Sashe 15
Buzu Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Ta wuce ta je ina? Kun san zata wuce ku ka dakatar da ni daga majalissa. Ya faɗi abin da dole sai ya fito ya kare maganar da ya yi. Ya ce yana da ɗa, ina ɗan yake? Kuma wacece uwar yaron? Idan kuma shaci faɗi ne to ta tabatta ba shi da lafiyar ƙwaƙwalwa da na faɗa ku ke ɓoyewa"
Matawalle ya ce "Imam Hammad ba mahaukaci ba ne ba, ka san abin da zaka din ga furtawa a kansa, ko babu alaƙar jini a tsakaninku shi shugaba ne."
"Eh Hammad ɗa na ne, kuma shugaba ne, amma ba zai yiwu na zuba ido ina ganin ba daidai ba, a ce yana shugaba babu cikakkiyar lafiya ba kuma ku na dannewa ku ɓoyewa ba. Ita larura ai ba abin kunya ba ce, kuma abu ne da yakamata a sani domin a nemi lafiya"
Cikin nutsuwa Sultan ya ce "Imam Hammad ba mahaukaci ba ne ba, ban sna meyasa ka ke aibata shi da da wannan larurar ba"
"Allah ya taimake ka, idan ba haka ba ne, mene ne gaskiyar batun É—an da ya ce yana da shi?" Tafawa ya yi maganar yana tsare Sultan da ido.
"Abu ne da muke kan bincike a kai, koma mene ne zaka ji daga baya"
Ya ce "Shikenan na ji wannan, ina son zan yi magana da shi, magana ce a kan É—iyata Asal"
Sultan ya kalli Tafawa cike da takaici, ya san yana sane yake wannan bin ƙwaƙƙwafin da bin diddigin a kan lallai sai ya ga Hammad."
Sultan ya ce "Za ka gan shi, amma nan da wani É—an lokaci" Hakan ya sanya Tafawa sake tabattar da maganganun Asal.
A ransa ya ce "Idan ka san wata baka san wata ba Jalaludeen"
*****
Tun washegarin dawowar Nana daga gidan su Hammad, yanayin jikinta take jin babu daɗi, kamar akwai wani abu mara daɗi da yake faruwa. Sai dai ta danganta hakan da kewa da kuma tashin hankali da take ciki a kan Muhsin. Amma idan ta nutsu sai ta ji wannan damuwar daban ce, wannan a cikin jikinta da ruhinta take jin damuwar, sai dai ta yi iya ƙoƙarinta gurin danne damuwar, da duƙufa da addu'a Allah ya dawo mata da ɗanta.
Yau da safe Nana ta fito ta tarar da Nana, ta ɗora tukkwane daban-daban har uku a kan murhu, tana ta harhaɗa wasu irin saiwoyi da sassaƙe-sassaƙe tana ta zubawa tana dafawa.
Nana ta ce "Umman Muhsin, yau kuma baya aka tuna wa ake dafa wa magani"
Nene ta yi murmushi ta ce "Ba kula ki zan yi ba ai ki ƙarata, daɗin abin ƙwaryar sama ce ke dukan ta ƙasa daga ni har ke"
Nana ta yi dariya ta ce "Yasin ni ban bayar da magani ba"
"A'a tuna dai, tuna dai yarinya"
"To ai Sayyid kawai na yi wa"
Nene ta ce "Kash, an zo gurin dan haka ki yi mini shiru" Ta ƙarasa maganar tana janyo wayarta da ta yi ƙarar shigowar saƙo. Ta tsuke fuska ta kira Mahmoudu a waya. Ya amsa tare da gaishe ta.
Bayan ta amsa ta ce "Wannan uban kuÉ—in fa da ka sako mini?"
"A'a ki yi haƙuri ai ba naki ba ne, na kula da Gimbiyar Imam ne"
"Da can ku kuke bani abin kula da ita? Lokacin da take gararambar neman taimakon ba ku neme ta ba ba barin ta ku ka yi tana gantali a titi ba?"
Ya ce "Dan Allah ki yi haƙuri, ba zan iya gaya masa haka ba. Haryanzu fa ma ni ban sake ganinsa ba tun ranar da ya je tare da ita. Ba ya gidansa baya fitowa zaman majillisa, ko hawa ba ya fitowa. Duk da na san an saka masa takunkumi shige da fice amma an tsaurara masa sosai. Ki yi haƙuri har gida za mu zo ban haƙuri. Dan Allah ki taya mu rarrashinta dan ta ƙi saurararsa gaba ɗaya, kuma wallahi hankalinsa a tashe yake nesa ba kusa ba. Ga tarin magauta da yake da su a cikin gidan su ma da ba barinsa suka yi ba. Dan Allah ku yi haƙuri Umma ke kin san sha'anin gidan sarauta kin san komai"
"Ni rabu da ni sai daÉ—in bakin tsiya, ai ko mutum zai danne ya yanka sai ka kare shi"
Yayi dariya ya ce "Ai ɗanki ne, kin san ba zai aikata haka ba, tuba muke ranki ya daɗe. Wallahi ina ta faɗi tashin na gan shi ne ma, na san halin da yake ciki. Amma a ƙara ba wa Gimbiyar Imam haƙuri"
"A'a babu ruwana, idan ku ka zo kwa bata da kanku" Suka yi sallama ta kashe wayar.
Ta kalli Nana ta ce "Kafin ki yi wanka, fara É—ibar ruwan maganin nan, ki je ki yi wanka ki gama, sai ki yi wanka da shi. Ki fito ki sha wannan maganin sai ki karya.
Nana ta ce "Shi kuma Nene na mene ne?"
"Na tsarin jiki da kariya ne, saboda kariya ne" Ta yi maganar tana basarwa, tare da tsuke fuska dan kar Nana ta addabe ta da tambayoyi.
Ganin hakan ya sanya Nana amsawa Nene, ba dan tana so ba.
*****
Mahmoudu ne ya iske Sultan a gurin shan iskarsa da yamma. Kasancewar shi ma ba shi da iyaka a shiga da fita a gidan Sultan, saboda Hammad, dan haka ganinsa ba wahala yake yi masa ba.
Sai dai yau kasancewar Sultan shikaÉ—ai ne, ya fi sakin jiki da shi.
"Barka da wannan yammaci Sultan"
"Barkanmu dai Mahmoudu, kuna lafiya?"
Ya amsa da "Alhamdillah. Alfarma nake nema daga gare ka Sultan"
"Ina sauraren ka"
"Dan Allah a yi mini izini na ga Imam Hammad ne.
Sultan ya numfasa ya ce "Hammad babu lafiya. Ta so muje ka gani"
Ya tashi cikin ladabi, ya bi bayan Sultan. Suka yi tafiya mai nisa a sashinsa, can cikin wani É—aki suka je ya buÉ—e masa É—akin.
Cikin damuwa ya ce "Mahmoudu ya tabatta Hammad hauka yake yi, haukan ma irin wanda ban taɓa ganin kalarsa ba. Na ce ko a Nigeria da ku ka zauna ya yi irin wannan? Yanzu idan ka je kusa da shi zai iya shaƙe ka, tsawon wannan lokacin bai ci abinci ba, a haka kawai yake"
Cikin tashin hankali ya ce "Yayi ciwo daban-daban, amma ban ga ya yi irin wannan ba, ina kyautata zaton mutum É—aya ne ya san matsalolinsa ciki da waje, ya san bakin zaren wannan ciwon nasa"
"Wane ne? Mahmoudu ba ma son asirinmu ya tonu fa"
"Da asirinmu zai tonu da tuni ta tona, sai dai a zo da Mahaifiyar Muhsin"
AREWABOOKS
Cikin rashin fahimta Sultan ya ce "Ban gane me ka ke nufi ba?"
Cikin girmamawa ya ce "Matarsa da ya zauna da ita a Nigeria, saboda ni kaina na fuskanci wasu abubuwa masu ban mamaki a tsakanin su, bayan sun yi aure." Ya yi maganar yana kallon inda Imam Hammad yake ta mimmiƙewa yana kakari, kamar ana yanka rago.
Cikin damuwa ya ce "Yanzu tun wancan lokacin a haka yake?" Sultan ya jinjina masa kai ya ce "Ko ruwa bai sake sha ba, hankalina a tashe yake. Ga Tafawa ya sako ni gaba a kan Imam Hammad sosai da sosai; Yanzu dai mu je ka yi mini bayani gwari-gwari na fahimta"
Bayan sun fito, suka zauna tare da Mahmoudu.
Mahmoudu ya numfasa ya ce "Idan ban manta ba, bayan mun dawo daga bikin buÉ—e gidan cin abincin Imam na MaraÉ—i, mun dawo ka sanar masa da batun tafiya Damagaran ya wakilceka a taron sarakuna da za a yi a Zinder. Ba zan manta ba an kai ruwa rana sosai a kan tafiyar.
A tsukin lokacin ya kan gaya mini cewa, shi gaba ɗaya ji yake yi baya ƙaunar zaman ƙasar nan, yana jin kamar a cikin wani bala'i da masifa yake. Da fari na zata da wasa yake yi, amma sai na fuskanci da gaske yake a lokacin. Na ce masa mu sanar maka ko ɗaga tafiyar za a yi, amma ya ce mini a'a kar na gaya wa kowa, baya son ya ɗaga wa kowa hankali.
Tare muke kwana da shi a cikin gidan nan, muna shirin tafiya , kawai ya ce mini na same shi a É—aya gidan nasa na kusa da gidan tarihi da yamma, mu yi tafiyar. Na ce masa mu tafi tare amma ya ce mini a'a.
Matawalle ya ce "Imam Hammad ba mahaukaci ba ne ba, ka san abin da zaka din ga furtawa a kansa, ko babu alaƙar jini a tsakaninku shi shugaba ne."
"Eh Hammad ɗa na ne, kuma shugaba ne, amma ba zai yiwu na zuba ido ina ganin ba daidai ba, a ce yana shugaba babu cikakkiyar lafiya ba kuma ku na dannewa ku ɓoyewa ba. Ita larura ai ba abin kunya ba ce, kuma abu ne da yakamata a sani domin a nemi lafiya"
Cikin nutsuwa Sultan ya ce "Imam Hammad ba mahaukaci ba ne ba, ban sna meyasa ka ke aibata shi da da wannan larurar ba"
"Allah ya taimake ka, idan ba haka ba ne, mene ne gaskiyar batun É—an da ya ce yana da shi?" Tafawa ya yi maganar yana tsare Sultan da ido.
"Abu ne da muke kan bincike a kai, koma mene ne zaka ji daga baya"
Ya ce "Shikenan na ji wannan, ina son zan yi magana da shi, magana ce a kan É—iyata Asal"
Sultan ya kalli Tafawa cike da takaici, ya san yana sane yake wannan bin ƙwaƙƙwafin da bin diddigin a kan lallai sai ya ga Hammad."
Sultan ya ce "Za ka gan shi, amma nan da wani É—an lokaci" Hakan ya sanya Tafawa sake tabattar da maganganun Asal.
A ransa ya ce "Idan ka san wata baka san wata ba Jalaludeen"
*****
Tun washegarin dawowar Nana daga gidan su Hammad, yanayin jikinta take jin babu daɗi, kamar akwai wani abu mara daɗi da yake faruwa. Sai dai ta danganta hakan da kewa da kuma tashin hankali da take ciki a kan Muhsin. Amma idan ta nutsu sai ta ji wannan damuwar daban ce, wannan a cikin jikinta da ruhinta take jin damuwar, sai dai ta yi iya ƙoƙarinta gurin danne damuwar, da duƙufa da addu'a Allah ya dawo mata da ɗanta.
Yau da safe Nana ta fito ta tarar da Nana, ta ɗora tukkwane daban-daban har uku a kan murhu, tana ta harhaɗa wasu irin saiwoyi da sassaƙe-sassaƙe tana ta zubawa tana dafawa.
Nana ta ce "Umman Muhsin, yau kuma baya aka tuna wa ake dafa wa magani"
Nene ta yi murmushi ta ce "Ba kula ki zan yi ba ai ki ƙarata, daɗin abin ƙwaryar sama ce ke dukan ta ƙasa daga ni har ke"
Nana ta yi dariya ta ce "Yasin ni ban bayar da magani ba"
"A'a tuna dai, tuna dai yarinya"
"To ai Sayyid kawai na yi wa"
Nene ta ce "Kash, an zo gurin dan haka ki yi mini shiru" Ta ƙarasa maganar tana janyo wayarta da ta yi ƙarar shigowar saƙo. Ta tsuke fuska ta kira Mahmoudu a waya. Ya amsa tare da gaishe ta.
Bayan ta amsa ta ce "Wannan uban kuÉ—in fa da ka sako mini?"
"A'a ki yi haƙuri ai ba naki ba ne, na kula da Gimbiyar Imam ne"
"Da can ku kuke bani abin kula da ita? Lokacin da take gararambar neman taimakon ba ku neme ta ba ba barin ta ku ka yi tana gantali a titi ba?"
Ya ce "Dan Allah ki yi haƙuri, ba zan iya gaya masa haka ba. Haryanzu fa ma ni ban sake ganinsa ba tun ranar da ya je tare da ita. Ba ya gidansa baya fitowa zaman majillisa, ko hawa ba ya fitowa. Duk da na san an saka masa takunkumi shige da fice amma an tsaurara masa sosai. Ki yi haƙuri har gida za mu zo ban haƙuri. Dan Allah ki taya mu rarrashinta dan ta ƙi saurararsa gaba ɗaya, kuma wallahi hankalinsa a tashe yake nesa ba kusa ba. Ga tarin magauta da yake da su a cikin gidan su ma da ba barinsa suka yi ba. Dan Allah ku yi haƙuri Umma ke kin san sha'anin gidan sarauta kin san komai"
"Ni rabu da ni sai daÉ—in bakin tsiya, ai ko mutum zai danne ya yanka sai ka kare shi"
Yayi dariya ya ce "Ai ɗanki ne, kin san ba zai aikata haka ba, tuba muke ranki ya daɗe. Wallahi ina ta faɗi tashin na gan shi ne ma, na san halin da yake ciki. Amma a ƙara ba wa Gimbiyar Imam haƙuri"
"A'a babu ruwana, idan ku ka zo kwa bata da kanku" Suka yi sallama ta kashe wayar.
Ta kalli Nana ta ce "Kafin ki yi wanka, fara É—ibar ruwan maganin nan, ki je ki yi wanka ki gama, sai ki yi wanka da shi. Ki fito ki sha wannan maganin sai ki karya.
Nana ta ce "Shi kuma Nene na mene ne?"
"Na tsarin jiki da kariya ne, saboda kariya ne" Ta yi maganar tana basarwa, tare da tsuke fuska dan kar Nana ta addabe ta da tambayoyi.
Ganin hakan ya sanya Nana amsawa Nene, ba dan tana so ba.
*****
Mahmoudu ne ya iske Sultan a gurin shan iskarsa da yamma. Kasancewar shi ma ba shi da iyaka a shiga da fita a gidan Sultan, saboda Hammad, dan haka ganinsa ba wahala yake yi masa ba.
Sai dai yau kasancewar Sultan shikaÉ—ai ne, ya fi sakin jiki da shi.
"Barka da wannan yammaci Sultan"
"Barkanmu dai Mahmoudu, kuna lafiya?"
Ya amsa da "Alhamdillah. Alfarma nake nema daga gare ka Sultan"
"Ina sauraren ka"
"Dan Allah a yi mini izini na ga Imam Hammad ne.
Sultan ya numfasa ya ce "Hammad babu lafiya. Ta so muje ka gani"
Ya tashi cikin ladabi, ya bi bayan Sultan. Suka yi tafiya mai nisa a sashinsa, can cikin wani É—aki suka je ya buÉ—e masa É—akin.
Cikin damuwa ya ce "Mahmoudu ya tabatta Hammad hauka yake yi, haukan ma irin wanda ban taɓa ganin kalarsa ba. Na ce ko a Nigeria da ku ka zauna ya yi irin wannan? Yanzu idan ka je kusa da shi zai iya shaƙe ka, tsawon wannan lokacin bai ci abinci ba, a haka kawai yake"
Cikin tashin hankali ya ce "Yayi ciwo daban-daban, amma ban ga ya yi irin wannan ba, ina kyautata zaton mutum É—aya ne ya san matsalolinsa ciki da waje, ya san bakin zaren wannan ciwon nasa"
"Wane ne? Mahmoudu ba ma son asirinmu ya tonu fa"
"Da asirinmu zai tonu da tuni ta tona, sai dai a zo da Mahaifiyar Muhsin"
AREWABOOKS
Cikin rashin fahimta Sultan ya ce "Ban gane me ka ke nufi ba?"
Cikin girmamawa ya ce "Matarsa da ya zauna da ita a Nigeria, saboda ni kaina na fuskanci wasu abubuwa masu ban mamaki a tsakanin su, bayan sun yi aure." Ya yi maganar yana kallon inda Imam Hammad yake ta mimmiƙewa yana kakari, kamar ana yanka rago.
Cikin damuwa ya ce "Yanzu tun wancan lokacin a haka yake?" Sultan ya jinjina masa kai ya ce "Ko ruwa bai sake sha ba, hankalina a tashe yake. Ga Tafawa ya sako ni gaba a kan Imam Hammad sosai da sosai; Yanzu dai mu je ka yi mini bayani gwari-gwari na fahimta"
Bayan sun fito, suka zauna tare da Mahmoudu.
Mahmoudu ya numfasa ya ce "Idan ban manta ba, bayan mun dawo daga bikin buÉ—e gidan cin abincin Imam na MaraÉ—i, mun dawo ka sanar masa da batun tafiya Damagaran ya wakilceka a taron sarakuna da za a yi a Zinder. Ba zan manta ba an kai ruwa rana sosai a kan tafiyar.
A tsukin lokacin ya kan gaya mini cewa, shi gaba ɗaya ji yake yi baya ƙaunar zaman ƙasar nan, yana jin kamar a cikin wani bala'i da masifa yake. Da fari na zata da wasa yake yi, amma sai na fuskanci da gaske yake a lokacin. Na ce masa mu sanar maka ko ɗaga tafiyar za a yi, amma ya ce mini a'a kar na gaya wa kowa, baya son ya ɗaga wa kowa hankali.
Tare muke kwana da shi a cikin gidan nan, muna shirin tafiya , kawai ya ce mini na same shi a É—aya gidan nasa na kusa da gidan tarihi da yamma, mu yi tafiyar. Na ce masa mu tafi tare amma ya ce mini a'a.