← Book details Namijin Zuma Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 71 OF 87

Sashe 71

Namijin Zuma Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

mutane suke ta serving mutane, hajiya mommy na bakin cikin nabeelah ta zauna, duk inda tayi seta bita da Ido, a ranta kawai bata yadda da ita ba,, nabeelah kanta a tsorace take ga uban ciwo jikinta nayi kafafuwanta sunyi Wani him, sun kumbure, Cikin jikinta yayi lakur saboda azabar yunwa SE a hnkli yake wutsil wutsil Daman a gida haka takeyi in taci abinci se ya hau motsi Sosai in tanajin yunwa se yayi lakur. DUk abubuwan da takeyi hankalinta na kan tunanin Aeezad ta tabbatar yanacan ya kusa hauka,ko seconds yayi beji taba zarewa yake neman yi, Ina maga wuni da kwana gashi Amma Kuma Wani wunin. Allah-allah nabeelah take ta bar gidan Amma Ina ranar ma Nan gidan ta kwana sbda bakin Basu watse ba wasu se jibi zasu watse Yan nesa kenan, wasu ma Yan kusan ne Amma Nan zasuyi sati daya sbda duk sun gama da mazajensu ba yadda zasuyi, itafa Hajiya mommy bata kawance da macen da namiji ya Isa da ita, sede tayi kawance da macen data isa da namiji. Daren Wannan ranar ita knta nabeelah gaza baccin tayi Sbda tunanin halin da mijinta yake ciki, ga ciwon ciki, gana baya, gana jiki Sbda azabar gajiya, duk de jikin ma ya mata ba dadih kmr ba nata ba. A gidan Aunty hafsat Kam Aeezad nata kira, tin tana daukar tana masa karya, harta kashe wayar kawai Sbda ta rasa ma yazata ce dashi, harga Allah bazata iya gaya masa inda nabeelah take ba, Sbda tsoro, Se Yanzu take datasanima da gaya masa gaskiya tayi tin farko,tana kashe wayarta ya fara Kiran lambar big Hajiya, nanma Aunty hafsat ta dauki wayar ta kashe, big Hajiya se matsifa takeyi, da ace zata gane gidan rafi'ah da tini ta tafi, Sbda de kawai bazata gane bane gashi Kuma aunty hafsat taki kaita ko barinta ta fita ma taki,. haka suka wuni a falo jungum jungum, suna jiran dawowar nabeelah Amma Shiru har dare , gabaki daya se hankali ya kuma tashi, Daman 2days din takeyi in taje gidan ko 1day, Amma Yanzu se aunty hafsat ke gani kmr an gane cikin jikin Nabeelah ne,. Ranar ko part din baban Noor bata jeba, sede tace masa mgni zatasha ta kwanta kawai a part dinta. Nan falo suka kwana zaune, aunty hafsat ta rasa yazatayi tunaninta ya kasu kashi kashi. big Hajiya tasakota gaba da matsifa da bala'i, gani takeyi kamar lefin tane, se fadi takeyi "Meyasa Baki tasoni ba?ai da dakikaga zuwan rafi'ah ni dase ki tasoni Ina dai-dai da ita a Wannan Karan bazan daga mata kafa ba wallahi bazan bata fuska ba, daman insda cikinta,bata isa ba tayi kadan, ga dumbin rashin imani rafi'ah yarinya da ciki kusan wata takwas a wata takwas kadan ne babu, Nan a asibiti ko wahala ance ba aso tadingayin aikin whla,, saboda Allah fa, wlhi da lefinki hafsatu da lefinki, Allah yasani, Yanzu in mijinta yadawo miza ace dashi? Ubangiji ya Allah ka tsare cikin jikin yarinyar Nan..." Aunty hafsat sede ta rafka uban tagumi ta zubowa big Hajiya ido kawai ,ita kanta tayi nadamar ma bari nabeelah ta fita a gidan, tayi Dana Sani yafi sau dari, se Yanzu take tunanin daman cewa tayi nabeelah bata Nan tana garinsu, itade ubangiji ne kawai yasan ma a Wani hali take ciki yanzu, tashin hankalinta ma Aeezad kwara na big Hajiya DUk me saukin ne, ita yanzu big hajiya maganarta kawai ta cikin jikin Nabeelah ne,, ta tabbatar duk yanayin da suke ciki be kai kwatan yanayin da Aeezad yake ciki ba , shida ma be garin kenan, duk inda yake Aunty hafsat tasan hankalinsa yanacan a tashe,. A bangaren Aeezad tinda ya kira Aunty hafsat yaji ta kashe waya hnklinsa ya tashi ya kira big hajiya itama bugu daya tayi aka kashe wayar, Nan take zuciyarsa ta Kuma tsinkewa, yashiga tunanin ko Wani Abu ne yasamu mommynsa, yayi innalillahi wa'inna ilaihirrajun yafi sau dubu, ji yake zuciyarsa na mugun bugu kmr zata fashe, a jikinsa yakeji Wani Abu yana faruwa da bangon zuciyarsa wato mommynsa , tunanin meya sameta da yayi yafi dubu? Kawai de ya fahimci dole Wani Abu ya samu mommynsa, aunty hafsat Kuma taki gaya masa, tabbas akwai abubuwan da take boye masa, shi komade mutuwa tayi ne mommy tasa? Se Kuma ya girgiza kai, yasan da mutuwata tayi dole ne a kirasa a gaya masa,. Ya kira wayar nabeelah data Aunty hafsat data big hajiya yafi sau dubu uku,. Wuraren karfe daya na dare ya fara tunanin barin garin zuwa garin katsina, Zaks ne ya dakatar dashi da kyar,ya dinga basa baki,, duk abubuwan dake faruwa Zaks na gefe, shine ya dinga kwantar masa da hankali kan ya bari giobe sesu kama hanyar zuwa katsina,. Gabaki daya Aeezad ya fita a hayyacinsa, Idanuwansa sunyi red sosai, ga uwar rama yayi, a lokaci kankani, tin randa bejita ba , har Yanzu ko ruwa be shiga cikinsa ba, bakinnan nasa yayi fari fattt, labbansa sun bushe rakayau idanuwansa sunyi narai-narai sun kankance Sbda damuwa, ji yakeyi kamar ya fashe da kuka,ya tabbar in Wani Abu ya samu mommynsa tabbas seya kusan mutuwa, shi da a taba masa mommy kwara shi a tabasa, da asa mommynsa kuka kwara shi asashi Kai inda halima a kashesa ko a nakasashi, duk ze dauka inde a kan mommy ne,.har bugun zuciyarsa ya chanza,haka ke kara bashi tabbacin Mahadin zuciyar tasa Bata cikin koshin lafiya. Be bar Kiran Aunty hafsat ba, da big hajiyar da lambar mommynsa, har safiya kamar yasamu aikinyi, haka ya kwana kira wlhi ko gajiya bayayi,Kuma amsar daya ce duk wayoyin kashe suke.washe gari tin adubah yaso subi fly suje katsina , sede an tashi da yanayin hazo, ta yadda jirgin sama bazeyu ya tashi ba,har wuraren karfe daya, Aeezad na Jira yaga ko hazon ze sauka Sbda bayajin ze iya bin mota zuwa katsina, gani yake kmr ze shekara a hanya basu isa ba. kawai jirgi yakeso yabi, duk lissafinsa ya kare Sbda baya hayyacinsa, ji yakeyi kmr ya kulle idanuwa ya bude ya gansa a gidan Aunty hafsat yaga meke faruwa da mommynsa. "Zaks aunty hafsat batamin adalciba...in Wani abu ne ya faru da mommyna,kwara a gayamin , kaga Yanzu fargaba na neman kasheni wlhi ji nake kmr zuciyata zata buga, mommy kawai nakeso nagani, wlhi inaso inga mommyna zaks, ko jinta nayi a waya baze wadatar Dani ba, so nakeyi kawai na ganta, mutuwa zanyi in Wani Abu ya samar min ita, wlhi har Aunty hafsat bazan bari ba in Wani Abu ya samu mommyna, saboda da gan-gan, ta kashe wayarta Kuma na tabbar tana sane, tinda harta amshi ta big Hajiya ta kashe again,,gaskiya akwai matsala! Akwai Wani Abu ba asone a gayamin kawai zaks,,Amma Ubangiji na Nan,insha Allahu mommyna tana Nan da Rai ita da babyna na cikinta..." Aeezad ya fadi da disasashiyar muryarsa wadda ta narke Sbda tashin hankali, da tsantsar fargaba, Ya kalli Zaks, wayarsa na hannunsa still se Kiran aunty hafsat yakeyi da lambar big Hajiyar data nabeelah shiru har yanzu, hankalinsa yafi na uban kowa tashi a ranar haka yake gani,. Cikin muryar kwantar da hankali Zaks yace "Karka damu Aeezad insha Allahu alkhairine, ka kwantar da hankalinka Dan Allah .." murya kmr ze kuka ya amshe da "ta yaya zan kwantar da hankalina? Eheee ta yaya zan kwantar da hankalina? Kai kasan tashin hankalin da nake ciki kuwa? Wallahi kwara ace mutuwa nayi na huta da Wannan tashin hankalin da nake ciki for now mommy fa? Mommyfa akace zaks ? Banganta ba, banjita ba, wlhi hauka cewa zanyi zaks!! Almost 3days yau banji mommy ba' wallahi fashewa zuciyata zatayi zaks! Rayuwata na barazana Zaks! Ji nike kmr ruhina ze fita daga jikina! aeezad ya karashe Yana Zamowa daga kan kujera ya zauna dabau kan tiles , Nan da Nan se wasu zafafan hawaye suka wanke masa kumatuna , ya kasae kwallah tinda abun ya faru se yau yasamu yayi. Kawai se bulbula hawaye keyi daga cikin idanuwansa. Zaks dashima yakejin kmr ya fashe da kuka,ya zamo kasan tiles din ya sharema Aeezad hawaye da rigar jikin zaka din ta shadda fara sol. "Wallahi mommy, ni mommy kawai, Zaks mommy kawai nasani a rayuwata, ji nakeyi yanzu kamar nayi hauka? Dan Allah ka dafemin zuciyata karta fashe..." Aeezad ya kara fadi still Yana kukan me tsuma zuciya kamar karamin yaro, duk yadda kakaiga rashin imani dole ka tausaya masa a yanayin da yake ciki a hslin yanzu . se uban bugu zuciyarsa keyi, ya kamo hannun Zaks ya daura a kan saitin zuciyar tasa,yayi dana sanin dawowarsa garin kano yafi a kirga, se yaji daman ma ajiye aikin yayi kawai da wannan tashin hankalin da yake ciki. Duk dakiya irin ta Zaks seda yayi kwallah shima Amma ya share, yashiga lallabar Aeezad da ban Baki cikin kalaman kwantar da hankalin,Amma Ina Sam beji yariga yayi nisa , yayi nisan da baya sauraren kira. Kawai zaks yace su tashi su hau car su kama hanyar zuwa garin katsina wuraren karfe daya da Rabi. Suka hayo mota dreva yajasu yayinda motocin sojoji takai mota ashirin suka kamo hanyar zuwa garin katsina, a motar ma Aeezad Se kwallah yakeyi Yana sambatun Kiran sunan mommy, shi inde a kan Aunty nabeelah ne bashi da dauriya ko kadan, karamin yaro ba koye ma yafisa hkri da juriya a kan mommy. A bangaren nabeelah washe garima haka ta wuni tsaye gashi ba baccin kirki tayi ba, ga jamaah makis a gidan an taru a Falon hajiya mommy kawayenta ne kawai cike taf da Falon se Na'eema da kawarta khady suna cikin manyan mata, sunzo zasu tashi hajiya naja'atu tace "Aah yarana ku zauna Ayi hirar daku ai kuma kawayenmu ne, duk wacce keda diyya mata ai kawayenta ne,,," nande suka zauna dasu aketa hiraraki Amma basa Sako baki sbda hirar tafi karfinsu, domin kuwa manyan mata sub fisu San mazajensu, Rabin hirarsu duk aKan mazajensu ne, tsofaffin mata ne marasa tarbiya Kuma marasa alkunya... Basu da girma Sena jikkunansu, manyan mata ne kowacce ta kama kasa,wato sun kama gidajen mazajensu sun rike gam se yadda sukayi da maza, saboda shige shige da azabar shaye-shayen magungunan mata (Ko a cikin dubu macen dake Shan maganin mata
Chapter 71 · 0% Book details