← Book details Buzu Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 82

Sashe 26

Buzu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Babu tsammani aka banko ƙofar ɗakin, Nana ta yi wata irin zabura, shi kuwa cikin nutsuwa ya waiwaya ya ga waye wannan ya shigo musu babu neman izni.
Da Asal ya yi tozali, jikinta na wata irin tsuma take bin su da kallo. Ta nuna Nana da yatsanta bakinta yana wata irin rawa, jikinta ma karkarwa kawai yake yi, tamkar ana kaÉ—a mata gangi.
Ba ta taɓa tsammanin abin da za ta gani ba kenan, ko a hasashe da tsammani ba ta taɓa hasko ganin Nana tare da mijinta ba. Kasamcewarta baƙar fata da ba ƙabilarsu ba.
"Ham..Ha.ha...Hammad!" Ta faɗa cikin wani irin ƙaraji mai razanarwa.

Bakin Asal ne ya ci gaba da rawa, dan da fari ma kanta gaba É—aya kullewa ya yi, ta manta wace ce ma Nana.
Ita da ta zo tambayarsa ba'asin ina ya samu É—a, sai ta riski abin da ya fi maganar da ta zo da ita tashin hankali.
Hankali kwance Nana ta gyara rigarta, ba tare da abin da ya faru ya É—aga mata hankali ba.
Ja da baya Asal ta fara yi, numfashinta na fita da kyar, jikinta na wata irin kyarma. A sukwane Imam Hammad ya diro daga kan gadon ya nufe ta, cikin tashin hankali bai so Asal ta san alaƙarsa da Nana ta wannan sigar ba. Amma ya san babanta shi ne ya lalata komai.

"Kar ka taɓa ni, kar ka ƙaraso inda nake Hammad. Ka yaudare ni ka zalunce ni, dama rashin lafiyar da ka ke yi ƙarya ka ke yi? Ka haɗa kai da mahaifinka ne dan ku yaudare ni ku cutar da ni? Lalata da wannan ƙasƙantacciyar ƙazamar matar? Na zaɓo ta a matsayin kukunka dan kawar da kanka daga kalle-kallen wasu matan, ashe yaudarata ka ke yi? Tun tsawon lokacin da ta gudu na neme ta na rasa, a she a nan ka ɓoye ta ku ke lalata."

Cikin azama Hammad, ya danƙo hannun Asal, da take ta fizge-fizge ya danna ƙofar ya datse ta. Ya kalli Asal ya ce "Ki nutsu cherié zan yi miki bayani, ni ba lalata nake yi da Asmy ba"
Cike da baƙin ciki take kokowar fizgewa cikin ƙaraji ta ce "Idan ba lalata ku ke yi ba, me ku ke yi? Tsawon wannan lokacin da ba ta nan, ashe ku na tare ka ji kunya ba ka ji daɗin halinka ba. Ke kuma 'yar iska mazinaciya wallahi sai na ƙasaƙantar da ke, sai na saka an kashe mini ke a kashe banza"

Nana ta ce "Point of correction my dear, ba da kukun mijinki ki ke magana ba a yanzu,  kuma ni ba mazinaciya ba ce ba. Ki dai nemi wani sunan ki kira ni da shi"
Ya kalli Nana da ta tsuke fuska ya ce "Ma vie dan Allah ki yi shiru, mu warware matsalar nan a hankali"

AREWABOOKS

Daskarewa Asal ta yi jin sunan da ya kira Nana da shi, wanda shi gaba É—aya ya manta, saboda yadda sunan ya shiga bakinsa ya zauna.

"Hammad gaskiya ne abin kunnuwana suke jiye mini? A gabana? Hammad" Ta furta tana ajiyar zuciya mai ɗauke da nannauyan baƙin ciki da tashin hankali.
Damƙar hannun Asal ya yi, ya buɗe ƙofar suka fita tare.

Kokowa ya shiga yi da Asal, yadda take kai masa duka, tana fizge-fizge.

"Asal, ki tsaya ki saurare ni, kar ki ji wa kan ki ciwo mana"

"Ba zan saurare ka ba, ba na buƙatar duk wasu kalaman yaudara da ƙarya da za su fito daga bakinka. Me ya rage bayan abin da na gani? Da girmanka da mutuncinka ka ɓoye kukunka a sashen mahaifinka kana zina da ita, ba ka ji daɗin halinka ba" Kalaman Asal sun yi wa Hammad zafi nesa ba kusa ba, da kyar ya haɗiye wani yawu mai zafi ya ce "Ni ba zina nake yi ba, idan ba ki tsaya kin saurare ni ba, ki ka fita ki ka yayata abin da ba shikenan ba za ki cutar da ni dan kin yi mini ƙazafi"

Kallonsa take yi, tana jinjina girman yadda ya ƙware a iya wasa da hankali, ta ci gaba da ƙoƙarin fizgewa, amma ya riƙe ta gam.

"Hammad ka gama raina mini hankali, dama ga batun ɗa ana yi, an ce ka na da ɗa da a ƙalla ya shekara biyu, yanzu kuma na kama ka da wata, amma kana iƙrarin zan cutar da kai? Da ni da kai waye ya cutar da wani? Wadda ka yi wa ciki ba ta ishe ka ba, ka ɗauki kukunka ka sanya a sashen Sultan ka ke lalata da ita"

"Ban taɓa cutar da ke ba Asal, a shekara goma sha biyu da muka yi da ke, idan zan iya aikata abin da ki ka faɗa kin sani, idan akasin hakan ne ma kin sani. Amma mu je gurin Sultan ɗin ki ji komai daga bakinsa.

Nana kuwa guntun tsaki ta yi bayan fitarsu, ta tashi ta shiga banɗakin ta yi wanka, ta yi alwala. Ta ƙura wa kanta ido a mudubin banɗakin, tana tunanin yadda Asal ta din ga yi mata kallon ƙasƙanci, da bautar da ita ta ƙarfi da yaji, saboda tana da kuɗi da mulki, a matsayinta na kishiyarta, kuma ta daure ta haɗiye. Ta ci gaba da tunanin daga bisani ta fito da niyyar ta canza kaya, amma ta kasa, ta nemi guri ta zauna ta yi shiru.
A zuciyarta take addu'a ta ce "Allah ga Nana, bakwarka ce ni mai raunin gaske, ga ɗan jaririn ɗa na da nake fatan ya samu kyakykywar rayuwa ya tashi a tsakanin uwa da uba. Ubangiji Allah ka na ji ka na gani, ka ga wahalar da na sha a baya, ga shi na zo wani bugire da nake sanya ran samun afuwa, sai dai alamu sun nuna an fi ƙarfina. Allah idan sun fi ƙarfina ba su fi ƙarfinka ba, da ni da su duk bayinka ne. Ubangiji Allah ka sassauta mini ka kawo mini ɗauki. Ubangiji Allah ka yaye mini wannan kishin da nake ji, ka sanya su bar ni na rayu da mijina da ɗa na. Ubangiji Allah ka ba wa mijina ingantacciyar lafiya ka yaye masa abin da yake damunsa, Allah ka ba kare mini ɗana daga dukkanin sharrin da ido ka iya gani, da wanda ma baya gani. Ƙaisar ma bawanka ne, Allah ka ba shi lafiya. Allah ka ga wahalar da na sha a baya, yanzu idan na koma suka raba ni da ɗa na, wata wahalar zan shiga, Allah ka kawo mini agaji" Sai kuma ta yi shiru tana nazari, duk abin da take faɗa ai Allahan yana ji yana gani.
'Idan ba ubangijina ba, wa nake da shi da zan kaiwa kukana kai tsaye ya share mini. Na san ya sani amma ƙara gaya masan, yana sama mini nutsuwa da kwanciyar hankali, ko da ina cikin damuwa. Ta ba wa kanta amsa.

Asal ce a gaban Sultan, tana ta uban kuka, fuskar nan ta yi jawurr, idanunta sun kumbura sosai da sosai.

Sultan ya yi shiru, saboda yadda abubuwan shi kansa suka kulle masa kai. Gaba É—aya bai yi tunanin abubuwan za su damalmale har haka ba, ya ma rasa ta ina zai fara.
Ya ce "Ki na ji na Asal. Wannan maganar abu ne mai faɗin gaske, da ko ba ki gano ba, dole za a yi miki bayani. Amma wannan bayanin ba ke kaɗai yakamata mu yi wa ba, a gaban mahafinki yakamata mu yi shi. Tabbas da gaske Imam Hammad ba shi da lafiya, kuma ke ma shaida ce, saboda kin zo kin gan shi a halin da yake ciki. Sai dai ita wannan yarinyar tana da alaƙa da samun sauƙinsa. Yanzu bayanin da zan yi miki ba za ki gane ba, ina son sai mun zauna gaba ɗaya za mu yi miki bayani. Amma ki samu nutsuwa ki kwantar da hankalinki.
Gaba ɗaya Asal ba ta fahimci abin da Sultan yake gaya mata ba, gani take kawai yana ƙoƙarin goyon bayan ɗansa ne.
Muryarsa ta sake tsinkayowa yana faÉ—in "Kar ki bari kowa ya ji maganar nan, sai mun zauna an yi miki bayani tukuna dan Allah." Ya dubi Imam Hammad ya ce masa ya kai Asal gida, ya rarrashe ta, ta samu nutsuwa kafin a yi mata bayanin komai.

Nana kuwa kajin gurin Nene ta samu ta ci, saboda taga alamun idan ta biye ta kishin nan, yunwa ce za ta kar ta a banza, duk da yanzu naman duk ya ishe ta, abinci take so ta ci sosai. Ga shi ta yi zaton ko zai dawo mata da Muhsin, amma bai dawo mata da shi ba.

Ba ta sake ganin Hammad ba, sai bayan sha É—aya na dare. Idanunsa jawur da alama yana cikin damuwa kuma ko abinci ba ta tunanin ya ci. Sau É—aya ta kalle shi ta basar, ba ta ko kula shi ba.

Gani ta yi ya cire rigar jiknsa ya yar a ƙasa, ya hau kan gadon ya kwanta, ba ta motsa ba ta ci gaba da zamanta, dan haushinsa ne ma ya kama ta. Jin ya fara numfarfashi ya sanya ta tashi tsaye. Ta kalle shi ta ga ya fara komawa ja. Sai kuma jikinta ya yi sanyi, abin da ta lura da shi kamar ciwon ya fi tsananta masa a Niger.
Ta fara ƙoƙarin ninke masa rigar, kawai wannan takardar ta faɗo daga aljihun rigar. Ta ɗauki takardar ta yi shiru tana kallon takardar.
Ta hau kan gadon ta juya shi da kyar, taga yana ta taune leɓensa yana jujjuya kansa.

"Ki yi mini addu'a, zan mutu" ya furta da kyar kamar numfasihinsa zai É—auke. Suratul Fatiha ta din ga karantawa da Bismillah tana tofa masa. Fizge-fizge ya fara yana girgiza kai ya ce "Tashi mu tafi"

Cikin rashin fahimta ta ce "mu je Ina?"

"Ki tashi nu tafi, kafin na rasa raina" Ya ƙarasa maganar yana dafe kansa da yake jin kamar zai yi bindiga. Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin aka yi. Amma ba damar Nana ta tashi, saboda yadda ya rirriƙeta. Ga shi ta san ko ta ce a shigo babu lallai a jiyota daga waje.
Chapter 26 · 0% Book details