Sashe 22
Buzu Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Mai karanto takardun ya warwareta, ya zuba wa takardar ido sannan ya numfasa ya ce "Zuwa ga Sultan da 'yan Majalisar sa baki ɗaya. Sanin duk wanda ya kwana ya tashi a Agadez ne, babu wani abu da muke martabawa, bayan addininmu kamar al'adarmu. Mu na kira ga Sultan da 'yan majalissar sa, su gaggauta duba ga al'amarin Imam Hammad. Babu yadda za a yi ya ci gaba da jagorantar majalissar Imam, ba tare da zoben tambari ba, wanda kawo yanzu babu wani cikakken bayani a kan inda zoben nasa yake. Sannan ya yi iƙirarin yana da ɗa, wanda haryanzu ba mu ji matsayar binciken da aka ce za a gudanar ba. A dan haka muke kira ga sauran 'yan uwanmu na majalissar Sultan, a gaggauta sanar da mutane sakamakon binciken da aka gudanar, sannan Imam Hammad ya fito gaban majalisar sarki, ya kare kansa, ko kuma ya sauka daga kan muƙaminsa na shugaban majalisar Imam, har zuwa lokacin da sakamakon binciken iƙirarin da ya yi na yana da ɗa zai fito. Idan kuma shaci faɗi ne abin da ya faɗa ta tabatta yana da matsalar ƙwaƙwalwa, kamar yadda jita-jita ta yi yawa.
86
A SAUKE HAKKI, A BIYA KUÆŠIN KARATU 0069685771 AISHA ADAM STANBIC 08081012143
Gaba ɗaya tsit majalissar ta yi, aka rasa wanda zai sake cewa wani abu. Wani abu mai ɗaci ya tsirga wa Sultan a zuciyarsa, yana takaicin kasancewar Tafawa ɗan uwansa, yadda yake nuna son ganin bayan jininsa wato Hammad duk saboda mulki. Ya san ko ba a gaya masa ba, da saninsa aka rubuta wannan takardar aka kawo. Surutu 'yan majalissar suka fara yi ƙasa-ƙasa. Sardauna ya numfasa ya yi gyaran murya, duk aka yi shiru Sannan ya ce "Ina ga wannan maganar mun riga mun yi ta a baya. Ban ga amfanin sake dawo da ita ba, mu na nan ana kan bincike a kan al'amuran kuma za a zo da sakamakon binciken, sake dawo da maganar ba abu ne da zai taimake mu ba, duba da yadda muke da tarin abubu a gabamu, da yakamata a ce an mayar da hankali a kai"
Ɗaya daga cikin mutanen majalisar ya ce "A'a Sardauna, ba na tunanin wannan ba maganar da za a tattauna ba ce ba. Kar ka manta goben Agadez ta ta'alaƙƙa da waɗannan Imam da aka naɗa, su ma suke jagorantar wasu al'amuran na sha'anin sarauta, muddin aka ce da tangarɗa kuma ba a ɗauki wani mataki ba, to yana nufin goben ƙasar nan yana cikin hakin da ba a sani ba"
Matawalle ya ce "Turaki ai dama sanin gobe sai Allah. Mu muna bulayinmu ne kawai. Amma kamar yadda mai girma Sardauna ya ce, a jira sakamakon binciken ya fito tukuna. Sannan wani batun taɓin hankali da ake danganta Imam Hammad da shi, batu ne mara tushe balle makama, sannan duk wanda muka samu da yaɗa wannan zancen, za a ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki a kansa."
Haka aka so tayar da hatsaniya, sai da Sultan ya tsawatar, haka aka watse daga zaman babu wata ƙwaƙwƙwarar magana. Sultan ya san tabbas tun da Tafawa ya samu magoya baya a Majalisa, al'amura za su sake dagulewa ne, kuma za su ci gaba da bibiya su ji ƙwal uwar daka.
*****
Shukura ce a kwance a ƙasa, sai burgima take yi, wani irin matsanancin ciwo yana ratsa ta. Sai jujjuya kanta take yi a galabaice. Kamar kullum mai ba ta abinci ya buɗe ƙofar ya ziro abincin ya ajiye mata ya tafi. Sai dai a duk lokacin da aka kawo mata abincin, idan aka rufe ɗakin duhu ne yake gauraye ko ina, amma sai ga yau da sauran haske. Ta ɗaga kanta a mugun galabaice ta kalli ƙofar ta ga kamar ƙofar ce ba ta rufu ba. Ta lumshe idanunta cike da azabar ciwo, wata zuciyar na azalzalarta ta je ta buɗe ƙofar ko a buɗe take, wata zuciyar kuma ta ce mata wahalar ciwo ne kawai amma ƙofar a rufe take. Ta ji ciwon na ƙara tsananta, yayin da wani abu mai ɗumi da ba za ta iya tantance ko na mene ne ba, yake bin ƙafarta.
Ta din ga jan jikinta a hankali, ta lalubi bango ta dafa, a durƙushe ta ƙarasa gaban ƙofar ta saka hannu ta ja, kawai ta ga ƙofar ta buɗe. Ta zura kanta ta lelleƙa ta ga babu kowa a harabar gurin, daji ne sosai aka yi ɗakin a cikinsa.
Tana faɗin "La'ila ha illa Anta Subhanaka Inni Kuntu mina Zalumin" Ta ci gaba da jan ƙafafuwanta tana takawa a hankali.
Ko da ta duba jikinta sai ta ga alamun faya ce ta fashe, ga ruwanan mai haɗe da jini a jikin ƙafafuwanta da rigarta. Ba ta damu da yadda take gani dishi-dishi ba, saboda azabar galabaitar da ta yi, da kuma haske da ya cika mata ido, kawai ta saɓi hanyar da ba ta san ina ne ba, ta hau tafiya. Duk da duk taku ji take yi tamkar ɗan cikinta zai faɗo saboda nauyin cikin da azabar ciwo. Tafe take tana addu'a Allah ya kuɓutar da ita.
Alhaji Fatuhu kuwa bayan komawarsa gida su na hira da Fadila ya ce "Fadila yakamata ku je ku duba Yaya Sa'a, saboda tana jin jiki nesa ba kusa ba, duk ta rame ta fita daga hayyacinta. Ta bani tausayi sosai da sosai haryanzu tana jin raÉ—aÉ—in mutuwar nan"
Fadila ta ce "Allah sarki, har na tuna lokacin da na rasa Muhsin É—ina, da ta ce ba ni da tawakalli kamar a kaina a ka fara haihuwa, Allah sarki yanzu ta ji abin da na ji"
Ya tsuke fuska ya ce "A taƙaice dai, gaya mini magana ki ke yi"
Ta girgiza kai ta ce "Wace ni? Ai ban isa ba, kawai dai na tuna abin ne, kuma ya daÉ—e yana yi mini zafi"
"To koma dai mene ne yanzu ya wuce, zan gaya wa Suwaiba, yakamata ku shirya ku je ku duba ta, a yi mata sannu, idan babu hali ma ina ga gara ta dawo gidan nan da zama, wataƙila kai komonmu zai rage mata damuwa da kaɗaici"
Cikin sanyin ta ce "Ka manta ne? Ka manta mu ma a under notice muke, daga yanzu ko wani lokaci an ce mu fita mu bar gidan nan?"
Ya yi shiru ya tafi zancen zuci. Ta ce "Dan Allah kar ka É—aga hankalinka, mun samu Allah ya sanya ka farfaÉ—o da kyar. Ni da Maman su Janna za ta yarda da É—an abin hannuna da nata, mu samu ko karamin gida ne a saya, ni ba na son hayar nan ko É—aki uku ne mu koma"
Ya waro ido ya ce "ÆŠaki kuma? Ina É—aki uku zai ishe mu rayuwa? Ko sashenki É—akuna huÉ—u ne da falo biyu, ya yi mana kaÉ—an"
Fadila ta ce "Daddy ka manta wacece Fadilan taka ne? Sai dai ku ya yi muku wahalar rayuwa ai ni na riga na saba, gidanmu ma na da daka auro ni ai É—aki biyu ne ni da Umma"
Ya ce "Ki daina tuna abin da ya wuce mana, ni ba ga shi kin zamo mana alkhairi ba. Da na tsaya duba wani shrime da ƙyale-ƙyale da daga ke har Suwaiba ba na tunanin za ku kasance da ni, duk da halin da muka tsinci kanmu. Ina ƙara yi muku godiya sosai da sosai"
Fadila ta ce "Haba Daddy, ka cancanci fiye da haka daga gare mu, lokacin da ka ke da wadata ba mu ba, na kusa da mu ma ka yi musu, ka gatantamu ka kula da mu, sai Allah ya kawo mana jarrabawa kuma mu juya maka baya, da Allah bai barmu ba kuwa"
Ya ce "Ke dai a yi sha'ani masoyiyya, idan Allah yana ƙaunar bawa, idan ya jarrabe shi ta nan, sai ya sassauta masa ta can, da yawa idan larura ta same su, iyalan nasu barin su suke yi. Kin san wani abu kuwa?"
Ta ce "A'a sai ka faɗa Angona" Ya tuntsure da dariya ya ce "Ango ko?" Ta ɗaga masa gira tana murmushi. Ya ɗan ja kumatunta yana murmushi. Ya ce "Wannan rahar ma da nake yi da ke, ba tare da kin sauya mini ba saboda ba ni da lafiya, kuma ba ni da abin hannun yanzu ba, wallahi ba ƙaramin daɗi nake ji ba. Haƙiƙa larurar nan ta ƙara mini tsoron Allah da imani, ya ƙara kusantar da ni da Ubangijina, a duk lokacin da na motsa ambaton Allah kawai nake yi, gani nake rayuwata ce ta zo ƙarshe. Saɓanin lokacin da nake da dukiya da lafiya, ina ambaton Allah amma ba can sosai ba, ba kamar yadda na ƙara samun kusanci da Ubangiji ba lokacin da na rasa komai. Kuma a jikina nake jin wani tagomashin alkhairi yana kusanto mu in sha Allah"
Ta ce "Haka ake so Daddy, ina fatan kuma ka canza tunaninka a kan magungunan gargajiya da na addini yanzu"
Ya yi dariya ya ce "Na canza tuni, ke dai madalla da ke matar aljanna" Suka ci gaba da hira cike da nishaÉ—i.
*****
86
A SAUKE HAKKI, A BIYA KUÆŠIN KARATU 0069685771 AISHA ADAM STANBIC 08081012143
Gaba ɗaya tsit majalissar ta yi, aka rasa wanda zai sake cewa wani abu. Wani abu mai ɗaci ya tsirga wa Sultan a zuciyarsa, yana takaicin kasancewar Tafawa ɗan uwansa, yadda yake nuna son ganin bayan jininsa wato Hammad duk saboda mulki. Ya san ko ba a gaya masa ba, da saninsa aka rubuta wannan takardar aka kawo. Surutu 'yan majalissar suka fara yi ƙasa-ƙasa. Sardauna ya numfasa ya yi gyaran murya, duk aka yi shiru Sannan ya ce "Ina ga wannan maganar mun riga mun yi ta a baya. Ban ga amfanin sake dawo da ita ba, mu na nan ana kan bincike a kan al'amuran kuma za a zo da sakamakon binciken, sake dawo da maganar ba abu ne da zai taimake mu ba, duba da yadda muke da tarin abubu a gabamu, da yakamata a ce an mayar da hankali a kai"
Ɗaya daga cikin mutanen majalisar ya ce "A'a Sardauna, ba na tunanin wannan ba maganar da za a tattauna ba ce ba. Kar ka manta goben Agadez ta ta'alaƙƙa da waɗannan Imam da aka naɗa, su ma suke jagorantar wasu al'amuran na sha'anin sarauta, muddin aka ce da tangarɗa kuma ba a ɗauki wani mataki ba, to yana nufin goben ƙasar nan yana cikin hakin da ba a sani ba"
Matawalle ya ce "Turaki ai dama sanin gobe sai Allah. Mu muna bulayinmu ne kawai. Amma kamar yadda mai girma Sardauna ya ce, a jira sakamakon binciken ya fito tukuna. Sannan wani batun taɓin hankali da ake danganta Imam Hammad da shi, batu ne mara tushe balle makama, sannan duk wanda muka samu da yaɗa wannan zancen, za a ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki a kansa."
Haka aka so tayar da hatsaniya, sai da Sultan ya tsawatar, haka aka watse daga zaman babu wata ƙwaƙwƙwarar magana. Sultan ya san tabbas tun da Tafawa ya samu magoya baya a Majalisa, al'amura za su sake dagulewa ne, kuma za su ci gaba da bibiya su ji ƙwal uwar daka.
*****
Shukura ce a kwance a ƙasa, sai burgima take yi, wani irin matsanancin ciwo yana ratsa ta. Sai jujjuya kanta take yi a galabaice. Kamar kullum mai ba ta abinci ya buɗe ƙofar ya ziro abincin ya ajiye mata ya tafi. Sai dai a duk lokacin da aka kawo mata abincin, idan aka rufe ɗakin duhu ne yake gauraye ko ina, amma sai ga yau da sauran haske. Ta ɗaga kanta a mugun galabaice ta kalli ƙofar ta ga kamar ƙofar ce ba ta rufu ba. Ta lumshe idanunta cike da azabar ciwo, wata zuciyar na azalzalarta ta je ta buɗe ƙofar ko a buɗe take, wata zuciyar kuma ta ce mata wahalar ciwo ne kawai amma ƙofar a rufe take. Ta ji ciwon na ƙara tsananta, yayin da wani abu mai ɗumi da ba za ta iya tantance ko na mene ne ba, yake bin ƙafarta.
Ta din ga jan jikinta a hankali, ta lalubi bango ta dafa, a durƙushe ta ƙarasa gaban ƙofar ta saka hannu ta ja, kawai ta ga ƙofar ta buɗe. Ta zura kanta ta lelleƙa ta ga babu kowa a harabar gurin, daji ne sosai aka yi ɗakin a cikinsa.
Tana faɗin "La'ila ha illa Anta Subhanaka Inni Kuntu mina Zalumin" Ta ci gaba da jan ƙafafuwanta tana takawa a hankali.
Ko da ta duba jikinta sai ta ga alamun faya ce ta fashe, ga ruwanan mai haɗe da jini a jikin ƙafafuwanta da rigarta. Ba ta damu da yadda take gani dishi-dishi ba, saboda azabar galabaitar da ta yi, da kuma haske da ya cika mata ido, kawai ta saɓi hanyar da ba ta san ina ne ba, ta hau tafiya. Duk da duk taku ji take yi tamkar ɗan cikinta zai faɗo saboda nauyin cikin da azabar ciwo. Tafe take tana addu'a Allah ya kuɓutar da ita.
Alhaji Fatuhu kuwa bayan komawarsa gida su na hira da Fadila ya ce "Fadila yakamata ku je ku duba Yaya Sa'a, saboda tana jin jiki nesa ba kusa ba, duk ta rame ta fita daga hayyacinta. Ta bani tausayi sosai da sosai haryanzu tana jin raÉ—aÉ—in mutuwar nan"
Fadila ta ce "Allah sarki, har na tuna lokacin da na rasa Muhsin É—ina, da ta ce ba ni da tawakalli kamar a kaina a ka fara haihuwa, Allah sarki yanzu ta ji abin da na ji"
Ya tsuke fuska ya ce "A taƙaice dai, gaya mini magana ki ke yi"
Ta girgiza kai ta ce "Wace ni? Ai ban isa ba, kawai dai na tuna abin ne, kuma ya daÉ—e yana yi mini zafi"
"To koma dai mene ne yanzu ya wuce, zan gaya wa Suwaiba, yakamata ku shirya ku je ku duba ta, a yi mata sannu, idan babu hali ma ina ga gara ta dawo gidan nan da zama, wataƙila kai komonmu zai rage mata damuwa da kaɗaici"
Cikin sanyin ta ce "Ka manta ne? Ka manta mu ma a under notice muke, daga yanzu ko wani lokaci an ce mu fita mu bar gidan nan?"
Ya yi shiru ya tafi zancen zuci. Ta ce "Dan Allah kar ka É—aga hankalinka, mun samu Allah ya sanya ka farfaÉ—o da kyar. Ni da Maman su Janna za ta yarda da É—an abin hannuna da nata, mu samu ko karamin gida ne a saya, ni ba na son hayar nan ko É—aki uku ne mu koma"
Ya waro ido ya ce "ÆŠaki kuma? Ina É—aki uku zai ishe mu rayuwa? Ko sashenki É—akuna huÉ—u ne da falo biyu, ya yi mana kaÉ—an"
Fadila ta ce "Daddy ka manta wacece Fadilan taka ne? Sai dai ku ya yi muku wahalar rayuwa ai ni na riga na saba, gidanmu ma na da daka auro ni ai É—aki biyu ne ni da Umma"
Ya ce "Ki daina tuna abin da ya wuce mana, ni ba ga shi kin zamo mana alkhairi ba. Da na tsaya duba wani shrime da ƙyale-ƙyale da daga ke har Suwaiba ba na tunanin za ku kasance da ni, duk da halin da muka tsinci kanmu. Ina ƙara yi muku godiya sosai da sosai"
Fadila ta ce "Haba Daddy, ka cancanci fiye da haka daga gare mu, lokacin da ka ke da wadata ba mu ba, na kusa da mu ma ka yi musu, ka gatantamu ka kula da mu, sai Allah ya kawo mana jarrabawa kuma mu juya maka baya, da Allah bai barmu ba kuwa"
Ya ce "Ke dai a yi sha'ani masoyiyya, idan Allah yana ƙaunar bawa, idan ya jarrabe shi ta nan, sai ya sassauta masa ta can, da yawa idan larura ta same su, iyalan nasu barin su suke yi. Kin san wani abu kuwa?"
Ta ce "A'a sai ka faɗa Angona" Ya tuntsure da dariya ya ce "Ango ko?" Ta ɗaga masa gira tana murmushi. Ya ɗan ja kumatunta yana murmushi. Ya ce "Wannan rahar ma da nake yi da ke, ba tare da kin sauya mini ba saboda ba ni da lafiya, kuma ba ni da abin hannun yanzu ba, wallahi ba ƙaramin daɗi nake ji ba. Haƙiƙa larurar nan ta ƙara mini tsoron Allah da imani, ya ƙara kusantar da ni da Ubangijina, a duk lokacin da na motsa ambaton Allah kawai nake yi, gani nake rayuwata ce ta zo ƙarshe. Saɓanin lokacin da nake da dukiya da lafiya, ina ambaton Allah amma ba can sosai ba, ba kamar yadda na ƙara samun kusanci da Ubangiji ba lokacin da na rasa komai. Kuma a jikina nake jin wani tagomashin alkhairi yana kusanto mu in sha Allah"
Ta ce "Haka ake so Daddy, ina fatan kuma ka canza tunaninka a kan magungunan gargajiya da na addini yanzu"
Ya yi dariya ya ce "Na canza tuni, ke dai madalla da ke matar aljanna" Suka ci gaba da hira cike da nishaÉ—i.
*****