Sashe 68
Buzu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Turaki ya ce "To ai ɗan gidan mulki ne, abu ne aka yi shi da babu wanda ya sani, kuma ya saɓa wa al'adarmu, wands a dalilinta an soke al'adar ma gaba ɗaya, dan haka dole a yi shagalin bikin domin nuna wa Duniya ita. Saboda gudun abin da ka iya biyo baya, saboda mutum ne mai mulki mai faɗa a ji a garin Agadez. Dan haka nan da mako guda za a yi bikin, duk adadin waɗanda za su je, za a ɗauki nauyinsu tun daga ƙasa Nigeria har can, domin yin wannan shagali" Daga cikin ɗakin Uwani ta rafsa wata irin guɗa mai ɗan karen sauti tana faɗin "Alhamdillah" har sai da hankalinsu ya koma kan inda sautin guɗar ya fito. Gaddafi dai daga baya ya shigo, suka yi ido huɗu da Imrana. Imarana ya tashi ya nufe shi, rungume juna suka yi. Gaddafi ya ce "Imrana, wannan karon nisan kiwon naka har ya kai tsawon wannan lokacin?"
Imrana ya ce "Wani nisan kiwo, kame ni a kayi, a ka kai ni makarantar dole, abubuwa ne da yawa suka faru" Ai tuni suka manta da wani batun ba sa jituwa, saboda girman alaƙar jini, suka din ga murnar ganin junansu.
Daga nan aka shiga shigo da kayan auren Nana, sai da Baba ya saki baki, a ransa ya fara tunanin anya mutanen nan su na da hankali kuwa. Saboda shi yanzu al'amuran abin duniya tsoro suke ba shi.
Domin karrama abin da su Baba suke da shi, su Turaki suka ci abincin da aka kawo musu.
Aka gabatar musu da 'yan uwan Nana, Yaya Atine sai rawar kai take, tana nanata musu ita yayar Baban Nana ce uwa É—aya uba É—aya, ita ta saki Nono ya kama.
Haushi sai da ya kama Imran, Gaddafi ma ya tsuke fuska ya ce "Matar nan duk abin da aka haÉ—a da ita sai ta yi hauka"
Imrana ya ce "Har da wani ita ta saki nono ya kama, kamar nonon akuya, ko kunya ba ta ji ba, kamar ba da ita aka dinga muzguna wa Nana ba"
Ta din ga rawar ƙafa tana jan su da hira, sai da ta ba wa kowa haushi.
Da suka tashi tafiya kuwa, Haka Ummi ta shiga maƙwabta ta karɓo kayan da aka shirya, na tukuci da za su tafi da shi, dan kar ma wani ya sanya zalama. Kaji, da kayan snacks masu yawan gaske, da dabino kusan kwano biyar da tasoshin turare.
Turaki ya ce karramawar da aka yi musu ta isa, ba za su karɓi komai ba, ai Nana 'yar Sultan ce.
Gaddafi ya ce idan ba su karɓa ba, ba za su ji daɗi ba.
Baba ya ga za su tafi ya yi musu godiya sannan ya ce "To ba za a kawo mini Nanan ba, ita yaushe zan ganta?"
Imam Zahradeen ya ce "Zaka ganta Baba, sai kun zo Agadez biki, za ku ganta in sha Allah, ga Imrana mun kawo maka har gida ai"
Jiki a sanyaye ya ce "Nanan dai nake son gani, amma shikenan mun gode sosai da sosai"
Imrana ya ce "Tun da ni baya son ganina, bari na biku mu koma"
Cikin sauri Baba ya ce "A'a Imrana, kai ma na yi murna da ganinka"
Suka yi murmushi baki É—aya, su Mahmoudu ya ce "Duk wanda za su je, a kira a gaya mana adadin mutane, za a É—auki nauyin zuwansu da dawowar su, sannan kuma idan an gama ganin kayan da su za a tafi. Daga nan suka hau mota suka tafi.
Da suka koma gida, aka fara sauke kaya ana bubbuÉ—ewa, Baba komawa ya yi gefe ya fashe da kuka, domin hatta shi akwati guda aka yi masa.
Uwani ta ce "Isa meye haka kuma, ai abin farinciki ne, ka daina kukan nan dan Allah"
Maƙwabta ma ba a bar su a baya ba, suka din ga shigowa, sun ɗauka ko kayan auren Jamila aka kawo ko na Suwaiba. Mama baƙin ciki ya cika mata ciki, ganin yadda nata 'ya'yan duk suka zama abin da suka zama, babu wani na kirki, ta din ga cizon yatsan ina ma nata 'ya'yan ta saka aka aura wa buzun ba Nana ba.
Uwani ta ce "Allah ba azzalumin sarki ba ne, Nana ta sha wahala a rayuwa, ta yi ɗawainiya da yaron nan, da jikinta da ƙarfinta. Allah ya yi tana da rabon jin daɗi tun a Duniya"
Ummi ta ce "Wallahi Uwani, Nana ta sha wahala, da shi sosai da sosai, Allah ya nuna ikonsa. Kuma shi ma ya yi halacci"
Uwani ta ce "Ba kaÉ—an ba, Allah dai ya ba su zaman lafiya"
Imran ya ce "Dan ma ba ku ji wahalar da ta sha a Niger É—in nan ba, da yawon nemansa" Nan Imrana ya gaya musu abin da ya sani. Yaya Atine ta ja baki ta yi shiru.
Uwani ta ce "To Isa, ina fatan ya zame maka izina, akan abubuwan da ka aikata wa yarinyar nan. Kuma ya zama dole a kira mahaifiyarta a sanar da ita komai, kuma a yi shirin tafiya da ita gurin bikin nan, dan ba za ka ci gaba da wannan jahilcin ba"
Imrana ya ce "To ai a Bauchi muka kwana, an je har gida an kai wa Umma lefen ta gani, an yi mata godiya sannan muka taho nan yau"
Uwani ta ce "Ikon Allah, haihuwa mai rana" Duk yadda Mama ta so ɓoye ɓakin cikinta abu ya ci tura.
Can gidan Umman su Nana, ta yi sujuda babu adadi na tsantsar murna da farinciki. Iliyasu kansa bakinsa ya ƙi rufuwa, amma ko kallo bai ishe ta ba. Dan ta wani fannin guduwar Nana, sauƙi ya sama mata, dan tun da ya san ya yi sanadin ɓatan Nana, duk abin da take yi masa baya cewa uffan.
"Mai Jidda kin ga ikon Allah ko? Ashe ta wani fannin gara da Nana ta je neman mijin nata, da tana zaune a nan babu lallai su haÉ—u. Allah sarki rayuwa"
Maijidda ji ta yi kamar ta make shi, ya ga abin Duniya, jikinsa sai tsuma yake yi.
*****
Asal na zaune ta damƙe wayarta iya ƙarfinta, saboda ganin hoton katin gayyatar bikin taron bikin Hammad da matarsa, da kuma naɗe-naɗen sarauta.
Hasna ta ce "Asal, ki ajiye wayar nan ki samu ki saka wani abu a cikinki mana" Ta girgiza kai hawaye na gangarowa daga idanunta.
Ji suka yi an buɗe ƙofar ɗakin, suka ɗaga baki ɗaya. Hammad ne ya shigo, jikinsa sanye da shiga ta alfarma. Ƙamshin turarensa ya mamaye ɗakin baki ɗaya.
Hasna ta risuna cikin girmamawa tana gaishe shi. Asal kuwa ta sunkuyar da kanta, zuciyarta na tsananta bugawa cike da tsoro da fargaba, saboda ba ta taɓa tsammanin ganinsa ba. Kuma ba ta san me yake tafe da shi ba. Da yatsunsa biyu ya yi wa Hasna alamar ta fita ta ba su guri.
Ayshercool
08081012143
100
LITTAFIN KUÆŠI NE, A BIYA KUÆŠIN KARATU KAN A KARANTA.
0069685771
AISHA ADAM STANBIC
08081012143
Asal ta sunkuyar da kanta ƙasa, ji take yi tamkar ƙasa ta tsage ta shige, saboda matsananciyar kunyarsa da take ji.
Ya ƙarasa ya zauna a gefenta, ya ce "Me ya same ki haka?" Ba ta ɗago ba, ta girgiza masa kai.
Shiru ya wanzu tsakanin su, babu wanda ya yi magana. Ya ce "Tun da ba za ki yi magana ba shikenan" Har ya yinƙura, ta riƙe rigarsa ta ce "Sakina ka zo ka yi ko?"
"A'a, dama ai ni ban kore ki ba, na dai ba ki zaɓin zama da ni ne, amma na ga kamar ke da mahaifinki, kun fi gamsuwa da na sauwwaƙe miki."
"Dan Allah Hammad ka yi haƙuri ka yafe mini, na san laifukana ba za su ƙirgu ba, sai a wannan karon Allah ya tona asirina"
Yayi murmushi ya ce "Ba zan yi miki dole ki zauna da ni ba, muddin kin san zuciyarki haryanzu tana son Omar" Wata irin É—agowa Asal ta yi a razane jin abin da ya ce.
"Hmm Asal kenan, duk tsawon zaman da na yi da ke, babu abin da ban sani ba, kar ma ki yi zaton ko wani ne ya gaya mini. Saka mini magani da duk wani nau'i na ƙoƙarin illata ni da ki ke yi, duk na sani, kuma ina kallonki. Ba domin babu yadda zan yi da ke ba, sai domin ina jin tausayinki, kuma ke ƙanwata ce"
Zamowa ta yi ƙasa cikin kuka ta riƙe rigarsa ta ce "Wallahi na yi nadama Hammad, na san ko ba ka ce mini komai ba, Hakkinka ba zai bar ni ba. Amma ba laifina ba ne ba, ka sani dan Allah ka yi haƙuri ka yafe mini, kar ka sake ni. Wallahi ina sonka"
"Dama ai ban ce zan sake ki ba, mahaifinki ne ya nemi hakan, kuma nima na so aikatawa amma na duba idan na yi haka, ba ki da wata kyakykywar makoma, bayan gama lalata rayuwarki da aka yi. Kuma ba na son asirinki ya ci gaba da tonuwa a idon Duniya. Uwa uba Nana tana ta yi mini magiyar kar na rabu da ke. Na so samarwa kaina cikakkiyar nutsuwa da rayuwa da wadda bata harin komai daga gare ni sai alkhairi, amma ban san me Allah zai yi mini a sanadin yafe miki ba. Asal zaki koma ɗakinki bisa sharaɗi, dan ta ni ko yanzu ki ci gaba da duk abin da ki ke yi mini, bai dame ni ba; amma muddin ki ka yi wani na yinƙurin cutar mini da matata ko ɗana, wallahi sai na ɗaure ki, ɗaurin rai da rai ma kuwa. Ba zan taɓa yin wasa da duk wani abu da ya shafe su ba, dan haka zaki amince da babu ruwanki da duk wani abu da ya shafe su, balle a zo ga batun cutarwa"
Wani abu raɗaɗi ya tsirga wa Asal, wai ita ake gindaya wa sharaɗi a kan Nana. Sai dai babu yadda ta iya ta jinjina masa kai ta ce "Na amince"
Ya ce "Ki yi tunani da kyau, kar ki saɓa abin da ki ka ce daga baya, na ɗauki mataki ki ji haushina"
"Na tabattar da na amince"
Imrana ya ce "Wani nisan kiwo, kame ni a kayi, a ka kai ni makarantar dole, abubuwa ne da yawa suka faru" Ai tuni suka manta da wani batun ba sa jituwa, saboda girman alaƙar jini, suka din ga murnar ganin junansu.
Daga nan aka shiga shigo da kayan auren Nana, sai da Baba ya saki baki, a ransa ya fara tunanin anya mutanen nan su na da hankali kuwa. Saboda shi yanzu al'amuran abin duniya tsoro suke ba shi.
Domin karrama abin da su Baba suke da shi, su Turaki suka ci abincin da aka kawo musu.
Aka gabatar musu da 'yan uwan Nana, Yaya Atine sai rawar kai take, tana nanata musu ita yayar Baban Nana ce uwa É—aya uba É—aya, ita ta saki Nono ya kama.
Haushi sai da ya kama Imran, Gaddafi ma ya tsuke fuska ya ce "Matar nan duk abin da aka haÉ—a da ita sai ta yi hauka"
Imrana ya ce "Har da wani ita ta saki nono ya kama, kamar nonon akuya, ko kunya ba ta ji ba, kamar ba da ita aka dinga muzguna wa Nana ba"
Ta din ga rawar ƙafa tana jan su da hira, sai da ta ba wa kowa haushi.
Da suka tashi tafiya kuwa, Haka Ummi ta shiga maƙwabta ta karɓo kayan da aka shirya, na tukuci da za su tafi da shi, dan kar ma wani ya sanya zalama. Kaji, da kayan snacks masu yawan gaske, da dabino kusan kwano biyar da tasoshin turare.
Turaki ya ce karramawar da aka yi musu ta isa, ba za su karɓi komai ba, ai Nana 'yar Sultan ce.
Gaddafi ya ce idan ba su karɓa ba, ba za su ji daɗi ba.
Baba ya ga za su tafi ya yi musu godiya sannan ya ce "To ba za a kawo mini Nanan ba, ita yaushe zan ganta?"
Imam Zahradeen ya ce "Zaka ganta Baba, sai kun zo Agadez biki, za ku ganta in sha Allah, ga Imrana mun kawo maka har gida ai"
Jiki a sanyaye ya ce "Nanan dai nake son gani, amma shikenan mun gode sosai da sosai"
Imrana ya ce "Tun da ni baya son ganina, bari na biku mu koma"
Cikin sauri Baba ya ce "A'a Imrana, kai ma na yi murna da ganinka"
Suka yi murmushi baki É—aya, su Mahmoudu ya ce "Duk wanda za su je, a kira a gaya mana adadin mutane, za a É—auki nauyin zuwansu da dawowar su, sannan kuma idan an gama ganin kayan da su za a tafi. Daga nan suka hau mota suka tafi.
Da suka koma gida, aka fara sauke kaya ana bubbuÉ—ewa, Baba komawa ya yi gefe ya fashe da kuka, domin hatta shi akwati guda aka yi masa.
Uwani ta ce "Isa meye haka kuma, ai abin farinciki ne, ka daina kukan nan dan Allah"
Maƙwabta ma ba a bar su a baya ba, suka din ga shigowa, sun ɗauka ko kayan auren Jamila aka kawo ko na Suwaiba. Mama baƙin ciki ya cika mata ciki, ganin yadda nata 'ya'yan duk suka zama abin da suka zama, babu wani na kirki, ta din ga cizon yatsan ina ma nata 'ya'yan ta saka aka aura wa buzun ba Nana ba.
Uwani ta ce "Allah ba azzalumin sarki ba ne, Nana ta sha wahala a rayuwa, ta yi ɗawainiya da yaron nan, da jikinta da ƙarfinta. Allah ya yi tana da rabon jin daɗi tun a Duniya"
Ummi ta ce "Wallahi Uwani, Nana ta sha wahala, da shi sosai da sosai, Allah ya nuna ikonsa. Kuma shi ma ya yi halacci"
Uwani ta ce "Ba kaÉ—an ba, Allah dai ya ba su zaman lafiya"
Imran ya ce "Dan ma ba ku ji wahalar da ta sha a Niger É—in nan ba, da yawon nemansa" Nan Imrana ya gaya musu abin da ya sani. Yaya Atine ta ja baki ta yi shiru.
Uwani ta ce "To Isa, ina fatan ya zame maka izina, akan abubuwan da ka aikata wa yarinyar nan. Kuma ya zama dole a kira mahaifiyarta a sanar da ita komai, kuma a yi shirin tafiya da ita gurin bikin nan, dan ba za ka ci gaba da wannan jahilcin ba"
Imrana ya ce "To ai a Bauchi muka kwana, an je har gida an kai wa Umma lefen ta gani, an yi mata godiya sannan muka taho nan yau"
Uwani ta ce "Ikon Allah, haihuwa mai rana" Duk yadda Mama ta so ɓoye ɓakin cikinta abu ya ci tura.
Can gidan Umman su Nana, ta yi sujuda babu adadi na tsantsar murna da farinciki. Iliyasu kansa bakinsa ya ƙi rufuwa, amma ko kallo bai ishe ta ba. Dan ta wani fannin guduwar Nana, sauƙi ya sama mata, dan tun da ya san ya yi sanadin ɓatan Nana, duk abin da take yi masa baya cewa uffan.
"Mai Jidda kin ga ikon Allah ko? Ashe ta wani fannin gara da Nana ta je neman mijin nata, da tana zaune a nan babu lallai su haÉ—u. Allah sarki rayuwa"
Maijidda ji ta yi kamar ta make shi, ya ga abin Duniya, jikinsa sai tsuma yake yi.
*****
Asal na zaune ta damƙe wayarta iya ƙarfinta, saboda ganin hoton katin gayyatar bikin taron bikin Hammad da matarsa, da kuma naɗe-naɗen sarauta.
Hasna ta ce "Asal, ki ajiye wayar nan ki samu ki saka wani abu a cikinki mana" Ta girgiza kai hawaye na gangarowa daga idanunta.
Ji suka yi an buɗe ƙofar ɗakin, suka ɗaga baki ɗaya. Hammad ne ya shigo, jikinsa sanye da shiga ta alfarma. Ƙamshin turarensa ya mamaye ɗakin baki ɗaya.
Hasna ta risuna cikin girmamawa tana gaishe shi. Asal kuwa ta sunkuyar da kanta, zuciyarta na tsananta bugawa cike da tsoro da fargaba, saboda ba ta taɓa tsammanin ganinsa ba. Kuma ba ta san me yake tafe da shi ba. Da yatsunsa biyu ya yi wa Hasna alamar ta fita ta ba su guri.
Ayshercool
08081012143
100
LITTAFIN KUÆŠI NE, A BIYA KUÆŠIN KARATU KAN A KARANTA.
0069685771
AISHA ADAM STANBIC
08081012143
Asal ta sunkuyar da kanta ƙasa, ji take yi tamkar ƙasa ta tsage ta shige, saboda matsananciyar kunyarsa da take ji.
Ya ƙarasa ya zauna a gefenta, ya ce "Me ya same ki haka?" Ba ta ɗago ba, ta girgiza masa kai.
Shiru ya wanzu tsakanin su, babu wanda ya yi magana. Ya ce "Tun da ba za ki yi magana ba shikenan" Har ya yinƙura, ta riƙe rigarsa ta ce "Sakina ka zo ka yi ko?"
"A'a, dama ai ni ban kore ki ba, na dai ba ki zaɓin zama da ni ne, amma na ga kamar ke da mahaifinki, kun fi gamsuwa da na sauwwaƙe miki."
"Dan Allah Hammad ka yi haƙuri ka yafe mini, na san laifukana ba za su ƙirgu ba, sai a wannan karon Allah ya tona asirina"
Yayi murmushi ya ce "Ba zan yi miki dole ki zauna da ni ba, muddin kin san zuciyarki haryanzu tana son Omar" Wata irin É—agowa Asal ta yi a razane jin abin da ya ce.
"Hmm Asal kenan, duk tsawon zaman da na yi da ke, babu abin da ban sani ba, kar ma ki yi zaton ko wani ne ya gaya mini. Saka mini magani da duk wani nau'i na ƙoƙarin illata ni da ki ke yi, duk na sani, kuma ina kallonki. Ba domin babu yadda zan yi da ke ba, sai domin ina jin tausayinki, kuma ke ƙanwata ce"
Zamowa ta yi ƙasa cikin kuka ta riƙe rigarsa ta ce "Wallahi na yi nadama Hammad, na san ko ba ka ce mini komai ba, Hakkinka ba zai bar ni ba. Amma ba laifina ba ne ba, ka sani dan Allah ka yi haƙuri ka yafe mini, kar ka sake ni. Wallahi ina sonka"
"Dama ai ban ce zan sake ki ba, mahaifinki ne ya nemi hakan, kuma nima na so aikatawa amma na duba idan na yi haka, ba ki da wata kyakykywar makoma, bayan gama lalata rayuwarki da aka yi. Kuma ba na son asirinki ya ci gaba da tonuwa a idon Duniya. Uwa uba Nana tana ta yi mini magiyar kar na rabu da ke. Na so samarwa kaina cikakkiyar nutsuwa da rayuwa da wadda bata harin komai daga gare ni sai alkhairi, amma ban san me Allah zai yi mini a sanadin yafe miki ba. Asal zaki koma ɗakinki bisa sharaɗi, dan ta ni ko yanzu ki ci gaba da duk abin da ki ke yi mini, bai dame ni ba; amma muddin ki ka yi wani na yinƙurin cutar mini da matata ko ɗana, wallahi sai na ɗaure ki, ɗaurin rai da rai ma kuwa. Ba zan taɓa yin wasa da duk wani abu da ya shafe su ba, dan haka zaki amince da babu ruwanki da duk wani abu da ya shafe su, balle a zo ga batun cutarwa"
Wani abu raɗaɗi ya tsirga wa Asal, wai ita ake gindaya wa sharaɗi a kan Nana. Sai dai babu yadda ta iya ta jinjina masa kai ta ce "Na amince"
Ya ce "Ki yi tunani da kyau, kar ki saɓa abin da ki ka ce daga baya, na ɗauki mataki ki ji haushina"
"Na tabattar da na amince"