← Book details Buzu Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 64 OF 82

Sashe 64

Buzu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Baba ya ce "Ashsha! Yarinyar da nake gaya muku shekara uku babu wanda ya san inda take, kuma babu wanda ya waiwaye ta tunda ku ka gudu kuka bar ta. Kuma ni mene ne haÉ—ina da Sarkin Agadez da zai kawo kayan aure? Ni dai na yi nadamar abin da na aikata na aurar da 'yata ga mutumin da ban san daga inda yake ba"
Imam Zahradeen ya lura ran Baba a ɓace yake.
Ya sassauta murya ya ce "Baba sunana Imam Zahradeen Jalaludeen Agadez, ni Yaya ne ga Imam Hammad Jalaludeen Agadez. Kuma 'ya'ya ga Sultan Jalaludeen Agadez, wato Sarkin Agadez na yanzu. Buzun da ka aura wa 'yarka, ɗan uwana ne, kuma  ɗa ne ga Sultan na Agadez."

Baba ya kalli Imam Zahradeen kamar yana raina masa hankali.
Ya ce "Ɗan sarki ne zai zo baro ƙasarsa ya zo Nigeria yana aikin gadi?"

Mahmoudu ya ce "Baba, idan baka manta ba, ko lokacin da aka yi aurensu, a yanayi na rashin lafiya yake,  rashin lafiya ce ta kama shi"

"To yaya za a yi a ce É—an sarki ya zo Nigeria gadi, ni abin ya bani mamaki ne. Kuma na kasa yarda, ni kar ku sake dugunzuma mini hankali bayan halin da nake cikix

Zahradeen ya ce "Baba ba dunguzuma maka hankali za mu yi ba. Mun zo mu sanar da kai batun zuwan baƙinka ne daga Agadez, kafin su zo ɗin."

"To wai su zo, su yi mini me?"

" 'yarka Nana, tana gurinmu tare da É—anta Muhsin"
Baba bai san ya aka yi ya tashi tsaye ba, yana zazzaro ido ya ce "Nana Asma'u dai 'ya ta? Yaya aka yi ku ka same ta? Tana ina? Kun taho mini da ita?"

Mahmoudu ya miƙe tsaye ya ce "Baba shi ne bayanin da muke yi maka, Nana tana tare da mu, za a kawo dukiyar aurenta Nigeria za kuma a yi bikin aurensu sosai da sosai. Duk abin da za mu gaya maka yanzu ba za ka fahimce mu ba, saboda a cikin damuwa ka ke, kuma abubuwan da suka faru su na da tsawo da sarƙaƙiya akwai buƙatar a yi maka bayani daki-daki. Ba Nana ba hatta Imrana yana tare da mu a Agadez, akwai tarin bayanai da sai ka nutsu, an yi maka bayani zaka fahimce su"

"Amm bawan Allah, ni ko yanzu a shirye nake, mu tafi Agadez ɗin na karɓi 'ya'yana. Bayan Nana kuma me ya haɗa ku da Imrana"

Imam Zahradeen ya ce "Alkhairi ne, a cikin satin nan, zuwa mai kamawa in sha Allah; za a sake turo maka baƙi daga can. Kuma za a yi bikin su al'ada saɓanin yadda ya gudana, kuma za a yi maka bayani kamar yadda nake nanata maka. Amma kafin nan mu na son za a gyara maka gidan nan, ko kuma a canza maka wani"

Baba ya girgiza kai ya ce "Ba na buƙatar haka, muddin Nana yake so, babu amfani a raina inda ta fito, ni dai fatana na gansu cikin ƙoshin lafiya"

Zahradeen ya ce "Ba raina maka aka yi ba, matsayinka da girmanka ne ya sanya za a yi maka." Fafur Baba ya ƙi yarda da hakan, da kyar suka rarrashe shi suka tafi, dan cewa ya yi ba za su bar ƙofar gidansa ba, ba tare da ya ga yaransa ba.
Kasancewar duniya makarantar da ko babu malami, ta biya maka darasi dole ka É—auka ce, ta karanta wa Baba darasin da duk son abin Duniyarsa, yanzu tsoro yake ji.
Zuwansu Imam Zahradeen babu wanda ya sanarwa, saboda gani yake yi tamkar ƙarya Buzayen nan suka zo suka sharara masa.
Ya kasa gaya wa kowa, sai Uwani ya kira ya sanar mata. Sai dai a ƙarshen maganar Baba ya ce "Amma Uwani ni ban ji na yarda ba, ji nake kamar ƙarya kawai suke yi ban ji na yarda ba"
Uwani ta ce "Alhamdillah, ni dai na ji na yarda har cikin zuciyata. Ko ba hakan ba ne, ina fatan Allah ya tabattar da shi ya zama gaske. Wallahi zuciyata ta daɗe tana bani, mijin Nana ba ƙaramin mutum ba ne, to ita Nanan da gaske tana gurinsu, kuma har da Imrana sun haɗa ku ko a waya ne?"

Ya ce "A'a, shiyasa na kasa yarda ma gaba É—aya"

"Isa, yarda ni dai na gama ta, zamu duƙufa mu ci gaba da addu'a in sha Allah Nana suna cikin kwanciyar hankali tare da ɗan uwanta" Kalaman Uwani suka ɗan ƙwarara wa Baba gwiwa.
Bayan sallar isha'i ya shiga gida, yana zaune yana jin radio, Mama tana cikin É—aki tare da Jamila da ta koma so silent, ko magana ba ta iya yi.
Ihun da Jamila ta yi ne, ya sany Baba jifa da radio ya tashi tsaye yana rarraba ido.
"Mama! Mama!! Dan Allah ki taimake ni, dodon ƙungiya zai shanye mini jini. Hajiya Sa'a kin cuce ni, kin cuci rayuwata, na kasa samun aminci da salama. Na baku Abba me kuma ku ke nama a gurina?"
Cikin rashin fahimta duk suke kallon Jamila, Baba ya ce "Me yarinyar nan take faÉ—a ne haka?"
Mama ta ce "Nima ban sani ba wallahi, ina ga jikin ne ya motsa."
Baba ya ce "Jikinta ya motsa kuma take irin wannan maganganun?"
Ba ta ko saurare su ba, ta ci gaba da surutanta. "Ni ban so shiga kungiyar nan ba, dole ki ka yi mini, ga shi kin sanya ni a bala'i, na rasa mutuncina, kin saka nayi kisan kai, yanzu kuma na kasa samun kwanciyar hankali, sai tsorata ni ake yi, nima ana nema na a kashe ni, kin cuce ni"
Baba ya ce "Jamila, meyafaru ne? Me ki ke faÉ—a wai?"

"Baba riƙe hannuna, Baba ku taimake ni"

Ya ƙarasa ya riƙe hannun Jamila, cikin kuka ta ce "Baba na shiga uku, na aikata mummunar ɓarna, Baba hakki ne zai yi ajalina"

Baba ya ce "Jamila, ki gaya mini, me ki ka aikata?"

"Ƙungiyar asiri, Baba ƙungiyar asiri aka shigar da ni, saboda na kai jinin Nana"

Kamar ta watsa wa Baba wuta, haka ya fizge hannunsa ya ja da baya, yana kallon Jamila da take ta uban kuka.
Mama ta ce "A'a baban su Jamila, dan Allah kar ka yarda da abin da ta faɗa, ka san ba ta da cikakkiyar lafiya, wataƙila zafin ciwo ne, amma wace irin magana ce wannan, a ina Jamila za ta ga wata kungiyar asiri ta shiga"

Alhaji Zailani ne a durƙushe a gaban gawar ɗansa Yusuf, bayan an dawo da shi daga makaranta, dama babu rai aka dawo da shi. Ba shi ne abin da ya ɗaga masa hankali ba, sama da ganin busashshen jini a baki da kuma hancin Yusuf. Ba dan ya yi iya ƙoƙarinsa ba, da tuni ya aikata abin da zai fallasa kansa. Wani irin raɗaɗi da zafi ya din ga ji a zuciyarsa ya kasa magana, ya kasa ko ƙwaƙwƙwaran motsi.
Ba a jima ba, gidansa ya cika da jama'a, Hajiya Amina sai kuka take, ga Shukura ta ɓata, ga kuma mutuwar Yusuf.
Ya hau neman lambobin yaransa, da ya sanya su kashe Shukura, a kan kar su kuskura su kashe ta, amma ya kasa samun su. Duk da daÉ—ewar da yayi yana aikata zalunci kala-kala, mutuwar Yusuf ta dake shi, ta tsaya masa. Ya din ga jin tamkar ya yi ta kururuwa yana burgima, ko zai ji daÉ—i.
Ko da aka yi jana'izar Yusuf, Alhaji Zailani tafiya ya yi ya kulle kansa a ɗaki. Kaf yaransa babu kowa sai Shukura yanzu, Shukuran ma ba a san inda take ba. Kuma ita ma baya tsammanin za ga tsallake sharrin dodon ƙungiya, tun da ya gaza bashi jinin shekara.

Sosai ake ta shirye-shiryen gudanar da bikin auren Imam Hammad, da matarsa 'yar Nigeria. Ita Nana abin har mamaki yake bata.
Tun da Sultan ya amince da auren Nana da Sultan, Nene take sintiri kawo wa Nana kayan gyaran jiki. Ban da matar da ake ware mussaman Nene take zuwa da ita, take yi wa Nana wani irin gyaran jiki na mussaman.
Nana ta ce "Nene duk wannan abin fa ihu ne bayan hari"
Nene ta ce "Ke, gyaran ne ba kya so?"
"To Nene ya riga ya sanni a yadda nake, me kuma zan gyara?"

Nene ta ce "To kar ki gyara, komai yana buƙatar gyara ai"
Aka ajiye wa Nana kayan sakawa, da na ado irin na Buzaye. Nana ta ƙudurce a ranta, bayan ta tare, kayanta na 'yan Nigeria za ta saka Hammad ya ajiye mata, saboda ita ma tana son tata al'adar.
Shi kansa Hammad ya so a ƙyale masa ita a haka, dan shi komai nata ya yi masa. Sai dai gyaran jikin da ake yi matan ba ƙaramin kyau take yi ba.
Ga shi tare da Muhsin suke kwana da Nene, hakan ya ƙara sanya ta farin ciki.
Hammad ya ce ta fita ta É—an zagaya, amma ta sanya takunkumi ta rufe fuskarta.
Har mamaki Nana take yi, yadda idan Muhsin ya ga raƙuma ko shayi, kamar zai tashi sama saboda murna. Sarkin baka ta hango, suka nufe inda yake.
Cikin jinjina ya ce "Barka da tattaki uwar gijiyata" Nana ta yi dariya ta ce "Dan Allah ka daina kunya ka ke bani"
Shi ma yana murmushin ya É—ago ya kalli Nene, ya ce "Ni kuwa dama ina ta son na yi miki magana, Allah bai yi ba"

Nene ta ce "Ni É—in ko? Ka sanni ne?"

Ya ce "Eh, ai duk inda muka ga juna, muna gane kanmu"

Ta yi dariya ta ce "Na ji, ai ban yi zaton haryanzu akawai abin da tattare da ni ba"

Sarkin baka ya ce "Ni na ji na gane ai. Kuma ni É—alibin marigayi Sa'adu Aska ne"

Nene ta waro ido ta ce "Kana nufin Babana?"

Sarkin baka ya ce "Ƙwarai da gaske, ya sanar da ni magunguna, sai muka kwana casa'in tare da shi, a mabanbantan dazuzzuka, daga bisani muka rabu, ban sake ganinsa ba. Mahaifinki mutumin kirki ne, ba zan manta da shi ba har abada"

Nene ta ce "Ikon Allah"

Nana ta ce "Sarki kai komai ma ka sani ne? Kuma kowa ya sa ka"
Chapter 64 · 0% Book details