Sashe 81
Buzu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Likitoci suka ce tiyata za a yi mata a cire abin da yake cikinta. Nana ta kira Hammad ta ce masa lallai ya dawo, tiyata za a yi wa Asal ana buƙatar a saka hannu.
Ya ce "Ki saka, ba zan iya dawowa a yau ba, sai zuwa gobe in Allah ya kaimu"
Nana ta ce "To ai ba zai yiwu ni na saka ba, ko a kira mahaifinta a waya?"
Da sauri ya ce "A'a bari na kira Sultan, kuma ki tsaya ki bayar da order, kar wani ya zo a ba shi É—ana, idan ba ke ko Sultan ba, babu yadda zan yi na dawo ne"
Haka aka yi, Sultan ya je Asibiti da kansa ba wakilici ba, ya sanya hannu aka ciro wa Asal jaririyarta. Nana aka fara ba wa yarinyar, ta yi wata irin ajiyar zuciya tare da gode wa Allah, sannan ta kai wa Sultan ita.
Ya rungume yarinyar yana kallonta cike da ƙauna, ya ce "Kin ga ikon Allah, bayan shekaru kusan ashirin da aure, sai yanzu Allah ya yi ikonsa"
Nana ta ce "Tabbas Allah abin godiya, Abin da na yi ta gaya wa Sayyid kenan, ba a cire rai da rahamar Allah.
Asal na kwance a post up room, ta buÉ—e idanunta a hankali, ta kalli Nana da take ta shafa kan jaririyar. Tsawon wannan shekarun, babu wata jituwar arziki a tsakaninsu, sai dai tun kiran da Sultan ya yi musu, ya yi musu nasiha Nana ta daina hana yaranta zuwa inda Asal take.
Aka sanar da haihuwar Asal, amma aka hana kowa zuwa Asibitin da take.
'ya'yan Nana haka suka kewaye Asal da jaririyar nan, wannan ya É—auka wannan ya É—auka.
Da kyar suka tafi gida, saboda makaranta. Ƙarfe sha biyu da rabi Hammad ya iso Asibitin. Ya tarar da Nana tana shirya jaririyar a cikin kaya.
Bakinsa ya kasa rufuwa, ya miƙa mata hannu ta bashi, Nana ta ce "Ba tukuici babu komai"
"Zan baki idan muka haɗu" Tana murmushi ta miƙa masa jaririyar, ta tashi ta basu guri. Ya ƙarasa kusa da Asal yana murmushi ys rungumota ya sumbaci goshinta. Ya ce "Kin ga ikon Allah ko Cherié?"
Ta yi murmushi ta ce "Na gani, kalli kamar ta É—aya da Yarima, duk kamar ka suke yi"
Ya yi dariya ya ce "Ba dole su yi kama da ni ba, ni É—in na wasa ne. Alhamdillah bayan samari da Allah ya bamu ga 'yar budurwa."
Asal ta ce "A saka mata Asma'u" da sauri ya waiwayo ya kalle ta, ya ce "Ba na son wasa"
"Da gaske nake, na ga kana sonta da yawa, ko ita ma za ta ci albarkacin son da ka ke yi wa rayuwarta, ka so ta sosai"
Hammad ya ce "Kin ga ni ba na son rigima daga haihuwar ki, ke cewa na yi ba na sonki ne?"
Ta girgiza kai ta ce "Ai ba ƙarya na yi ba, da na ce ka na sonta sosai, kuma ta cancanci ka so ta, na gane hakan bayan da na saurari yadda aka yi ka aure ta, da irin rayuwar da ku ka yi da kunnen basira. Duk a ajiye wannan a gefe, tsawon wannan lokacin na rayu da ci gaba da sanya ran samun haihuwa da kalamanta da suka bani ƙwarin gwiwa. Lokacin da na dawo gidanka, babu daɗewa, cikin dare na tashi fitsari saƙo ya shigo wayarka ƙarfe uku na dare. Na ɗau wayar na duba sai na ga saƙonta ne, ta ce ; Albishirinka yanzu na tashi daga barci, na yi mafarkin Asal ta haihu, ana ta shagali har na tashi ina jin abin a jikina da zuciyata, ko a kusa ko a nesa mafarkin nan zai zama gaske in sha Allah, ka samu maƙubaci ka bayar da nannauyar sadaka, Allah ya tabattar mana. Kuma idan mace ce sunana za ka saka"
Duk da a lokacin da naga saƙon nan, na cire rai da samun haihuwa, amma a duk lokacin da na tuna saƙon nan, sai na ji ina ƙara sanya rai. Tsawon shekara goman nan, wannan saƙon nata yana cikin kaina, ina jin sa ina fatan Allah ya tabattar da shi. Babu wanda na taɓa gayawa sai yanzu da nake gaya maka. Bayan haka sanin sirrina, da abubuwan da na aikata bai taɓa sanyawa ko sau ɗaya ta kalle ni ta yi mini gori, da abubuwan da na aikata ba, banda barazanar da ta yi mini, lokacin da na gano matarka ce ita. Kuma bata taɓa yi mini wani abu, na gadara ko makamancin haka ba, saboda ta haihu da kai ni ban haihu ba. Ko na yi yunkurin sanya wa zuciyata irin wannan tunanin Hasna da Fadila su na ankarar da ni, mussaman da Fadila ta gaya mini Nana tana addu'ar ka da Allah ya sanya mata jin wani abu a ranta, dan ta haihu ni ban haihu ba, balle ta yi wani abu da zai sosa mini rai.
A ƙarshe, na san maganin da ka kawo mini, ita ta sarrafa shi a kaina ta yi gwajin maganin haihuwa, kuma Allah ya amsa.
Babu riba yin adawa da mutane irinta, rayuwarta take yi kai tsaye, ba tare da ƙyashi ko baƙin ciki ba. Kuma kasancewata tare da su Hasna, suna ƙara saita ni, saɓanin da da nake tare da miyagun ƙawaye.
Na san ba zan taɓa kai wa ko rabinta a zuciyarka ba, kuma ba zan yi maka dole ba, iya wannan jihadin na zama da ni ka yi, ya isa a kira ka gwarzo, kuma hakan ne hukuncin da ya dace da ni, kana iya ƙoƙarinka a kaina, amma ni dai ka saka mini sunanta, ba kuma na yi hakan dan na burge ku ba ne, ko a ce tsirfa ba ce, a'a na yi hakan ne saboda jin wani sashin na damuwata da ta yi kamar tata."
Gaba É—aya jikin Hammad ya yi sanyi sosai da sosai.
Ya rungumo Asal a jiknsa, yana sumbatar goshinta ya ce "Abubuwan da suka faru sun riga sun wuce, ki daina dawo da su. Kuma tun farko abubuwan ku ne na kishi da yake damunku, amma tabbas Nana tana da halaye da É—abi'u na kirki, ina fatan Ubangiji Allah ya haÉ—a mini kanku gaba É—aya ya shirya mini yarana".
Nana ta ƙwanƙwasa ƙofar ta yi sallama, suka amsa, ta shigo da kwanukan Abinci.
Hammad ya ce "Wai gida ki ka je?"
"Eh na je na É—aukko Abinci ne, mutane na ta son su zo su ga jaririya fa."
"Ki ƙyale su, idan sun koma gida a ganta"
Har ranar suna Nana ba ta san sunanta za a saka wa jaririyar ba, aka shirya gagarumin suna a Agadez. Nana ta yi wa jaririyar nan kaya na alfarma. Kawai ta ji Hammad yana gaya wa Zahradeen wai sunan jaririya Asma'u. Nana ta yi turus ta ce "Sayyid, amma da wasa ka ke yi ko?"
"Kamar yaya wasa? Da gaske nake"
Cikin damuwa ta ce "Dan zatin Allah ka yi haƙuri, wannan ai rigima ce, kawai salon ka ja mini magana a garin nan, shekara da shekaru tana neman abu, ta sha wahala ta haihu kuma a saka sunana?"
"To ai ita ta nemi hakan ba ni ba"
Nana ta girgiza kai ta ce "A'a ka yi mata fin ƙarfi dai, Asal ba za ta yarda a saka wa yarinyarta sunana ba. Ni dai dan Allah ka canza"
Kawai ya hau dariya, ya ce "To ni yaya zan yi muku? Idan kin je gurin sunan, ki tambaye ta"
Nana ta ce "A'a ni dai na yafe, dan Allah ka canza mata suna, ya za a yi ka yi mata haka, salon kawai ka saka a ƙara tsana ta"
"To ai ni ina sonki dan a tsane ki ba komai tun da ina sonki"
Da gaske Nana ta fututtuke ta ce bata yarda ba, sai da ya É—auke ta suka je gidan.
Asal ta ce "Dan na ce a saka wa jaririyar ki sunanki shi ne za ki ce ba kya so? Kina jin haushina kenan tun abubuwan da suka faru tsawon shekaru goma"
Nana ta ce "Wallahi ba haka ba ne ba, ba na son a yi miki fin ƙarfi ne, a takura miki abin da ba kya so"
Asal ta ce "A'a ni na ce a saka mata, babu wanda ya takura mini" Nana ta yi wa Nana bayani kamar yadda ta yi wa Hammad, sannan ta ɗora da cewa "Nana ni da ke mu na da tabon juna, da ba zai taɓa yiwuwa na ce sai mun yi nu'amala da juna ba. Amma ina son yaranmu su tashi da haɗin kai, kamar yadda ki ka kawar da kai ki ka nuna mini yaranki nawa ne. Ba na fatan a sake samun matsala na rabuwar kawuna saboda mulki ko abin Duniya a tsakanin yaranmu. Ina fatan za ki saka mini takwarar ki a cikin su Yarima, ta samu kyakykywar kulawa. Kuma ina godiya da dukkanin wasu abubuwa na alkhairi da ki ka yi mini, da ɗaukar damuwa ta taki, duk da ba jituwa muke yi ba"
Wani irin farinciki ya mamaye ta, ta ce "Tabbas takwarata kin haife ta ne, amma ni ki ka haifawa. Kuma na yi wannan alƙawarin na sanya ta cikin jerin 'ya'yana. Ya hayyu ya ƙayyum Ubangiji Allah ya kawo biyar a bayan ta"
Asal ta ce "Biyar sun yi yawa ai, yadda shekaruna su ka ja É—in nan? Ita É—in ma na gode Allah"
Nana ta ce "Taskar Allah babu abin da babu, ko ba biyar ba Allah ya ƙaro mana wasu, shekara iyanzu a ce an kusa haifo mana wasu. Na gode sosai da sosai da karamcin nan da ki ka yi mini"
Jin sunan da aka saka wa jaririya, ya janyo cecekuce sosai da sosai a garin. Da ganin kamar ba a yi wa Asal adalci.
Kwanan Husna arba'in, Nana ta buÉ—e cibiyar magungunan musulunci.
Manyan mutane duk sun halarta, har da 'yan uwan Nana na Nigeria. A daidai lokacin ta kammala rubutun littafinta, da ta yi bincike tsawon shekaru, a kan aljanu, da ilimin ruƙiyya da ladduban yin ta.
A cikin sunayen mutane masu muhimmanci da ta lissafo a cikin littafin, sai da ta sanya sunan Ƙaisar Giyaz.
Ya ce "Ki saka, ba zan iya dawowa a yau ba, sai zuwa gobe in Allah ya kaimu"
Nana ta ce "To ai ba zai yiwu ni na saka ba, ko a kira mahaifinta a waya?"
Da sauri ya ce "A'a bari na kira Sultan, kuma ki tsaya ki bayar da order, kar wani ya zo a ba shi É—ana, idan ba ke ko Sultan ba, babu yadda zan yi na dawo ne"
Haka aka yi, Sultan ya je Asibiti da kansa ba wakilici ba, ya sanya hannu aka ciro wa Asal jaririyarta. Nana aka fara ba wa yarinyar, ta yi wata irin ajiyar zuciya tare da gode wa Allah, sannan ta kai wa Sultan ita.
Ya rungume yarinyar yana kallonta cike da ƙauna, ya ce "Kin ga ikon Allah, bayan shekaru kusan ashirin da aure, sai yanzu Allah ya yi ikonsa"
Nana ta ce "Tabbas Allah abin godiya, Abin da na yi ta gaya wa Sayyid kenan, ba a cire rai da rahamar Allah.
Asal na kwance a post up room, ta buÉ—e idanunta a hankali, ta kalli Nana da take ta shafa kan jaririyar. Tsawon wannan shekarun, babu wata jituwar arziki a tsakaninsu, sai dai tun kiran da Sultan ya yi musu, ya yi musu nasiha Nana ta daina hana yaranta zuwa inda Asal take.
Aka sanar da haihuwar Asal, amma aka hana kowa zuwa Asibitin da take.
'ya'yan Nana haka suka kewaye Asal da jaririyar nan, wannan ya É—auka wannan ya É—auka.
Da kyar suka tafi gida, saboda makaranta. Ƙarfe sha biyu da rabi Hammad ya iso Asibitin. Ya tarar da Nana tana shirya jaririyar a cikin kaya.
Bakinsa ya kasa rufuwa, ya miƙa mata hannu ta bashi, Nana ta ce "Ba tukuici babu komai"
"Zan baki idan muka haɗu" Tana murmushi ta miƙa masa jaririyar, ta tashi ta basu guri. Ya ƙarasa kusa da Asal yana murmushi ys rungumota ya sumbaci goshinta. Ya ce "Kin ga ikon Allah ko Cherié?"
Ta yi murmushi ta ce "Na gani, kalli kamar ta É—aya da Yarima, duk kamar ka suke yi"
Ya yi dariya ya ce "Ba dole su yi kama da ni ba, ni É—in na wasa ne. Alhamdillah bayan samari da Allah ya bamu ga 'yar budurwa."
Asal ta ce "A saka mata Asma'u" da sauri ya waiwayo ya kalle ta, ya ce "Ba na son wasa"
"Da gaske nake, na ga kana sonta da yawa, ko ita ma za ta ci albarkacin son da ka ke yi wa rayuwarta, ka so ta sosai"
Hammad ya ce "Kin ga ni ba na son rigima daga haihuwar ki, ke cewa na yi ba na sonki ne?"
Ta girgiza kai ta ce "Ai ba ƙarya na yi ba, da na ce ka na sonta sosai, kuma ta cancanci ka so ta, na gane hakan bayan da na saurari yadda aka yi ka aure ta, da irin rayuwar da ku ka yi da kunnen basira. Duk a ajiye wannan a gefe, tsawon wannan lokacin na rayu da ci gaba da sanya ran samun haihuwa da kalamanta da suka bani ƙwarin gwiwa. Lokacin da na dawo gidanka, babu daɗewa, cikin dare na tashi fitsari saƙo ya shigo wayarka ƙarfe uku na dare. Na ɗau wayar na duba sai na ga saƙonta ne, ta ce ; Albishirinka yanzu na tashi daga barci, na yi mafarkin Asal ta haihu, ana ta shagali har na tashi ina jin abin a jikina da zuciyata, ko a kusa ko a nesa mafarkin nan zai zama gaske in sha Allah, ka samu maƙubaci ka bayar da nannauyar sadaka, Allah ya tabattar mana. Kuma idan mace ce sunana za ka saka"
Duk da a lokacin da naga saƙon nan, na cire rai da samun haihuwa, amma a duk lokacin da na tuna saƙon nan, sai na ji ina ƙara sanya rai. Tsawon shekara goman nan, wannan saƙon nata yana cikin kaina, ina jin sa ina fatan Allah ya tabattar da shi. Babu wanda na taɓa gayawa sai yanzu da nake gaya maka. Bayan haka sanin sirrina, da abubuwan da na aikata bai taɓa sanyawa ko sau ɗaya ta kalle ni ta yi mini gori, da abubuwan da na aikata ba, banda barazanar da ta yi mini, lokacin da na gano matarka ce ita. Kuma bata taɓa yi mini wani abu, na gadara ko makamancin haka ba, saboda ta haihu da kai ni ban haihu ba. Ko na yi yunkurin sanya wa zuciyata irin wannan tunanin Hasna da Fadila su na ankarar da ni, mussaman da Fadila ta gaya mini Nana tana addu'ar ka da Allah ya sanya mata jin wani abu a ranta, dan ta haihu ni ban haihu ba, balle ta yi wani abu da zai sosa mini rai.
A ƙarshe, na san maganin da ka kawo mini, ita ta sarrafa shi a kaina ta yi gwajin maganin haihuwa, kuma Allah ya amsa.
Babu riba yin adawa da mutane irinta, rayuwarta take yi kai tsaye, ba tare da ƙyashi ko baƙin ciki ba. Kuma kasancewata tare da su Hasna, suna ƙara saita ni, saɓanin da da nake tare da miyagun ƙawaye.
Na san ba zan taɓa kai wa ko rabinta a zuciyarka ba, kuma ba zan yi maka dole ba, iya wannan jihadin na zama da ni ka yi, ya isa a kira ka gwarzo, kuma hakan ne hukuncin da ya dace da ni, kana iya ƙoƙarinka a kaina, amma ni dai ka saka mini sunanta, ba kuma na yi hakan dan na burge ku ba ne, ko a ce tsirfa ba ce, a'a na yi hakan ne saboda jin wani sashin na damuwata da ta yi kamar tata."
Gaba É—aya jikin Hammad ya yi sanyi sosai da sosai.
Ya rungumo Asal a jiknsa, yana sumbatar goshinta ya ce "Abubuwan da suka faru sun riga sun wuce, ki daina dawo da su. Kuma tun farko abubuwan ku ne na kishi da yake damunku, amma tabbas Nana tana da halaye da É—abi'u na kirki, ina fatan Ubangiji Allah ya haÉ—a mini kanku gaba É—aya ya shirya mini yarana".
Nana ta ƙwanƙwasa ƙofar ta yi sallama, suka amsa, ta shigo da kwanukan Abinci.
Hammad ya ce "Wai gida ki ka je?"
"Eh na je na É—aukko Abinci ne, mutane na ta son su zo su ga jaririya fa."
"Ki ƙyale su, idan sun koma gida a ganta"
Har ranar suna Nana ba ta san sunanta za a saka wa jaririyar ba, aka shirya gagarumin suna a Agadez. Nana ta yi wa jaririyar nan kaya na alfarma. Kawai ta ji Hammad yana gaya wa Zahradeen wai sunan jaririya Asma'u. Nana ta yi turus ta ce "Sayyid, amma da wasa ka ke yi ko?"
"Kamar yaya wasa? Da gaske nake"
Cikin damuwa ta ce "Dan zatin Allah ka yi haƙuri, wannan ai rigima ce, kawai salon ka ja mini magana a garin nan, shekara da shekaru tana neman abu, ta sha wahala ta haihu kuma a saka sunana?"
"To ai ita ta nemi hakan ba ni ba"
Nana ta girgiza kai ta ce "A'a ka yi mata fin ƙarfi dai, Asal ba za ta yarda a saka wa yarinyarta sunana ba. Ni dai dan Allah ka canza"
Kawai ya hau dariya, ya ce "To ni yaya zan yi muku? Idan kin je gurin sunan, ki tambaye ta"
Nana ta ce "A'a ni dai na yafe, dan Allah ka canza mata suna, ya za a yi ka yi mata haka, salon kawai ka saka a ƙara tsana ta"
"To ai ni ina sonki dan a tsane ki ba komai tun da ina sonki"
Da gaske Nana ta fututtuke ta ce bata yarda ba, sai da ya É—auke ta suka je gidan.
Asal ta ce "Dan na ce a saka wa jaririyar ki sunanki shi ne za ki ce ba kya so? Kina jin haushina kenan tun abubuwan da suka faru tsawon shekaru goma"
Nana ta ce "Wallahi ba haka ba ne ba, ba na son a yi miki fin ƙarfi ne, a takura miki abin da ba kya so"
Asal ta ce "A'a ni na ce a saka mata, babu wanda ya takura mini" Nana ta yi wa Nana bayani kamar yadda ta yi wa Hammad, sannan ta ɗora da cewa "Nana ni da ke mu na da tabon juna, da ba zai taɓa yiwuwa na ce sai mun yi nu'amala da juna ba. Amma ina son yaranmu su tashi da haɗin kai, kamar yadda ki ka kawar da kai ki ka nuna mini yaranki nawa ne. Ba na fatan a sake samun matsala na rabuwar kawuna saboda mulki ko abin Duniya a tsakanin yaranmu. Ina fatan za ki saka mini takwarar ki a cikin su Yarima, ta samu kyakykywar kulawa. Kuma ina godiya da dukkanin wasu abubuwa na alkhairi da ki ka yi mini, da ɗaukar damuwa ta taki, duk da ba jituwa muke yi ba"
Wani irin farinciki ya mamaye ta, ta ce "Tabbas takwarata kin haife ta ne, amma ni ki ka haifawa. Kuma na yi wannan alƙawarin na sanya ta cikin jerin 'ya'yana. Ya hayyu ya ƙayyum Ubangiji Allah ya kawo biyar a bayan ta"
Asal ta ce "Biyar sun yi yawa ai, yadda shekaruna su ka ja É—in nan? Ita É—in ma na gode Allah"
Nana ta ce "Taskar Allah babu abin da babu, ko ba biyar ba Allah ya ƙaro mana wasu, shekara iyanzu a ce an kusa haifo mana wasu. Na gode sosai da sosai da karamcin nan da ki ka yi mini"
Jin sunan da aka saka wa jaririya, ya janyo cecekuce sosai da sosai a garin. Da ganin kamar ba a yi wa Asal adalci.
Kwanan Husna arba'in, Nana ta buÉ—e cibiyar magungunan musulunci.
Manyan mutane duk sun halarta, har da 'yan uwan Nana na Nigeria. A daidai lokacin ta kammala rubutun littafinta, da ta yi bincike tsawon shekaru, a kan aljanu, da ilimin ruƙiyya da ladduban yin ta.
A cikin sunayen mutane masu muhimmanci da ta lissafo a cikin littafin, sai da ta sanya sunan Ƙaisar Giyaz.