← Book details Rabiatul Addawiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 38

Sashe 21

Rabiatul Addawiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Khairi miyasa kikayi haka? Ba'a fad'a in fad'a da mahaifiyya, girma ake bata koda aya take, inkina son dawo da ita hanya ai asannu zaki bita, ko yanzu kinsan kuwa kina cikin fushin Allah sabida tayi fushi dake, kuma hakan zai iya shafan karatunki burinki na son kiyi saukan alqu'ani zaki iya rasarashi, don haka tashi maza in rakaki ki bata haquri.
"Addawiy baza ta haqura ba, zata dokeni ne.
"Ba hujja bace hakan khairi, tashi maza autan ummi tayi miki jagora, insha Allahu baza tayi miki komi ba.
"To aunty, nagode da kulawarku gareni, Allah yasa da khairan.
"Amin.

Sun cimmata zaune ta tsokala d'ankali gaban goshi, ture kaga tsiya kenan sai huci takeyi ita 1.

"Kuficemin a parlor tun banji muku ciwo ba!! Tace dasu cikin tsawa.

Juyawa khairi tayi a tsorace zata fita Addawiyya ta kamo hannunta tana girgiza mata kai, suka iso gabanta suka russuna "momyn khairi kiyi haquri bazata qaraba kinji?
Kallon banza ta saukewa Addawiyya, zatayi magana ta kafeta da idanu, atake tayi shiru tana jan wa'innahu sulaimanu acikin zuciyarta dan gani tayi idanunta sun koma mata kamar bana muta ne ba, anya 'yannan cikakkiyar mutum ce kuwa?
Tambayar da tayi cikin zuciyarta kenan kuma tagaza lalibo amsarshi.

Murmushi addawiyya ta sakar mata ta tashi ta koma samar kushin ta zauna tana ci gaba da kafeta da idanu.

"Momyna ki yafemin ba burina na bata miki ba, sharrin zuciya ne yasa nayi sa'insa dake amma ina roqon affuwarki don Allah badan halina ba.

Kamo khairin tayi ta rumgume tana shafa bayanta tace "Nayafe miki 'yata amma bisa shara'in zakidawo part d'ina "zan dawo momy "ohk tam komi ya wuce "thank you my momma.

Sai kuma ta zame jikinta ta zauna tare da lankwashe qafafunta ta soma magana "ina son don Allah momy ki cire tsanar da kikayiwa su aunty Hindu aranki domin sud'imuta nen kirkine, kinga wannan tanuna Addawiyya da yatsa tacigaba Allah sanadi ita ce silar komawata mai hankali amai makon mara shi, mai matsuwa amai makon mara tarbiyya, mai ilimi amai makon jahila, mai kwarjini amaimakom mai bakin jini, mai ibada amai makom mai wasa da sallah, nasamu abubuwa da dama atarayyana da dasu na 'yan lokaci qanqani duk kuwa da ada nayi ta zaginta amma dayake Allah yasoni da shiriya sai tayi galaba akaina batare da nasani, don haka ina roqonki da ki daure ki cirekomai aranki muzauna lafiya dasu, kinji ko momyna?

"Uhmm naji, kutashi ina son yin runani akai, sukayi mata godiya suka fice, ta tabe baki tana mai cewa "ba shiri atsakaninmu har abadan abidina, kedai da suka mallake kiyi ta zama dasu amma ni kam ina kan bakana sai naga qarshensu har iyayensu.

*nikam nace uhmm wanda yayi nisa baijin kira sam*

Daf dazasu shiga part d'in Hindu, Addawiyya taji caraf an damqe mata hannu ta juya atsorace tayi arba da Haydar,ta tura baki tare da qoqarin kwace hannunta, yaja ta da qarfi zuwa part d'insu batare da yace da ita kanzil ba.

Khairi tasoma yimusu dariya har suka bacewa ganinta, ta d'aga hannuta sama tace "ya ilahu kasadani da mai sona da qauna mai tsafta kamar yarda ya Haydar yake son Addawiyya.

*mrs j moon*
[1/17, 4:07 PM] Mrs J Moon😊: *RABI'ATUL ADDAWIYYA*

NA
SAFIYYA.

*33*

Sai da ya zaunar da ita abisa cushion sannan ya saki hannu.
Miqewa tayi da sauri zata fita yayi hanzarin shan gabanta ya miqa hannu zai riqota taja baya tana hararan shi "Ya Ali wallahi banson haka.
Shiru yayi mata ya koma ya zauna, batare da ta kalle inda yake bas ta nufi hanyar ficewa.
"Don Allah kada kitafi, magana nakeso muyi dake.
Tsayawa tayi cak, ya tako zuwa wurinta ya dafan kafad'anta tayi saurin zamewa ta had'e rai tace "nace kabar son tabamin jiki, baya da kyau hakan sam a cikin addininmu.

Rungume hannayensa yayi aqirjinshi ya langabar da kai ya motsa labbanshi kad'an yace "Sorry my heart bazan qaraba.

Kallon shi tayi sosai bako qiftawa, ya gyada mata kai murmushi d'auke afuskanshi, itama mirmushin ta saki tana mai kauda fuskanta cike dajin kunyar kallon data yi mishi na ido cikin ido.

"Uhmm my angel zo kizauna in bud'e miki asirin zuciyata yau, maqe kafad'a tayi kanta qasa, "au bakya sonjin sirrin kenan? Ta girgiza kai, "uhmm kinsoma azumin rashin magana ne? "Eh ta amsa, yasa dariya sosai ya saita voice dinsa cikin serious yace "Rabi'a zo nan magana nakeson muyi dake mai mahinmanci.

"To kazo muje garden sai muyi maganar acan.
Kallonta yayi na 'yan daqik'u kamar zai zanyi magana sai kuma yayi shiru tare da miqewa ya doshi qofar fita tabiyo bayarshi.

Zama sukayi samar kujerun roba dasuke cikin wata madai daiciyar rumfa a cikin garden d'in.

"Rabi'atu bakiyar dani bako? Kina tunanin zan iya cutar dake ko? Yace da ita cikin sanyin murya.
Amsawa tayi itama cikin sanyi "A'a ya Haydar banufina kenan ba ina dai qoqarin ganin mun kiyaye haqk'ok'in addininmu ce ta islama, inda ya tabbatar da cewa duk inda mace da namiji suka kebe su biyu musanman baligai to shed'anne na ukunsu, alokacin komi zai iya faruwa atare dasu koda kuwa sud'in kamilallu ne domin sharrin kaidin shed'an la'ananne saninsa sai Allah kad'ai ba mutum ba, don haka naga ya dace muyi taka tsantsan da hakan, amma in hakan baiyima dad'i ba ina neman affuwarka please.

Jan doguwar nufashi yayi yace "lallai ked'in tadabance Addawiyya, duk yarda zakiyi magana sai ilimi ya fita cikinsa, sosai naji dad'in samunki arayuwata, nafahimce ki kuma bakiyin komi ba, Allah yacigana da karemana gabbanmu daga sharrin shed'an da afkawa barna.

"Amin ya rabbi yayana.

Sosai sukasha hiransu ta masoya inda kowa aranar yanunawa d'an uwarshi irin matsanancin son da yake danqare cikin ruhinshi.

Basu sukayi haramar barin wurinba sai daf da magriba.
Ta dubeshi cikin murmushi tace "Ya Aliyu lokaci salla ta gabato, yakamata mutashi hakanan.

"Ya salam!! Beauty namanta banyi sallar la'asar ba gashi har lokacin magrib ta shiga.
"Ya ilahi, affuwan mantawa nayi ban tuna maka ba don ni ina fashin sal....tunawa da tayi dawa take magana yasa tayi saurin rufe fuskanta da tafukan hannayenta ta kwasa da gudu tabi ta qofar kitchen tashige ciki.

Murmushi ya saki mai sauti ya furta "kunyarki tana dad'a jefani cikin sonki tare da begenki ainun, i luv u wit ol my herat.

Sai da yabatar da sallar la'asar sannan ya nufi masallaci don yabi jam'in magrib.

Bashi yabaro masjid ba sai da ya sallaci isha'i kuma yaga batar da shafa'i yabar wuttiri sai yazo kwanciya.

Yana shigowa get ya hango Hameed yaci uban kwalliya zai shiga car d'insa.

Da sauri ya qaraso wurin ya kama kunninsa ya murd'a da qarfi yako saki 'yar qasa don yaji zafi sosai.
"Hameed mi yasa har yanzu hankali ba zo maka ba? "To minayi kuma Abbana. Yace cikin fushi tare da fizge kunninsa yana liliyawa.

"Kafi kowa sanin abinda nake nufi, yanzu ace ga baki ga hanci amma ka kasa zuwa bin jam'in sallah masjid?
" kai bros ya sayyidi, Kadai san sanyi akeyi don haka na had'a arollar sallar magrib da isha'i nakeyi nayisu lokaci d'aya.

"Ya rasulillahi!! Hameed yaushe zaka daina wasa da ibada ne wai? "Uhmm kai ne kake ganin ina wasa da ita amma ni kam nasan inayinta yarda ta dace.

" uhmm ko? To kasani Wannan abin da kakeyi baka da hujjar kare kanka ranar gobe qiyama a gaban Allah don haka ka hanzarta dawowa bisa hanya na kwarai tun kafin lokaci ya qure maka, don mutuwar fuji'a yanzu ake yayin yinta kuma ita alamar tambaya ce gawanda ta riska.
"Allah ya tsaremu da ita dan alfarman Annabi SAW. "To Amin, adai gyara kaji ko? "Tam Allah yabani iko "Amin.

"Uhm yanzu da ka kasa zuwa masjid sallah sabida sanyi to yanzu kuma ina zaka?

Sai da yasaki lafiyayyiar murmushi ya wani kwanbare sannan ya amsa "gidan su heart d'ina, sabida gidansu ba'a wuce 9:30pm ana hira so shine zanje da wuri kafin tym d'in nasan abinda na yaga.

Idanu waje Haydar yace "mi zaka yaga Hameed?
Sirrin tsaki yaja yace "kai dalla malam ba abin ashsha zanyi ba kawai hirace ta ma'abota k'auna zan yarfar mata itama ta yarfomin shine ma'anar yagowar.

"To Allah ya shirya ka, inka isa kace ina gaishe da ita.
"Amin bros, insha Allahu zataji.
Yana tsaye har ya fice, ya juyo jikinsa a sanyaye saka makon tuno mahaifiyarshi da yayi.

Tun suna yara ummansu hajiya Rahmatu take yaqi da Hameed akan sallah har suka soma mallakan hankalinsu tana aikin abu 1, baya son juwa jam'i haka bayayinta cikin lokacinta sai yaga dama, bayan rasuwarta Alh. Muktar ya d'ora akai, kullum sai yazo dakanshi ya tashesu zuwa masallaci sallar subahi amma Hameed baya zuwa sai Abban yayi da gaske, dakyat aka samu yake zuwa batare da qorafin shi barci bai isheshi ba, sanyi yakeji.
Amma sauran sallolin kuwa wannan agida ko office yake yinsu baya yinsu cikin jam'i suma wata rana rankasu yakeyi, Haydar kullum fad'a yake yi masa ya bar wanna d'abi'ar ta ranka salloli amma yaqi dai nawa.

Matsar dake damunshi kenan amma inbanda ita shid'in mutum ne mai kirki da tausayi ga iya barkwanci, kowa nashi ne haka nan baya shashanci da 'yan mata sam, soyyar shan minti bata cikin tsarin shi, bar shi dai da iya yiwa mace kallon qurillah in abokanshi sunyi masa qorafin kan hakan sai yace abarshi ya tantance d'iri, sura, siga tare da class d'inta sabida anan zai gano wacce zai bawa kyautar ruhinshi.

**cikin sati d'aya da bayanawa junarsu sirrin zuciyoyinsu, sukayi wani mugun shaqu na ban mamaki, basa gajiya da hira duk in haydar yana gida haka in yatafi office suna maqale da waya ana zubawa juna kala man soyayya.

Abin da yayi mugun bawa Hameed mamaki, ai ko ya hana Haydar saqat da tsokana ya kance "sumumu kasau ashe munafunci ne da kai haka, da kayi ta wani noqewa kamar sufi nan ko majnun ne.
Aduk sanda yaji haka sai dai ya bishi da murmushi kawai bai iya ce mishi komi.

Lokacin tafiyar su Hindu yana zuwa suka yi bankwana da dangi suka tafi tare da Addawiyya da khairi sabida rainon su twins.

Hajiya karima taqaraci jarabarta ta haqura.
Chapter 21 · 0% Book details