Sashe 39
Buzu Part 3 Complete Hausa Novel · about 3 min read
Ya ce "Matso na rungume ki, ki nutsu sai mu ci gaba" Ya ƙara matsawa kusa da ita, ya rungumota jikinsa, yana murmushi. Ta kwanta lamo a jikinsa yana shafa bayanta a hankali.
A ransa ya ce "Asmy, ba za ki taɓa jin rabi a kwatankwacin abin da nake ji a kan ki ba, ina ƙaunarki ina kishinki, Allah ya bamu haƙurin zama da juna"
Asal kuwa na can a tsaye, tamkar ta haɗiyi taɓarya, idanunta suka sauka a kan agogon bangon ɗakin. Idanunta sun bushe, zuciyarta ta ƙeƙashe sai raɗaɗi da idanun kawai suke yi mata.
Haryanzu ta kasa yadda Hammad ne yake da wata matar, matar ma baƙar fata da a kyau ba ta kai ta komai ba. Babban abin da ya ƙara rikita ta bai wuce batun ɗa da Tafawa ya tabattar mata da Hammad yana da shi ba, har ɗan shekaru biyu ba.
Zuciyarta ta din ga bugawa da sauri da sauri, tsawon lokacin nan ba ta taɓa tunanin son da take yi wa Hammad ya kai haka ba, ashe duk abin da take yi bonono take rufe ƙofa da ɓarawo. Tana zaman zamanta ta janyo masifa da kanta jikinta. Ta din ga tunanin ko dai wata ƙulla-ƙullar ce ta daban aka yi. Sai kuma ta tuna babu yadda za a yi Nana ta samu zarafin shiga har sashen Sultan, su keɓe da Hammad idan ba matarsa ba ce ba. Kenan Sultan ya goyi bayan abin da Hammad ya yi na auren baƙar fata da ba ƙabilarsu ba?. Kawai ta ɗora hannu a ka ta rushe da kuka, hawaye ya ƙi zubo mata sai azabar zafi da zuciyarta take yi.
Gimbiya Bilkisu ce ta shigo É—akin tana faÉ—in "Asal lafiya kuwa?"
"Na shiga uku na lalace Gimbiya, wallahi Hammad ya cuce ni ba zan yafe masa ba. Kuma wallahi sai ya rabu da ita, an cuce ni an cuci rayuwata"
Ta rungume Asal tana rarrashinta, ta ce "Ki yi haƙuri, ki daina wannan kukan kar ki samu matsala, ki kwantar da hankalinki na san Sultan ba zai ƙyale shi ba, zai ɗauki mataki" Asal ta ci gaba da kuka da babu abin da yake ƙara mata sai nauyin zuciya.
*****
Imam Hammad kuwa a hankali ya É—an É—ago fuskar Nana ya ce "Bacci ki ke yi ne?"
Ta girgiza kai alamar a'a.
"To tashi mu ci gaba" Ta noƙe kafaɗa tana ƙara rungume shi.
Ta ce "Imam ka ci gaba mu yi mu bar gurin nan, Aljanun gurin nan sun fara tsorata ni, kar a samu matsala"
"Kina ganinsu ne?"
"Su na bayyana a siffofi daban-daban, tsofaffi tukuf da matasa da wasu halittun daban, duk ina ganinsu addu'a kawai nake yi tun É—azu"
"Ni da ke duniyarm daban take, ƙalubale iri ɗaya, Ubangiji Allah ya bamu lafiya rayuwar Hammad".
Ta sake lafewa a jikinsa ta ce "Ka ci gaba to"
Ya numfasa.
A ransa ya ce "Asmy, ba za ki taɓa jin rabi a kwatankwacin abin da nake ji a kan ki ba, ina ƙaunarki ina kishinki, Allah ya bamu haƙurin zama da juna"
Asal kuwa na can a tsaye, tamkar ta haɗiyi taɓarya, idanunta suka sauka a kan agogon bangon ɗakin. Idanunta sun bushe, zuciyarta ta ƙeƙashe sai raɗaɗi da idanun kawai suke yi mata.
Haryanzu ta kasa yadda Hammad ne yake da wata matar, matar ma baƙar fata da a kyau ba ta kai ta komai ba. Babban abin da ya ƙara rikita ta bai wuce batun ɗa da Tafawa ya tabattar mata da Hammad yana da shi ba, har ɗan shekaru biyu ba.
Zuciyarta ta din ga bugawa da sauri da sauri, tsawon lokacin nan ba ta taɓa tunanin son da take yi wa Hammad ya kai haka ba, ashe duk abin da take yi bonono take rufe ƙofa da ɓarawo. Tana zaman zamanta ta janyo masifa da kanta jikinta. Ta din ga tunanin ko dai wata ƙulla-ƙullar ce ta daban aka yi. Sai kuma ta tuna babu yadda za a yi Nana ta samu zarafin shiga har sashen Sultan, su keɓe da Hammad idan ba matarsa ba ce ba. Kenan Sultan ya goyi bayan abin da Hammad ya yi na auren baƙar fata da ba ƙabilarsu ba?. Kawai ta ɗora hannu a ka ta rushe da kuka, hawaye ya ƙi zubo mata sai azabar zafi da zuciyarta take yi.
Gimbiya Bilkisu ce ta shigo É—akin tana faÉ—in "Asal lafiya kuwa?"
"Na shiga uku na lalace Gimbiya, wallahi Hammad ya cuce ni ba zan yafe masa ba. Kuma wallahi sai ya rabu da ita, an cuce ni an cuci rayuwata"
Ta rungume Asal tana rarrashinta, ta ce "Ki yi haƙuri, ki daina wannan kukan kar ki samu matsala, ki kwantar da hankalinki na san Sultan ba zai ƙyale shi ba, zai ɗauki mataki" Asal ta ci gaba da kuka da babu abin da yake ƙara mata sai nauyin zuciya.
*****
Imam Hammad kuwa a hankali ya É—an É—ago fuskar Nana ya ce "Bacci ki ke yi ne?"
Ta girgiza kai alamar a'a.
"To tashi mu ci gaba" Ta noƙe kafaɗa tana ƙara rungume shi.
Ta ce "Imam ka ci gaba mu yi mu bar gurin nan, Aljanun gurin nan sun fara tsorata ni, kar a samu matsala"
"Kina ganinsu ne?"
"Su na bayyana a siffofi daban-daban, tsofaffi tukuf da matasa da wasu halittun daban, duk ina ganinsu addu'a kawai nake yi tun É—azu"
"Ni da ke duniyarm daban take, ƙalubale iri ɗaya, Ubangiji Allah ya bamu lafiya rayuwar Hammad".
Ta sake lafewa a jikinsa ta ce "Ka ci gaba to"
Ya numfasa.