai dai Hajiya ta ga Mimi sarkin Ya ji kamar daga sama kuma ba domin mganar Daddy ba, hutun ta ya ƙare ya zama dole ta dawo.
Hajiya ta yi murna Baaba Uwani ta ce daman gidan shuru da ba ta nan, ta kira Daddy ta ce masa ta dawo kila anan Mama taji ta gayama Jaheed daman tun da ya ji ta Dawo gida ya addabeta da waya yana gaya mata yana kan bakan shi ta ce ba shi ma da hankali da auranta ai ba ya mutu ba ne.
Sai da ya ji ta dawo wai zai biyo jirgi gobe su yi mgana. Daman a gidan Madiha zuwan sa uku wajenta yana mata magiya ta faɗa masa Mijinta bai saketa ba amman ya na ce wai zai taya ta karɓan sakin daman ai ba su da ce da juna ba, shi a tunanin shi Madiha na goyon bayan shi, shike nan ya same ta ya gama. Tun da ya ce mata zai zo washegari ta ce masa ka da ya zo, domin ita ta san abin da take yi da auranta ba za ta zo tana haɗuwa da shi ba.
Washegari hutawa ta yi a gida, shi kuma Jaheed bai samu dama a wajen aiki ba Shi ya sa bai zo ba, Aji kuma Daddy da kansa ya kira shi ya faɗa masa Mimi ta dawo daman ranar sun karɓi lambar wayar juna sai ya ce zai shigo gidan ko a ranar da daddare ko washegari da yammah.
Bai samu zuwa a daran ba sai washegari bayan la'sar daga gida yake ya je ya gaida Inna sai da ta kara masa mganan Mimi ya ce daga nan wajen ta zai nufa.
A motarsa ya je yana sanye da ƙananun kaya, megadi na buɗe masa get ya shiga motarsa Mimi na fitowa tare da Rukky da ta zo ta rakota sun tsaya suna mgana sai ganin Aji suka yi ya fito daga motarsa duk da ya saka hula P. cap ta rufe rabin fuskar shi ba zai hana taƙi gane shi ba.
*Janafty*
[9/8, 19:53] Auntyna: *INZB3008*
*INZ IS A PAID BOOK PAY N500 FOR REGULAR OR 1K FOR VIP SECTION. VIA 0007468217 ZAINAB INUWA TAJ BANK,*
*09069067488*
https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC
No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba.
Mansor na tsaye a tsakiyar falon gidan tsohon Sanata Alhaji Hamza sulaiman Dabo. Hannayensa harɗe a kirjinsa, lokaci ɗaya yana nazarin falon, ya taɓa shigowa falon kusan sau biyu wani lokacin a can baya Mimi ta matsa masa ya shiga suka gaisa na farko rashin lafiyan Hajiya na biyu ya manta falilin.
A haka Daddy ya zo ya same shi yana tsaye bai zauna ba, yana ƙarisowa ya miƙa masa hannu suka yi masabaha.
Sannan Daddy ya nuna masa kujera ya ce ya zauna amman sai bai zauna ba sai ya zauna a saman tattausan cafet É—in da ya malale fallon gabaÉ—aya saboda ya tuna wayar su da Mu'azzam yana hanyar tahowa nan ya yi ta hadadda masa ya je neman sulhu ne kuma surukinsa ne ya kamata ya nuna masa girma da daraja.
"Haba ka tashi ka zauna saman kujera mana."
Kan Mansoor na ƙasa ya ce"A aa nan ma ya isa Alhaji."
Sai Daddy bai ja ba kawai sai ya gyara zama suka gaisa yana tambayan shi wajen iyayanshi a sanyaye ya ce Alhamdulillah, shuru na wani lokaci ba daɗewa sai ga Anty ta shigo da farantin ruwa da lemu ta sauke nan saman center table ɗin dake falon, Itama Mansoor ya gaisheta ta amsa cikin sakewa kafin ta ce"Ah yallaɓai ya ka bar surukin namu ya zauna a ƙasa kuma?
Daddy ya yi mirmishi kafin ya ce" Biko ya zo shi ya sa ya ninka biyayyarsa." Tare suka yi dariya shi da Anty sannan ta fice shi ko Mansoor kansa na ƙasa domin sai ya ji Daddy ya yi masa kwarjini ya kuma rasa ta ina zai fara ma mganar, In hr Mimi ta faɗa musu dukkan abin da ya aikata mata ai da Kunya, Shi kuma Daddy nazarinsa yake yi ta gefen ido amman bai nuna ba, wata Jarida ma ya ja anan gefe yana karantawa kamar yadda Daddy ya yi masa kwarjini haka shima Daddy ya ga ƙwarjinin Mansoor ya cika falon gabaɗaya.
"Ka sha ruwan mana."
Daddy ya katse shi lokaci ɗaya yana kallon sa, sai Mansoor ya muskuta ya ɗan mike ya isa ga wajen ruwa ya saka kofi ya tsiyaya Kaɗan ya sha sannan ya ijiye kofin sannan ya koma in da ya tashi ya zauna. Shuru ya sake wanzuwa na wani lokaci kafin Daddy ya sake katse shurun da cewa" Ya wajen aikin na ku? Kwanaki abokanka da ƙaninka suka zo sun ce wasa gare ku masu yawa baka samun lokaci."
Sai ya samu kansa da amsawa da E, shi kuma Daddy sai ya jinjina kai kafin yac e"Good! Allah ya saka albarka," Aji ya amsa da Amin cikin yanayin maganarsa amman muryansa ta yi kasa sosai.
Gani ya yi Daddy ya yi kamar bai san dalilin zuwanshi ba, ya ma cigaba da karatun Jaridarsa lokaci É—aya kuma ya na amsa waya in an kira shi.
Mansoor kuma na duke ya rasa ta in da zai fara dakyar ya iya kundunbalan É—agowa ya na kallon Daddy kafin lokaci É—aya ya fara da faÉ—in.
"Alhaji dama kan mganar Fatima ne.."
Sai ya dakata shi kuma Daddy sai ya kalle shi kafin ya ce"E, ina jin ka, Mimi ba ai ta dawo mana nan cikin kuka, ta ce ka ce ba ka sonta sannan ta ce za ta tafi ka ce is better da ta tafi É—in, ni kuma da na ji haka sai na ce ai ba dole a cikin aure kuma in ka ga alaqa ta fara lalacewa gwara rabuwar shi ya fi alheri."
Mansoor ya yi shuru kafin yac e" Alhaji ni ban ce ta tafin da gaske ba"
"To me ya sa bayan ta taho a daran ko washegari ba ka biyo sahun ta ba, in ba ka nufin ta tafin ba?
Kai tsaye Mansoor ya gyara zama yana faɗin" Ina da dalilina Alhaji, saboda ka san su mata wani lokacin in ransu ya ɓaci gwara ka yi nesa da su su huce, na ga ranta ya ɓaci a lokaci to ba laifi ba ne domin ta dawo gida ta huta amman ba na nufin wai ta tafi saboda ba na sonta, in ba na sonta ai ba zan yarda na aureta ba. Kawai na bata lokaci ne ta huta sannan ta huce daga ɓacin ran da take ciki."