Sashe 57
Buzu Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ya É—an yi shiru sannan ya ce "Mahaifiyata, Gimbiya Bilkisu, sun haÉ—a baki da É—an uwanta, mai girma Tafawa, suka yi masa sihiri, aka haÉ—a shi da aljanin da zai bar garin da shi gaba É—aya.
Wallahi ban san sun yi ba, sai daga baya take gaya mini, saboda su na son ko ni ko Asadullah wani ya gaji kujerar Hammad. Na nuna mata rashin jin daɗina, ta ce mini aikin gama ya riga ya gama, muddin Hammad ya dawo Agadez sai ya haukace, ko ma ya rasa rayuwarsa. Shi ne na ɓoye lamba, na nemi Mahmoudu, a lokacin bai riga ya bar ƙasar ba, abin dai ya fara taɓa shi ne. Yanzun ma ba ni da yadda zan yi ne, amma ban so na tona wa mahaifiyata asiri ba"
Hammad ya sunkuyar da kai hawaye na zuba daga idanunsa, Sultan ya rikice cikin tashin hankali da damuwa ya ce "Yanzu Zahradeen amma ka ɓoye mini wannan abin baka gaya mini ba? Yanzu ƙiyayyar da mahaifiyarka take yi wa Hammad har ya kai ga ta nemi ta zauta mini ɗa ya bar gida?"
Zahradeen yana kuka ya ce "Dan Allah ka yi haƙuri Abie, ban san komai a kai ba, sai daga baya. Kuma gudun kar idan ya dawo ya samu matsala, shiyasa na ce kar ya dawo Niger"
Nana ta ce "Gidan tarihi, a gidan tarihin Agadez aka yi masa sihirin, kuma ba sihiri ɗaya ba ne, mutane daban-daban sun yi masa. Ranar da muka je cikin gidan tarihin tare da shi, na ji ƙamshin turaren Gimbiya Bilkisu a gurin. Sannan bayan ƙamshin turaren ta, na ji ƙamshin turaren wani ma.
Gaba É—aya suka É—aga kai, su na kallon Nana.
"Duk wanda yake ƙamshin nan, da alama yana ziyartar gurin, kuma wanda yake yi musu aikin sihirin a cikin gidan tarihin yake. Idan gidan tarihin nan babu kowa a cikin sa, to wannan mai gadin ne bokan da yake aikin, ko kuma ya san bokan da yake yi.
A rikice Sultan ya ce "Wane gidan tarihin wai, waye mai gadin?" Sai kuma ya rufe bakinsa, suka dubi Hammad a rikice, yadda ya runtse idanunsa yana zubar da hawaye.
Nana ta rikice ta tashi ta nufe shi, Sarkin baka ya ce "Kar ki taɓa shi, Giyaz ne yake zungurarsa, zai iya yi miki wani abin ya cutar da ke"
Ya tafi gaban Hammad, ya kama goshinsa ya din ga karanta Bismillah da suratul Fatiha, yana tofa masa a tsakiyar kansa.
Daga bisani ya ɗaga rigarsa ya ciro jakar nan da ya bawa Nana, ya ce "Idan baka tafi ka ƙyale shi ba, zan illataka da jakar nan kamar yadda Ƙaisar ya yi maka"
Nana rikicewa ta yi, duk da ba yau ta saba ganin abin mamaki ba, jakar da take hannunta, ta neme ta ta rasa, ta ganta a gurin Ƙaisar, yanzu kuma ta koma hannun mai ita Sarkin baka.
Ya kalli Nana ya ce "A gurin ƙamshin turaren wa ki ke ji?"
Nana ta yi shiru tana satar kallon Sultan, tana kuma kallon Zahradeen.
"Kar ki ji tsoron kowa, gaya mini" Ta ƙi magana tana jinjina yadda za su ɗauki abin.
Ya ce "Muje ki nuna mini gurin, ai babu abin da zai gagara da ƙarfin ikon Allah"
Sultan ya tashi a rikice jikinsa yana tsuma, idanunsa sun yi jawur saboda ya kaÉ—u da abubuwan da suka fito daga bakin Imam Zahradeen. Wani irin mugun tausayin Hammad ya mamaye masa zuciya.
Ya kalli su Nana ya ce "Yanzu can gidan tarihin za mu je kenan?"
N
Sarkin baka ya ce "Eh Allah ya baka yawan rai"
Imam Zahradeen ya ce "Ko a yi wa su Matawalle magana, a tafi da wani daga cikin su, ko hadimai"
"Bana buƙata" Sultan ya faɗa fuskarsa babu annuri, ba tare da ya kalli inda Imam Zahradeen yake ba.
Ya dubi Hammad da ya buÉ—e idanunsa, sai dai baya magana, dan tun da ya zo wa Sultan ya ce masa Zahradeen ne, bai sake yin magana ba.
Ya shafa kansa ya ce "Hammad, ka na ji na?" Ya jinjina kai.
"Ko zaka bi mu ne?" Ya girgiza kai.
"Ka na nan mu je mu dawo?" Ya É—aga masa kai alamar eh.
Ya girgiza kai ya ce "Ina Mahmoudu ne, ban ganku tare da shi ba, a nemo shi ya zo ya zauna da shi tukuna sai mu tafi"
Imam Zahradeen ya tafi ciro wayarsa, ya hau laluben lambar Mahmoudu. Sultan da ya kalli Imam Zahradeen sai ya ji ransa ya ɓaci, ya yi mamaki ya kaɗu matuƙa da jin abin da Gimbiya Bilkisu ta yi wa Hammad. Ga abubuwan da Tafawa ya din ga yi masa, da tursasa shi a kan yi masa abubuwan da yake so, da shi da 'yarsa amma hakan bai ishe su ba, suka nemi a ɓatar masa da ɗansa.
Sai da Mahmoudu ya zo, Imam Zahradeen ya ce "Imam Hammad ba ya jin daÉ—i ne, ka zauna tare da shi, zamu je mu dawo"
Tiryan-tiryan suka bi ta ɗakin da su Nana suke zaune, suka buɗe wannan ƙofar kamar yadda Nana ta yi musu bayanin ta nan suka bi, suka gangara har gidan tarihin.
Mai gadin na ganin Sultan, jikinsa ya hau tsuma ya zube a ƙasa tamkar zai yi masa sujuda yana kwasar gaisuwa. Sai dai gaba ɗaya ya rikice da ganin Sarkin baka.
Ko da suka shiga cikin gurin, kawai Sarkin baka ya bushe da dariya, duk suka tsaya suna kallonsa. Ya tsaya yana ƙare wa gurin kallo, yadda aka rarake dutse aka gina wannan gurin, mutanen zamanin da suka yi wannan aikin sun cancanci yabo.
Sarkin baka ya sake bushewa da dariya ya ce "Sarki a dawa Sarki a gida, Ni mai Duna ni mai Salamatu, ni mai Mairo 'yar Fulani. Ni ake yi wa inkiya biyu, Garba ga Baka ga Aska, na yi gadon gidanmu, na ƙwaci wanda ban gada ba, na fi 'yan na gada iyawa. Ni Abubakar Garba mai taƙama da ikon Allah. Na ga mutum na ga Aljan, na ga cuta na bada maganinta, idan babu na ce ba ruwan Garba. Ya buga ƙafarsa ɗaya ya ce "Uwar gijiyata, ƙamshin turaren wa ki ka ce kina ji?"
Nana ta sake kallon su Sultan, Sarkin Baka ya ce "FaÉ—i kanki tsaye, ba wanda zai yi miki abin da Allah bai yi miki ba"
Ta É—an sunkuyar da kai ta ce "Akwai wani Imam Omar, wanda ya kawo wa Imam Hammad ayaba tare da Yayan Asal"
"Ƙamshin turarensa ne?" Imam Zahradeen ya tambaye ta cikin zaƙuwa.
Ta ce "Ni tsoron faÉ—a nake, ba na son haÉ—a husuma ne"
Sultan ya sassauta murya ya ce "Ki na ji na? Ba haÉ—a husuma ba ne ba, mijinki za ki taimaka tun da ke Allah ya yarje miki gano wasu abubuwan da mu ba mu gano ba"
Bakinta na rawa ta ce "Wannan mai kama shi ɗin, da ku ke yawan zama ku uku, mai saka shuɗin rawani, bayan ƙamshin turaren Gimbiya Bilkisu, ranar da muka zo nan, ƙamshin turarensa ne yake tashi, alamar bai daɗe da tafiya ba"
A rikice Imam Zahradeen ya ce "Sardaunan Agadez, ƙamshin turarensa ne"
Buɗe baki Sultan ya yi, ya fara numfarfashi yana kallon Nana, ya ce "Me hakan yake nufi? Ina fatan ba dai wani abin ya yi ba?" Nana ta girgiza kai cikin tsoro ta ce "Ba ni da tabbas, tun da kowa yana da damae zuwa gurin nan, mussaman a cikin manyan Agadez kamar yadda Imam Hammad ya gaya mini. Amma me zai kawo shi nan cikin dare wajen ƙarfe sha biyu na dare. Kuma a mudubin Ƙaisar na ga wani abu da ya sanya ban ji na yarda da ɗakin can ba, amma ba ni da tabbas tun da maganar aljani ba abar yadda ba ce ba wasu lokutan"
Sarkin baka kawai ya nufi ƙofar ɗakin, da Nana ta yi ta nacin a buɗe ta, yana zuwa ya jijjiga ƙofar, amma ya ga ƙaton mukulli a jiki.
A nutse ya ƙare wa sauran ƙofofin kallo, ya saki mukullin ya nufi hanyar fita, yana zuwa ya janyo mai gadin nan har zuwa inda su Sultan suke.
Ya kalle shi ido cikin ido Sarkin baka ya ce "Waye kai?"
"Mai gadin gidan tarihin Agadez" Ya ba shi amsa.
Sarkin baka ya ce "Kai, mugu shi ya san makwantar mugu. Kai da gani idanun nan nawa ka san babu abin da ban gani ba. Waye da waye suke zuwa gurin nan?"
Mai gadin ya yi wa Sarkin baka wani irin kallo, ya ce "Kowa ma yana iya zuwa"
"Ba kowan ba, muhimman mutanen da ka ke yi wa aiki"
"Ni ba ni da wani aiki bayan buÉ—ewa da rufewa, da kula da ababen tarihi"
"Ka tabattar?"
Ya ce "Eh"
Wallahi ban san sun yi ba, sai daga baya take gaya mini, saboda su na son ko ni ko Asadullah wani ya gaji kujerar Hammad. Na nuna mata rashin jin daɗina, ta ce mini aikin gama ya riga ya gama, muddin Hammad ya dawo Agadez sai ya haukace, ko ma ya rasa rayuwarsa. Shi ne na ɓoye lamba, na nemi Mahmoudu, a lokacin bai riga ya bar ƙasar ba, abin dai ya fara taɓa shi ne. Yanzun ma ba ni da yadda zan yi ne, amma ban so na tona wa mahaifiyata asiri ba"
Hammad ya sunkuyar da kai hawaye na zuba daga idanunsa, Sultan ya rikice cikin tashin hankali da damuwa ya ce "Yanzu Zahradeen amma ka ɓoye mini wannan abin baka gaya mini ba? Yanzu ƙiyayyar da mahaifiyarka take yi wa Hammad har ya kai ga ta nemi ta zauta mini ɗa ya bar gida?"
Zahradeen yana kuka ya ce "Dan Allah ka yi haƙuri Abie, ban san komai a kai ba, sai daga baya. Kuma gudun kar idan ya dawo ya samu matsala, shiyasa na ce kar ya dawo Niger"
Nana ta ce "Gidan tarihi, a gidan tarihin Agadez aka yi masa sihirin, kuma ba sihiri ɗaya ba ne, mutane daban-daban sun yi masa. Ranar da muka je cikin gidan tarihin tare da shi, na ji ƙamshin turaren Gimbiya Bilkisu a gurin. Sannan bayan ƙamshin turaren ta, na ji ƙamshin turaren wani ma.
Gaba É—aya suka É—aga kai, su na kallon Nana.
"Duk wanda yake ƙamshin nan, da alama yana ziyartar gurin, kuma wanda yake yi musu aikin sihirin a cikin gidan tarihin yake. Idan gidan tarihin nan babu kowa a cikin sa, to wannan mai gadin ne bokan da yake aikin, ko kuma ya san bokan da yake yi.
A rikice Sultan ya ce "Wane gidan tarihin wai, waye mai gadin?" Sai kuma ya rufe bakinsa, suka dubi Hammad a rikice, yadda ya runtse idanunsa yana zubar da hawaye.
Nana ta rikice ta tashi ta nufe shi, Sarkin baka ya ce "Kar ki taɓa shi, Giyaz ne yake zungurarsa, zai iya yi miki wani abin ya cutar da ke"
Ya tafi gaban Hammad, ya kama goshinsa ya din ga karanta Bismillah da suratul Fatiha, yana tofa masa a tsakiyar kansa.
Daga bisani ya ɗaga rigarsa ya ciro jakar nan da ya bawa Nana, ya ce "Idan baka tafi ka ƙyale shi ba, zan illataka da jakar nan kamar yadda Ƙaisar ya yi maka"
Nana rikicewa ta yi, duk da ba yau ta saba ganin abin mamaki ba, jakar da take hannunta, ta neme ta ta rasa, ta ganta a gurin Ƙaisar, yanzu kuma ta koma hannun mai ita Sarkin baka.
Ya kalli Nana ya ce "A gurin ƙamshin turaren wa ki ke ji?"
Nana ta yi shiru tana satar kallon Sultan, tana kuma kallon Zahradeen.
"Kar ki ji tsoron kowa, gaya mini" Ta ƙi magana tana jinjina yadda za su ɗauki abin.
Ya ce "Muje ki nuna mini gurin, ai babu abin da zai gagara da ƙarfin ikon Allah"
Sultan ya tashi a rikice jikinsa yana tsuma, idanunsa sun yi jawur saboda ya kaÉ—u da abubuwan da suka fito daga bakin Imam Zahradeen. Wani irin mugun tausayin Hammad ya mamaye masa zuciya.
Ya kalli su Nana ya ce "Yanzu can gidan tarihin za mu je kenan?"
N
Sarkin baka ya ce "Eh Allah ya baka yawan rai"
Imam Zahradeen ya ce "Ko a yi wa su Matawalle magana, a tafi da wani daga cikin su, ko hadimai"
"Bana buƙata" Sultan ya faɗa fuskarsa babu annuri, ba tare da ya kalli inda Imam Zahradeen yake ba.
Ya dubi Hammad da ya buÉ—e idanunsa, sai dai baya magana, dan tun da ya zo wa Sultan ya ce masa Zahradeen ne, bai sake yin magana ba.
Ya shafa kansa ya ce "Hammad, ka na ji na?" Ya jinjina kai.
"Ko zaka bi mu ne?" Ya girgiza kai.
"Ka na nan mu je mu dawo?" Ya É—aga masa kai alamar eh.
Ya girgiza kai ya ce "Ina Mahmoudu ne, ban ganku tare da shi ba, a nemo shi ya zo ya zauna da shi tukuna sai mu tafi"
Imam Zahradeen ya tafi ciro wayarsa, ya hau laluben lambar Mahmoudu. Sultan da ya kalli Imam Zahradeen sai ya ji ransa ya ɓaci, ya yi mamaki ya kaɗu matuƙa da jin abin da Gimbiya Bilkisu ta yi wa Hammad. Ga abubuwan da Tafawa ya din ga yi masa, da tursasa shi a kan yi masa abubuwan da yake so, da shi da 'yarsa amma hakan bai ishe su ba, suka nemi a ɓatar masa da ɗansa.
Sai da Mahmoudu ya zo, Imam Zahradeen ya ce "Imam Hammad ba ya jin daÉ—i ne, ka zauna tare da shi, zamu je mu dawo"
Tiryan-tiryan suka bi ta ɗakin da su Nana suke zaune, suka buɗe wannan ƙofar kamar yadda Nana ta yi musu bayanin ta nan suka bi, suka gangara har gidan tarihin.
Mai gadin na ganin Sultan, jikinsa ya hau tsuma ya zube a ƙasa tamkar zai yi masa sujuda yana kwasar gaisuwa. Sai dai gaba ɗaya ya rikice da ganin Sarkin baka.
Ko da suka shiga cikin gurin, kawai Sarkin baka ya bushe da dariya, duk suka tsaya suna kallonsa. Ya tsaya yana ƙare wa gurin kallo, yadda aka rarake dutse aka gina wannan gurin, mutanen zamanin da suka yi wannan aikin sun cancanci yabo.
Sarkin baka ya sake bushewa da dariya ya ce "Sarki a dawa Sarki a gida, Ni mai Duna ni mai Salamatu, ni mai Mairo 'yar Fulani. Ni ake yi wa inkiya biyu, Garba ga Baka ga Aska, na yi gadon gidanmu, na ƙwaci wanda ban gada ba, na fi 'yan na gada iyawa. Ni Abubakar Garba mai taƙama da ikon Allah. Na ga mutum na ga Aljan, na ga cuta na bada maganinta, idan babu na ce ba ruwan Garba. Ya buga ƙafarsa ɗaya ya ce "Uwar gijiyata, ƙamshin turaren wa ki ka ce kina ji?"
Nana ta sake kallon su Sultan, Sarkin Baka ya ce "FaÉ—i kanki tsaye, ba wanda zai yi miki abin da Allah bai yi miki ba"
Ta É—an sunkuyar da kai ta ce "Akwai wani Imam Omar, wanda ya kawo wa Imam Hammad ayaba tare da Yayan Asal"
"Ƙamshin turarensa ne?" Imam Zahradeen ya tambaye ta cikin zaƙuwa.
Ta ce "Ni tsoron faÉ—a nake, ba na son haÉ—a husuma ne"
Sultan ya sassauta murya ya ce "Ki na ji na? Ba haÉ—a husuma ba ne ba, mijinki za ki taimaka tun da ke Allah ya yarje miki gano wasu abubuwan da mu ba mu gano ba"
Bakinta na rawa ta ce "Wannan mai kama shi ɗin, da ku ke yawan zama ku uku, mai saka shuɗin rawani, bayan ƙamshin turaren Gimbiya Bilkisu, ranar da muka zo nan, ƙamshin turarensa ne yake tashi, alamar bai daɗe da tafiya ba"
A rikice Imam Zahradeen ya ce "Sardaunan Agadez, ƙamshin turarensa ne"
Buɗe baki Sultan ya yi, ya fara numfarfashi yana kallon Nana, ya ce "Me hakan yake nufi? Ina fatan ba dai wani abin ya yi ba?" Nana ta girgiza kai cikin tsoro ta ce "Ba ni da tabbas, tun da kowa yana da damae zuwa gurin nan, mussaman a cikin manyan Agadez kamar yadda Imam Hammad ya gaya mini. Amma me zai kawo shi nan cikin dare wajen ƙarfe sha biyu na dare. Kuma a mudubin Ƙaisar na ga wani abu da ya sanya ban ji na yarda da ɗakin can ba, amma ba ni da tabbas tun da maganar aljani ba abar yadda ba ce ba wasu lokutan"
Sarkin baka kawai ya nufi ƙofar ɗakin, da Nana ta yi ta nacin a buɗe ta, yana zuwa ya jijjiga ƙofar, amma ya ga ƙaton mukulli a jiki.
A nutse ya ƙare wa sauran ƙofofin kallo, ya saki mukullin ya nufi hanyar fita, yana zuwa ya janyo mai gadin nan har zuwa inda su Sultan suke.
Ya kalle shi ido cikin ido Sarkin baka ya ce "Waye kai?"
"Mai gadin gidan tarihin Agadez" Ya ba shi amsa.
Sarkin baka ya ce "Kai, mugu shi ya san makwantar mugu. Kai da gani idanun nan nawa ka san babu abin da ban gani ba. Waye da waye suke zuwa gurin nan?"
Mai gadin ya yi wa Sarkin baka wani irin kallo, ya ce "Kowa ma yana iya zuwa"
"Ba kowan ba, muhimman mutanen da ka ke yi wa aiki"
"Ni ba ni da wani aiki bayan buÉ—ewa da rufewa, da kula da ababen tarihi"
"Ka tabattar?"
Ya ce "Eh"