← Book details Matar Taj Part 2 Complete Hausa Novel. Local reading mode
CHAPTER 58 OF 66

Chapter 111

Matar Taj Part 2 Complete Hausa Novel. · about 23 min read

Kamar ana jan kafarta tana goge hawayen fuskarta hannunta na rawa tsabar bacin rai haka ta nufi part din taj, da wani kuduri aranta, as’usual part din na bude ta samu shiga kai tsaye ta wuce sitting room sannan ta haura sama, babu wani darr aranta.
Tana hawa saman tayi knocking daya biyu daga ciki ya amsa da come in don a tunaninshi ko me gyaran part dince.
Kai tsaye ta bude babu ko sallama, ya gama shirinshi kenan zai futa ya zauna bakin gado yana kokarin saka wrist watch dinshi akayi knocking din, bayan ya bada izinin shigowa baima dago yaga ko wayene ba yaji muryar maya.
“Inason magana dakai…
Ahankali ya dago da mamaki ya ganta tsaye idanunta sunyi jaa sosai, jikinta har wani rawa rawa yake,
maida hankalinshi yayi ga abunda yakeyi yayi kamar baisan da ruwan mutun a wajen ba, ganin haka yasa ta soma takowa “stop right there”
Ya dakatar da ita, “fadin abunda ke tafe dake daga nan”
Wani abu taji ya tokare mata a maqogaro, shima zai nuna mata iyakarta kenan? A harzuka ta soma takowa tana danne abunda ke taso mata ta hana kanta hawaye a daidai lokacin shi kuma ya miqe tsaye, ya mata wani irin kallo dayasa tasha jinin jikinta.
Abunda taso yi ta kasa kawai ta sauke idanunta kasa hawaye ya soma sauko mata, yanajin tana sheshekar kuka nan yabita da kallo da mamaki.
“Dan allah karka gujeni, idan duk kowa ya nuna baya sona karka qi ni, wallahi ina sonka uncle taj, inasonka sosai fiye da raina, ka taimakeni ka aureni,”
Ta karashe tana kallonshi, shima kallon nata yake sai yaji wani dan tausayinta ya ratsa shi, da ranshi harya soma baci sai kuma data fara kuka yaji bacin ran ya tafi, bayason ganin mace na kuka ko kadan, a sanyaye ya kauda idanunshi sannan yace “stop…crying, clean those”
Ya fada yana mata nuni da fuskanta, wani irin sanyi taji aranta, plan dinta is working,
“meke damunki? Who hate you?” Ya tambayeta a natse.
Daga yanda yake magana ta gane cewa ya danji wani abu game da kuka nata, so shes going to play a victim game, don ya tausaya mata.
Matsar kwalla ta sakeyi tare da sunkuyar da kanta, sannan tace
“Kowa, duk basa sona sunfi son wannan munafukar, ta rabani da kowa, sanadiyarta kowa baya sona”
Tunda ta soma maganar sabeeha yaji bacin ran nashi ya dawo sabo haryama wanda ya fara ji data shugo mashi daki babu sallama, babu gaisuwa kai tsaye.
Wato daga yanda take magana ya hango jealousy, da bakin ciki a cikin magan ganun nata, harma da rashin kunya a ciki, don harda anne ta sako a maganar tana fadi mashi yanda dama chan ba sonta take ba, banda rashin hankali irin nata bai kamata tace sabeeha ruined her life ba ta rabata da kowa hasalima sanadiyar chanzasu da akayi ne yasa sabeehar ta shiga rayuwa mai kunci, rayuwarta ta gaza inganta saboda rabata da akayi da asalin iyayenta ita kuma akayi replacing dinta a matsayin sabeehar.
Kwata kwata bata dago taga yanayin da yake ciki ba take ta zuba, trying to make him pity her, nanko ta tabo inda bai kamata taje wajen ba.
“Youre ungrateful” ya fada rai a bace sai a
Lokacin tayi saurin dagowa ta kalleshi saida gabanta ya fadi kuwa, ranshi a bace ya cigaba “are you trying to blame her for what your biological mother did? Did fatima hate you for being on her seat this whole time, did you even know what she had to go thru????” Ya sake jefo mata tambaya trying to add sense to her brain don yaga yarinta ma yana daya daga cikin abunda ke damunta bayan she’s being brutally selfish.
“Instead of you to be grateful?”
Bakinta ta soma motsawa tana hawaye, “yess because saboda ita na rasa komai, kowa fatima fatima fatimaa…i hate her, i wish ta dade da mutuwaaaa…”
nuni ya mata da kofa, baice komai ba tsabar bacin rai amma tasan abunda yake nufi, jikinta na rawa ta kalleshi tana tattara courage din yi mashi magana a wannan yanayin “whys everyone siding on her?? Meysa ka tsaneni Uncle taj?”
Bai sake kallonta ba ya nufi hanyar futa tayi saurin shan gabansa, without any second thought ta soma kokarin zare veil din dake kanta sannan ta soma kwance igiyar rigarta, a tsorace take dashi amma wani confidence takeji kawai nayin abunda yazo ranta.
“Wallahi zan iya baka komai, har kaina zan iya sallama maka,…” ta karashe tana kokarin sauke rigar tata kasa taji saukan mari tasss akan kuncinta ranshi a mugun mugun bace, babu abunda ya tsana kamar yaga loose mace, musamman wannan yarinya qanqanuwa.

Ay baisan futsararriya bace ta karashe sai yanxu, bai iya dukan mace ba ammada da akwai belt a jikinshi babu abunda zai hanashi zaneta, a very young girl like her har tana iya yin tunanin sakin jikinta to a man? For the fact yana matsayin uncle dinta, ranshi inyayi dubu ya baci sosai ba kadan ba hannunshi har karkarwa yake ya mata nuni da yatsa “before i count to 3, if i dare see any sights of you here, you’ll regret it”
Ay ko marin daya mata yasata gama shiga hayyacinta, tayi saurin maida rigar jikinta a furgice ta futa tana kuka.
He feel so disgusted, ranshi yayi mugun mugun baci, irin yara kamar wannnan abun tsoro ne musamman a cikin ahali babba kamar haka, she can go to any extent don ta samu abunda takeso, kuma ko kunyar idanunsa bataji ba, bayason yayi making abun as an issue but zai iya zaneta sosai akan wannan don ya ladab tata.
A furgice ta futo ta wuce part dinsu, tana shigowa as usual ta tadda basira na goge goge, tabi takan ruwan mopping din ya bare rai a bace ta wuce sama, basira ta kalleta ta bita da harara “mai baqin hali, mteww dama ance abunda ka shuka shi zaka girba, waye zai taba tunanin kece yar hadiza, kai allah ya wadai, itako sabeeha babu ruwanta halinsu daya da hajiya ashe shiyasa ma babu ruwanta saboda itace yarta ta asali bake ba yar masu da fadin rqi da izgilanci,mtewww”
Haka nan ta dingi kwashe ruwan don harya jiqa carpt din walkway din wajen.
Maya na shiga daki ta soma fashe fashen data saba tana hawaye, gana daya turartukanta dake kan dresser saida ta fashesu duka har hannunta na fidda jini, kamar wadda ta haukace haka ta miqe ta soma watso kayan wardrobe dinta hartayi nasarar daukan wani box irin na jewelry box haka dake boye a wajen, ta bude shi, take kwayoyintabda kayan mayenta suka bayyana a ciki, ba tare da wani tunani ba ta fiddosu ta aje bakin gado, ta fara ambulawa cikinta, kan kace me kawai tayi over dosing kanta sosai, muyagun kwayoyi ne da shansu keda hadari sosai don har mental asylum yana iya kai mutun idan ya zama addictive kuma ya fara taba kwakwal.
Tana layi ta zaro wata allura ta dura a cikin syringe sannan ta chaka ma kanta tana gamaqa ta soma sauke ajiyar zuciya ahankali hankali chan kuma ta bange dipp.

Acahn wajen taj kuwa bayan futarta haka ya futo ranshi a bace zuwa main house yana shiga ya wuce part din nanna, suka gaisa, ta tambayi jikinsa yace mata da sauki, ya futo ya wuce part din anne don achan zai karya, yana shiga ya zauna, fadila ma na part din annen suka gaisa dashi tasa laila karama tayi serving dinshi abunci yaci anan parlor.
Yanaci suna hira, shida anne sama sama,har ta tambayehsi jikinsa don nannna tace shima zazzabi ya hanashi zuwa yin breakfast yace mata da sauki, fadila tayi murmushi tace “abun naku kamar hadin baki kaida fatima, itama haka ta tashi da zazAbi saida aka hada mata allurai ma allah dai ya kra sauqi”
Yayi shiru baice komai ba, yana tuna abunda ya faru dasu jiya da daddare, ya gama deciding situation dinsu shida ita, daman shima bawai so yake asan da aure a taakaninau ba don idan nanna tasan irin rayuwar dayayi a baya she will be heart broken, bama ita kadai ba.
And har yanxu yana jin guilt din abunda yayi ma sabeehar da yanda ya qulaqantata a chan saudiyar aftwr all he has done for her.
Yana cikin wannan tunanin anne tace “ inka gama ga shiga ka dubata, nasan ta farka yanxu ko?”
Fadila ta dubi laila tace “yanxu kika fito daga dakinta ta farka kuwa?”
“Ah ah mami tana tare da mummy ma sanda na fito amma bari na sake dubawa”ta amsa sannan ta futa daga dakin.
Bayan ya gama cin abunci ya fito daga part din anne har zai sauka kasa kuma ya dakata, yana mai duban bangaren sabeehar, samun kanshi yayi da shiga part din da sallama, sabeeha da farkawanta kenan laila na zaune gefenta while bahijja ta koma part dinta don ta mata corn chicken soup da zata dan sha.
Tana jin sallamanshi gabanta ya wani irin fadi dam, saiga kamshinsa ya biyo baya wanda laila tunda ya shugo dazu taji kamar kamshin sa taji a dakin sabeeha,ba ita kadai bama hatta bahijjar saida taji wannan kamshin.
“Bismillah uncle taj” laila ta fada ahankali, sabewha kuma ta kauda kanta zuwa gefe,
Zama yayi wajen cute resting chair setting din da akayi a gefe yana fuskantarsu.
Gaba daya wajen saiya zama awkward, laila ta dubi sabeeha data hade ranta tayi kamar batasan da zuwanshi ba kasa kasa tace “madam yadai? Yazo dubaki”
Yi tayi kamar batajita ba wanda duk hakan akan idanunshi akayi, ya dubi laila da itama a lokacin ta dago karaf suka hada idanu, wani irin signaling yayi mata da ita kanta batasan yanda akayi ta gane me yake nufi ba wanda yasa ta tashi ta zura flats dinta sannan ta futa, sabeeha har zata mata magana sai kuma tayi shuru kawai wajen ya dauki silence.
Sun dauka wajen minti biyar a haka baice qala ba haka zalika bata dubeshi ba, ya kafeta da idanu, she looked so pale kamar wadda tayi jinyar kwanaki, ta wani hade rai sosai tama qi yarda ta kalleshi, saiya kara jin haushin kansa for what he did yesterday, urge dinshi zai kaishi ya baroshi,

a sanyaye ya soma magana kamar bashi ba” “Fatima!!…” ya kira sunanta datajishi har tsakiyar kanta, amma bata juyo ba balle ta kalleshi, saima runtse idanunta datayi sannan ta fara kokarin tashi, “i’m sorry….bibi” ya fada yana kallonta, ganin tana kokarin barin wajen ya sashi cewa “are you upset with me???” Ya sake jefo mata tambaya, bata tsaya sauraronsa ba ta tunkari bathroom, maganar dayyai yasa ta tsaya chak.
“Inada nawa dalilin dayasa ban rabu dake ba,kuma naqi rabuwa dake tun bayan tafiyarki,”
Ya dan dakata bai cigaba ba, ita kuma abubuwa da dama na yawo aranta at the same time gabanta na faduwa, what could be the reason? Tunda tasan basuyi rabuwar arziki ba, sannan kuma bayan ya dawo nan allah yayi haduwarsu cikin inuwa daya maisa bai rabu da itan ba? What could be the reason?” Ta tambayi kanta kafin ta bama kanta answer “Propably beacuse yanajin guilt din abunda yayi min bayan yamin korar wulaqanci, daga baya kuma ya gano cewa nice mai gaskiya amaimakon yan uwansa” ta karashe tana jin wani abu na tokare mata a maqoshi, ko da wasa bata kawo tunanin wai ko maybe he has something for her ne ba.
Rai a bace ta juyo, “idan har kanada naka dalilin naqin rabuwa dani a lokacin yanxu babu wani dalili, let’s just ends this”
“Sure!!!” Ya fada kai tsaye, yana takowa har inda take tsaye amma nesa da ita, take gabanta ya fadi,ta kafeshi da idanu shima ita yake kallo.
Hannunshi ya daga ahankali ya dora kan gashinta yana dabbing din kan nata kamar wata yar pet yace “bansamu damar yin haka ba a lokacin daya kamata amma yau zanyi…FATİMA thank you for being part of my life, thank you for standing with me, thank you for protecting Tajudeen that was blinded by evils, thank you for caring for the tajudeen that was helpless, kin haskaka rayuwata a lokacin da komai ya zamto min duhu ne”
Take jikinta ya soma rawa hawaye ya soma sauka akan fuskarta tana kallon cikin idanunshi kamar yanda yake kallon nata, it was a tough moment for him but tougher for her don wani abu takeji a cikin zuciyarta da ta kasa fasaarashi, fargaba ko tsoro? Ta kasa tantance menene
Hannunshi har zuwa lokacin na kan gashinta yana caressing kan nata kamar yar kankanuwar yarinya.
Saitaga sak didin ta, didin data bari achan saudiyya, didin daya kasance shine pillar kuma source of comfort dinta.
Hawayenta daya gani shi kansa yayi confusing dinsa, yana tuna mashi da rayuwar da sukayi da ita achan saudiyyan.
Har zai bude baki yayi magana kenan kawai sukaji motsin kofa za a bude, laila data fara hango su tayi saurin daga murya tace “mummy let me help da wannan”
Cikin hanzari ya dan matsa gefe sabeeha tayi saurin juyowa taga laila na kokarin karban tray din hannunta, cikin sauri ta soma goge hawayen fuskanta.
“Au tajudeen ashe kana nan, kazo dubiya ne kaima”
Gyaran murya yayi ya dubeta sannan ya gaisheta, yanayin shi gaba daya ya sauya, badan shugowarsu ba da yayi abunda he will regret for the rest of his mind.
Kallonta bahijja tayi sannan tace, “oh no…, mun barki ke kadai ko dear”
Tana kokarin boye yanayin da take ciki muryanta ciki ciki tace “No mummy ba komi, daman zan shiga bathroom ne”
“Muje na taimaka maki” bahijja ta fada tana kama hannunta with so much care.
Suna wucewa taj ya sauke ajiyar zuciya sannan ya futa daga dakin laila ta bishi da kallo.
Yana futa ya fuce daga gidan gaba daya, dan ko dinner bai samu anyi dashi ba a gidan.
Sabeeha ko tun bayan zuwan da yayi harya fits gaba daya kamar ya tafi da tunaninta ne, haka kawai ta kasa natsuwa maganganunsa na yawo a kwakwalwarta.
Bahijja taso su koma chan part dinta amma tace mata ah ah tafison nan, nan fadila tace ma laila tazo ta tayata kwana anan, daddy ma yazo ya sake dubata kuma suka sha hira shida ita kamar koda yaushe, kai kamar ma shakuwaraa da sabeeha yafi wadda ke tsakaninta da bahijja, he’s her total comfort zone, shima kanshi yanda yakeji game da sabeeha bai taba jin hakan da maya ba, wani irin connection ne tsakaninsu da yakeji da ita sosai, murnarsu da farin cikinsu daya shine yanda suka lura allah ya tsarkake masu diyarsu bai barta ta wulakanta ba ko ta kaucewa hanya, sabeeha akwai hankali, ladabi, biyayya, natsuwa, a yanda ta taso cikin rashin kulawa da muzgunawa da hadiza ta mata badan ikon allah babu abunda zai hanata lalacewa ta shiga duniya ko ta kasance futsararriya mara kunya da sanin ya kamata sai allah ya nuna karfin iyawarsa na qin barin hakkin wani ya hau kan wani.

Har wajen karfe daya tana daga zaune ta kasa barci, laila na daga gefenta tana barcinta hankali kwance.
Ganin ta kasa samun natsuwa a zuciyarta yasa ta tashi ta dauro alwala ta fito ta tada sallah.

Bangaren maya tana chan a mangare kamar matacciya, abun har ya kaita ga yin miyagun allurai da tasan zai lalata mata rayuwarta allah ya shirya mana zuri’a.

After 2 days, yau ta kasance sunday, su sabeeha na shirin komawa school, alhamdulillah taji sauqin jikinta sosai ba kadan ba, rabonta da taj tun ranar nan, har fargabar haduwa take dashi, don ranar badan mummy ta shigo daki ba maganar su bazata tsaya daga nan ba, har zuwa lokacin tanajin wani irin yanayi game dashi, daya kasa fasaarawa, duk wannan haushinsa da takaicinsa da takejin tun bayan abunda ya mata a saudiya lokaci guda taji ya wanye tun da sukayi maganar nan, idan ta zauna saitayi shuru tana tunani, amma fa bata yarda kowa yasan tana cikin damuwa ba musamman bahijja data tare a part din annen, don anan take wuni sai dare take komawa main house.
Alamarin bahijja da anne kuwa Sanadiyar diyarsu ita da majeed yasa anne ta aje komai a gefe dama chan bawai ta tsanesa bane kawai dai tana jin zafin abunda ya faru ne a baya sanadiyar aurensu.
Bangaren maya ko tundaga ranar nan datayi allurar nan wadda cikin kawayenta wata tayi mata introducing allurar, tundaga lokacin ta aje syrups da take sha wasu kwayoyi ta koma durama kanta allurarnan, ta gama isolating kanta gaba daya, wanda bahijja ta kasa controlling dinta akai,tsakani da allah har zuwa lokacin bata fasa nuna kulawa ga maya ba, kuma tana sonta har cikin zuciyarta amma allah bai nuna mata wannan sabuwar hanyar da maya ta nufa ba.
Misalin karfe sha biyu duk suka futo, domin zuwa shopping, babu yanda bahijja batayi akan maya ta shirya ta bisu amma ta shiada mata bazata iya zwa ba kanta na ciwo,wannan yasa ta barta kawai, sai laila ne ta futo suka wuce da sabeehar hamad zai kaisu.
Tunda suka fito sabeeha taji wata ni’ima ta ratsata kamar yanda suka saba itace a gaba tana daga zaune laila nata zuba masu surutu, hamad kuma jefi jefi yake kallon sabeehar datayi shuru.
Sun dade wajen shopping, laila ta jidar masu abubuwa kamar babu gobe hanad ya biya suka fito suka wuce saloon aka gyara masu kai akayi ma sabeeha kalba, silky jajan gashi ya sauko har kwankwasonta masha allah, laila sai faman sha’awar gashin take tana rokon dama itama tanada gashi haka kamar na sabeeha, totally yarinyar halfcast ce, yanxu dataji gyara asalin ta yake bayyana sosai.
Ana gama masu akayi masu pedi and medicure, kai spa dinma badai haduwa ba waishi blushup_beauty, nan ceo din hajiya rukky tayi masu introducing sabon installment da sukayi na gyaran jiki, kuma da suka kasance vips akwai discount da za a basu specially for them, laila data kasance itama yar gwalli take tacema sabeeha suyi, kudi ba matsala bane ba kawai dai suna tsoron batama hamad lokaci wannan yasa laila ta kirashi a waya sabeeha ta rokesa ya amince sannan aka fara masu gyaran jiki, body polish ne, waxing ne, dukhoon steam duka babu wanda ba ayi masu ba Masha allah, kowaccensu ta fita tarr tarr musamman sabeeha da idan ka ganta zaka rantse kamar an sauyata ne ta koma kamar kaza yar shila da aka ciro daga gashi masha allah, fatarta wane ta jariri, har wani yellowish milky haske tayi, kai mace da gyara ba a cewa komai, su kansu matan wajen yabawa sukeyi da kyanta da kuma fatarta,ana gama masu sukayi payment suka fito hamad na jiransu.
Wallahi tunda ya sanya idnaunshi kanta ya kasa daukewa, tun daga nesa ya hango yanda tayi wani extra dashing kyau,sai faman kyalli take, suna shigowa motar kuwa kamshinsu na dukhoon by @amrukt_incence ya bade gaba daya matar ya hade da sanyin ac, ay saida ya lumshe ido ya bude ya kalli sabeeha da itama shi take kallo a lokacin don gaishesa tayi bai amsa ba saboda ya tafi.
“Whats with this lovely scent?”
Laila tayi dariya tace “sirri ne yaya…kaima ya tafi dakai ko?”
Wani irin kallo ya mata tare da harara dayasa ta guntsw dariyarta suka futa daga harabar wajen.
Basu suka dawo gida ba sai gab da magrib, suna dawowa kafin su akiga shiga gida call din bahijja ya shugo wayar sabeeha data riketa a hannu, duniya dadi, bata taba tunanin rike irin waennan wayoyinba sai yanxu, allah sarki rayuwa, irinta wadda taj ya bata tana nan ajiye tunda ta kasheta bata kunna ba.
Kai tsaye suka wuce part din bahijar da sallama, lokacin tana kitchen futowar kenan, tana ganin sabeeha tace masha allah lakuwwata illa billa sannan ta sumbaci goshi ta tace “gaskia wannan saloon dole nayi sponsoring kaina a wajen, haka suka gyara min diyata, wannan kamshi haka kamar amarya”

Dariya laila tayi tace “mummy ay wallahi sun iya gyara sosai, just look at skin din sabewha kamar an bareta a leda saima kinga kalaban da aka mata”
Sabeeha tayi dariya tace “mummy itama bakiga nata ba yayi kyau soaai”
Murmushi bahijja tayi tana mai shafa fuskar sabeeha tace “allah ya maku albarka, kuje kuyi sallah yau anan zakuyi dinner, kinqi dawowa wajen mummynki da daddy ko? Anne da nanna sun kwace mana ke”
Sunkuyar dakai sabeeha tayi, bahijja na ganin haka tace “kuje dakinki kuyi sallah” da toh suka amsa sannan suka wuce dakin nata dake kusa dana maya, har zaau shiga laila tace bari na leka maya naji meysa bata zo mun fita gaba daya ba.
Sabeeha ta girgiza mata kai kawai sannan ta wuce daki ita kuma ta shiga part din maya, tana ahiga da sallama ta taddata zaune bakin gado ta dora kafa daya kan daya tana taunar gummies, laila ta karaso ta zauna gefen gado “baby gurl how far? Bakizo mun fita ba, ke wallahi wa had alot if fun, kinsan blush ta gyara wajenta, wallahi bakiga gyaran datayi ma sabeeha ba ke kyace amarya”
Saurin dakatar da ita maya tayi idanunta yayi jaa jin ta ambato sabeeha.
“Dallah dakata malamaa….munafuka, annamimiya, ai bansan ke munafuka bace sai yanxu, kinata wani abu saboda ke gaki ga cousin dinki ko? Toh nace maki inason naji me kukayi ne????ay wallahi tunda kika zabeta kike binta babu ni babu ke munafuka”
“Karki sake cemin munafuka maya…”
“An fada din munafuka fooliah idiot, mugaye, ni zakici amana, kuna wasu abubuwa kamar ciki daya kuka fito kina binta?”
“Kwarai kuwa na bita, saboda itace asalin cousin dita, saboda yanda nake tsakanina dake shi zaisa karna dunga kulata kenan? Toh ke asuwa zaki hanani mu’amala da yar uwata ta jini?, ba damuwa ni nazo wajenki shiyasa kike fada min maganar banza mteww” tana kaiwa nan ta miqe, laila bata iya fada ba amma fa idan aka kaita bango itama ba kyalle bace.
Batun yanxu maya ke pissing dinta off ba da abubuwan da take yi yanxu, bata kaunar taga kowa a kusa da sabeeh a infact da an fara maganar sabeeha zakaga tsana karara akan fuskarta ko ta fusata.
Ita sabeehar da ya kamata ace itace kejin haushinta saboda sabadiyarta uwarta ta sauyata, don ita tasha wahala rayiwa ita kuma ta taso cikkn jin dadi.
Laila na fita maya ta miqe tana zarya tsakanin dakin, ji take kamar tabi lailar ta shaqeta itama ta huta kawai.
Laila ko tana futa ta shiga part din sabeeha daidai nan sabeeha ta idar da sallah,ta dubi laila data shugo rai a bace ta tambayeta meya sameta tace mata babu komi wani ne ya bata mata rai a waya.

The next day..
Tunda asuba bahijja ta shugo dakin maya ta tasheta tayi sallah, daga yanda ta tashi a fusace kamar zata zagi bahijjar ko ince ta zagenta ma don kncking din da bahijja ta dunga yi a dakin saboda qin budewar sa maya tayi saboda bugewar datayi yasa ta tashi a harzuke.
Tana ganin bahijja ce ta koma ta kwanta ko gaisheta batayi ba bahijja ta tambayeta meke damunta kwana biyu duk ta sauya, abu kadan fada, tace mata babu komi, karahe dai ma kusan futsara ta mata tace “kije ki damu da yarki, nida ba yarki bace daman ba damuqa kikayi da damuwata ba”
Bahijja was so shock ta dubi maya tace “maya wannan wani irin magana ne babu manners?”
Maya tayi shuru batace mata komai ba, bahijja ta dubeta tace “meke damunki”
Tayi banza da ita, bahijja tayi shuru gabanta na faduwa kafin tace “jekiyi sallah, sannan ki shirya da wuri ki sauko breakfast zaku koma school yau”
tana fadin haka ta futa jiki a mace, bata taba taammanin haka daga mayar ba amma tayi mata uzuri.
Maya ta bita da harara, bayan sabeeha babu wadda takeji tsanarta kamar bahijja, kamar yanda nace maku itafa duk wanda taga yana kaunar sabewha to fa babban maqitinta ne duk yabda take da mutun, bakin bahijja take gani,ko ganinta bata kaunaryi tana ganinta take ganin sabeeha akan fuskarta tunda itace ta kawota duniya, ta manta yanda bahijja ta nuna mata so da kauna kuma ta rike a yanxu data kasance ba itace yarta ta asli ba.
Ay yanxu ta gama sama ranta cewa ba sonta suke ba kwata kwata, kuma nan gaba zasu wulaqantata saboda haka ta dauka kudirin duk yanda zatayi saita mallaki taj, don shi kadai ne power da zata samu a gidan, tayi abunda taga dama.
Komawarta tayi kwanciyarta ba tare da tayi sallar ba.
Misalin wajen karfe takwas daidai suka gama breakfast laila ta shugo part dinsu anne ta tadda sabeeha ta gama breakfast, sallama sukayi ma nannan da anne sannan suka futo suka nufi part dinsu maya, suna shiga sabeeha ta taho da sauri ta rungumi bahijja dake zaune a parlor hankalinta yayi nisa sosai game da tunanin maya, saijin sabeeha tayi a jikinta, wani irin farin ciki taji ya lulubeta ta dubi sabeehar tace “morning diyar kirki kin tashi lpy?”
“Lpy lau mummy”
Laila ma ta gaisheta ta amsa sannan ta tambayesu idan akwai wani abu da zasu tafi dashi idan sunaso sukace mata ah ah, laila na duban time a watch din hannunta tace “mummy maya fa? Zamuyi latti”
Sai a lokacin bahijja ta kwalama basira kira tace ta kira maya, basira ta hau sama ko minti biyu bata yi ba ta sauko kasa ta dubesu, bahijja tace “yadai?”
“Hajiya tace wai bata gama shiri ba su tafi kaqai zata taho daga baya”
“Kamar ya bata gama ba?”
“Eh tana shafa mai ne wai”
Mikewa bahijja tayi ta hau saman da sallama tana budewa ta hangota gaban dresser da waya akunnenta tana dariya, ko shafa man ma bata fara ba, ta karaso gabanta maya na ganinta amma tayi knar bata ganta ba ta cigaba da abunda take, “yea babess” maya ta fada wayarta na kunenta har zuwa lokacin,
Bahijja takai wajen minyi daya a tsaye expecting zata kashe wayar amma bata kashe ba, saida ta karba wayar sannan ta dubi screen din taga an saka sweetness, take gabanta ya fadi amma ta dake ta kashe wayar maya ta dubeta tace “waya fa nake mummy”
“Yes na gani, who’s on the line??”
“Ay kin gani” ta bata amsa kai taaye babu respect
“Maya where are you leading to?meke damunki ne eh??? Answer me”
Miqewa tayi tsaye zata juya ta wuce ta gaban bahijja ta dakatar da ita, “don’t dare walk on me maya!!!!” Bahijja ta daka mata tsawa, “dama kin damu dani ne??? How would you know where im leading tunda tsinanniyar yarki kawai kika sani mteww”
Tana kaiwa nan ta juya batayi auni ba sai jin saukar mari tayi akan fuskarta tassssa, cikin sauri maya ta dago ta dage fuskarta, mamaki ya gama cikata sai hawaye, zqta iya cewa mummy bata taba marinta ba amma yau ta mareta saboda wannan tsinanniyar..
Bahijja na huci taabar bacin rai tace “now get ready na baki nanda minti biyar ki sauko kasa” tana fadin haka ta wulla mata wayan nata kan gado ta wuce rai a bace, tanajin wani abu kamar hawaye na neman sauko mata, she felt ao disappointed akan maya, da bata ganin abunda take kwata kwata amma yanxu kamar an vude mata ido haka take ganin komai.
Tana fita maya ta bita da wani matsanancin kallo, abubuwa da dama na yawo a mind dinta.
Bahijja na saukowa ta taddasu zaune lokacin wajen 8:50 saura, sabeeha tayi shuru tana tuna yanayin data ga maman nata, bahijja na zama kan kujera ta dubeau tace “zata sauko yanxu”
Sabeeha ta dago ta kallwta sannan ta kamo hannunta tacw “mummy akwai abunda kw damunki ne?”
Mumushun yaqe bahijja tayi kafin tace “babu komi baby, na tashi da ciwon kaine”
“Subhanallah, ko zakije asibiti,?”
Ta fada tana taba goshin mummyn with so much care, bahijja ta kalleta sai kaqai taji zuciyanta na karaya tayi kakarin danne hawayen dataji yana neman sauko mata.
Maya kam bata suako ba sai tara daidai, ta saka riga da wando ta aza mayafi akanta, ko kallonsu batayi ba ta fuce, bahijj ta bita da kallo ta girgiza kai, suka tashi sabeeha ta mata sallama suka miqe ita da laila suka fita bhijja ta bisu da kallo.
Toh haka dai aka shiga mota cikin bacin rai maya kamar zata balla kofar motar, hamad ko ta kanta baibi ba don ko gaishesa batayi ba, laila ta zagayo ta dayan side din ta zauna, sabewha kuma tace gaba.
Shuru babu wand ayace sa dan uwansa tak sai laila ke dan nagana jefi jefi sabeeha na amsata har suka iso.
Suna isowa itace ta fara bange motar bayan ta futa, sabeeha ta girgiza kanta kawai sukayi sallama da hamad suka wuce class ita da laila don course daya zasuyi.
Hamad bai dade da wucewa ba wata arniyar mota tazo daukan maya, ta fito daga class ko permission bata dauka ba tayi gaba abunta.
Tana shiga motar salim ya dubeta yana smirking yace “duk yanda akayi akwai dalilin dayasa kika kirani, ive been calling you kina denying, kina tunanin threat din danayi maki da nudes dinki karya ne ko?“
“Let’s go please, i need to relive all of my stress and worries”
Yana jin haka ya wage hakora baiyi expecting haka ba kwata kwata, “as you wish” ya bata amsa sannan yaja motar.
Basune sukayi landing ba sai a abuja continental hotel, already yayi booking don kwananshi biyu kenan yana ta’asarsa son ransa.


MATAR TAJ (destined with you)
   Written by 
          Queenmarh

Book2 
PAID
Chapter 58 · 0% Book details