Sashe 24
Rabiatul Addawiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bata jimaba ta fito ta tadda khairi zaune bakin bed tana aikin yi mata bincike a cikin phone, ko kulata batayiba ta qarasa gaban mirror tayi 'yan shafeshafenta ta sanya inner wear tare da zira english wear na riga da sket masu santsi ta tako asannu ta haye bed ta ja blanket ta rufa ruf har zuwa face d'inta.
Da hanzari khairi ta janye blanket d'in tayi jifa da shi gefe.
A fusace ta tashi zaune tana doka mata harara tace "wani salon iskanci kenan haka khairi? "Salon iskancin da kika koyamin ne.
Kallonta tayi na daqiqa ta girgiza kai tare da komawa ta kwanta tana mai dafe goshinta da left hand d'in.
"Malama tashi zakiyi ki sanar da ni abinda ke damunki ba wai kiyi ta cin magani ba.
"Wai ina ruwanki da lamari nane da kikabi kika takurawa kanki dole sai kinji matsalata?
"Au haka kikace? Tam yayi kyau haka kuma nagode, tamiqe cikin fushi har ta kama handle zata murd'a Addawiyya tace "am sorry qawata dawo kiji matsalata, ko juyowa batayi ba tayi ficewarta cike da fushi.
tabe bakinta Addawiyya tayi tana mai cewa "jikin ya motsa kkenan? sarakan fushin sun matso kusa, to Allah ya saukeku lafiya.
"Mikike cewa? Dariya ta saka ta amsa "abinda iska yakawo miki, wato labe kika koma ko? "Bansani ba, nidai Abbie yace kizo, dafe qirji tayi idanu waje tace "wayace kice mishi idanuna biyu? "Au qarya kike nufin zanyi mishi ko mi? "Bamsani ba dalla magananyi kawai, ta furta cike da jin haushi.
Dariya khairi tasa mata sosai tace eh, din nadai ji alamaun ilimi kenan. "Uhmm ni kirabi danj tam.
"To momy sai kisami da tashi ko nakoma nasanar dashi kince sai yazo da kamshi don dama ina fita naci karo dashi zaizo kiranki da kanshi shine nace bara na kira mishi ke.
"To kin kyauta ai, sai kibani hanya in wuce, duk kinbi kin isheni da uban surutu kamar parrot.
Gwalo tayi mata takoyo kanta da sauri ta kwasa da gudu tayi downstairs ta rufa mata baya.
**** Hajja bakya ganin in akayi haka ba'a tauye mata hakki taba?
"Aliyu kasani yin haka shine zai baka damar sanin lafiyarka sannan shi aure, haihuwa, mutuwa tare da k'addara duk in lokacinsu yayi bawanda ya isa ya tsaidasu sai ikon Allah.
"Haka ne Hajja, amma dai ina duba alkawarin danayi mata ne nacewa sai ta kammala karatunta har tasoma aiki sannan zamuyi aure.
"Uhmm Ali ka kwantar da hankalinka ka natsu ka ajiye wannan zancen agefe, ka d'auka cewa haka Allah ya tsara baza ta kammala ba zakuyi aure.
Nisawa yayi ya amsa "tam Hajja Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi "Amin Amin Ali gadanga qusar yaqi, murmusawa yayi tare da miqewa yafice.
Cike da jin tausayi Hajja tabi bayamshi da kallo ta d'aga hannunta sama tace "Allah kabawa bayanka Aliyu lafiya alfarmar manzon rahama.
**** Cikin parlon Abbie Addawiyya ce zaune ta lankwashe qafafunta kanta duqe a qasa, ta daiyi zama irin ta ladabi.
Sai da Abbie ya dubi gefensa inda ummie take zaune ya sauke ajiyar zuciya ahankali sannan ya soma da cewa "Alhamdulillahi ala kulli halin, yayi jim zuwa can yace "Rabi'atul Addawiyya, tad'ago kanta da hanzari tayi tana dubanshi, yayimata murmushi ta koma da kanta qasa ta amsa "Na'am Abbie.
"Rabi'a ya kuma kiranta akaro nabiyu,, ina mai baki haquri abisa katse miki cikan burinki da zanyi dafatan zaki gafar ceni?
Muryan na rawa ta amsa "Abbie tsakanin iyaye da abin ikonsu wato 'ya'yansu, babu abinda zasuyi musu indai bai sabawa shari'aba ace zasu tsaya roqonsu gafara, don haka bakayimin komiba kuma baza kataba yimin shi ba sabida nasan kai d'in uba nagari ne mai hangen nesa kafin ya aywatar da komi.
Tana rufe baki suka had'a baki wurin cewa "Allah yayi miki albarka har izuwa qarshen rayuwar.
"Amin ta amsa fuskanta yana mai nunajin dad'in addu'ar.
"Rabi'a bakomi bane illah d'azun na amshi sadakin aurenki da Aliyu wurin su Alh. Muktar sannan har mun tsaida lokacin biki nan da sati biyar masu zuwa, dafatan baza ki bani kunya ba.
Ahankali ta amsa "insha Allahu zaka sameni mai ladabi da biyayya a lamarin zamantakewar aurena.
Sai kuma tamiqe tafuce da gudu don sosai maganar ya jefata cikin jin kunyar su Ummie.
"Auta hoo, jibafa kunya wai taji, ya amsa "hakan shi yanuna tana maraba da lamarin kena, "eh, malam dama ai nace maka bazata qiba sabida tana sonshi sosai, "to Allah ya barsu tare da karesu cikin amincin Allah "Amin.
Koda ta shiga room d'inta khairi da maryam tasamu suna cin food, suna ganinta suka sa shewa ta had'e rai ta zauna suka kuma sakin dariya maryam tace "munji komi abakin Adda Salma ai.
"Adda Salama fa kuka ce? "Eh ita "to yaushe tazo gidan?
"Inanan tun bitarki zuwa school baji mawa, don haka agabana akayi komi Abbie ya kyautarwa Haydar dake.
"Malamandu gyara zancenki akadai neman mishj aurena.
Yeeeee!! Tafad'i da bakinta, su Amaren Ali kenan manya, maryam tace.
Ficewa tayi da gudu tana cewa "magul matan banza kawai sai kuyi da wata ai ba ina ba.
Tana jiyo dariyan dasuke kyalkyalawa tashige kitchen ta fice zuwa garden tasami wuri ta zauna ta kulle eyes d'inta tace "Haydar yana tare da lalura ko ta miye?
Saukam Iska taji agefenta ba tare da ta bud'e idanunta ba tace "sanar dani lamarin uncle.
"Kasheki zanyi yanzu kowa ya huta.
Wata murya mai bantsoro ta amsa mata.
*mrs j moon*
[1/22, 3:47 PM] Mrs J Moon😊: *RABI'ATUL ADDAWIYYA*
NA
SAFIYYA.
*37*
Arazane ta kai dubanta inda sautin voice d'in yafito, wani zabura tayi sakamakon yin arba da wani halitta da tayi shi ba mutum ba bakuma dodo ba, yana d'auke da fuskan mutane kanshi na rago jikinsa na jaki har da bindi dogo qafafunshi na mutace.
Bud'e baki tayi zata kwalla qara raji an hannu ya kulle mata baki tare daijn shigar wani sanyi cikin qirjinta, cikin second tasami kanta cikin jarumta na rashin jin tsoro.
Komawa tayi ta zauna ta had'e fuska cikin kaurin voice kamar banata ba ta dubi halittan tace "to bissmillah, gani kamiqani barzahu, tunda kai ka halicceni.
Wani zaro idanunshi halittan yayi cike da kid'ima sabida yazaci firgicin ganinshi zaisa ta suma yarda zaiji dad'in sheqawa da ita qiyoma.
"Kana batamin lokaci fa, kallonta ya kumayi sosai, atake yagano wani baqon lamari cikin idanunta, yasoma ja baya tana biyoshi bakita na motsi alamar addu'a takeyi.
Ganin burinta ta damqeshi da hannunta yasa yayi girgiza ya zama qaton shaho ya bud'e fuka fukanshi yayi sama.
Abin mamaki sai da tabari ya lula sosai sannan ta bud'e bakinta ta hura iska sama atake shahon ya fad'o tim, ya saki razananniyar qara, yaja baya ya kuma girgiza ya koma kura yayo kanta kamar walqiya ta bace bat zuwa can wani qosasshen zaki ya bayya, yayi kan kurannan suka soma fafatawa wani baqin hayaqi ya rufesu ruf, tsowon lokaci suna abu d'aya zuwa can farin haske ya bayyana.
Habibullah ne zaune bisa chair d'insa mai ruwan gold fuskansa kamar dare don rashin walwala.
Ya dubi kuran da take yashe aqasa bakinta da hancinta sai zuban jini yake, yasa qafa ya shureta tayi wani sama sama sannan ta fad'o tim iska ya tashi ya rufeta, koda ya baje saiga wata mata baqa qirin fuskanta kamar na gorilla, zubewa tayi gaban Habibullah tana yin wani yare kamar na 'yan China.
Wani tsawa ya daka mata ta zabura ta koma wata budurwa mai mugun kyau.
Kallon sosai yayi mata yace "waya aikoki wurin kayana? "Kayimin rai ya kai adalin shugaba.
"Tambayarki nayi, kuma amsa nakeso ba ban haquriba.
"Matar Aliyu ce, wani Aliyun? "Wanda zai auri jaririyanka Addawiyya.
"Uban wa ya d'aura musu aure?
Shiru tayi ya kuma tambayarta saitayi qasa dakanta, taqi cewa komi.
Shiru yayi kamar bazai kuma magana ba zuwa can yace "tashi ki tafi amma inamai gardad'inki kada ki kuma zuwa domin cutar da mai babban suna.
Zubewa tayi gabanshi tana godiya, d'agamata hannu yayi atake ta bace bat.
Kallon wata bishiyar itaciyar tumfafiya yayi saiga Addawiyya ta bayyana sai zare idanu takeyi.
Dariyansa taji agefenta yasa ta juyo ta kama hannunshi bakinta na rawa tace "uncle naga abin tsoro yanzu anan wurin har yana cewa yazo kashe ni ne, don Allah sanar dani mike faruwa.
"Mai babban suna, hakiqa rayuwarki tana gamuwa da ababen ban al'ajabi, don haka nakeso ki dage da yawan ibada da tsayuwar dare tun daga yanzu har izuwa gidan mijinki.
"Tam uncle zan dage dayinsa daga yau in Allah yaso.
"Madallah, yanzu shiga ciki.
"A'a uncle sanar dani labarin wannan halittan dana gani da kuma matsalar Ya Ali danaji d'azun a parlon Abbie kacemin na amince dashi shid'in mai raunine domin lafiya bata isheshi ba.
"Mai babban suna tabbas Aliyu baya da qoshin lafiya sosai, ada bansan miye matsalarba sabida hijabi da abin yake dashi amma bayyanar wannan halitta agareki nagano komi don haka kibar sonjin komiyeshi, ki dai zamo mai yawar addu'a Allah yana tare da mai yawan miqa lamuransa gareshi.
"Idanu ta zuba mishi taqi cewa komi.
Iska ya hura mata, lumshe idanu tayi tare da jan ajiyar zuciya tace "shikenan uncle nabar sake matsa maka akan sai naji ko miye amma don Allah kasanar dani waye wannan halittan?
"Baiwace ta wata basarakiya, anturo tane domin ta cutar dake abisa dalilin banza da wofi na sarauniyar, atunaninta nayi nisa dake sabida taji nace zanyi tafiya to shine ta turo a kasheki sai gashi Allah ya kareki.
"Uncle miye had'inta dani? "Kaddaran maganar aurenki ya had'aku.
"Kamar ya? "Kamar yar yawan bincike baya da kyau sam.
"Uhmm Uncle wallahi ban fahimce kaba.
"Dama bana son ki fahimceni yanzu sai nan gaba.
Zata kuma magana ya rigata "tafi ki shirya tarban zuwan masoyin Haydar.
Yana fad'an haka ya zama haske ya bace.
Barin wurin tayi jikinta duk yayi sanyi.
Adaren ranar Haydar yakawo mata ziyara.
Cikin parlor suka zauna yayin dasu ummie sukabar musu wurin.
Haydar yasha mamaki jin batayi masa qorafin ya daqile mata karatu ba sam, shi kuma baitada zancen ba.
Bai bar gidansuba sai bayan ten na dare.
Daren ranar Addawiyya bata rintsaba sai bayan da ta sallaci subahi.
Anan bisa sallaya ta bingire barci mai dad'i ya kwasheta.
Da hanzari khairi ta janye blanket d'in tayi jifa da shi gefe.
A fusace ta tashi zaune tana doka mata harara tace "wani salon iskanci kenan haka khairi? "Salon iskancin da kika koyamin ne.
Kallonta tayi na daqiqa ta girgiza kai tare da komawa ta kwanta tana mai dafe goshinta da left hand d'in.
"Malama tashi zakiyi ki sanar da ni abinda ke damunki ba wai kiyi ta cin magani ba.
"Wai ina ruwanki da lamari nane da kikabi kika takurawa kanki dole sai kinji matsalata?
"Au haka kikace? Tam yayi kyau haka kuma nagode, tamiqe cikin fushi har ta kama handle zata murd'a Addawiyya tace "am sorry qawata dawo kiji matsalata, ko juyowa batayi ba tayi ficewarta cike da fushi.
tabe bakinta Addawiyya tayi tana mai cewa "jikin ya motsa kkenan? sarakan fushin sun matso kusa, to Allah ya saukeku lafiya.
"Mikike cewa? Dariya ta saka ta amsa "abinda iska yakawo miki, wato labe kika koma ko? "Bansani ba, nidai Abbie yace kizo, dafe qirji tayi idanu waje tace "wayace kice mishi idanuna biyu? "Au qarya kike nufin zanyi mishi ko mi? "Bamsani ba dalla magananyi kawai, ta furta cike da jin haushi.
Dariya khairi tasa mata sosai tace eh, din nadai ji alamaun ilimi kenan. "Uhmm ni kirabi danj tam.
"To momy sai kisami da tashi ko nakoma nasanar dashi kince sai yazo da kamshi don dama ina fita naci karo dashi zaizo kiranki da kanshi shine nace bara na kira mishi ke.
"To kin kyauta ai, sai kibani hanya in wuce, duk kinbi kin isheni da uban surutu kamar parrot.
Gwalo tayi mata takoyo kanta da sauri ta kwasa da gudu tayi downstairs ta rufa mata baya.
**** Hajja bakya ganin in akayi haka ba'a tauye mata hakki taba?
"Aliyu kasani yin haka shine zai baka damar sanin lafiyarka sannan shi aure, haihuwa, mutuwa tare da k'addara duk in lokacinsu yayi bawanda ya isa ya tsaidasu sai ikon Allah.
"Haka ne Hajja, amma dai ina duba alkawarin danayi mata ne nacewa sai ta kammala karatunta har tasoma aiki sannan zamuyi aure.
"Uhmm Ali ka kwantar da hankalinka ka natsu ka ajiye wannan zancen agefe, ka d'auka cewa haka Allah ya tsara baza ta kammala ba zakuyi aure.
Nisawa yayi ya amsa "tam Hajja Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi "Amin Amin Ali gadanga qusar yaqi, murmusawa yayi tare da miqewa yafice.
Cike da jin tausayi Hajja tabi bayamshi da kallo ta d'aga hannunta sama tace "Allah kabawa bayanka Aliyu lafiya alfarmar manzon rahama.
**** Cikin parlon Abbie Addawiyya ce zaune ta lankwashe qafafunta kanta duqe a qasa, ta daiyi zama irin ta ladabi.
Sai da Abbie ya dubi gefensa inda ummie take zaune ya sauke ajiyar zuciya ahankali sannan ya soma da cewa "Alhamdulillahi ala kulli halin, yayi jim zuwa can yace "Rabi'atul Addawiyya, tad'ago kanta da hanzari tayi tana dubanshi, yayimata murmushi ta koma da kanta qasa ta amsa "Na'am Abbie.
"Rabi'a ya kuma kiranta akaro nabiyu,, ina mai baki haquri abisa katse miki cikan burinki da zanyi dafatan zaki gafar ceni?
Muryan na rawa ta amsa "Abbie tsakanin iyaye da abin ikonsu wato 'ya'yansu, babu abinda zasuyi musu indai bai sabawa shari'aba ace zasu tsaya roqonsu gafara, don haka bakayimin komiba kuma baza kataba yimin shi ba sabida nasan kai d'in uba nagari ne mai hangen nesa kafin ya aywatar da komi.
Tana rufe baki suka had'a baki wurin cewa "Allah yayi miki albarka har izuwa qarshen rayuwar.
"Amin ta amsa fuskanta yana mai nunajin dad'in addu'ar.
"Rabi'a bakomi bane illah d'azun na amshi sadakin aurenki da Aliyu wurin su Alh. Muktar sannan har mun tsaida lokacin biki nan da sati biyar masu zuwa, dafatan baza ki bani kunya ba.
Ahankali ta amsa "insha Allahu zaka sameni mai ladabi da biyayya a lamarin zamantakewar aurena.
Sai kuma tamiqe tafuce da gudu don sosai maganar ya jefata cikin jin kunyar su Ummie.
"Auta hoo, jibafa kunya wai taji, ya amsa "hakan shi yanuna tana maraba da lamarin kena, "eh, malam dama ai nace maka bazata qiba sabida tana sonshi sosai, "to Allah ya barsu tare da karesu cikin amincin Allah "Amin.
Koda ta shiga room d'inta khairi da maryam tasamu suna cin food, suna ganinta suka sa shewa ta had'e rai ta zauna suka kuma sakin dariya maryam tace "munji komi abakin Adda Salma ai.
"Adda Salama fa kuka ce? "Eh ita "to yaushe tazo gidan?
"Inanan tun bitarki zuwa school baji mawa, don haka agabana akayi komi Abbie ya kyautarwa Haydar dake.
"Malamandu gyara zancenki akadai neman mishj aurena.
Yeeeee!! Tafad'i da bakinta, su Amaren Ali kenan manya, maryam tace.
Ficewa tayi da gudu tana cewa "magul matan banza kawai sai kuyi da wata ai ba ina ba.
Tana jiyo dariyan dasuke kyalkyalawa tashige kitchen ta fice zuwa garden tasami wuri ta zauna ta kulle eyes d'inta tace "Haydar yana tare da lalura ko ta miye?
Saukam Iska taji agefenta ba tare da ta bud'e idanunta ba tace "sanar dani lamarin uncle.
"Kasheki zanyi yanzu kowa ya huta.
Wata murya mai bantsoro ta amsa mata.
*mrs j moon*
[1/22, 3:47 PM] Mrs J Moon😊: *RABI'ATUL ADDAWIYYA*
NA
SAFIYYA.
*37*
Arazane ta kai dubanta inda sautin voice d'in yafito, wani zabura tayi sakamakon yin arba da wani halitta da tayi shi ba mutum ba bakuma dodo ba, yana d'auke da fuskan mutane kanshi na rago jikinsa na jaki har da bindi dogo qafafunshi na mutace.
Bud'e baki tayi zata kwalla qara raji an hannu ya kulle mata baki tare daijn shigar wani sanyi cikin qirjinta, cikin second tasami kanta cikin jarumta na rashin jin tsoro.
Komawa tayi ta zauna ta had'e fuska cikin kaurin voice kamar banata ba ta dubi halittan tace "to bissmillah, gani kamiqani barzahu, tunda kai ka halicceni.
Wani zaro idanunshi halittan yayi cike da kid'ima sabida yazaci firgicin ganinshi zaisa ta suma yarda zaiji dad'in sheqawa da ita qiyoma.
"Kana batamin lokaci fa, kallonta ya kumayi sosai, atake yagano wani baqon lamari cikin idanunta, yasoma ja baya tana biyoshi bakita na motsi alamar addu'a takeyi.
Ganin burinta ta damqeshi da hannunta yasa yayi girgiza ya zama qaton shaho ya bud'e fuka fukanshi yayi sama.
Abin mamaki sai da tabari ya lula sosai sannan ta bud'e bakinta ta hura iska sama atake shahon ya fad'o tim, ya saki razananniyar qara, yaja baya ya kuma girgiza ya koma kura yayo kanta kamar walqiya ta bace bat zuwa can wani qosasshen zaki ya bayya, yayi kan kurannan suka soma fafatawa wani baqin hayaqi ya rufesu ruf, tsowon lokaci suna abu d'aya zuwa can farin haske ya bayyana.
Habibullah ne zaune bisa chair d'insa mai ruwan gold fuskansa kamar dare don rashin walwala.
Ya dubi kuran da take yashe aqasa bakinta da hancinta sai zuban jini yake, yasa qafa ya shureta tayi wani sama sama sannan ta fad'o tim iska ya tashi ya rufeta, koda ya baje saiga wata mata baqa qirin fuskanta kamar na gorilla, zubewa tayi gaban Habibullah tana yin wani yare kamar na 'yan China.
Wani tsawa ya daka mata ta zabura ta koma wata budurwa mai mugun kyau.
Kallon sosai yayi mata yace "waya aikoki wurin kayana? "Kayimin rai ya kai adalin shugaba.
"Tambayarki nayi, kuma amsa nakeso ba ban haquriba.
"Matar Aliyu ce, wani Aliyun? "Wanda zai auri jaririyanka Addawiyya.
"Uban wa ya d'aura musu aure?
Shiru tayi ya kuma tambayarta saitayi qasa dakanta, taqi cewa komi.
Shiru yayi kamar bazai kuma magana ba zuwa can yace "tashi ki tafi amma inamai gardad'inki kada ki kuma zuwa domin cutar da mai babban suna.
Zubewa tayi gabanshi tana godiya, d'agamata hannu yayi atake ta bace bat.
Kallon wata bishiyar itaciyar tumfafiya yayi saiga Addawiyya ta bayyana sai zare idanu takeyi.
Dariyansa taji agefenta yasa ta juyo ta kama hannunshi bakinta na rawa tace "uncle naga abin tsoro yanzu anan wurin har yana cewa yazo kashe ni ne, don Allah sanar dani mike faruwa.
"Mai babban suna, hakiqa rayuwarki tana gamuwa da ababen ban al'ajabi, don haka nakeso ki dage da yawan ibada da tsayuwar dare tun daga yanzu har izuwa gidan mijinki.
"Tam uncle zan dage dayinsa daga yau in Allah yaso.
"Madallah, yanzu shiga ciki.
"A'a uncle sanar dani labarin wannan halittan dana gani da kuma matsalar Ya Ali danaji d'azun a parlon Abbie kacemin na amince dashi shid'in mai raunine domin lafiya bata isheshi ba.
"Mai babban suna tabbas Aliyu baya da qoshin lafiya sosai, ada bansan miye matsalarba sabida hijabi da abin yake dashi amma bayyanar wannan halitta agareki nagano komi don haka kibar sonjin komiyeshi, ki dai zamo mai yawar addu'a Allah yana tare da mai yawan miqa lamuransa gareshi.
"Idanu ta zuba mishi taqi cewa komi.
Iska ya hura mata, lumshe idanu tayi tare da jan ajiyar zuciya tace "shikenan uncle nabar sake matsa maka akan sai naji ko miye amma don Allah kasanar dani waye wannan halittan?
"Baiwace ta wata basarakiya, anturo tane domin ta cutar dake abisa dalilin banza da wofi na sarauniyar, atunaninta nayi nisa dake sabida taji nace zanyi tafiya to shine ta turo a kasheki sai gashi Allah ya kareki.
"Uncle miye had'inta dani? "Kaddaran maganar aurenki ya had'aku.
"Kamar ya? "Kamar yar yawan bincike baya da kyau sam.
"Uhmm Uncle wallahi ban fahimce kaba.
"Dama bana son ki fahimceni yanzu sai nan gaba.
Zata kuma magana ya rigata "tafi ki shirya tarban zuwan masoyin Haydar.
Yana fad'an haka ya zama haske ya bace.
Barin wurin tayi jikinta duk yayi sanyi.
Adaren ranar Haydar yakawo mata ziyara.
Cikin parlor suka zauna yayin dasu ummie sukabar musu wurin.
Haydar yasha mamaki jin batayi masa qorafin ya daqile mata karatu ba sam, shi kuma baitada zancen ba.
Bai bar gidansuba sai bayan ten na dare.
Daren ranar Addawiyya bata rintsaba sai bayan da ta sallaci subahi.
Anan bisa sallaya ta bingire barci mai dad'i ya kwasheta.