Sashe 17
Idan An Ciza Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gabatowar wasan da suka shirya ne ya sa ya rage Tunani da damuwar Mimi sai da aka buga wasa aka ta shi lafiya sannan ya dawo natsuwarsa, kuma shi abin da ke ba shi mamaki Inna ƙiri ƙiri ta nuna ta fi son Mimi a kansa tsakani ga Allah shi fa Ɗanta ne, Ita fa Iyayenta ba su juya mata baya ba sai shi? Haka zai je Inna Meri ta yi kamar ba ta gan shi ba da ya Kira Mu'azzam ya yi masa ƙorafin abin da inna ke yi masa kai tsaye ya ce"Ni fa ba ruwana tunda ka ce kowa ya cire bakin shi a ciki."
Cikin haɗe rai Aji ya ce"A maganar Mimi ba, maganar Inna fa dole za ka yi min amfani ka kira ta ka nuna mata ni fa Ɗan ta ne ai bai kamata tana banzarta da ni ba, ita kanta Mimin da take min haka saboda Ita iyayenta ai ba su nuna son fi sona da ita ba, Itama Inna ta gane mana kowa fa nashi ya sani."
Mu'azzam na ta faman danne dariyansa, amman sai da ta fito Aji ya ji sa.
Sai kawai ya yi kafci kafin ya ce" Au dariya na baka? Ya yi maka kyau."
Daga nan ya kashe wayarsa, Mu'azzam ya biyo bayan kiran aka yi banza da shi ba'a É—auka ba.
Dole ya Kira inna Meri domin yi ma fan'uwansa biko, ya kuma maida mata abin da Mansoor ɗin ya ce kowa fa na shi ya Sani inna, ki yi masa hakuri in sha Allahu zai daidaita komai. Sai da ta gama jinsa sarai kafin ta ce"Mu'azzamu in kana son kanka da arziƙi a wajena kada ka ƙara kirana kan mganar ɗan'uwanka, ni na ce na yafe masa amman na tsame hannuna a kan rayuwarsa ya yi duk yadda ya ga dama."
Mu'azzam ya ce"Inna to ai baki haƙuran ba kenan, cewar da ki ke yi kin tsame a hannun ki a kansa kamar baki ne fa ki ka yi masa"
Inna Meri ta ce"Ban yi masa baki ba, kuma na yafe masa saboda ɓacin raina ma kaɗai bala'I ne wajensa, amman ba zan ƙara bari Baban inna ya ɓatamin rai ba, tunda shi haka ya ke ba ya jin mgana sannan abin da ya ga dama shi yake yi to ba sai ya je ya yi ta yi ba, ai yanzu ba mai ce masa don me, ni ce kuma na tsame bakina da hannuna a kan sa."
Mu'azzam na so ya ƙara mgana. Amman Inna Meri ta ƙi sauraran shi cewa ta yi in mganar da ya kirata su yi kenan za ta kashe wayarta dole ya bar maganar.
Sai washegari ya samu Aji ya É—auki wayarsa shi kuma ya gaya masa yadda suka yi da Inna numfashi ya furzar kafin ya ce" Ai shike nan."
Mu'azzam ya ce"Mafi masalaha ka je ka Dawo da Anty Mami in har kana son Inna ta Daina fushi da kai."
Cikin jin haushi ya ce"Wai ba na je ba. Tayi tafiyarta wai Abuja domin ta raina ni, da aurena a kanta amman iyayenta sun barta tana yawon tafiye tafiye."
Yadda ya faÉ—i mganar ne ya sa Mu'azzam ya yi shuru yana danne dariya kada ta fito abin a ya shafe sa.
"Gaskiya ba ta kyauta ba. To ka kira ta a waya mana?
"To taba É—auka ne? Wani irin kira ne ban yi mata ba ta É—aga kirana ba."
Mu'azzam ya yi tsai kafin ya ce"Topha! To ko za ka shirya ka je can Abujan ne ka same ta? Kasan mata fa yan Lallashi ne in ta ga ka Bbta za ta sauko sai ta Saurare ka."
Kai tsaye ya ce"Amman ba ka da hankali Mu'azzam ni ne zan bi ta har Abujan? Lalle to ta shekara a can."
Mu'azzam na shafa kansa daga can bangaren ya ce"Ba za a yi haka ba. Ya kamata ka samo mafita saboda Inna."
"To ai daman saboda ita ne ya sa ka ga ina bin ta amman ni har Mimi ta isa ina kiran ta a waya tana min wulaƙanci?
Sai ya yi kafci kuma shi kaɗai irin abun ya nan ya gama ɓata masa rai. Shi ko Mu'azzam wayar ya matsar gefe yana ta dariya shi kaɗai sai ji ya yi Aji na faɗin"Ni na ce ba zan kara kiranta ba amman kai in za ka kirata ne ba zan hana ka ba tunda ka matsa"
Mu'azzam ya yi ta dariya bayan sun gama waya da daddare ne lokacin Hibba na tiolet ta na wanka tun tana ciki ta ke jiyo dariyan Mijinta sanda ta fito ta iske shi ya na Dariya shi kaÉ—ai cikin mamaki ta ce"Me ka samu ne kake ta dariyan nishaÉ—i?
Yana dariya yana tuna amsar da ya bama Yayan na shi da cewa" Nima fa ba ta ɗaukan wayata. Sannan daga baya ma ina jin rufe ni ta yi ko na kira ta ba na samun ta, Ai ina ganin wannan faɗan ya fi karfin ƙanin miji sai dai mijin da kansa."
Kawai sai Aji ya ce"Kai dai ka sani."
Da haka ya katse wayarsa ya bar Mu'azzam na Kwasan dariya shi kaÉ—ai.
"Ina nan ina dariyan Yaya Mansoor, ina tunanin mu kusa mu ji shi a garin Abuja ya je biko."
Hibba ta ƙariso gefensa da sauri tana faɗin" Ba ni in sha, me ya faru?.
Nan ya labartamata abin da Yayan na shi ya gaya masa yaje gidan Hajiya Mimi ta tafi abuja sannan ya na kiran wayanta ba ta É—auka.
Hibba ta saka dariyan ƙeta kafin ta ce"Kai na gode ma Mimi, ai sannu sannu ba ta hana zuwa sai dai a ɗaɗe ba'a je ba."
Mu'azzam ya ce"Ina tsausayin shi ni nasan duk ya damu amman ba ya son ya nuna ace ya damu da ita, kuma muna nan dake zai kirani ya ce zai je Abuja amman saboda Inna ne."
Hibba na dariya ta ce"Nan gaba kaÉ—an zai ce saboda ke ce rayuwata. Sunan Inna tuni zai manta da shi."
Dariya suka saka har suna tafawa, Mu'azzam ya san waye yayan shi fiye da kowa amman ya na tausaya masa Saboda ga duk alamu wannan karon Mimi sai ta Jijiiga yan maza. Daran shi da Hibba kusan raba dare suka yi suna ta tattauna batun Hibba na goyon bayan Mimi shi kuma Yana goyon bayan Yayan shi yana tausayin shi ita kuma Hibba ta ce ai gwara dai a jijjiga shi saboda duk abin a ya faru shi ya ja. Daman ance ai dama É—aya take zuwa a rayuwa shi ya bar daman na shi tun a farko ga shi yanzu ya fara nadama dukda dai bai fito ya furta ba amman kowa ya san ya yi nadaman maganganun da ya faÉ—a Mimi a wannan daran.
******
Mansoor bai ƙara tsinkewa da lamarin ba sai daran ranar jumma'a da ya zo gidan, shima ɗin ya zo duba Baba ne da baya jin daɗi mura ta kwantar da shi.Shima sanin shi Yaya Amina ce ta kira shi take gayamasa Mu'azzam ma ya kira shi baya kusa da kuma ya zo ya gani bai kira ba.
Baban ya ji sauƙi amman ranar bai fita ko'ina ba yana gida. Zuwan Mansoor ne ya Dauke sa zuwa wani ƙaramin cinic suka amso mganguna ya biya ya siya masa tsire da fura sannan ya dawo da shi gida ya kuma kaisa har ɗakinsa ya tsaya a kansa ya ci naman ya sha furan kaɗan ya balla masa magunguna ya sha ya kwanta.
Inna Meri ta yi ta shigowa duba shi. Anan ne na yake ce mata ta ɗauki tuwon ta ya yi kwantai. Tsire Baban inna ya siya masa ya ci ya ƙoshi, ba musu Inna ta ɗauke kwanukanta Mansoor yana shirin ya ci ne ya ga Tuwo ne miyar Kuɓewa ɗanya amnan tunda Inna ta kwashe kayanta ya san sai dai ya haɗiye yunwarsa.
Shigowar Magajiya ya sa ya bar ɗakin zuwa bangaren Inna ba wutar nepa amman akwai hasken farin wata sannan garin an fara zafi. Da ya sawo kanshi shashen ya ga mutun kwance gabda ƙofar ɗakin Inna Meri, ya ɗauka Walida ce bai kawo ma kansa matar Saddiqu ba ce shi ya sa yana karisowa ya fara faɗin" Ke Walida ƙofar ɗaki ne wajen kwanciya? Ba na son wawanci kwashe wannan shinfiɗar a wajen"
Shuru ba magana sai ranshi ya ɓaci ya Daka mata tsawa ya na mai kiran sunanta amman Maeesha ko gizau daman tun fara zafi ta samu wannan iskancin sai ta zo ta simfiɗa abin shimfida ƙofar ɗakin Inna, ko innar ne sai da ta raɓa ta gefe ta wuce Walida ta yi mata magana ta ce ɗan cikinta ba ya son zafi ko za ta hana ta kwanciya ne Inna ta ce ta ƙyaleta kada ta kara mgana.
"Yayanmu gani nan fa."
Walida ta katse shi daga Kiran sunanta da yake yi, ya ɗaga kai yana kallonta cikin mamaki kafin Ya yi mgana da sauri ta ce"Matar Yaya Saddiqu ce."
BuÉ—e ido ya yi kafin ya ce"Oh iskancin nata nan kuma ya dawo? In iskar take son sha ta je Kofar É—akin magajiya mana sai anan duk ta tare ma mutane hanya"
Bai tsaya ba kawai ya nufeta gadan gadan kamar zai takata da sauri ta matsa baya da sauri da kwanciyar sarakai ta yi tana hararan shi tana ko matsawa ya saka takalminshi ya ture shimfiÉ—ar yana faÉ—in"In ta sake kwanciya kada wanda ya kauce mata, ku taka ta ku wuce"
"A taka ni fa ka ce? Saboda ba ka da asara.?
Cikin haɗe rai Aji ya ce"A maganar Mimi ba, maganar Inna fa dole za ka yi min amfani ka kira ta ka nuna mata ni fa Ɗan ta ne ai bai kamata tana banzarta da ni ba, ita kanta Mimin da take min haka saboda Ita iyayenta ai ba su nuna son fi sona da ita ba, Itama Inna ta gane mana kowa fa nashi ya sani."
Mu'azzam na ta faman danne dariyansa, amman sai da ta fito Aji ya ji sa.
Sai kawai ya yi kafci kafin ya ce" Au dariya na baka? Ya yi maka kyau."
Daga nan ya kashe wayarsa, Mu'azzam ya biyo bayan kiran aka yi banza da shi ba'a É—auka ba.
Dole ya Kira inna Meri domin yi ma fan'uwansa biko, ya kuma maida mata abin da Mansoor ɗin ya ce kowa fa na shi ya Sani inna, ki yi masa hakuri in sha Allahu zai daidaita komai. Sai da ta gama jinsa sarai kafin ta ce"Mu'azzamu in kana son kanka da arziƙi a wajena kada ka ƙara kirana kan mganar ɗan'uwanka, ni na ce na yafe masa amman na tsame hannuna a kan rayuwarsa ya yi duk yadda ya ga dama."
Mu'azzam ya ce"Inna to ai baki haƙuran ba kenan, cewar da ki ke yi kin tsame a hannun ki a kansa kamar baki ne fa ki ka yi masa"
Inna Meri ta ce"Ban yi masa baki ba, kuma na yafe masa saboda ɓacin raina ma kaɗai bala'I ne wajensa, amman ba zan ƙara bari Baban inna ya ɓatamin rai ba, tunda shi haka ya ke ba ya jin mgana sannan abin da ya ga dama shi yake yi to ba sai ya je ya yi ta yi ba, ai yanzu ba mai ce masa don me, ni ce kuma na tsame bakina da hannuna a kan sa."
Mu'azzam na so ya ƙara mgana. Amman Inna Meri ta ƙi sauraran shi cewa ta yi in mganar da ya kirata su yi kenan za ta kashe wayarta dole ya bar maganar.
Sai washegari ya samu Aji ya É—auki wayarsa shi kuma ya gaya masa yadda suka yi da Inna numfashi ya furzar kafin ya ce" Ai shike nan."
Mu'azzam ya ce"Mafi masalaha ka je ka Dawo da Anty Mami in har kana son Inna ta Daina fushi da kai."
Cikin jin haushi ya ce"Wai ba na je ba. Tayi tafiyarta wai Abuja domin ta raina ni, da aurena a kanta amman iyayenta sun barta tana yawon tafiye tafiye."
Yadda ya faÉ—i mganar ne ya sa Mu'azzam ya yi shuru yana danne dariya kada ta fito abin a ya shafe sa.
"Gaskiya ba ta kyauta ba. To ka kira ta a waya mana?
"To taba É—auka ne? Wani irin kira ne ban yi mata ba ta É—aga kirana ba."
Mu'azzam ya yi tsai kafin ya ce"Topha! To ko za ka shirya ka je can Abujan ne ka same ta? Kasan mata fa yan Lallashi ne in ta ga ka Bbta za ta sauko sai ta Saurare ka."
Kai tsaye ya ce"Amman ba ka da hankali Mu'azzam ni ne zan bi ta har Abujan? Lalle to ta shekara a can."
Mu'azzam na shafa kansa daga can bangaren ya ce"Ba za a yi haka ba. Ya kamata ka samo mafita saboda Inna."
"To ai daman saboda ita ne ya sa ka ga ina bin ta amman ni har Mimi ta isa ina kiran ta a waya tana min wulaƙanci?
Sai ya yi kafci kuma shi kaɗai irin abun ya nan ya gama ɓata masa rai. Shi ko Mu'azzam wayar ya matsar gefe yana ta dariya shi kaɗai sai ji ya yi Aji na faɗin"Ni na ce ba zan kara kiranta ba amman kai in za ka kirata ne ba zan hana ka ba tunda ka matsa"
Mu'azzam ya yi ta dariya bayan sun gama waya da daddare ne lokacin Hibba na tiolet ta na wanka tun tana ciki ta ke jiyo dariyan Mijinta sanda ta fito ta iske shi ya na Dariya shi kaÉ—ai cikin mamaki ta ce"Me ka samu ne kake ta dariyan nishaÉ—i?
Yana dariya yana tuna amsar da ya bama Yayan na shi da cewa" Nima fa ba ta ɗaukan wayata. Sannan daga baya ma ina jin rufe ni ta yi ko na kira ta ba na samun ta, Ai ina ganin wannan faɗan ya fi karfin ƙanin miji sai dai mijin da kansa."
Kawai sai Aji ya ce"Kai dai ka sani."
Da haka ya katse wayarsa ya bar Mu'azzam na Kwasan dariya shi kaÉ—ai.
"Ina nan ina dariyan Yaya Mansoor, ina tunanin mu kusa mu ji shi a garin Abuja ya je biko."
Hibba ta ƙariso gefensa da sauri tana faɗin" Ba ni in sha, me ya faru?.
Nan ya labartamata abin da Yayan na shi ya gaya masa yaje gidan Hajiya Mimi ta tafi abuja sannan ya na kiran wayanta ba ta É—auka.
Hibba ta saka dariyan ƙeta kafin ta ce"Kai na gode ma Mimi, ai sannu sannu ba ta hana zuwa sai dai a ɗaɗe ba'a je ba."
Mu'azzam ya ce"Ina tsausayin shi ni nasan duk ya damu amman ba ya son ya nuna ace ya damu da ita, kuma muna nan dake zai kirani ya ce zai je Abuja amman saboda Inna ne."
Hibba na dariya ta ce"Nan gaba kaÉ—an zai ce saboda ke ce rayuwata. Sunan Inna tuni zai manta da shi."
Dariya suka saka har suna tafawa, Mu'azzam ya san waye yayan shi fiye da kowa amman ya na tausaya masa Saboda ga duk alamu wannan karon Mimi sai ta Jijiiga yan maza. Daran shi da Hibba kusan raba dare suka yi suna ta tattauna batun Hibba na goyon bayan Mimi shi kuma Yana goyon bayan Yayan shi yana tausayin shi ita kuma Hibba ta ce ai gwara dai a jijjiga shi saboda duk abin a ya faru shi ya ja. Daman ance ai dama É—aya take zuwa a rayuwa shi ya bar daman na shi tun a farko ga shi yanzu ya fara nadama dukda dai bai fito ya furta ba amman kowa ya san ya yi nadaman maganganun da ya faÉ—a Mimi a wannan daran.
******
Mansoor bai ƙara tsinkewa da lamarin ba sai daran ranar jumma'a da ya zo gidan, shima ɗin ya zo duba Baba ne da baya jin daɗi mura ta kwantar da shi.Shima sanin shi Yaya Amina ce ta kira shi take gayamasa Mu'azzam ma ya kira shi baya kusa da kuma ya zo ya gani bai kira ba.
Baban ya ji sauƙi amman ranar bai fita ko'ina ba yana gida. Zuwan Mansoor ne ya Dauke sa zuwa wani ƙaramin cinic suka amso mganguna ya biya ya siya masa tsire da fura sannan ya dawo da shi gida ya kuma kaisa har ɗakinsa ya tsaya a kansa ya ci naman ya sha furan kaɗan ya balla masa magunguna ya sha ya kwanta.
Inna Meri ta yi ta shigowa duba shi. Anan ne na yake ce mata ta ɗauki tuwon ta ya yi kwantai. Tsire Baban inna ya siya masa ya ci ya ƙoshi, ba musu Inna ta ɗauke kwanukanta Mansoor yana shirin ya ci ne ya ga Tuwo ne miyar Kuɓewa ɗanya amnan tunda Inna ta kwashe kayanta ya san sai dai ya haɗiye yunwarsa.
Shigowar Magajiya ya sa ya bar ɗakin zuwa bangaren Inna ba wutar nepa amman akwai hasken farin wata sannan garin an fara zafi. Da ya sawo kanshi shashen ya ga mutun kwance gabda ƙofar ɗakin Inna Meri, ya ɗauka Walida ce bai kawo ma kansa matar Saddiqu ba ce shi ya sa yana karisowa ya fara faɗin" Ke Walida ƙofar ɗaki ne wajen kwanciya? Ba na son wawanci kwashe wannan shinfiɗar a wajen"
Shuru ba magana sai ranshi ya ɓaci ya Daka mata tsawa ya na mai kiran sunanta amman Maeesha ko gizau daman tun fara zafi ta samu wannan iskancin sai ta zo ta simfiɗa abin shimfida ƙofar ɗakin Inna, ko innar ne sai da ta raɓa ta gefe ta wuce Walida ta yi mata magana ta ce ɗan cikinta ba ya son zafi ko za ta hana ta kwanciya ne Inna ta ce ta ƙyaleta kada ta kara mgana.
"Yayanmu gani nan fa."
Walida ta katse shi daga Kiran sunanta da yake yi, ya ɗaga kai yana kallonta cikin mamaki kafin Ya yi mgana da sauri ta ce"Matar Yaya Saddiqu ce."
BuÉ—e ido ya yi kafin ya ce"Oh iskancin nata nan kuma ya dawo? In iskar take son sha ta je Kofar É—akin magajiya mana sai anan duk ta tare ma mutane hanya"
Bai tsaya ba kawai ya nufeta gadan gadan kamar zai takata da sauri ta matsa baya da sauri da kwanciyar sarakai ta yi tana hararan shi tana ko matsawa ya saka takalminshi ya ture shimfiÉ—ar yana faÉ—in"In ta sake kwanciya kada wanda ya kauce mata, ku taka ta ku wuce"
"A taka ni fa ka ce? Saboda ba ka da asara.?