Sashe 78
Buzu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Katafaren Hotel ne, suka sauka a ciki, gaba É—aya Nana jin ta take yi, kamar ba ita ba, kamar mafarki take yi.
Ya yi order Abinci, aka kawo mata, ta yi wanka tayi salla.
Abinci kawai ya iya bari ta ci, ba tare da bata damar hutawa ba, ya ce sai ta biya shi kwanakin da ta yi a Nigeria ba ta nan.
Nana dai da ya ishe ta, kawai ta hau kuka, ya lumshe idanu yana ƙare mata kallo.
Ya yi murmushi ya ce "Ke yanzu dan Allah ba ki ji kunya ba abin da ki ke yi mini?"
"Kai dai za ka ji kunya, haba daga zuwana?" Ta yi maganar tana hawaye.
Ya tashi zaune yana leƙa fuskarta, fafur taƙi kallonsa, ƙoƙarin kare fuskarta take yi, amma yaƙi bata damar hakan. Ya ce "Ni fa zuwan nan namu da biyu, honeymoon muka zo"
"Wane honeymoon, wanda ka yi a Agadez bai ishe ka ba, sai ka dame ni, daga zuwana ni dama ban zo ba"
Hammad ya ce "Gaskiya na Agadez bai ishe ni ba, na fuskanci ƙanin Yarima da rigima ya zo, lokacin Yarima ai ni ake lallaɓawa ina jan aji. Idan kuma ba haka ba, mutum ya musa na tuno wa mutum abin da ya aikata" Murguɗa masa baki ta yi, tana goge hawayen fuskarta. Shi kuwa ya saka ta a gaba, ya din ga yi mata dariya.
Sai da suka shafe kwana uku, da zuwa, har sai da Nana ta manta da abin da ya kawo su, sai dai ta ci abinci Hammad ya yi rigimarsa.
Kwana na huÉ—u suka bar garin da suka sauka, suka tafi garin da malamin yake. Kafin su bar garin, sai da ya zagaya da ita ta ga gari sosai da sosai.
A can garin ma da suka je, a Hotel suka sauka, sai dai a wannan karon ta tarar da Sultan da Matawalle su ma duk su na Hotel É—in kowanne É—akinsa daban amma.
Sultan kamar ya ga 'yar cikinsa, ya din ga tambayarta ya ta baro 'yan uwanta da iyayenta.
Washegari da safe suka hau mota, suka tafi gidan mutumin.
Balarabe ne, sai dai yana jin turanci, tun da suka je gaban Nana ya tsananta faÉ—uwa.
Ya yi musu kyakykyawar tarba, sai dai Nana ko buÉ—e bakinta ta kasa yi, balle ta gaishe shi.
Ya kalli Nana cikin harshen turanci, ya ce "Sannu da zuwa"
Ta sunkuyar da kai ta yi shiru, ta ɓangaren Hammad ma, jikinsa sai tsuma yake yi.
Da larabci suka din ga tattaunawa, Sultan da mutumin, tana iya fahimtar abin da suke faÉ—a amma ba duka ba.
Ya miƙe tsaye ya kalli Hammad, ya ce ya biyo shi, da shi da Sultan.
Nana ta koma gefe ta rakuɓe, ta din ga tunane-tunanen da ita kanta ba ta san daga ina take yin su ba.
Gaba É—aya ba ta cikin nustuwarta, ba ta kuma iya tantance abin da take ji. Wani irin sanyi ya din ga ratsa ta, sannu a hankali ta din ga jin wani irin ihu mara daÉ—in ji.
Ta saka hannu biyu ta toshe kunnuwanta, ta din ga jin tamkar ana ɓarar da kaya, ko ana kokowa da wani irin abu mai nauyi.
Har azahar ta yi, Nana ba ta ga fitowar Hammad ba. Aka bata ruwa ta yi alwala ta yi salla, aka kawo mata abinci, amma ta kasa ci, hankalinta a tashe ba ta ga Hammad ba, ga kuma yanayin da take ji a jikinta mara daÉ—i.
Sai wajen la'asar, sannan aka fito da Hammad, Sultan ya riƙo shi idanunsa a lumshe.
Hankalin Nana ya tashi, ta miƙe tsaye tana faɗin "Lafiya meya same shi?"
Sultan ya ce "Babu abin da ya faru, ki kwantar da hankalinki zai wartsake in sha Allah"
Dattijon nan shi ne mai maganin, ya fito ya jagorance su har wani É—aki.
A ciki aka kwantar da Hammad, sai ajiyar zuciya yake yi, jikinsa yayi jawur hatta gashin kansa a hargiste, rawaninsa ma da babbar rigarsa a hannu Matawalle ya fito da ita. Ta din ga mamakin, yaya aka yi haka? Me aka yi masa ya fita daga hayyacinsa haka. Sai warin wasu mayuka yake yi, da ta gaza gane kowane iri ne.
Su Sultan suka fita yin salla, Nana ta ƙarasa kusa da Hammad, ta taɓa shi, ta shafa gashin kansa ta ce "Sayyid, Sayyid ka na ji na kuwa?"
"Mmm" ya amsa da kyar.
"Mene ne, me ya yi maka?"
Ya girgiza kai ba tare da ya buÉ—e idanunsa ba.
Da su Sultan suka dawo, suka tarar da ita hankali a tashe.
Matawalle ya ce "Ki kwantar da hankalinki, zai wartsake a hankali in sha Allah. Ya ce sai dai mu kwana a nan, mu ga yanayin jikin nasa tukuna, sannan kema ya duba ki"
Kasancewar mutumin babban malamin ruƙiyya ne, da magungunan musulunci yana da gurin saukar baƙi, saboda yadda ake zuwa daga garuruwa gurinsa.
Sannu a hankali Hammad ya dawo hayyacinsa, har ya yi salla ya ci abinci, amma kana kallonsa zaka gane ba ya jin daÉ—i. Nana dai ba ta iya tambayarsa komai ba.
Sultan ya tambaye ta, za ta iya kwana da shi, ko a bata wani É—akin, ta ce zata iya zama tare da shi.
Ba da wani shiri suka taho ba, kasancewar ba su san za su kwana a gidan ba. Gidan Sarkin baka ne ya faÉ—o mata, da irin gane-ganen da ta yi a gidan.
Ta nemi guri ta kwanta a kusa da Hammad, ta ji ya matso da ita jikinsa, ya ƙanƙame ta.
Kamar wadda ta farka daga bacci, haka ta ganta a Libraryn Ƙaisar.
Sai dai gurin ya ɗan yi duhu, sheshsheƙa ta din ga jiyowa daga wani guri, ta tafi a hankali tana sanɗa. Tana buɗe ƙofar da take jiyo sautin ta ga wani irin ƙaton guri, Ƙaisar na durƙushe a kan gwiwoyinsa, ya saka wani abu dogo da ba ta san ko menene ba a gabansa, yana wani irin kuka. Da sauri ta ƙarasa gabansa, ta gefen mayafin take hango wani abu baƙi ƙirin kamar an ƙona itace.
Sandar Giyaz ta gani kwance a gefen abin da yake gaban Ƙaisar ɗin, a razane Nana ta ce "Giyaz ne ya mutu?"
Kawai Ƙaisar ya sake fashewa da kuka, yana yaye mayafin da ya rufe Giyaz. Ya yi wani irin baƙi kamar dutse yayi gobara. Ga wani irin tsawo mara misali da yayi, sai gemunsa da ya ƙara wani irin tsawo. Nana ta ja da baya a razane. Ƙaisar ya kifa a kansa yana wani irin kuka.
Ji ta yi an girgiza ta, ta buɗe idonta, ta ga Hammad ya tsare ta da ido ya ce "Lafiya kuwa? Meyafaru?" Kasa magana ta yi, sai ajiyar zuciya da take yi kamar za ta shiɗe. Duk da jikinsa babu ƙwari haka ya din ga rarrashinta, yana tambayarta mene ne, amma taƙi magana. Da kyar ta tashi ta yi sallar asuba. Aka kawo musu abin karyawa, amma ta ƙi ko kallon abincin. Da ta tuno yadda Ƙaisar ya rungume Giyaz yana kuka, sai ta hawaye yana zubo mata.
Hammad ya fita daga ɗakin, bayan mintuna kaɗan, ya dawo ya ce ta taso. Jikinta gaba ɗaya babu ƙwari, ta tashi ta bi bayansa.
Ko su Sultan kasa gaisar da su ta yi, tana ganin Hammad ya nufi hanyar da aka bi da shi jiya, ta ja ta tsaya.
Ya ce "Meya faru ne? Mu ƙarasa mana" Ta girgiza kai ta ce "Kai dai ka je, ni ba zani ba"
"Saboda me?" Ta yi shiru ba ta ce komai ba.
"Ma viee, ki yi haƙuri babu abin da zai faru in sha Allah, magani za a yi mana mu rabu da wannan larurar, mu samu kwanciyar hankali mu zauna lafiya mu rayu kamar sauran mutane"
Ta ce "Ni ba na so" Ta yi maganar tana kuka.
Sultan ya ƙaraso ya ce "Meyafaru ne?"
"Ni ba zan je ba, a ƙyale ni ba na so"
Da gaske Nana ta kafe, ta ce ba za ta shiga ba, Matawalle ya shiga ya yi wa mutumin magana. Mutumin na fitowa ta juya zata arta da gudu. Hammad ya riƙo ta, ya ce "Amsy me yake damunki ne?"
"Wallahi ba za a kashe Ƙaisar kamar yadda aka kashe Giyaz ba. Wallahi ba zan je ba. Da ya kashe shi gara ni ya kashe ni"
"Asma'u, kin zaɓi aljani a kaina da rayuwar aurenmu kenan? Ki nutsu mana"
Hammad ya yi mata magana cikin tsawa.
Tana kuka ta ce "Wallahi ba zan tsaya ba, shi ma mai rai ne, kuma yana son rayuwarsa, ba zan tsaya a kashe ƙaisar ina gani ba"
Mutumin ya tambayi Hammad, me take faÉ—a ne.
Hammad ya yi masa bayani, cikin harshen turanci, yake gaya wa Nana, ba shi ya kashe Giyaz ba, taurin kai Giyaz yayi shi ya kashe kansa da kansa, amma ba shi ya kashe shi ba"
"Ni dai ku ƙyale ni, zamu rabu a hankali, idan na bari aka kashe shi a dalilina ban yi masa adalci ba, ko ya cutar da ni ta wani bangaren bai cutar da ni ba. Ni dai kar a kashe shi dan Allah."
Sultan ya sassauta murya ya ce "Kina ji, ba kashe shi za a yi ba, za yi miki tsakani da shi ne ya rabu da ke, amma ba kashe shi za a yi ba. Wancan ɗin ma ba shi ya kashe shi ba, shi ne ya kashe kansa dan kawai an nemi ya musulunta ko a ƙona shi"
Nana ta girgiza kai ta ce "Ƙaisar kuka yake yi, an kashe babansa, ni ku bari zan yi magana da shi, yana cikin jimami dan Allah kar ku kashe shi" Ta ƙarasa maganar har da haɗa hannayenta biyu alamar magiya.
Hammad ya rungume ta, ganin yadda take neman ta fita daga hayyacinta, ga shi yana kyautata zaton tana É—auke da juna biyu.
Nana tana da matuƙar raunin zuciya, da tausayi banda haka ya za a yi abin da ya wahalar da ita, ta din ga wannan kukan ta ce ba za a raba ta da shi ba.
104
Ya yi order Abinci, aka kawo mata, ta yi wanka tayi salla.
Abinci kawai ya iya bari ta ci, ba tare da bata damar hutawa ba, ya ce sai ta biya shi kwanakin da ta yi a Nigeria ba ta nan.
Nana dai da ya ishe ta, kawai ta hau kuka, ya lumshe idanu yana ƙare mata kallo.
Ya yi murmushi ya ce "Ke yanzu dan Allah ba ki ji kunya ba abin da ki ke yi mini?"
"Kai dai za ka ji kunya, haba daga zuwana?" Ta yi maganar tana hawaye.
Ya tashi zaune yana leƙa fuskarta, fafur taƙi kallonsa, ƙoƙarin kare fuskarta take yi, amma yaƙi bata damar hakan. Ya ce "Ni fa zuwan nan namu da biyu, honeymoon muka zo"
"Wane honeymoon, wanda ka yi a Agadez bai ishe ka ba, sai ka dame ni, daga zuwana ni dama ban zo ba"
Hammad ya ce "Gaskiya na Agadez bai ishe ni ba, na fuskanci ƙanin Yarima da rigima ya zo, lokacin Yarima ai ni ake lallaɓawa ina jan aji. Idan kuma ba haka ba, mutum ya musa na tuno wa mutum abin da ya aikata" Murguɗa masa baki ta yi, tana goge hawayen fuskarta. Shi kuwa ya saka ta a gaba, ya din ga yi mata dariya.
Sai da suka shafe kwana uku, da zuwa, har sai da Nana ta manta da abin da ya kawo su, sai dai ta ci abinci Hammad ya yi rigimarsa.
Kwana na huÉ—u suka bar garin da suka sauka, suka tafi garin da malamin yake. Kafin su bar garin, sai da ya zagaya da ita ta ga gari sosai da sosai.
A can garin ma da suka je, a Hotel suka sauka, sai dai a wannan karon ta tarar da Sultan da Matawalle su ma duk su na Hotel É—in kowanne É—akinsa daban amma.
Sultan kamar ya ga 'yar cikinsa, ya din ga tambayarta ya ta baro 'yan uwanta da iyayenta.
Washegari da safe suka hau mota, suka tafi gidan mutumin.
Balarabe ne, sai dai yana jin turanci, tun da suka je gaban Nana ya tsananta faÉ—uwa.
Ya yi musu kyakykyawar tarba, sai dai Nana ko buÉ—e bakinta ta kasa yi, balle ta gaishe shi.
Ya kalli Nana cikin harshen turanci, ya ce "Sannu da zuwa"
Ta sunkuyar da kai ta yi shiru, ta ɓangaren Hammad ma, jikinsa sai tsuma yake yi.
Da larabci suka din ga tattaunawa, Sultan da mutumin, tana iya fahimtar abin da suke faÉ—a amma ba duka ba.
Ya miƙe tsaye ya kalli Hammad, ya ce ya biyo shi, da shi da Sultan.
Nana ta koma gefe ta rakuɓe, ta din ga tunane-tunanen da ita kanta ba ta san daga ina take yin su ba.
Gaba É—aya ba ta cikin nustuwarta, ba ta kuma iya tantance abin da take ji. Wani irin sanyi ya din ga ratsa ta, sannu a hankali ta din ga jin wani irin ihu mara daÉ—in ji.
Ta saka hannu biyu ta toshe kunnuwanta, ta din ga jin tamkar ana ɓarar da kaya, ko ana kokowa da wani irin abu mai nauyi.
Har azahar ta yi, Nana ba ta ga fitowar Hammad ba. Aka bata ruwa ta yi alwala ta yi salla, aka kawo mata abinci, amma ta kasa ci, hankalinta a tashe ba ta ga Hammad ba, ga kuma yanayin da take ji a jikinta mara daÉ—i.
Sai wajen la'asar, sannan aka fito da Hammad, Sultan ya riƙo shi idanunsa a lumshe.
Hankalin Nana ya tashi, ta miƙe tsaye tana faɗin "Lafiya meya same shi?"
Sultan ya ce "Babu abin da ya faru, ki kwantar da hankalinki zai wartsake in sha Allah"
Dattijon nan shi ne mai maganin, ya fito ya jagorance su har wani É—aki.
A ciki aka kwantar da Hammad, sai ajiyar zuciya yake yi, jikinsa yayi jawur hatta gashin kansa a hargiste, rawaninsa ma da babbar rigarsa a hannu Matawalle ya fito da ita. Ta din ga mamakin, yaya aka yi haka? Me aka yi masa ya fita daga hayyacinsa haka. Sai warin wasu mayuka yake yi, da ta gaza gane kowane iri ne.
Su Sultan suka fita yin salla, Nana ta ƙarasa kusa da Hammad, ta taɓa shi, ta shafa gashin kansa ta ce "Sayyid, Sayyid ka na ji na kuwa?"
"Mmm" ya amsa da kyar.
"Mene ne, me ya yi maka?"
Ya girgiza kai ba tare da ya buÉ—e idanunsa ba.
Da su Sultan suka dawo, suka tarar da ita hankali a tashe.
Matawalle ya ce "Ki kwantar da hankalinki, zai wartsake a hankali in sha Allah. Ya ce sai dai mu kwana a nan, mu ga yanayin jikin nasa tukuna, sannan kema ya duba ki"
Kasancewar mutumin babban malamin ruƙiyya ne, da magungunan musulunci yana da gurin saukar baƙi, saboda yadda ake zuwa daga garuruwa gurinsa.
Sannu a hankali Hammad ya dawo hayyacinsa, har ya yi salla ya ci abinci, amma kana kallonsa zaka gane ba ya jin daÉ—i. Nana dai ba ta iya tambayarsa komai ba.
Sultan ya tambaye ta, za ta iya kwana da shi, ko a bata wani É—akin, ta ce zata iya zama tare da shi.
Ba da wani shiri suka taho ba, kasancewar ba su san za su kwana a gidan ba. Gidan Sarkin baka ne ya faÉ—o mata, da irin gane-ganen da ta yi a gidan.
Ta nemi guri ta kwanta a kusa da Hammad, ta ji ya matso da ita jikinsa, ya ƙanƙame ta.
Kamar wadda ta farka daga bacci, haka ta ganta a Libraryn Ƙaisar.
Sai dai gurin ya ɗan yi duhu, sheshsheƙa ta din ga jiyowa daga wani guri, ta tafi a hankali tana sanɗa. Tana buɗe ƙofar da take jiyo sautin ta ga wani irin ƙaton guri, Ƙaisar na durƙushe a kan gwiwoyinsa, ya saka wani abu dogo da ba ta san ko menene ba a gabansa, yana wani irin kuka. Da sauri ta ƙarasa gabansa, ta gefen mayafin take hango wani abu baƙi ƙirin kamar an ƙona itace.
Sandar Giyaz ta gani kwance a gefen abin da yake gaban Ƙaisar ɗin, a razane Nana ta ce "Giyaz ne ya mutu?"
Kawai Ƙaisar ya sake fashewa da kuka, yana yaye mayafin da ya rufe Giyaz. Ya yi wani irin baƙi kamar dutse yayi gobara. Ga wani irin tsawo mara misali da yayi, sai gemunsa da ya ƙara wani irin tsawo. Nana ta ja da baya a razane. Ƙaisar ya kifa a kansa yana wani irin kuka.
Ji ta yi an girgiza ta, ta buɗe idonta, ta ga Hammad ya tsare ta da ido ya ce "Lafiya kuwa? Meyafaru?" Kasa magana ta yi, sai ajiyar zuciya da take yi kamar za ta shiɗe. Duk da jikinsa babu ƙwari haka ya din ga rarrashinta, yana tambayarta mene ne, amma taƙi magana. Da kyar ta tashi ta yi sallar asuba. Aka kawo musu abin karyawa, amma ta ƙi ko kallon abincin. Da ta tuno yadda Ƙaisar ya rungume Giyaz yana kuka, sai ta hawaye yana zubo mata.
Hammad ya fita daga ɗakin, bayan mintuna kaɗan, ya dawo ya ce ta taso. Jikinta gaba ɗaya babu ƙwari, ta tashi ta bi bayansa.
Ko su Sultan kasa gaisar da su ta yi, tana ganin Hammad ya nufi hanyar da aka bi da shi jiya, ta ja ta tsaya.
Ya ce "Meya faru ne? Mu ƙarasa mana" Ta girgiza kai ta ce "Kai dai ka je, ni ba zani ba"
"Saboda me?" Ta yi shiru ba ta ce komai ba.
"Ma viee, ki yi haƙuri babu abin da zai faru in sha Allah, magani za a yi mana mu rabu da wannan larurar, mu samu kwanciyar hankali mu zauna lafiya mu rayu kamar sauran mutane"
Ta ce "Ni ba na so" Ta yi maganar tana kuka.
Sultan ya ƙaraso ya ce "Meyafaru ne?"
"Ni ba zan je ba, a ƙyale ni ba na so"
Da gaske Nana ta kafe, ta ce ba za ta shiga ba, Matawalle ya shiga ya yi wa mutumin magana. Mutumin na fitowa ta juya zata arta da gudu. Hammad ya riƙo ta, ya ce "Amsy me yake damunki ne?"
"Wallahi ba za a kashe Ƙaisar kamar yadda aka kashe Giyaz ba. Wallahi ba zan je ba. Da ya kashe shi gara ni ya kashe ni"
"Asma'u, kin zaɓi aljani a kaina da rayuwar aurenmu kenan? Ki nutsu mana"
Hammad ya yi mata magana cikin tsawa.
Tana kuka ta ce "Wallahi ba zan tsaya ba, shi ma mai rai ne, kuma yana son rayuwarsa, ba zan tsaya a kashe ƙaisar ina gani ba"
Mutumin ya tambayi Hammad, me take faÉ—a ne.
Hammad ya yi masa bayani, cikin harshen turanci, yake gaya wa Nana, ba shi ya kashe Giyaz ba, taurin kai Giyaz yayi shi ya kashe kansa da kansa, amma ba shi ya kashe shi ba"
"Ni dai ku ƙyale ni, zamu rabu a hankali, idan na bari aka kashe shi a dalilina ban yi masa adalci ba, ko ya cutar da ni ta wani bangaren bai cutar da ni ba. Ni dai kar a kashe shi dan Allah."
Sultan ya sassauta murya ya ce "Kina ji, ba kashe shi za a yi ba, za yi miki tsakani da shi ne ya rabu da ke, amma ba kashe shi za a yi ba. Wancan ɗin ma ba shi ya kashe shi ba, shi ne ya kashe kansa dan kawai an nemi ya musulunta ko a ƙona shi"
Nana ta girgiza kai ta ce "Ƙaisar kuka yake yi, an kashe babansa, ni ku bari zan yi magana da shi, yana cikin jimami dan Allah kar ku kashe shi" Ta ƙarasa maganar har da haɗa hannayenta biyu alamar magiya.
Hammad ya rungume ta, ganin yadda take neman ta fita daga hayyacinta, ga shi yana kyautata zaton tana É—auke da juna biyu.
Nana tana da matuƙar raunin zuciya, da tausayi banda haka ya za a yi abin da ya wahalar da ita, ta din ga wannan kukan ta ce ba za a raba ta da shi ba.
104