← Book details Rabiatul Addawiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 38

Sashe 22

Rabiatul Addawiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Haydar duk sai yaji kamar yabisu, badan aikin office yayi mishi yawaba ba tabbas da dashi za'ayi tafiyar.

Kewa tayi mugun daminshi duk sai yadawo shiru2 kamar yarda yake ada can, jin dad'in shi 1 shine kullum dare sai sunyi video call da juna.
Yayi tazuba mata shagwaba tana biye mishi.

Lokacin aikin Hajja yana zuwa su Abbie suka tashi atare dukkansu, acan suka had'u dasu Addawiyya wa d'anga qasa mai tsarki ta amshesu suka saje da larabawa.

Duk inda Addawiyya tayi idanun Salma na kanta har ta tsargu ta matso jikinta ta kwantar da kanta akafad'arta tace "Adda mai tulelen ciki na sanza miki ne halan?
Duka ta faska mata a cinya ta zabura taja baya tana tura baki "Allah kinci albarkacin takwaran ummi dake cikinki da sai na rama ko mi za'ayi.

"'Yar buhu zokirama mana "uhmm nidai fad'amin mi jikina yayi kike tabina da kallo kamar wata mayya.

"Ohk kinrama ke nan ko? Dariya tayi ta amsa "eh'man ban mantaba ai har yanzu
"to yayi miki kyau, matso kiji abinda nagani atare da ke.

Matsowa tayi ta kanga kunninta daf da bakin Salma.
"Addawiy wallahi kin qara girma, haske, wayewa sannan uwa uba komi najikinki yaciko kin zama big lady mai kayan alatu ainun, anya kuwa Haydar zai ganeki in kuka had'u?

Da gudu tafice daga d'akin tana cewa "Allahumma yahadiki Adda Salma. Dariya duka d'akin su kasa, Hindu tace "bakwa gajiya da shiririta duk in kun had'u da juna ko Salma? "Aunty wasan saqo da saqo kenan ai.

Haqiqanin gaskiya Addawiyya tayi mugun sanzawa, duk alamun cikan 'yan matanci sun bayyana gareta, har abin sai da yabama Hindu tsoro ta tsareta sai ta fad'a mata abinda take sha da boobs d'inta tare da ships d'inta suka koma haka, sai da tayi ta rantsewa sannan ta yarda, kuma khairi ta tabbar mata da ba abinda takesha tunda duk inda zasuje tare suke zuwa, sai tabar abin alokacin zuwansu ne yayi, haka itama khairi ta cika ba laifi don tafi yarda tazo.

Cike da nasara suka kammala aikin hajjinsu suka nufo gida Nigeria cike da d'okin ganin dangi.

Addawiyya kam d'okin ganin bubby nta takeyi kawai, ji take kamar tayi tsuntsu ta ganta gabanshi.

Jirginsu ya sauka lafiya, duk abinda za'a anyi angama suka d'auko kayansu suka fito inda su Haydar suke jiransu.

Abin mamaki Addawiyya takasa kallon inda Haydar yake sam, kuma koda akazo tafiya sai shiga motar ubaiyu amai makon tashiga na Haydar, suka nufi gidan Abbie.

Haydar kamar zai kwalla ihu awurin amma sai yayi ta maza ya daure yashiga motarshi yaja suka tafi gidan amma inransa yayi ya baci.

*mrs j moon*
[1/18, 10:24 PM] Mrs J Moon😊: *RABI'ATUL ADDAWIYYA*

NA
SAFIYYA.

*34*

Kwance take cikin bedroom d'in Ummi ta rufe jikinta har zuwa samar kanta da qaton bargo amma duk da haka sai rawan sanyi takeyi.
A qalla ta d'auki mintoci 20 sannan tasoma zufa alamar zazzabin dake damunta zai sauka.

K'ara gyara blanket d'in tayi tare da jan siririyar tsaki ta furta "duk da ban kyauta mishi ba ai tunda na kira phone d'insa sai ya d'auka yaji uzirina ba wai yayi watsi da niba, takuma jan wani tsakin cike da d'acin zuciya.

Wani sarawa taji gefen kanta yayi mata ta dafe wurin tana matsan kwalla.
"Wai dama haka fushin masoyi yake? Ta tambayi kanta afili.

Lallai in haka abin yake masoya suna shan azaba, "wash ni Addawiyya, Allah kakawomin mafita, ka karkatomin da hankali ya Ali ya bar fushi nan ko nasami sa'ida a ruhina.

Kimanin kwanaki uku kenan da dawowarsu amma ko sau d'aya Haydar baizo gidansu ba kuma bai kirata a waya ba ita ce ta kirashi ranar da suka kwana biyu da dawowa yaqi d'agawa abinda yayi mugun bata mata rai har ya haifar mata da zazzabi mai zafi kuma tunda lokacin bata sake kiranshi ba duk da muradin son jin muryanshi da takeyi kamar me.

Sai bayan azuhur ta falka saboda barci da ya kwasheta bata sani, da hanzari ta shige bathroom, tana fitowa ta shimfid'a sallaya ta hau, bayan ta idar ta miqe ta shafa lotion ta zura wata doguwar riga roba mai d'auke da qananar stones golden ta yane kanta da qaramin gyale shima golden tafito parlor.

Gyefen ummi ta zauna a kasalance tace "Ummi barka da war haka, nabarki da aiki ko?
Cike da kulawa ta amsa "Alhamdulillahi auta, yajikin naki, kin warware ko dai nakira miki Salma ko Hameed wani yazo ya dubaki?

"A'a na warke, kasala ce kawai taragenmin yanzu kuma itama zata bari.
"Tam Allah yaqara lafiya "Amin.
"Ga abinci can a dining kije kici zakiji qarfin jikin, "ohk tam ummina.

Tura abincin takeyi kawai kamar tana cin magana sabida gaba d'aya zuciyarta taqi yi mata dad'i ga bakinta ba d'and'ano sam.

Tana gamawa ta gyara wurin ta dawo ta zauna ta bud'e data,, wata qila zatasami abin d'ebe mata kewa.

Ganin Maryam a online yasa ta tura mata saqo.
'''Ki turomin document d'in Babban goro (khadeeja candy) da cigaban Gidan k'unci (bebeelo) da kuma document d'in Wata uwar (Haemeebrah) ke da dai novels masu dad'i.
Yana shiga ta duba Haydar taga yana online, kamar zatayi mishi magana kuma sai ta fasa ta wank had'e fuska tana hararan wayarta kamar shine agabanta.
Tana shirin sauka taga ya turo mata da massage da sauri ta duba *malamansu kicire photo nan dake dpnki now* quri tayiwa gajeren saqon kamar wacce ta warke makanta cikin tura baki ta shiga setting tayi remove ta sauka da sauri batare da ta duba massage d'in maryam da taga ya shigo.

Haydar ganin ta sauka yaja tsuka. "Wato tafi qarfin ta amsamin kenan? Uhmm to ko sabon saurayi tayi balarabe, shi yasa tasomamin wulaqanci irin tasu na mata? Wani shashi na zuciyar shi ya amsa mishi "kaima baka kyauta mata ba Ali, komi tayi maka ai ka nemeta ka saurari uzurinta ba wai kayi ta fushi da babu gaira babu daliliba.

"Yesss!!!! Ya amsa da qarfi ya miqe ya zari key d'in motarshi yafice har yana had'awa da gudu.

A parking lot ya had'u da Hameed yace "ya haydar sai ina zuwa haka kuma? "Inda ka aike ni, ya masa mishi bai kuma jira cewar shiba ya shige motarshi ya fizgeta da qarfi, get man ya wangale mishi get ya fice.

"Allah yayi maka sauqi kai kam, Hameed ya furta cikin tabe baki.

Tana kwance a bisa cushion, suna hira da Ummi ta tsinkayi sallamarsa, Ummi ce ta amsa mishi ya shigo a natse ya russuna ya gaida ummi ta amsa cikin fara'a tare da miqewa ta bar parlor n.

Kallon kallo sukayiwa juna sai taga yarame mata amma yayi mata kyau sosai.

Shima kallo daya yagano ta rame sai dai yana cike da mamakin girma da cikan da tayi wanda sam bai lura da suba sanda suka had'u airport.
Itace ta soma janye idanunta, cike da yanga ta motsa lips d'in tace "ina yini, ya office?

Bai amsa mata ba illah idanu ya kuma bud'ewa yana qare mata kallo, kamar yau yasoma ganinta.

Wani matsanancin kunya ne ya kawo mata jiyara domin ta tuna rigan jikinta ta kamata tsantsan gyalenta bai rufe mata komi ba.

Cikin shagwababbiyar murya tace "please ya Ali d'an jirani a sitting room.
Ko motsi baiyi ba balle ta saran zai tashi.
Tashi tayi ta haya upstairs cikin sarsarfa don ta sanyo hijab.

Murmushi ya saki mai sauti yana mai furta "komi naki mai kyau da burgewa ne Rabi'atu,ya Allah ka mallakamin ita da sauri.

*sleep*😴🤦🏻‍♀

*mrs j moon*
[1/19, 11:10 AM] Mrs J Moon😊: *RABI'ATUL ADDAWIYYA*

NA
SAFIYYA.

*35*

Koda ta sauko tuni yabar parlor n, wani sanyi takeji yana sauka mata cikin heart ta runtse idanunta ta daka tsalle ta soma rawa tana d'iban shaky tana juyi cike da nishad'i tana waqan soyyaya soyayya.

Sautin dariyan Ummi taji abayanta yasa tayi saurin dakatawa da rawar ta juyo cike dajin kunya sai kuma ta diba da dugu zata fice.

"Auta zo ki tafi mishi da wani abu mana, juyowa tayi kanta aqasa ta shige kitchen, tana jera drinks tare da snacks tajiyo ummi na fad'in "uhmm auta dai da qarfi da yaji taqi yaron nan ubaiyu, to Allah yasa haka shine mafi Alkhairi.

Can qasan maqoshi ta amsa da "Amin sai kuma ta rufe fuskanta wai taji kunya, haka ta fito kanta a qasa taqi kallon inda Ummi take, rankwashi Ummin ta kai mata tana mai cewa "kunyar qarya ba, bacin yanzu kika gama cashewarki har da d'iban shaky.

Da sauri tafice tana dariya mai sauti, itama ummin dariyan tasa ta furta "auta hoo ita dai abinjin kunya bayayi mata wuya sam.

'Dauke da sallama ta shiga sitting room d'in, ya amsa mata can qasa, ta qaraso ta d'ora tire d'in bisa table ta tsiyaya mishi lemon mango with apple data had'a da hannunta, ta miqa mishi mai makon ya amsa sai ya damqe hannunta yana son su had'a idanu ita kuma ganin haka ta qara soke kanta qasa murmushi ya saki mai sauti yace "kinsan Allah idan har baki d'ago kin kalleni ba sai dai mu kwana ahaka.

Taqi motsawa ya matse hannunta da qarfi ta ritse idanu, jus d'in dake hannunta yasoma zubeqa sabida rawar da hannunta yasomayi.
miqa hannun nata yayi zuwa bakinshi ya kafa kai yana tsotsan jus d'in eyes d'insa bisa kanta, tana jinsa duk abinda yakeyi amma taqi d'ago kanta ta kalleshi.

Sai da ya shanye tas sannan ya saketa ya koma ya lafe cikin cushin yana tsotsan labbanshi cike da nishad'i yace "oya hajiya Rabi'atu sami wuri ki zauna haka nan kada qafafunki yayi tsami, miqewa tayi ta zauna nesa dashi kanta qasa tanayin wasa da ya tsun hannunta.

"Uhmm sarkin jin kunya sai kisaki jikinki hakan ko maji dad'in yin hiran yaushe gamo duk da nasan yanzu batani kikeyi ba kinsami kyakykyawan d'an balarabe tuni ya sace miki zuciya.

Da sauri ta d'ago idanu waje tace "inji wa? "Inji ki.
Ta langabe kai cike da marairaita tace "kai ya Ali yaushe mukayi haka da kai? Shima langabe kan yayi ya amsa "ranar da kuka dawo daga saudi a airport kika tabbatarmin da bana gabanki sam yanzu.
Chapter 22 · 0% Book details