← Book details Buzu Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 82

Sashe 12

Buzu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya ƙaraso gabanta, ya fesa mata turare, ya zura hannu a aljihunsa, ya ciro zobuna da abin hannu ya saka mata. Ta yi ƙuri da ido tana kallon hannun nata, rabon da ta sanya wani abu na ado, har ta manta.
A tsorace ta ce "Ni dai zan cire wannan abin tsoro nake ji"
Banza ya yi mata ya gyara zaman mayafin rigar a kanta. Ya din ga ƙare mata kallo yana mamakin yadda Asal take aibata Nana da muni, dan kawai baƙar fata ce.
Idanunta manya sexy eyes, farare ƙal da su, gwanin ban sha'awa, ga shi rigar tamkar dan jikinta aka yi ta.

Ya numfasa ya ce "Ina ƙara tuna miki, duk wani abu da za a tambaye ki, kar wanda ya baki tsoro, kar kuma ki rufa komai, muddin ki na son Muhsin ya dawo hannunki"

"Meyasa kai ba za ka yi musu bayani ba kawai?"

"Da bayanina ya wadatar, ba zan bari a zo wannan gaɓar ba". Ya ciro niƙab ya saka mata.
Sannan ya saka hannunsa ya ciro wayarta daga aljihun rigarsa.

Nana ta waro ido ta ce "Wayata, ya aka yi ta zo hannunka? Dama kai ka É—auka?"

"Eh ni na ɗauka, kin ƙi saurarata, balle na yi miki bayanin komai, mu je" Ya yi maganar yana nuna mata hanya.
Bakinta fal magana, amma ya yi mursisi, ya yi mata shiru. Ta tarar da takalma a falon gidan. Nana ta din ga ganin abin tamkar a mafarki.

Su na zaune a baya ita da shi, ana jan su a motar. Ta yi shiru tana zabga addu'a Ubangiji Allah ya bata nasarar karɓar ɗanta, dan ko kaɗan ba ta sha'awar gidan nan, ɗan zamanta a gidan kawai ta fuskanci akwai kitimurmura a gidan.

Tun da aka doshi gidan gaban Nana yake tsananta faɗuwa, haka kurum take jin ba ta ƙaunar gidan. Gefe guda kuma Nana tana ta tunanin halin da Ƙaisar yake ciki.

Tun da aka yi parking suka fito, hadimai suke gaida Imam Hammad yana ɗaga musu hannu. Ya riƙe hannun Nana yana ratsa cikin gidan da ita. Gaba ɗaya aka zubo musu ido, ana son sanin wacece wannan ya riƙo hannunta, saboda kowa ya san ba Asal ba ce, saboda ba ta kai Asal tsawo ba, kuma Asal ba ma'abociyar niƙab ba ce, ko kanta ma ba ta damu da rufewa ba.

Jikin Nana ya hau rawa, bayan da suka shiga É—akin zama na musamman na cikin fadar Sultan.
A can suka tarar da Sultan É—in, ga Matawalle ga Sardauna, su na jiran isowarsu.
Nana ta ja ta tsaya jikinta yana wata irin rawa, har ƙafafuwanta, gabanta ya din ga faɗuwa. Duk ta kowacwa kusurwar ɗakin, akaai na'urar sanyaya ɗaki, amma Nana ta kasa gane wane irin yanayi ma take ji.

Ya kalli Nana ya ce "Ki nutsu mana, kar ki ji tsoro, dan Allah kar ki yi wani abu da zai rusa mana rayuwa, kar haushina da ki ke ji, ya sanya ki makance, ki yanke mana hukuncin da zai cutar da rayuwarmu" Nana dai ta gaza ko ƙwaƙƙwaran motsi.

Ya ja hannun Nana, suka ƙarasa tsakiyar ɗakin suka zauna. Duk suka zubo musu ido.

Sardauna ya yi wa Nana alama da ta cire niƙabinta. Ta saka hannu ta cire tana sunkuyar da kai.

Abdou matawalle ya ce "Wannan kamar na taɓa ganinki ko?" Nana ta sunkuyar da kai.

Sardauna ya dube ta ya ce "Ya sunanki?"

"Nana Asma'u" Ta yi maganar kanta a sunkuye.

"Daga ina ki ke?"

Ta ce "Nigeria"

"Kin san wannan?" Ya yi maganar yana nuna mata Imam,Nana ta É—aga kai ta kalli Imam, ta kalli Sardauna, ta sunkuyar da kai.

Matawalle ya ce "Ki yi magana mana, kin san shi?"

AREWABOOKS

Nana ta kalle shi, ya kalle ta, ya tsare ta da idanunsa, yana jiran ya ji me za ta ce.

Abdou matawalle ya ce "Mu za ki kalla ki yi wa bayani. Ke ba ke muka gani cikin waÉ—anda suka kawo abinci ranar da aka yi taro ba?"
Ta jinjina kai alamar eh.

"To kin san shi ne dama?" Ya sake jefo mata tambayar.

Ta jinjina kai. Sardauna ya ce "Ki buÉ—e baki ki yi magana mana, ki daina amsa mana da kai".

"Eh na san shi"

"Waye shi a gurinki?"

Ta yi shiru tana nazarin amsar da za ta bayar, kar ta zama ta kwafsa su hana ta É—an ta. Cike da karaya ya sake kallon Nana ya ce "Ma viee, talk ki yi magana mana"

"Ni sai na ga Muhsin zan yi magana, dan Allah ka fara nuna mini É—a na"

Ya ce "To shikenan"

Ya ce "Ina neman alfarma, zan saka a kawo mata Muhsin, za ta yi magana"

Matawalle ya ce "Wane irin abu ne wannan? Ta san a gaban su wa take kuwa?"

Sardaunan Agadez ya ce "Bari Matawalle, a saka a kawo shi, mu ji me za ta ce"

Sardauna ya ciro wayarsa yana ɗan taɓawa, yana satar kallon Nana.

Sultan kuwa rasa abin yi ya yi, ya tuna fuskarta a gurin taron cin abinci da aka yi, ya so ya bibiyi me ya kawo baƙuwa wannan gurin, amma abubuwa suka sha kansa.
Wani irin gumi ne yake tsatstsafo masa bayan tuna irin taɓargazar da Hammad ya aikata, ka iya janyowa. Babban abin da ya ƙara sanya masa fargaba, shi ne abin da yake iya gani daga idanun Hammad a kan yarinyar. Ko a yanzu ya tattara hankalinsa a kanta, ta sunkuyar da kai sai zubar da hawaye take, da alama ma tamkar ya manta da zamansu a gurin.

Wata hadima ce ta shigo, hannunta ɗauke da Muhsin. Yana ganin Nana, ya yi wani irin zillo daga jikin hadimar, yana wata irin ƙara yana cewa "Naaa" kamar yadda yake kiranta, Nene  kuma ya ce mata umma"

Nana ta yi wata irin zabura ta nufe shi da gudu ta ɗauke shi, ta ƙanƙame shi a jikinta, tana zubar da hawaye cikin damuwa da kewar tilon ɗan nata. Shi na Muhsin ɗin, ƙanƙameta ya yi ya fashe da kuka.

Jikin Sayyid ya yi sanyi sosai, ya din ga jin abin da ya aikata bai kyauta ba, kamar ya shiga hakkinsu da yawa, amma babu yadda ya iya ne, hakan ne kawai masalaha a garesu baki É—aya.

Sultan ya kalli Abdou matawalle suka haɗa ido, suka mayar kan Nana da ta durƙushe a gurin tana ta uban kuka.

Matawalle ya yi gyaran murya ya ce "Wannan yaron wane ne shi a gurinki?"

"ÆŠa na ne" Ta faÉ—a cikin kuka.

"Shi kuma wannan fa?" Ya nuna mata Hammad.

"Mijina ne" Ta furta cikin sanyin jiki.

"Waye baban yaron naki?" Ya sake tambayarta. Ta kalli Hammad ta ce "Shine"

"Kin tabattar shi ne mahaifin yaron nan, kuma ke ki ka haifi yaron?"

Ta jinjina kai ta ce "Na tabattar"

"Ya aka yi ku ka haÉ—u ku ka yi aure?"

Ta numfasa ta ce "A Nigeria muka haÉ—u, a can muka yi aure"

"Waye shaidarki cewa mijinki ne shi?"

Takaici ya fara kama Nana, wace shaida kuma bayan wannan É—an wata shaida suke nema?.

"Ni ba ni da wata shaida, Allah ne shaidata sai babana da ya É—aura mana aure."

Sardauna ya ce "Yaya aka yi mahaifin naki ya aura miki wanda bai san daga inda yake ba, ko ku ƙasarku ba ka bincike ku ke aure?"

Jiki a sanyaye Nana ta ce "Ana yi, akwai 'yan uwansa da suke gadi tare, sun san aure muka yi, su Habu"

Matawalle ya ce "Ban gane gadi ba, gadi kamar yaya?"

Hammad ya ce "Ina neman alfarma dan Allah a tsagaita yi mata tambayoyin nan haka, duk a rikice take. Ga wannan wayar akwai video da hotuna a ciki, lokacin da muna rayuwa ne da ni da ita a Nigeria"

Sulta ya ce "Hammad, ya zama dole ka yi mana shiru, a kammala binciken da yakamata, domin tabattar da gaskiyar lamarin nan"

Sardauna ya sake kallon Nana ya ce "Ya aka yi ki ka zo gidan nan yin aiki?"

Ta haɗiye yawu ta ce "Mu na Nigeria lokaci ɗaya na nemi 'yan uwansa na rasa, ya haɗu da larurar zuciya, ina tsaka da jinyarsa na neme shi na rasa. Kawai na yanke shawarar na zo Nijar ko zan haɗu da shi" Mamaki ya kama Hammad, yadda kai da fata taƙi bayanin ainihin ciwon da ya din ga yi bayan hawan jini.

Matawalle ya ce "Ya aka yi da ku ka haɗu ba ki sanar da kowa mijinki ne ba? Kuma me yasa wacan karon da ya kira ki a nan, ki ka ce ba ki san shi ba? Anya akwai ƙamshin gaskiya a maganar nan?"

Imam ya ce "Wancan karon laifina ne, kuma gaba É—aya a ruÉ—e take"

"Ba kai ake tambaya ba, ita muke tambaya" Matawalle ya katse Sayyid.

Cikin kuka Nana ta ce "Dan Allah ku yi haƙuri, ni ba na buƙatar na ci gaba da zama da shi, ku bani ɗa na kawai zan tafi na yi muku alƙawarin ba za ku sake ganina a inda yake ba"

Suka yi tsit suna kallon Nana, daga bisani Sardauna ya ce "Haƙiƙa idan ta tabatta kin auri Imam Hammad, to kun tafka babban kuskure mussaman shi da ya san ƙa'ida da dokar masarauta. Sai dai uzuri ɗaya za a yi muku, shi ne shi ya haɗu da larura, ke kuma ba ki san wannan ƙa'idar ba. Babban mai laifi shi ne Mahmoudu kuma sai ya haɗu da tsatsauran hukunci. Babu buƙatar mu ci gaba da bincike da wani bin diddigi.
Daga nan za a ɗauke ki a kai ki gidan baƙi na musamman, ki huta kwana biyu zamu haɗa miki sha tara ta arziki, za kuma mu sanya a mayar da ke har ƙasarku.
Imam Hammad dole zamu san yadda zamu juya wannan lamarin, mu ɓoye gaskiyarsa, idan haryanzu da aurenka a kanta, zaka sauwwaƙe mata zamu karɓi ɗanmu a mayar da ita Nigeria"

Wani irin mugun kallo Hammad ya yi wa Sardauna. Nana kuwa zabura ta yi tana ƙanƙame Muhsin ta ce "A'a Sayyid ne ɗanku, Muhsin kuma ɗa na ne, ba zan baku ɗa na ba, da shi zan tafi Nigeria"
Chapter 12 · 0% Book details