Sashe 84
Namijin Zuma Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
yi, cikin ruwan sanyi kawai take azabtar dashi, tinda yasata kuka , ta kulla a zuciyarta shima seyayi kuka fin nata, kusan kullum in zatayi bacci se tayi kwallah bakin cikinsa, Danma tama kanta natsiha ta rage damuwa, kawai shi take jefawa a damuwa yanzu, ji yake kmr ze haukace. naeema ta kasa gane Kansa, se faman kulle kulle sukeyi ita da uwarta, yana ankare da ita kullum seta fita, ya kula bata dawo da niyar zaman Aure ba, tinda duk cikin halinta ba wanda ta chanza, Daman ya bata chance ne last, a hnya take Yana iya sakinta Sam ko a jikinsa. Kusan yau nabeelah tayi Arba in, hakan yayi dai-dai da dawowar naeema gidan da kwana goma., amma kullum seta fita ko randa aka kawota washe gari seda ta fita, dande kawai Aeezad baya hayyacinsa ne da tini ya Taka mata burki, bata isa ta dinga masa iskancinnan ba yanzu gaskiya. A bangaren nabeelah har yanzu ba fuska dukda yana tsananin bukatarta amma ko kallanta a tsorace yakeyi, ko magana seya sadda kansa kasa yake iya mata ita, yayi-yayi tagaya masa Meya mata amma sede tace bakomai. Inda abinda yafi komi matsifa a rayuwarsa ya tambayeta tace bakomai, ya bata hakuri kuma taki hakura, taki chanza masa duk yabi yayi zuru-zuru, kallo daya zaka masa kasan baya hayyacinsa, a gigice yake, yakamata ya koma bakin aikinsa Amma ya kasa,bayajinma ze iya komawa beci gindi ba. Bayan Azahar, ya shigo falon jiki sakaka, idanuwansa suka sauka a kanta ita kadai ce zaune a falon sanye da Atamfa doguwar Riga irin me fidda dirin jikinnan ce, cikin kayan da Aunty hafsat ta Dinka mata ne ta kawo mata ranar suna, babbar grant super ce,. Daga ita se Inna Ade a falon babbar macece magidanciya Hajiya maryam ce ta kawo mata ita saboda kula da yaran kusan su uku ta kawo mata age mate din inna Aden sbda kula da yaran , aiki nayima ummih da big hajiya yawa, Reno is not easy,. Big hajiya da Ummih basa nan sunje gidan Hajiya maryam domin su mata ban gajiyar suna, da hidimar Arziki sbda tayi hidima sosai a sunan,. Inna ade Rike take Mahnoor da Manaal, Mushfiqa na hannun nabeelah, yaran sun kara girma sosai sunyi wayau kyaunsu ya kuma bayyana yafi sanda suna jarirai, Kai inka Gansu kasha yan wata uku ne, ga lafiya ubangiji ya wadacesu dashi, abun shaawah, tinda naaeema taxo gidan bata gansu ba, ko haduwa ma da nabeelah basuyi ba. Inna ade na ganin Aeezad yashigo ta gaidasa ya amsa, ya karasa ya Duba yaransa ya musu Adduah, daman Mahnoor na goye bayanta, ta karasa ta amshi Mushfiqa dake hannun nabeelah. Bacci ma duk sukeji inna a kwantar dasu tinda basajin yunwa zasuyi bacci Cewar nabeelah, da tayi mgnr tanata bin yaranta da ido, Mushfiqa ma ita kawai take kallo tama uwarta kuri da ido. Inna ade tace Toh bari, in Kira su Asma u da Hadiza se a goyasu kawai su Asma u da Hadiza sune aka kawosu tare gidan wato de sune masu rainon triplet din, an yadda da iya rainsunsu domin daga company aka dakkosu ba irin locals dinnan bane, sunada kwarewa a raino. Gidan de ynzu cike yake da masu Aiki sunfi goma. Yawwah inna a goyasu kawai Cewar nabeelah da tayi mgnr cikin girmamawa. Inna ade tace toh ta nufa dakin dasu Asma u suke. Karasowa Aeezad yayi ya zauna kan kujerar dake facing nabeelah, tinda ya shigo jikinta kawai yake kallo amma tsoro ya hanasa Kallan fuskarta, azababben kwadayinta kawai ke dawainiya dashi kuma duk macen daze kallah ba wadda yakejin kwadayinta se ita, a kullum be iya bacci sbda Azabar shawarta dake damunsa, ya rasa ma ina zesa rayuwarsa yaji dadih Gashi rabonsa ma daya taba ko hannunta ya manta. Ina wuni mommy ya gaidata sbda shide yasan shi yayi lefi, tini ya fahimci duk sbda dawowar naeema ne take wannan abun, kuma ta kasa fahimtar shi bashi yace naeema ta dawo gidan ba. Tinda ya shigo har yanzu ko Kallan inda yake batayi ba, ko amsa gaisuwar batayi ba. Ya dago ya kalleta yaga idonta na kan TV , kallo daya ya mata ya dauke idanuwansa, wlhi inya kalleta yaga ta hade rannan gabansa yankewa yakeyi ya fadi. Sunfi 2mnt be sake cewa komi ba se kuma yace Big hajiya da Ummihna basa nan ne? A takaice tace ina sukaje? yanata tambayar ne kawai so yakeyi yasamu ta masa mgna me tsayi ko ze samu dmr tura Aniyarsa, da ace normal suke ai da yanzu de ya fara tura Aniyarsa ko samu yayi ya shiga gun nan ko hankalinsa ze kwanta, yanzu hankalinsa yafi na barawon asubah tashi, kafin de su big hajiya su dawo yasan sun gama abinda zasuyi. Mikewa tayi ba tare data basa amsa ba, ta fara kokarin barin falon. Ya mike cikin hanzari yasha gabanta, kawai seya tsugunna, yayi knell a kan guiwowinsa, ya RIKO hannayenta duka biyu cikin nasa, ta kwace ta kauda face finta the other side. Ya fara magana cikin rashin nutsuwar , damuwa Fal lullube da muryarsa, duk wanda ya gansa dole ya tausaya masa a wannan halin da yake ciki, duk rashin imaninka . Dan girman Allah mommy ki rufamin asiri Wacce iriyar Azaba kikemin haka dan Allah? Ai ta isa in ba gawata kikeson gani ba...Ki rufamin Asiri mommy dan girman Allah, wlhi ma Azabtu ki barni haka, bana normal dake ina kikeso nasa rayuwata naji dadih, Dan girman Allah mommy Dan Zatin Annabi SAW ki rufamin Asiri kiyi hakuri pls, ki rufamin Asirina na duniyarnan Dan Allah,Dan Annabi SAW kiji tausayina, bani da kowa seke, wlhi ji nake kmr zan hauka, ki dubeni da idanuwanki nada, wlhi in kika ci gaba da azabtar Dani, wayar gari za ayi nayi hauka Kona mutu ya karashe wasu zafafan hawaye na wanke masa kunci, a kanta ne kawai beda dauriya a rayuwarsa, a kanta ne kawai zakaga hawaye a kan kuncinsa, shi mutum ne me dakiya da juriyya amma be iya katafus a kanta, zuciyar jariri ma tafi tasa kwari inde a kanta ne, shi kadai yasan matsifun daya shiga a kwanakinnan ji yakeyi kmr sunyi shekarun a hakan, har Rama yayi, safe rana dare yana ziryar part dinta, tinda yaje part din naeema sau daya be sake zuwa ba, ya kasa katafus tini Zaks ya koma bakin aiki Amma shi Kam ba rana balle wata, to Ina yagama nutsuwa bayan ana azabtar dashi a zahiri da bad'ini, shida bacci sunyi hannun riga, ga Abu ya damesa kullum mike yake baya ko rissinawa. This book is 1k 08101626484** NAMIJIN ZUMA .last page AlhamduLillah and finally, komi yayi farko zeyi karshe! Duniya tayima na'eema tsanani, Sam Aeezad yanzu ma baya kwana da ita, sede ranar girkinta ya roketa ta saida masa kwananta, saboda shi da nabeelah yakeso ya kwana, Sam Se taki saida masa karshe ma sede su watse da fada, itakam nabeelah bata Taba yadda, ya dakko kwanan naeema ya kawo mata. Kunci iya kunci na'eema Na Cikin, komi Aeezad na mata na Aure Amma banda saduwa, Harga Allah ya gaya mata ma kawai shi baze iya hada nabeelah dako Wacce mace ba, shi bayin kansa bane, yanzu Kam ai ya kuma rikicewa dayaji gindi ya Kuma dadih da Zaki komi yayi zakwai, kullum cikin naci yake mata, kamar ze fada mata inya ganta, Yana samun nutsuwar da yake bukata gun nabeelah, gabaki daya ya kasa komawa bakin aikinsa, gashi Ayyuka na gabansa, yace nabeelah ta bishi kanon taki, shi Kuma inde babu ita baze iya zuwa garin kano ba, ko kallanta yayi se gabansa ya tashi, toh in basa kusa aise yayi hauka. Nabeelah nata kasuwancinta,sosai business ya amsheta tako ina se Sam barka,. Alhaji sadi kullum Yana ziryar gidan ba Wanda be fahimci saboda ummih yake zuwa gidan ba, har big hajiya ma ta fahimci hakan. Bikin Zaks da Dr Salmah nata matsowa. Triplet se wayau sukeyi sun, Gashi sun tashi cikin koshin lafiya ba laulayi. A bangaren Hajiya mommy ma gabaki Daya ta kasa gane kan gadon Alhaji sunusi gashi gaba Daya asirinta dayake kansa ya karye, yanzu bata da value a garesa , ada seta wuni Tana yawo Amma yanzu Ina Bata isa ta fita ba, gashi ya rike hannu bata samun komi a gurinsa, gabaki daya jarinta ya kare a yawon bin bokaye, gashi ba biyan bukata, har kaf shagunanta komi ya kare Kuma ta daga shagunan ta siyar, bata da komi ynzu se gwala-gwalai Suma sun kusa karewa kaf a kan bin malamai, gashi ba Wani ci gaba, data samu Labarin malami seta daga kadararta ta siyar tasa hajiya naja'atu ta aika mata wata kawarta sajida gun malamin, se asara kawai takeyi ba biyan bukata, Ji takeyi kmr zatayi hauka, kaf malamanta inta Kai musu aiki sesuce su bazasu iya ba sbda akwai Tsari sosai a jikin mijinta, in suka matsa zasu mutu, wasu Kuma sede suci mata kudi ita da yarta na'eema de duk abinda suka Tara ya kare, kaf motocin da Aeezad ya siya mata ta siyar, sun bawa malaman tsubbu babbar matsifar ba biyan bukata, komi de ya kare musu gwalagwalannma babu yanzu kebura kawai suke amsa na Azaba, yanzu Naeema a napep take yawo in zatazo gun mahaifiyarta, danma Khady kawarta ta bata Wasu kudi akn tadawo da hankalin mijinta knta sbda itama ta tausaya mata halin da taga sun shiga, ko a mafarki batayi tsammanin zasu zama hkn ba ita da uwarta, tini khady ta janye jiki daga naeema saboda harga Allah ita bata kawance da mara Arziki kaf kawayenta masu kudi ne. duniyar juyi juyi kwado a ruwan zafi! Ita kanta hajiya mommy bata taba tsammanin wannan matsifar zatai mata wankan tsarki ta afka musu ba ita da na'eema, a kullum kara tsanar nabeelah sukeyi sbda zuwanta ne ya haifar da matsifar Nan. da hajiya mommy Taga ba nasara taako Ina gashi komi ya kare mata, ta fara tunanin yadda zasuyi su kashe Aeezad da matarsa da yaransa gado ya zama nasu, daganan su dawo su kashe Alhaji Sunusi bayan anyi shekaru sbda kar a zargesu, gabaki daya sun gama tsara yadda zasuyi na'eema da uwarta, itade Hajiya naja'atu Tinda taji maganar kisa taja baya ta zame, saboda zunubin