← Book details Rabiatul Addawiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 38

Sashe 23

Rabiatul Addawiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Uhmm ya Haydar kenan baka rabo da zolaya.
"Allah ba zolayanki nakeyi ba pretty, kece da kanki kika nunawa duniya bakya yayina tunda ko darajan kallon arziki samuba ba daga gareki, ya qarasa zance cikin dacin rai.

Tuni idanunta ya kawo ruwa ta dawo gabanshi ta zauna ta soma magana "wallahi Allah ya Ali ba abinda kake tuna akai shine ba, kawai kunyar yima magana naji agaban su Abbie amma sosai ranar naji dad'in ganinka.

Ya amsa adaqile "Uhm naji, kallonshi tayi sosai tace "don Allah kayarda dani ba wanda ya sace maka heart d'inna, wallahi taka ce har abada bata taba son waniba sai kai kuma bazata qara son waniba bayan kai, kayafe min dan girman Allah kaji my life.

Murmushi ya kufce mishi ba shiri ya jinjina kai ya amsa "komi ya wuce sweetie.
"Aha thank you habibi.

Sosai suka sha hiransu ta masoya kamar wani abu bai taba faruwaba.

Suna tsaka da hira Addawiyya ta had'e rai tayi shiru, jikinsa yana bari yasoma magana "beauty mi nayi kuma? Sai da taja lokaci sannan tace cikin shagwaba "jiya nakiraka kaqi d"auka, kasa zazzabi ya kamani ya wahalar dani nakasa hassala komi nayi ta kuka har hawayena ya kusa d'aukewa.

Dariya yasaki mai sauti tabishi da kallo cike da so da qauna, ya kanne mata ido d'aya yace "ramawa nayi, kuma Alhamdulillah kinji abinda naji dafatan nan gaba zaki kiyaye yimin hakan.

Cike da mamaki ta jefa mishi tambaya "da gaske wai kayi kuka da hawaye kaima? "Yes, ya wuce wai hakik'a nayi kukan zucci wanda yafina na zahiri zafi da rad'ad'i,kad'an yarage heart d'ina bata tasami attack ba.

Zamewa tayi bisa gwaiwoyinta muryanta na rawa tace "don girman Allah da manzonsa ka yafemin bansan zaka fad'a mawuyacin hali haka ba da tuni nayakice kunyar gefe na kula ka.

Shima zubewa yayi gabanta yace "hakan yayimin dad'i sannan qimarki ta qaru sosai ya ruhina, lallai ina alfahari da samun mace mai kunya da kawaici tare da hangen nesa irinki, azancinki yana qaramin jin sonki har namanta da kaina.

Miqewa tayi ta koma mazauninta tana murmushi mai cike da kunya wanda yin hakan yariga yazama d'abi'arta.

Sai da Abbie ya dawo suka gaisa sannan ya wuce gida cike da annashuwa.

A parlor ya zauna dirshen bisa carpet ya zuge zip d'in d'an madai daicin akwatin data bashi sanda zai wuto tace tsarabarshi ne ciki.

Kayan barci ne masu laushi sai vests d boxes masu kyau da wasu littafan addu,o'i sai wata qaramar leda mai kyalli ya bud'eta ya fiddo wani box ya bud'e agogone mai uban tsada tare da zobben azurfa mai kyau, cike da jin dad'i ya zura zobben a yatsrshi nagefen qaramar ya tsarshi yayi mishi cif kamar angwada shi, subba ya kaiwa yatsar ya lumshe idanunsa ya furta "i really love you my angel.

"Uhmm soyayya ruwan zuma, in ansha aba masoyi oooo.
Bud'e idanunsa yayi da sauri ya watsama Hameed harara, yako sheqe da dariya har na buga qafa sai kuma ya matso ya soma duba kayan tare da cire night wear biyu vest da boxer bibiyu ya kwasa ya nufi room d'insa yana waqar "shi zumunci yana qarfafa son 'yan uwa.

Murmushi Haydar yayi tare da tattare sauran kayan ya nufi room d'inshi da su, yana shiga ya hango phone d'insa yana haske koda ya duba yaga Addawiyya ce ta kirashi har 3 miss call da hanzari yayi back call yanajin yasoma ringing yahaye bed d'insa yakwanta hanunshi d'aya cikin sumarsa.

***** Addawiyya tasoma karatunta na pharmercy a BUK duk medicine taso sai suka bata parmacy yayin da Maryam kuma suka bata medicine amai makon choice d'in na pharmacy, ita kuma khairi abinda tanema shi suka bata wato mass communication.

Sosai suka maida hankali akaratunsu amma fa Addawiyya tafi son medicine aranta don haka kullum Haydar yazo sai tayi mishi qorafi ita fa yasan yarda zaiyi a maidata medicine burinta ya cika inyaso sai maryam ta koma pharmacy d'in.

Yauma da yazo da shi tasoma yi masa maraba, ganin yaqi ce mata komi ta soma kukan shagwaba har da hawaye, baice mata kanzil ba har tagaji tayi shiru baki a ture.
Jan bakin yayi tayi sauri gyarashi yayi qasa da murya yace "Addawiyya ki zamo mai godiya ga Allah akan dukkanin abinda yazamo qaddaranki, ki amshi wannan qaddara tako da hannu bibiyu kicigaba da neman zabin Allah tare da nasaranshi sannan ina roqonki daki maidahankali sosai akan karatunki kada kiga ba choice d'inki bane shi ki soma shiririta, dafatan daga yau zakibar qorafi akai.

"Insha Allahu bazan kuma ba sannan nayi maka alqawarin dagewa sosai abisa karatuna.

"That's good my heart.
Idanu ta kad'amishi face d'inta d'auke da murmushi, tayi ihu kad'an ya kwanta baya tare da dafe qirjinsa ya furta "washhh!! Mashin so ya sokeni a ruhi, wannan irin fari ai sai a d'au gawata yanzu.
Dariya tasa tana mai kulle idanunta da tafukan hannayenta.

******* 11:00am at school.
Addawiyya, maryam tare da khairi suna zaune a wurin love garden suna ta hirasu na qawaye cike da nishad'i.

Qamshi turarenshi taji ya doso wurin sai kuma iska mai qarfi ta tashi agefenta tabi wurin da kallo uncle habibullah ne ya baiya a zaune bisa kujeranshi mai d'aukan idanu.

Addawiyya ta juya ta kalli su maryam taga sai hiransu suke tayi da alama basu ganshi ba.

"Mai babban suna tashi ki matsa wurin bishiyar mango d'incan magana nazo miki da ita mai mahinmanci.
Batare da tayi magana ta miqe ta nufi wurin mango tree d'in yayin data ga su maryam sun juya musu baya suna ta hiransu basu ko lura da tashinta a wurin ba.

"Mai babban suna aurenki yazo, za'ayishi nan da kusa kwanaki arba'in masu zuwa, to abinda nakeso dake shine da zarar magabatanki sunzo miki da zancen ki amince batare da gardama ba domin baki san me Allah ya boye ciki ba kamar yarda nima ban san komi akai ba, dafatan kin fahimceni da kyau.

Muryamta na rawa tace "a'a uncle nakasa gane inda zancenka ya dosa, wai kana nufim ni Addawiyya autan Ummi zanyi aure ciki qanqanin lokacin nan? "Eh mai babba suna. Idanu waje tace "to waye miji nawa "Aliyun kine "uhmm uncle ya Ali fa ya tabbatarmin sai na kammala karatuna har zuwa sanda zan gama service sannan zamuyi aure.
"Inkinje gida kinji zancena ya tabbata sai mucigaba da magama, bye sai nazo tayaki hira abarcinki yau.
Kokafin tayi magana ya bace bat.

Jikinta ba inda baya rawa, ta qaraso wurin su maryam ta d'auki purse tare phone d'inta tayi gaba batare data ce dasu qalaba.

*mrs j moon*
[1/20, 4:40 PM] Mrs J Moon😊: *RABI'ATUL ADDAWIYYA*
NA
SAFIYYA.

*36*

Ko kafin su maryam su iso inda take tamuza key ta fizga motar da gudu ta ta nufi get d'in fita.

Khairi tuni ta hassala tasoma fad'a, "ai wannan iskancin banzane tana ganinmu amma takasa tsayawa jiba yarda mutane ke kallonmu suna dariya.
Maryam da dubi mutanen ta tabe baki ta dafa kafad'an khairi cikin sigan rarrashi tace "Uhmm share kawai sis basa da aikin yine zo mukoma inda muka taso kafin nan da 25 minutes yaqarasa na shiga lecture.

Bata ce da ita komiba suka juya. Saida suka zauna tace "Maryam mi kika sani agame ta ficewar addawiyya cikin fushi?

"Wallahi bansan komiba khairi.
"Ok, let me call her muji. Tace tare dasoma dialing number ta.

Addawiyya kam driving takeyi kamar zata tashi sama, ikon Allah kawai yakawota gida lafiya.
Tana shiga harabar gidan taci karo da motoci gabanta yana bugawa ta sami gefen bishiyar umbrella tayi parking ta kife kanta bisa Stereo ta rasa meke mata dad'i.

Kiran khairi ya kuma shigowa tana kallo har ta tsinke batayi picking ba.
Kira na biyar kenan tayi mata tana kallo har ya tsinke amma taqi d'auka.

Khairi ta dubi maryam hankalinta atashe tace "bara na bita inajin ko lafiya.
"Ohk, ni inna fito class zan biyo inji mike faruwa"tam sai kinzo, ta qarasa parking lot taja motarta ta fice tana zancen zuci.

Jin maganganun su Abbie yasa ta d'ago tana hangensu daga inda take, Abbie, Abban su ubaiyu, Abban su Hameed tare da wani dattijo mai kama da Haydar sosai ta hango faces dinsu d'auke da fara'a, jikin wata mota babba suka tsaya zuwa can sai ga Hajja, Ummie tare da umman su ubaiyu sunyo mata rakiya.
Tana isowa suka shiga mota suka wuce Abbie da Abban su ubaiyu sukayi ciki tare da su Ummie.

Hakanan sai taji jikkinta yayi mugun sanyi, tasaka fitowa saima ta kuma gyara kwanciya a seat d'in data kwantar baya ta lumshe idanunta kamar mai barci nan kuwa tunanine ya baibayeta kuma tarasa wanne zata kama ciki.

Qaran bud'e get dataji yasa ta bud'e idanunta wanda suka koma red color.
Kusa da ita khairi ta parker motarta, bayan ta kulle ta fito tanufi ciki batare da ta lura da Addawiyya.

'Dan tsaki taja sanda taga su Ummie sunfito suna dube dube, tasan sarai ita suke nema donmin tasan khairi ta riga da ta kai gulma.

Kafin su qaraso wurinta ta fito tanayin murmushin yaqe, aqoqarinta na ganin ta boye halin da take ciki.

Umma ce ta kamo hannunta cike da kulawa tace "Ayya Rabi'atu mike faruwa kika boye kanki cikin mota alhalin kin jima da shigowa gidan?

Sai da ta saita muryanta sannan ta amsa "kaina yakemin ciwo ga kuma kasala yana damuna shine na zauna ciki amma yanzu dama zan shigo.

"Ayya sannu, Allah yaqara lafiya.
"Amin umma.
Juyawa tayi ta kalli inda ummi take tsaye ta zuba musu idannu, da aurin ta d'auke kanta sakamakon kallon tuhuma dataga ummin tana binta da shi.
Jan hannunta umma tayi suka nufi ciki, khairi ta matso daf da kunninta tace "madam Haydar mushiga ciki ki fad'a misu abinda kika boye mana amatsayinmu na qawayenki.

Harara ta wulla mata, itama hararan nata tayi ta kuma bud'e murya tace "dole dai kifad'a musu duk boye boyenki ehe.

Abinci umma ta matsa mata taci sannan ta bata magani tasha, ta umurceta data tafi ta kwanta, intasami barci zataji tadawo normal.

Koda ta shiga room d'in mai makon ta kwanta sai kawai tashige bathroom ta sakarwa kanta shower.
Chapter 23 · 0% Book details