Sashe 5
Buzu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya girgiza kai ya ce "Asal ba ta haihu ba, ɗa na kuma ba shi da alaƙa da kowace mace a Agadez a ma Nijar gaba ɗaya"
Sultan da ya fara harzuƙa ya ce "Kai ba na son shashanci fa, zan ci maka mutunci yanzun nan, wane irin shirme ne haka? Ko sai ka gazgata maganar Tafawa cewa baka da hankali"
Cikin girmamawa ya ce "Tuba nake ranka ya daÉ—e, amma idan an bani dama zan yi bayanin komai".
Abduou matawalle ya ce "Mu na sauraren ka".
Ya ciro wayarsa a aljihunsa, ya daddana.
"Ga Balaraba can tana jiran ki, ana neman ki a gidan Sultan" Nana ta ajiye tukunyar da take wankewa, ta kalli Asal ta ce ana nema na kuma a gidan Sultan? Laifi na yi?"
"Idan kin je kya ji. Nima ban san me ki ka yi ba, Imam ne ya ce a kai ki"
Gaba É—aya sai jikin Nana ya yi sanyi, ta kammala abin da take yi a gurguje, ta shirya ta bi Balaraba.
Su na tafe ta ce "Mama Balaraba, ko kin san abin da na yi ake nema na?"
"A'a nifa Gimbiya ce kawai ta ce na raka ki? Amma idan kin san babu abin da ki ka yi, bai kamata ki ɗaga hankalinki ba, wataƙila Imam Hammad ne kawai yake neman ki"
Cikin sanyin jiki Nana ta ce "Kuma a gidan Sultan?"
"Eh wataƙila alkhairi ne, ko kuma girkin za ki yi" Duk da wannan kalaman na ƙwarin gwiwa, da Balaraba ta faɗa wa Nana, ita dai Nana ta ji ba ta gamsu da kiran ba.
Tun daga nesa aka dakatar da Balaraba, aka turo wani ya shiga da Nana.
Nana ta yi turus, bayan ganin manyan mutane har da Sultan a wajen, gabanta ya yi wata mummunar faɗuwa, suka yi mata wani irin kwarjini ta ja ta tsaya a bakin ƙofar tana rarraba idanu.
Su ma duk suka zura mata idanu, su na mamakin ita wannan da aka kirawo, me ya kawo ta nan.
"Ƙaraso mana" Sayyid ya yi maganar yana kallonta. Sai ta diririce ta kasa gaba ta kasa baya.
Da kansa ya fara takawa, yana tunkarar inda take, yana zuwa ya kamo hannunta, yana tafe tana bin sa a baya har zuwa tsakiyar gurin. Bai saki hannunta ba ya kalli idanunta ya ce "Ma Vie"
Gabanta ne ya yi wata irin mummunar faÉ—uwa, tsigar jikinta ta tashi, numfashinta ya fara fita sama-sama, jin abin da ya fito daga bakinsa tamkar almara.
"Ki shaida musu ni ba juya ba ne, ina da yaro"
Ƙoƙarin ja da baya ta fara yi, tare da son fizge hannunta tana girgiza masa kai.
Sardauna ya ce "Imam, wace ce wannan ɗin? Me ka ke ƙoƙarin yi ne haka?"
"Matata ce, ita ta haifa mini yaro" Ya ba shi amsar yana kallon Nana da idonta ya yi ja, ya cika da hawaye.
Cikin rashin fahimta Matawalle ya ce "Ta yaya, wace ce wannan É—in daga ina take?"
Hammad ya yi shiru bai ce komai ba, shi kuwa Sultan tuni ya karaya, bayan ganin asirin Hammad ya tonu na taɓin hankali sa saboda soki burutsun da yake yi.
Sardauna ya ce "Wai Imam kan ka É—aya kuwa? Ita wannan É—in daga ina ka samo ta, ta ina ta zama matarka?"
Matawalle ya dubi Nana ya ce "Ke Baiwar Allah, daga ina? Kuma mene ne alaƙarki da shi?"
Cikin ruɗewa da hawaye Nana ta ce "Ni babu wata alaƙa tsakanina da shi, aiki kawai Gimbiya Asal ta ɗaukko ni na yi mata, ni ban san shi ba"
Hammad ya girgiza kai ya ce "A'a Husnah, kar ki ji tsoro, ina tare da ke. Kar ki yi mini haka dan Allah"
"Dan Allah ka yi haƙuri ni ban san ka ba" Ta yi maganar kuka mai ƙarfi na ƙwace mata.
"Cika ta tafi" Sardauna ya yi maganar cikin bayar da umarni. A hankali ya saki hannunta, ta juya da sauri ta fice.
"Hammad, anya maganar Tafawa babu ƙamshin gaskiya a cikin ta, na ga baƙa ce kamar ma ba 'yar ƙasar nan ba ce? Meye haɗin ka da ita?"
Ya yi shiru ya sunkuyar da kai ya ƙi magana.
Sultan ya yi gyaran murya ya ce "Ina ga a bari zan yi magana da shi"
Nana kuwa tun da ta fita take kuka, tana zuwa babu kowa a falon, ta wuce ɗakinta ta tattare kayanta cif ta yi waje. Sauri take zumbuɗawa tamkar za ta tashi sama, tana tafe tana fatan Allah ya bata nasarar ficewa daga gidan, ba tare da dakarun Asal sun ganta ba su hana ta fita, kamar yadda suka taɓa yi mata aka hana ta fita daga gidan.
Sai dai ba ƙaramar tafiya ba ce ba, daga sashen da gidan Imam Hammad yake a cikin gidan zuwa shi kansa gidan.
Ta sha doguwar tafiya kafin fita babban gate.
Masu gadin ƙofar suka ƙare mata kallo ɗayan ya ce "Maraɗi za ki tafi ko? Ga mota can Imam ya ce a kai ki"
Ta girgiza cikin mamaki ta ce "Ba zan hau ba, ni ba can zan je ba"
"Idan ba za ki hau ba, ga wannan ya ce a baki" Aka miƙa mata envelope. Ba ta duba meye a ciki ba, ta karɓa suka buɗe mata ƙofa ta fice. Tana tafe tana waiwaye tana fatan kar a biyo ta a mayar da ita gidan nan.
Ta ƙudurce a ranta, tana zuwa gidan Nene za ta ɗauke Muhsin ta yi Nigeria.
Sai dai tana tafe tana kuka zuciyarta cike da takaici, yanzu dama duk tsawon wannan lokacin Sayyid ya gane ta. Amma ya bari take ta wahala saboda shi, ya ci amanarta bai yi mata adalci ba.
Ba ƙaramin gudu motar da ta hau take yi ba, amma gani take kamar ba a sauri.
Ta buÉ—e envelope É—in da aka ba ta kuÉ—i sabbi kar a ciki.
Sai wata takarda. "Dan Allah ki samu nutsuwa, za mu yi magana Asmy, kar ki yanke mini hukunci a yanayin da ki ke" Wani uban tsaki ta ja a fili. Tana furta "Ba ka yi mini adalci ba, ka cutar da ni" Ta yi maganar kaÉ—an-kaÉ—an.
Sun sha tafiya ba kaÉ—an ba a hanya, kafin su isa MaraÉ—i. Daga nan Nana ta nemi abin hawa zuwa garin da suke da Nene. Sai dai tana zuwa ta tarar da gidan a rufe, ga babu waya a hannunta.
Cikin matsananciyar damuwa ta shiga gidan su Ashura.
Ashura na ganinta ta hau tsalle ta rungume ta, Nana ta maze suka gaisa cikin yaƙe.
Suka din ga yi wa Nana maraba da zuwa, mutan gidan su na ta yaba yadda Nanan ta yi haske ta ƙara ƙiba.
Nana da gabanta ke tsananta faÉ—uwa ta ce "Nene fa, ko ta tafi gurin sayar da Abinci?"
"A'a Nene kusan kwana huÉ—u ba ta nan"
Gaban Nana ya faÉ—i, ta ce "Ba ta nan ina ta tafi?"
"Gaskiya ba na tunanin akwai wanda ta yi wa sallama, kawai dai gani muka yi ba ta nan"
"Babar Ashura, dan Allah ku bani aron waya na kira ta" Ta yi maganar cikin tashin hankali, muryarta na rawa.
Aka ba wa Nana waya, ta saka lambar Nene, wayar ta shiga, amma ba ta É—auka ba.
Nana ta kasa zaune ta kasa tsaye, ji take yi tamkar ta kurma ihu, gaba É—aya ta rikice, ta ji numfashinta yana fita sama-sama.
Da kyar ta iya daidaita nutsuwarta ta gabatar da sallolin da suke kanta.
Su ka kawo mata abinci, amma ta ƙi ci, ta yi musu sallama ta ɗauki kayanta ta fice.
Gidan Hajara ta nufa, inda suka kawo ta gidan Nene.
Hajara ta din ga murna ganin Nana, suka rungume juna cikin farin ciki, duk da Nana cikin tashin hankali take.
Hajara ta kawo mata Abinci, ta din ga jan ta da hira.
Nana ta numfasa ta ce "Na je gida gurin Nene, na tarar ba ta nan, ga babu waya a hannuna, ko za ki kira mini ita a wayarki?"
Hajara ta ce "Bari na kira ta"
Sai da aka kira sau biyu, sannan Nene ta É—aga.
Cike da rawar jiki Nana ta ce "Nene"
"Na'am Nana, ki na lafiya?"
Nana ba ta amsa ba ta ce "Nene na zo ba kya nan, na kira wayarki ba kya É—agawa ina ku ka tafi?"
Nene ta numfasa ta ce "Nana ina mai baki haƙuri, baban ɗan ya zo ya karɓi ɗan sa"
Cikin matsanancin tashin hankali Nana ta tashi tsaye ta ce "Nene waye baban É—an? Nene wa ki ka ba wa É—a na? Haka muka yi da ke Nene?"
"Dan Allah Nana ki yi haƙuri, nima fin ƙarfina aka yi, babu yadda na iya, masu garin ne"
"Nene ba ki kyauta mini ba, bamu yi haka da ke ba, dan zatin Allah Nene ki gaya mini inda É—a na yake, dan Allah Nene, ki yi mini rai ki bani É—a na"
Nene ta ce "Nana da zan cutar da ke, da ban zauna da ke tsawon wannan lokacin ba, yadda muka yi a rubuce, haka ya karɓi ɗan sa a rubuce da hukuma, idan na hana su matsala zan shiga"
Cikin rauni da hawaye Nana ta ce "Nene waye ya karɓe shi?"
"Imam Hammad Jalaludeen Agadez "
"Na shiga uku" Nana ta furta cikin matsanancin kuka da tashin hankali.
AREWABOOKS
Cikin tausayawa Hajara ta ce "Dan Allah Nana ki yi haƙuri ki daina kukan nan haka? Kuma wai me yake faruwa ne?"
Nana ba ta saurari Hajara ba, ta ci gaba da kuka, tare da lissafa yadda za ta ninka ta koma Agadez, ta ƙudurce a ranta gara ajalinta ya riske ta, a yi duk wadda za a yi ta karɓi ɗan ta, ko hakan zai yi silar tarwatsewar Agadez gaba ɗaya.', a kan ta tafi ta bar ɗan ta, a wannan gidan.
Bugun ƙofar gidan aka din ga yi da ƙarfi ana sallama.
Hajara ta tashi ta fita, ba a jima ba ta dawo, ta dubi Nana ta ce "Ki na da baƙi a waje"
Nana ta É—ago jajayen idanunta da suka kumbura saboda kuka ta ce "Suwaye?"
"Ki je ki gani, baƙinki ne dai"
Sultan da ya fara harzuƙa ya ce "Kai ba na son shashanci fa, zan ci maka mutunci yanzun nan, wane irin shirme ne haka? Ko sai ka gazgata maganar Tafawa cewa baka da hankali"
Cikin girmamawa ya ce "Tuba nake ranka ya daÉ—e, amma idan an bani dama zan yi bayanin komai".
Abduou matawalle ya ce "Mu na sauraren ka".
Ya ciro wayarsa a aljihunsa, ya daddana.
"Ga Balaraba can tana jiran ki, ana neman ki a gidan Sultan" Nana ta ajiye tukunyar da take wankewa, ta kalli Asal ta ce ana nema na kuma a gidan Sultan? Laifi na yi?"
"Idan kin je kya ji. Nima ban san me ki ka yi ba, Imam ne ya ce a kai ki"
Gaba É—aya sai jikin Nana ya yi sanyi, ta kammala abin da take yi a gurguje, ta shirya ta bi Balaraba.
Su na tafe ta ce "Mama Balaraba, ko kin san abin da na yi ake nema na?"
"A'a nifa Gimbiya ce kawai ta ce na raka ki? Amma idan kin san babu abin da ki ka yi, bai kamata ki ɗaga hankalinki ba, wataƙila Imam Hammad ne kawai yake neman ki"
Cikin sanyin jiki Nana ta ce "Kuma a gidan Sultan?"
"Eh wataƙila alkhairi ne, ko kuma girkin za ki yi" Duk da wannan kalaman na ƙwarin gwiwa, da Balaraba ta faɗa wa Nana, ita dai Nana ta ji ba ta gamsu da kiran ba.
Tun daga nesa aka dakatar da Balaraba, aka turo wani ya shiga da Nana.
Nana ta yi turus, bayan ganin manyan mutane har da Sultan a wajen, gabanta ya yi wata mummunar faɗuwa, suka yi mata wani irin kwarjini ta ja ta tsaya a bakin ƙofar tana rarraba idanu.
Su ma duk suka zura mata idanu, su na mamakin ita wannan da aka kirawo, me ya kawo ta nan.
"Ƙaraso mana" Sayyid ya yi maganar yana kallonta. Sai ta diririce ta kasa gaba ta kasa baya.
Da kansa ya fara takawa, yana tunkarar inda take, yana zuwa ya kamo hannunta, yana tafe tana bin sa a baya har zuwa tsakiyar gurin. Bai saki hannunta ba ya kalli idanunta ya ce "Ma Vie"
Gabanta ne ya yi wata irin mummunar faÉ—uwa, tsigar jikinta ta tashi, numfashinta ya fara fita sama-sama, jin abin da ya fito daga bakinsa tamkar almara.
"Ki shaida musu ni ba juya ba ne, ina da yaro"
Ƙoƙarin ja da baya ta fara yi, tare da son fizge hannunta tana girgiza masa kai.
Sardauna ya ce "Imam, wace ce wannan ɗin? Me ka ke ƙoƙarin yi ne haka?"
"Matata ce, ita ta haifa mini yaro" Ya ba shi amsar yana kallon Nana da idonta ya yi ja, ya cika da hawaye.
Cikin rashin fahimta Matawalle ya ce "Ta yaya, wace ce wannan É—in daga ina take?"
Hammad ya yi shiru bai ce komai ba, shi kuwa Sultan tuni ya karaya, bayan ganin asirin Hammad ya tonu na taɓin hankali sa saboda soki burutsun da yake yi.
Sardauna ya ce "Wai Imam kan ka É—aya kuwa? Ita wannan É—in daga ina ka samo ta, ta ina ta zama matarka?"
Matawalle ya dubi Nana ya ce "Ke Baiwar Allah, daga ina? Kuma mene ne alaƙarki da shi?"
Cikin ruɗewa da hawaye Nana ta ce "Ni babu wata alaƙa tsakanina da shi, aiki kawai Gimbiya Asal ta ɗaukko ni na yi mata, ni ban san shi ba"
Hammad ya girgiza kai ya ce "A'a Husnah, kar ki ji tsoro, ina tare da ke. Kar ki yi mini haka dan Allah"
"Dan Allah ka yi haƙuri ni ban san ka ba" Ta yi maganar kuka mai ƙarfi na ƙwace mata.
"Cika ta tafi" Sardauna ya yi maganar cikin bayar da umarni. A hankali ya saki hannunta, ta juya da sauri ta fice.
"Hammad, anya maganar Tafawa babu ƙamshin gaskiya a cikin ta, na ga baƙa ce kamar ma ba 'yar ƙasar nan ba ce? Meye haɗin ka da ita?"
Ya yi shiru ya sunkuyar da kai ya ƙi magana.
Sultan ya yi gyaran murya ya ce "Ina ga a bari zan yi magana da shi"
Nana kuwa tun da ta fita take kuka, tana zuwa babu kowa a falon, ta wuce ɗakinta ta tattare kayanta cif ta yi waje. Sauri take zumbuɗawa tamkar za ta tashi sama, tana tafe tana fatan Allah ya bata nasarar ficewa daga gidan, ba tare da dakarun Asal sun ganta ba su hana ta fita, kamar yadda suka taɓa yi mata aka hana ta fita daga gidan.
Sai dai ba ƙaramar tafiya ba ce ba, daga sashen da gidan Imam Hammad yake a cikin gidan zuwa shi kansa gidan.
Ta sha doguwar tafiya kafin fita babban gate.
Masu gadin ƙofar suka ƙare mata kallo ɗayan ya ce "Maraɗi za ki tafi ko? Ga mota can Imam ya ce a kai ki"
Ta girgiza cikin mamaki ta ce "Ba zan hau ba, ni ba can zan je ba"
"Idan ba za ki hau ba, ga wannan ya ce a baki" Aka miƙa mata envelope. Ba ta duba meye a ciki ba, ta karɓa suka buɗe mata ƙofa ta fice. Tana tafe tana waiwaye tana fatan kar a biyo ta a mayar da ita gidan nan.
Ta ƙudurce a ranta, tana zuwa gidan Nene za ta ɗauke Muhsin ta yi Nigeria.
Sai dai tana tafe tana kuka zuciyarta cike da takaici, yanzu dama duk tsawon wannan lokacin Sayyid ya gane ta. Amma ya bari take ta wahala saboda shi, ya ci amanarta bai yi mata adalci ba.
Ba ƙaramin gudu motar da ta hau take yi ba, amma gani take kamar ba a sauri.
Ta buÉ—e envelope É—in da aka ba ta kuÉ—i sabbi kar a ciki.
Sai wata takarda. "Dan Allah ki samu nutsuwa, za mu yi magana Asmy, kar ki yanke mini hukunci a yanayin da ki ke" Wani uban tsaki ta ja a fili. Tana furta "Ba ka yi mini adalci ba, ka cutar da ni" Ta yi maganar kaÉ—an-kaÉ—an.
Sun sha tafiya ba kaÉ—an ba a hanya, kafin su isa MaraÉ—i. Daga nan Nana ta nemi abin hawa zuwa garin da suke da Nene. Sai dai tana zuwa ta tarar da gidan a rufe, ga babu waya a hannunta.
Cikin matsananciyar damuwa ta shiga gidan su Ashura.
Ashura na ganinta ta hau tsalle ta rungume ta, Nana ta maze suka gaisa cikin yaƙe.
Suka din ga yi wa Nana maraba da zuwa, mutan gidan su na ta yaba yadda Nanan ta yi haske ta ƙara ƙiba.
Nana da gabanta ke tsananta faÉ—uwa ta ce "Nene fa, ko ta tafi gurin sayar da Abinci?"
"A'a Nene kusan kwana huÉ—u ba ta nan"
Gaban Nana ya faÉ—i, ta ce "Ba ta nan ina ta tafi?"
"Gaskiya ba na tunanin akwai wanda ta yi wa sallama, kawai dai gani muka yi ba ta nan"
"Babar Ashura, dan Allah ku bani aron waya na kira ta" Ta yi maganar cikin tashin hankali, muryarta na rawa.
Aka ba wa Nana waya, ta saka lambar Nene, wayar ta shiga, amma ba ta É—auka ba.
Nana ta kasa zaune ta kasa tsaye, ji take yi tamkar ta kurma ihu, gaba É—aya ta rikice, ta ji numfashinta yana fita sama-sama.
Da kyar ta iya daidaita nutsuwarta ta gabatar da sallolin da suke kanta.
Su ka kawo mata abinci, amma ta ƙi ci, ta yi musu sallama ta ɗauki kayanta ta fice.
Gidan Hajara ta nufa, inda suka kawo ta gidan Nene.
Hajara ta din ga murna ganin Nana, suka rungume juna cikin farin ciki, duk da Nana cikin tashin hankali take.
Hajara ta kawo mata Abinci, ta din ga jan ta da hira.
Nana ta numfasa ta ce "Na je gida gurin Nene, na tarar ba ta nan, ga babu waya a hannuna, ko za ki kira mini ita a wayarki?"
Hajara ta ce "Bari na kira ta"
Sai da aka kira sau biyu, sannan Nene ta É—aga.
Cike da rawar jiki Nana ta ce "Nene"
"Na'am Nana, ki na lafiya?"
Nana ba ta amsa ba ta ce "Nene na zo ba kya nan, na kira wayarki ba kya É—agawa ina ku ka tafi?"
Nene ta numfasa ta ce "Nana ina mai baki haƙuri, baban ɗan ya zo ya karɓi ɗan sa"
Cikin matsanancin tashin hankali Nana ta tashi tsaye ta ce "Nene waye baban É—an? Nene wa ki ka ba wa É—a na? Haka muka yi da ke Nene?"
"Dan Allah Nana ki yi haƙuri, nima fin ƙarfina aka yi, babu yadda na iya, masu garin ne"
"Nene ba ki kyauta mini ba, bamu yi haka da ke ba, dan zatin Allah Nene ki gaya mini inda É—a na yake, dan Allah Nene, ki yi mini rai ki bani É—a na"
Nene ta ce "Nana da zan cutar da ke, da ban zauna da ke tsawon wannan lokacin ba, yadda muka yi a rubuce, haka ya karɓi ɗan sa a rubuce da hukuma, idan na hana su matsala zan shiga"
Cikin rauni da hawaye Nana ta ce "Nene waye ya karɓe shi?"
"Imam Hammad Jalaludeen Agadez "
"Na shiga uku" Nana ta furta cikin matsanancin kuka da tashin hankali.
AREWABOOKS
Cikin tausayawa Hajara ta ce "Dan Allah Nana ki yi haƙuri ki daina kukan nan haka? Kuma wai me yake faruwa ne?"
Nana ba ta saurari Hajara ba, ta ci gaba da kuka, tare da lissafa yadda za ta ninka ta koma Agadez, ta ƙudurce a ranta gara ajalinta ya riske ta, a yi duk wadda za a yi ta karɓi ɗan ta, ko hakan zai yi silar tarwatsewar Agadez gaba ɗaya.', a kan ta tafi ta bar ɗan ta, a wannan gidan.
Bugun ƙofar gidan aka din ga yi da ƙarfi ana sallama.
Hajara ta tashi ta fita, ba a jima ba ta dawo, ta dubi Nana ta ce "Ki na da baƙi a waje"
Nana ta É—ago jajayen idanunta da suka kumbura saboda kuka ta ce "Suwaye?"
"Ki je ki gani, baƙinki ne dai"