← Book details Buzu Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 67 OF 82

Sashe 67

Buzu Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Hasna wallahi ina son Hammad, ji nake mutuwa zan yi idan ya sake ni, ga shi haryanzu ban san a wani bugiren ya ajiye ni ba, bai sake ni ba, bai ce mini komai ba. Babanmu ne duk ya janyo mini da zigar Imam Omar."

"Asal ki yi haƙuri mana, kar ki illata kanki a kan sa, shi fa yanzu ya samu wata ne da yake rawar ƙafa a kanta, ke sai ki kashe kanki fisabilillahi"

"Hasna ba ki san me nake ji ba, wai ni ce nake da kishiya, wadda na ɗauka ƙasƙantacciya mara galihu na shiga uku"
Hasna ta rungume ta, ta din ga rarrashinta tana yi mata nasiha.

Kwanan Yusuf huɗu da mutuwa, tsufan Alhaji Zailani ya sake fitowa, duk ya fita hayyacinsa ya yi wani iri. Alhaji Zailani ya zo duba shi, yana ta rarrashinsa yana ba shi haƙuri. Mutane jefi-jefi na shigowa su na yin gaisuwa.
Wani mutum ne ya yi sallama, suka amsa masa ya shiga, duk suka bi shi da kallo, dan babu wanda ya san shi a cikinsu.

AREWABOOKS

Sai da suka Shukura ta biyo bayan mutumin, sannan suka rikice gaba ɗaya suka miƙe, banda Alhaji Zailani. Hajiya Amina ta nufi Shukura da gudu har tana neman faɗuwa, ta rungume ta cikin tsananin tashin hankali da manakin ganinta ta ce "Shukura, ke ce? Ina ki ka shiga aka din ga neman ki, ina cikin jikin naki?" Wani irin tausayin Hajiya Amina ya shiga ran Shukura, ta rungume Hajiya Amina tana kuka.
Alhaji Fatuhu ma cikin matsanancin mamaki yake faÉ—in "Ikon Allah, Allah da girma da iko yake. Sannu Shukura" Alhaji Zailani dai yana zaune yana kallon su, bai ko motsa ba.
Idanun Shukura suka sauka a cikin nasa, ta ji tamkar ta yi tsalle ta shaƙe shi, saboda wani abu mai ɗaci da ya tsirga mata.
Mutanen da ya sabauta rayuwarsu, duk ga su a tare da shi a zaune.
Ta ce "Mummy wai na ga rumfa a harabar gidan nan, me yake faruwa ne?"
Hajiya Amina ta ce "Ba wani abu bane ba, Shukura ina ki ka tafi?" Kan ta ba wa Hajiya Amina amsa ta durƙusa ta gaida Alhaji Zailani ya amsa mata cikin damuwa ya ce "Shukura kin sanya mu a tashin hankali, meyafaru wannan bawan Allah kuma waye?"
Shukura ta numfasa ta ce "Garkuwa aka yi da ni, wannan mutumin Likita ne, shi ne wanda ya taimake ni, a gidansa na ƙarasa jinya"
Suka gaisa da mutumin, Alhaji Fatuhu ya din ga yi masa godiya. Hajiya Amina ta ce "Daddy, ba ka ga Shukura ba, Shukura ce fa ta dawo" Ya sauke numfashi ya ce "Na ganta"

Alhaji Fatuhu ya ce "Haba Zailani, amma atleast yakamata ka yi farincikin dawowarta ko, yarinyar da ake ta nema ba a gani ba, ta dawo kuma ka yi fuska"

Alhaji Zailani ya ce "Ni yanzu ta mutuwar ɗana nake yi, dan Allah ku ƙyale ni" A burkice Shukura ta ce "Wane ɗan nasa?"
Tsit suka yi aka rasa mai yi mata bayani, Alhaji Zailani da kansa ya gaya mata Yusuf ne ya mutu. Shukura ta gigice cikin matsanancin tashin hankali ta hau kuka, tana faÉ—in "Shi ma ka kashe shi ko? Da ni ba a kashe ni ba sai ka kashe mini É—an uwa, wallahi ba zan yadda ba sai na tona maka asiri Duniya kowa ya san abin da ka ke yi" Likitan da ya rako ta, ya tashi tsam ya yi musu sallama, ya ce zai dawo.
Duk yadda suka so Shukura ta nutsu amma ta ƙi, ta din ga surutan da ba su gane kansu ba, kuma Alhaji Zailani ya yi mursisi ya yi shiru.

*****
Nana jikinta har wani sheƙi yake yi, ta yi kyau sosai da sosai, sai dai ganin Hammad ya yi mata wahala, saboda yana ta kai kawon shirin bikinsu. Yadda ta lura lamarin ba da wasa suka ɗauke shi ba, sai gayyatar mutane suke yi. Bangaren Sultan yana ta shan suka, da ƙorafe-ƙorafe, a kan ya ci mutuncin Al'adar da aka gada daga iyaye da kakanni. Bai tsaya a iya nan ba, ya ayyana rushe majalisar Imam da ake da ita. Ya sauke Tafawa, ya sauke Sardaunanda wasu daga cikin muƙarrabansa, tare da cewar za a ayyana waɗanda za su maye guraben su, a lokacin shagalin bikin Hammad da matarsa ta ɓoye da zai bayyana wa Duniya yanzu.
Nana a ranta take ƙara jinjina ikon Allah, sai dai tana ganin lamarin bikin nasu, kamar a ƙasar turawa, sun yi aure sun haihu har da ɗa, sannan za a yi shagalin bikinsu.
Gefe guda sannu a hankali take ƙara yi wa kanta fashin baƙin, bayanan da Ƙaisar ya yi mata a game da rashin lafiya da ya ce ruhin ɗan Adam yana yi. Kuma ga yadda ta fuskanta, babu wani magani tattare da hakan face ka yadda kana da ciwon, sannan ka tsananta addu'a Allah ya raba ka da shi.
Tabbas ko a kankin kanta ta ga misali, ta ƙara samun nutsuwa da yarda da komai lokaci ne, lokacin da take addu'a Allah ya kawo mata ɗauki a kan matsalolinta, gani take kamar ba za su wuce ba, kamar waraka ba za ta zo ba. Ashe wannan addu'a da take yi, ke ƙara samar mata da nutsuwa da kwanciyar hankali, tabbas banda haka, da irin azabar da ta ci da tuni ta amince da al'amarin bori, ko ma haukace saboda wahala da yadda ratuwarta ke tafiya kamar ba ta mutane ba.
Ta kalli yadda a yanzu ba ta aikin fari bata na baƙi, sai dai kawai a kawo mata ta ci, ta yi ibada ta kwanta. Sai dai ta dage da roƙon Allah, kar Ni'ima ta sanya ta shagala da neman kusancinta da shi.

****
Gidansu Nana, Mama ta yi mamaki, ganin Uwani ta zo ranar Asabar, wai zata kwana, da azahar ma sai ga Ummi da uban kayan cefane, har ma da Yaya Atine.
Mama ta ce "Wai lafiya duk na ganku, meke faruwa ne?"
Uwani ta ce "Kamar yaya meke faruwa? Karɓar kayan auren Nana muka zo ayi da mu mana"
Ta yi saroro ta ce "Nana kuma, wace Nanan?"
"Nana wacce da wacce ku ke da ita a gidan nan? Ba dangin mijinta ne za su zo daga Agadez ba?"

Mama ta ce "Ban fa gane ba, yaushe aka ganta"

Uwani ta ce "Ke Ummi, ba ku gaya mata ba ne?"

Ummi ta ce "Ina ga Baba bai gaya mata ba, Nana tana Agadez can hannun dangin mijinta, gobe in Allah ya kaimu za su zo kawo kayan aurenta"

"Shi ne kuma dan munafunci ba a gaya mini ba? Kuma wane irin kayan aure kuma bayan wanda aka yi"
Ummi ta ce "Wallahi nima ban sani ba, sai dai sun zo za mu ji"
Mamaki ya cika Mama, domin babu wanda ya tsaya ya yi mata cikakken bayani, kamar ma ba a son ta ji abin da yake faruwa.
Washegari tun ƙarfe sha ɗaya na safe, gidan abincin da aka sai Abinci a hannunsu, suka kawo abinci mai rai da lafiya cikin kuloli na alfarma. Baba ya din ga shiga yana fita, shi fatansa kawai ya ga Nana ba wai abin da za a kawo na auren ba.
Da azahar motoci biyu suka iso, É—aya guda É—aya ta alfarma É—aya kuma ta matafiya.
Ƙaton carfet dama aka shimfiɗa a tsakar gidan, aka shirya wannan uban kayan Abincin.
Manyan mutane ne, farare sol Turaki da Matawallen Agadez, sai kum Tafida, sai kuma Imam Zahradeen, Mahmoudu Sulei, sai kuma Imrana.
Kai tsaye Imarana ya nufi Baba, aikuwa Baban ya rungume shi yana fashewa da kuka. Yadda ya ga Imarana a nutse cikin kamala kawai ya sanya shi mantawa da tarin baƙin cikin da yake ciki, kuma sai a lokacin ya gazgata mutanen nan da gaske suke.
Imrana ya ce "Baba kar ka yi magana, ka ga mu na tare da baƙi" Baba dai kai kawai ya iya jinjinawa yana sake riƙe shi, kamar zai sake guduwa.
Ta taga Mama take ɗan leƙowa, ta saki baki tana kallon ikon Allah, suturar jikin buzayen kawai ya fallasa cewar a cikin rufin asiri suke, ba ƙananan mutane ba ne.
Bayan Baba ya ɗan nutsu, duk sun nemi guri sun zauna, suka gaggaisa. Imam Zahradeen ya ce "To Baba mun sake dawowa, mun zo mu cika alƙawari da muka ɗauka, waɗanan 'yan uwan mahaifinmu ne, ga shi muka zo tare da su"

Suka sake gaisawa Matawalle ya ce "Ɗan uwa, Sultan ne ya aiko mu wakilci mussaman, mu zo mu yi godiya, mu jinjina wa namijin ƙoƙarin da ka yi, na aura wa ɗanmu 'yarka ba tare da sanin waye shi ba. Haƙiƙa mu yarinyarka alkhairi ga ahalinmu da ƙasar Agadez baki ɗaya ma. A madadin Sultan Jalaludeen ya ce "Mu ce maka mun gode, mun sake gode wa. Mu na tafe da dukiyar aurenta, kamar yadda ake yi wa kowace 'ya da ake yi wa kabilar buzaye. Sannan ya ce ita wannan 'ya yanzu ta zama tasa, yana kuma gayyatarka da duk wani wanda yake sha'awar zuwa, gagarumin shagalin bikin yaran nasa. Hammad da kuma Gimbiya Asma'u."
Baba ya numfasa yana ganin abin kamar a mafarki, ya ce "To ai tun da dai da aure a tsakaninsu, a ganina da an haƙura da bikin shagalin nan"
Chapter 67 · 0% Book details