← Book details Namijin Zuma Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 87

Sashe 29

Namijin Zuma Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

tace ne. Da daddare har 12:am kowa duk aka watse da zunmmar gobe zasu dawo sbda jiran farkawar Aeezad din kawai akeyi ,wad'and'a sukaxo daga garuruwa da dama suka nufa hotel, Alhaji sunusi Nan ya kwana sbda dakin da Aeezad din yake akwai kusan falo biyu special room yake, hajiya rafi'ah Kam ita da na'eema tini suka nufa hotel tin 10:pm, tace ita bacci takeji a gajiye take, ba kunya suka wuce hotel ita da yarta, Alhaji sunusi kawai sebin hajiya rafi'ah yake da Ido, Ashe bata da hali kamar yadda aketa gulmarta be tabbatar ba se yau,ya bata da mutane da dama a kan Hajiya rafi'ah danshi luf-luf take masa. Baban Noor ya nufa gidan abokinsa Alhaji sadi wanda har dare shima Yana Nan asibitn har 12:am ,a zuciyarsa sbda nabeelah yake zaune a asibitin shifa tinda yayi tozali da ita yace yaga matar Aure, gabaki daya hankalinsa ya tashi, kwad'ayinsa kaf ya koma kan nabeelah, daman Alhaji sadi matarsa Daya yaransu bakwai, a kallah Alhaji sadi ya haurawa shekaru hamsin ba sa'an baban Noor bane Kawai jininsu ya hadu suka fara abota. Suna tafe a mota kafin su karasa gidan Alhaji sadi ke shaidawa baban Noor shifa yana kaunar wannan daya gansu tare kuma so na Aure. Nan baban Noor ya hade Rai sbda ya fahimci nabeelah yake nufi. Duk hade ran da baban Noor yayi sam Alhaji sadi be fahimta ba se raftago zance yakeyi yariga yayi nisa a soyayyar nabeelah wai a haka danma a rikice ya ganta, Amma hakan be hanasa gano surar jikin da ubangiji ya mata ba. "Wannan ba karamar yarinya bace bafa alhajin Allah..."cewar baban Noor. Alhaji sadi ya kalli baban Noor cikin rashin fahimta yace "kamarya? Bangane ba! ba kamar yarinya bace ba?,wannan dagani ai bata wuce 20yrs in tayi wuta kenan, kawai de kayan morewa ne ubangiji ya bata tako ina taf-taf Alaji kaga nonuwa tantsan-tantsan..." Baban Noor ya amshe da "TAB wallahi wannan ta girmi matata ma in gaya maka..." "A duniyar Aljanu kou?'' cewar alhaji sadiDakewa baban Noor kallon mara hankali. Baban Noor yace "a duniyar mutane, wannan fa ita ta raini Commander Aeezad, Aeezad he's 22yrs , matata kuma 26yrs, ita Kuma wannan me Aiki cefa nanny din Aeezad ce, shine yanzu tadawo Aiki gidana gun iyalina,a kallah zata Kai 32yrs haka Naji iyalina tace, kawai karamin jikine da kyau take dashi na matsifa..." Baban Noor yayi mgnr ne sbda kawai ya cirewa Alhaji sadi batun nabeelah a ransa. Alhaji sadi ya tabe baki ba tare Daya yadda da shekarun nabeelah Da baban Noor ya fadi ba yace "Dan wannan ni ina ruwana, nifa ko shegiya ce ita ba nanny ba ina santa, Kai wannan macen me tsada waze ganta ya bari, ai tanama da tsoron Allah datake aikatau har yanzu, ade matan yanzu babu kamarta, saboda wallahi da matan yanzu ne masu budadden Ido ai da yanzu tana zaman kanta, da tini ta mallaki kudade a duniyar Nan sbda kalarta ai kalar manyan mutane ne irin mu. ...ni wlhi Naji ma ta kuma kwanta min a zuciyata dakace min me Aiki ce, kaga hakan na nuni Da tanada kamun Kai, ni zan fara bude gindinta a leda kenan Masha Allahu.."Alhaji sadi ya karashe Yana wani shu'umin murmushi har ya fara mafarkin gashi a marar wannan kyakyawar macen , a Ido ya tabbatar dole farjinta yayi dadih. Wani kololon bakin ciki ya cika zuciyar baban noor domin ya kula Alhaji sadi yayi nisa bazeji kira ba yanzu. Har suka isa gidan Alhaji sadi nata sambatun nabeelah, Sam baban Noor be sake ce masa komi ba se Uhumm A'ah kawai, kasan zuciyarsa fal haushi. Daren ranar Sam nabeelah batai bacci ba, ita da Hafsat ne a falon, hafsat tayi kwanciyarta tayi baccinta a kan kujerar 3ctr , nabeelah Kam ko kyafta idanuwanta bafai ba da zummar bacci, se lekawa takeyi tana kallon dakin Aeezad ji takeyi kamar taje dakin, Amma ina ba dama har yanzu ko ina zagaye yake da securities suna tsaitsaye ko zama basayi, dukda dare ya tsala Amma ko gyangyadi bameyi. Haka tadawo Falon ta shiga toilet ta dauro alwala dai-dai biyu na dare ta fara sallolin nafila tanata Addu'ah Allah bawa Aeezad dinta lafiya, tana sallar tana tangadi sbda har ynzu bataci ba bata shaba, aunty hafsat tayi-tayi da ita taci abinci Amma taki sbda bazata iya ba tanada tabbacin koda taci baze wuce cikinta ba Sbda hayyacin lissafinta na komi baya jikinta. har asubahi tanata sallah, datayi sallarh asubahi taci gaba da lazimi, duk kwarewar satar bacci be samu nasara a kanta ba ranar, burinta kawai taji ance AEEEZAD ya farfad'o. Zuwa karfe goma na safe mutane suka fara hallara asibitin, hajiya rafi'ah Kam bata iso asibitin ba ita da yarta se wuraren Sha biyu na rana, koda suka iso tini mutane sun cika fam. Alhaji sunusi se kallonta kawai yakeyi,zuwa ynzu mamakin hali irin nata kawai yakeyi, tinda ya aureta beyi kukan rashin mahaifiyar su Aeezad ba se jiya da daddare, yaci kukansa ya koshi takaici da tunanin lafiyar d'ansa be barsa ya rintsa ba. 2:30pm zuwa lokacin jikin kowa ya fara sanyi sbda shirun yayi yawa, an kara masa jini dai-dai Wanda jikinsa ke bukata, drip ne a jikinsa yanzu. Wani doctor ne ya fito daga dakin da Aeezad ke kwance, idanuwansa sanye da siririn glass, yayinda yake sanye da kananun kaya. Daddy na ganinsa ya mike a rude ganin doctor din ya tinkarosu Nan Alhaji sunusin yashiga tambayar "Ya jikin d'ana doctor munji shirun yayi yawa..." Da fara'ar kwantar da hankali dauke a kan fuskar doctor nazir yace "Ka kwantar da hankalinka sir, jikinsa Alhamamdulillahi kam da sauki, yama farka Amma yanata kiran sunan mommynsa,,, seda yadawo hayyacinsa duka yace Yana son ganin Nabeelah,,..." Da karfi doctor ke mgnr yayinda aunty nabeelah dake sauraren doctor taji ya kira sunanta ta mike a zabure, zata isa insa doctor din yake hajiya rafi'ah tayi hanzarin yin caraf kafin Alhaji sunusi yace komi ta amshe da "Kai doctor nabeelah yace kode na'eema, Anya kaji da kyau kuwa?" Doctor dake kallon hajiya rafi'ah be manta ba itace ta zage securities jiya. "Gaskiya kmr nabeelah yace ba na'eema ba..." Cewar doctor. Cikin tsiwa hajiya rafi'ah Tace "inaga de kunnenka ne beji da kyau ba,, ko baka lafiya ne...Amma na'eema yace, sbda mude kaf danginmu babu wata nabeelah, sede na'eema gatanan iyalinsa ce,..." Sam doctor be hayewa hajiya rafi'ah ba danya kula bata da mutunci tana iya masa zagin uwa da uba. "Wait hajiya bari inje in kara tambayarsa..." Cewar doctor nazir. Ya juya ze koma dakin da Aeezad yake hajiya rafi'ah tace "Harse ka tambayosa? Yo wai meze hana duk mu shiga mu gansa..." Doctor ya juyo yace "Kuyi hkri ba yanzu kowa ze shiga ba se Nan da zuwa la'asar..." Yana fadar hakan ya juya zuwa dakin da AEEEZAD din ke kwance. Nabeelah Kam tinda taji kalaman hajiya rafi'ah takoma da baya, Sam bata damu da munanan kalaman hajiya rafi'ah gareta, domin tasan tass tasan da ita nabeelah Amma tace basu da wata nabeelah. Aunty hafsat Kam abin ya mata ciwo Amma bata data cewa, sbda bata isa ta tanka ba, daddy ma yayi mukus ya kasa mgna kmr Wani wa-wa, kuma tabbas yasan nabeelarh da Ake nufi, se kallonta kawai yakeyi. jawo hannun nabeelah aunty hafsat tayi, tace "zauna ki kyalesu kawai aunty nabeelah wannan cin fuska dame yayi kama..." Aunty hafsat ta fadi a matukar hasale. Aunty nabeelah ta koma ta zauna yayinda heart beat dinta ya chanza Nan da Nan, duk ta zaku taganta gata ga Aeezad, ji takeyi daman zama aljana domin taje ta gansa. Ba jimawa doctor Nazir ya sake fitowa daga dakin da Aeezad yake. Hajiya rafi'ah na ganinsa tace "Kaje kajin kou? Ai nagaya maka na'eema yakeson gani, yo was yakeda ita a duniya bayan na'eema matarsa..." Na'eema Kam na gefe se Wani cika takeyi tana batsewa ita a dole game miji tanata Wani fankama da uwar kibar fuska kamar fanke yaji yeast a cikin man gyada,se Wani feelings takeji jiya zuwa yau dinnan , ganin uban manyan mutanen dasuka taru a asibitin manyan kasan kuma wai duk sbda mijinta, bata tabbatar mijinta bana wasa bane se jiya zuwa yau. "Nop ba na'eema yace ba am sorry hajiya.... please in akwai nabeelah a Nan mara lafiyar yace ta shigo Dan Allah, ita kawai yakeson gani , tin farkawarsa sunanta kawai yake kira, inma bata Nan a kirata cikin gaggawa Dan Allah in har ana bukatar saituwar Brain din mara lafiyar please, ku temakemu a kan aikinmu, dajin yadda yake Kiran sunanta ita ta musamman ce a garesa da sunanta ya bude bakinsa, yanzuma yunkurin tashi yakeyi wai ze fito ya duba yaga ko ita nabeelarh tana Nan din, Danya kasa tashi ne da tini ya fito da kansa wlhi..." Cewar doctor nazir. Saadatubintuabdullahi NAMIJIN ZUMA PAID PAGE 15 *This book is 1k 08101626484* "Baka jiba kenan danagaya maka...bari in kara fada maka da babban harshe, Kaf danginmu babu wata nabeelah,! Sede cikin masu aiki marasa lasisi hajiya rafi'ah ta fadi Yayin datakeji kmr ta rufe doctor nazir dake tsaye da duka, Tas hajiya rafi'ah tagane wace nabeelah Ake nufi, Amma tayi kmr bata ma San wata halitta wai nabeelah ba, ta kudirta a ranta inde tana gurin wata nabeelarh banza bata isa ta shiga ba. A bangaren Na'eema Kam se yanzu ta fahimci nabeelaeh da Ake nufi, ita fa a rayuwa ma ta mance da wata nabeelah tinda ta koma gidan Aunty hafsat na'eema ta mance ta ita gabaki daya, koda taxo ma bata kula da wata nabeelah ba, se yanzu da Dr Nazir yayi maganarta ta ganta daga can gefe ita da Aunty hafsat Wani irin bakin cikinta ya tokarewa na'eema zuciya ji tayi tamkar ta karasa ta jawota ta shakure, haka kawai taji kiyayyar datakewa nabeelah ada yanzu ya ninku tayi doubles. Zaks dake gefe ya zubo ma hajiya rafi'ah Ido da Aunty nabeelah, be tabbatar hajiya rafi'ah bata da kirki ba ta wuce inda ake fadarta ba se jiya zuwa yau, Zaks ya kula a lamarin hajiya rafi'ah harda jahilci ke dawainiya da ita, shi tinda aka kawo Aeezad asibitin yazo asibitin baya hayyacinsa har yanzu ya rakube gefe yanata tunanin a Wani hali
Chapter 29 · 0% Book details