← Book details Rabiatul Addawiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 38

Sashe 20

Rabiatul Addawiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Uhmm mai babban suna angirma ansoma soyayya ko?
Tura baki tayi tana kallon shi tace "uncle mi yasa kayi watsi dani?
"Sabida kin girma yanzu, bakya da lokacin kanki.
Idanu waje tace "nid'in? "E, "to aikin mi nakeyi? "Ta tunanin masoyinki Ali.
Kauda kanta tayi cike da jin kunya, ya saki 'yar dariya yace "Allah yabarku tare, shima yana sonki sosai amma akwai jarabawar rayuwa azamanta kewarku, ina yi miku fatan cinyewa da kuma samum sakamako mai amfani, yaja numfashi yace "sorry mai babban suna, daya yau zanyi nesa dake agame da ganina dakikeyi azahiri amma dai zakiriqa jin maganata lokaci zuwa lokaci.

Idanuta ya ciko da kwalla zatayi magana ya rigata "kada ki damu mai babban suna ina tare da ke ako ina, bye.
Ko kafinta tayi magan ya bace bat.

zaunawa tayi jiki asanyaye tana son gano inda maganganun uncle d'inta ya dosa amma ta kasa gano komi.
Jarabawa wacce iri kenan? Ganintana batawa kanta lokaci yasa ta miqe ta fito parlor ta tadda duk sun shirya ita suke jira.

Haydar ne zai kaisu, yana ganinta yayi saurin bud'e mata front seat sai da ta zauna sannan ya bud'ewa su Hindu back suka shiga, khairi tace "ya Haydar mata tafi uwa ko?
Ahanzarce ya juyo yana kallonta ta gyad'a kai tana cewa "eh'man kana ganin aunty amma sai da kayiwa Addawiy wuri sannan ka tuna da ita.

Kauda kai yayi yana murmushi su kaka Abu suka saka mishi dariya itama Addawiyyan dariya tasa tayi qasa da murya tace "abin boye dai yau yafito fili.
Mintsilin cinyarta yayi ya amsa "muna isa zakiyimin bayanin me zancenki yake nufi.

Cikin kwabe fuska kuma cike da shagwaba ta ture hannunshi tace "Mugunta dai baya da kyau.

"Haydar ko mufita mubaku wuri ne, ku gama soyayyar?

Cike da jin kunya ya shafi sumar kanshi yace "uhmm aunty gyara zama takeyi fa, banza tayi mishi, ya waiga ya watsawa khairi kallon zakisani ne yarinya sannan ya yiwa motar key suka fice.

*mrs j moon*
[1/16, 4:02 PM] Mrs J Moon😊: *RABI'ATUL ADDAWIYYA*

NA
SAFIYYA.

*Pape d'in nakine sis Barakah, Allah yabar so da k'auna, inajinki sosai a❤👈🏻😘 kuma Addawiyya tace ki saurari zuwanta garin barno don duk sai ta tone asirrin boye da masu bama bamai suka binne maku* 😅lol.

*32*

Kaka Abu suka soma saukewa agidanta, sun cikata da kayan arziki sosai sai godiya take tayi tare da samisu albarka.

A gidan Abbie ummi tarasa inda zata sakasu tayi don murna, ta d'auki hassan ta koma ta d'auki hussain sai kiran "masha Allah takeyi cike da murna.
Addawiyya sai dariya take mata tare da tsokanarta tace "su ummi anga yara masu kalan larabawa duk anbi an rud'e to kisani dai ko yaye baza mu baki su ehe.

Ta amsa cikin wasa "nima banso, kuyita riqe 'ya'yanku nawa sun isheni.
Suka saka dariya su dukansu.

Anan suka yini sai bayan la'asar Haydar yadawo d'aukansu.

Yana shigowa idanun shi ya hango mishi Addawiyya zaune da wani suna hira sai dariya takeyi, wani abu yaji ya sokeshi azuciya yasami kanshi da kasa fitowa bayan da yagama gyara parking.

Addawiyya kam Sarai taga isowarshi, tayi kamar bata gani ba, ta cigaba da sauraren hiran Aisha wanda ubaiyu yake mata.

Afusace ya fito ya wucesu zuwa ciki, bayanshi tabi da kallo tana murmushi.
Ubaiyu ya dubeta "Addawiy ko shine wanda ya kasani? "Uhm tace tana sunkuyar da kanta qasa.
Ah lallai yaciri tuta kam, Allah yabar so da qauna mai nagarta, ta amsa Amin cike dajin kunya.

"Abinda yaja kenan nafad'a tarkon sonki a baya, wato kunyarki da natsuwarki.
"Uhmm Allah yabaka wacce tafini komi ai, gata babba ba yarinya kwaila kamata ba.
"Kece kwailan? Aikam Ko makaho ya laliba yasan kinfi qarfin akiraki da kwaila.

kauda kai gefe tayi ta nunashi da yatsa "kaikoh? Baka da dama ya ubaiyu Allah.

Dariya ya saki yana sosa gemunsa ya miqe yayi gaba sannan ya juyo "tafi wurin mijinki kada yazaci muna soyewa ne.

"Uhmm kafa samu abinyi tsokanata kenan yanzu, to a inkaje kagai damin da Aisha kasanar da ita zanzo cikin satinnan muga juna.
"Zataji, amma ni zanzo nayi mikk jagora ko? "Ai kasan nasoma makanta hqr nasoma shelan neman d'an jagora.
Dariya yasa sosai yana nunata da yatsa, "a'a bance ba autan ummi, harara da dalla mishi tace "banson jin sunar nan abakinka tam.
Sai da ya russuna ya dunqule hannu yayi mata jinjina sannan ya amsa da "angama ranki shi dad'e.
Baqaramin dariya abin yabata ba, tana cikinyi ta hango fitowar su Hindu, ta d'agawa ubaiyu hannu alamar bye tayi ciki da sauri.

Qarasawa yayi wurin su Hindu ya gaishe da ita yaga su twins ya fidda kud'i mai yawa ya miqawa khairi yana cewa "asayawa su twins pampers.
Godiya Hindu tayi mishi, ya juya tare da miqawa Haydar hannu sukayi musa baha, ya shige motarsa ya fice yana jin jina lamarin Haydar ganin yarda ya amsa mishi sallamar kamar baya so.

A bisa hanyarsu ta komawa gida sai harara yake ta wullama Addawiyya, ita kam sai murmushi take sakar mishi da zarar sun had'a idanu abinda ya qara tunzira zuciyarshi yaji kamar ya tsaya ya fiddata a cikin motarshi.

Suna isa tayi saurin ficewa tayi ciki harda had'awa da gudu.

Cije labbanshi yayi yana jijjiga kai, yana ayyana irin hukuncin da zaiyi mata in suka had'u.

Wasan 'yar buya suka soma, duk inda tasan yake bazata je wurinba haka nan da zarar ya shigo part d'in Hindu ko Hajja indai tana ciki bazata bari ya ganta ba.

Yashiga cikin damuwa sosai, har yaji ya tsani kansa, da ace bai nuna mata yana qumunta ba da duk haka bai faru ba. "Yau ko ta tsiya sai naganta, ya furta tare da miqewa yafad'a toilet.

"Khairiyya wallahi inbaki fita shirgin 'yar banzan yarinyar nan ba mai siffan aljannu ba zanci mutuncinki.

Tura baki khairi tayi tana qunquni.
"Fito fili ki zageni kawai khairi ba ki tsaya yimin gunaguni ba.
"Ni ba zaginki nake yiba momy kawai cewa nayi nakusa komawa gaba d'aya part d'in aunty Hindun ma, sabida can yafi nan dad'i kuma mutane suna kai da kawo sosai fiye da nan part d'in, ba'a zama shiru kullum cikin nishad'i ake, muyi karatunmu tare da ita, muyiiwa su twins wanda mu shiryasu mu goyasu har suyi barci sannan acan nakoyi abu buwa masu yawa wanda ke kika kasa koyamin kamar girmama babba, girki mai dad'i, sallah cikin time d'in tare da koyon had'a baqin ajami wanda mugun gatan da kika nunamin yasa bansan komai ba akai amma yamzu alhamdulillahi taraiyata da Addawiyya nasami abu buwa masu tarin alfanu wanda ada nagaza samunsu don.... Saukan marin da Hajiya karima ta falla mata yasa take maganarta ya cinke ba shiri.

Baya taja tana kallon uwar nata idanu waje hannunta dafe da quncinta.
"Momy ni yau kika mara? "Eh, kuma ina daf da lakad'a miki dukan kawo wuqa indai har baki rabi da wad'ancan harsabiban muta nen ba.
Ja baya takuma yi tana girgiza kai, hawaye tuni yagama wanke mata fuska tace "billahil azim bazan rabu da mutanen kirki irin su ba, koda kuwa zaki zamo ajali nane.

Salati hajiya karima tasaka tana tafa hannayenta, ta nuna qirjinta tace "wato kina nufin nid'in mutumiyar banza ce kenan ko khairi?
Muryanta na rawa ta amsa "a'a momy baha nake nufiba.
Ta soma matsowa inda take tana ja baya "to ya kike nufi fad'amin inji sallamammiya wacce aka gama bata rubutun kashe zuciya ta shanye.

"Momy kibar fad'an haka baya da kyau don shine ake kira zato zunubine koda yakasance gaskiya ne.
"Yau nagama ganin Ikon Allah mai mana ruwa, ni karima nagata kaina, wato wa'azi suka turoki kiyimin kenan? "A'a momy nadai san hakan ne ayayin had'uwata da Addawiyya dan ita mai tarin ilimi ne sosai musanman na islama, to ita take koyamin da zarar mundawo daga islamiyya kuma ina ganewa sosai don haka ina roqonki dan girman Allah da manzon sa kidaina aibata su kije kigode musu na dawo miki da 'ya dAsu kayi hayya miqaqqiya amai makon da datake aband'are.

Wani marin ta kuma sauke mata ta fizgota tayi cikin bedroom d'inta da ita, sai ihu take tana kiran wallahi ina tare dasu koda zaki zama ajalina ne.

"Bazan zama ba amma zaki gane kurenki yau, sai naga uban da yatsaya miki agidan nan.

Afusace aka banko qofar aka shigo Hameed ne yashigo cikin fushi ya kwaceta ahannunta, da gaggawa khairi ta koma bayarshi ta lafe tana maida numfashi.

"Uban wa yabaka izinin ka shigomin part.
"Ubana, mari ka kawo mishi ya tare yana zare mata idanu ta zabura zata kamota abayarshi ya daka mata tsawa "wallahi kibar ganin ke kika haifeta to bashi zai hana in faffalla miki mari akan taba.

"Ni d'in zaka doka Hameed?
Gyada mata kai yayi tare da juyawa ya kama hannun khairi yace "muje ki kwashe kayarki daga part d'in nan ki koma na aunty kuma koda lokacin tafiyarsu yayi gidan su Addawiyya zaki tafi har sai sundawo.
Ta amsa mishi da "to jikinta duk yayi sanyi.

Duk jaraban da hajiya karima take musu bai sa sun tsaya da abinda sukeyiba, khairi ce ma tayi qasa da murya tace 'ya Hameed momy fa tana sona kada intafi hawan jininta ya tashi.

Shima murya can qasa ya amsa "walata zamuyi ai, wata qila zata san Allah d'aya ne.
"Ohk nafahimta.

Ranar haukane kawai batayiba gashi har yanzu part d'in Hindu baya shiguwa mata balle taje ta d'auko 'yarta, haka dai tayi ta zage zagenta bawanda ya kulata hattako da 'yar nata khairi.

Hajja ta kaiwa qara itama ta goyi bayan Hameed inda tace "da part d'inki dana Hindun ai duk d'aya ne.
Cikin fushi tabaro part d'in tana jiran Alh. Yadawo daga tafiyar da yayi qasar Germany ayi wacce za'ayi sabida bazata taba lamunta ba arabata da 'yarta d'aya tilo.
Chapter 20 · 0% Book details