Chapter 95
Matar Taj Part 2 Complete Hausa Novel. · about 27 min read
Saudi…
Jamid baibar detention center dinnan ba saida hidaya ta fada mashi komai, asalin fadwa yanda ta kashe tareeq saboda shine ya fara sanin sirrinta da kuma bacewar taj, da yanda ta dunga amfani da ita don cinma burinta, dukda itama tana da nata kason a cikin duk abubuwan da suka faruwa.
Abunda yafi bama jamid mamaki shine asalin fadwar, ba yar taheel bace? All those years haka suka dunga venting akan taj, Hating on him, ganging up on him, suka kusa salwantar da rayuwarshi, kuma ba kowa bane kan gaba sai hidayar, ashe shine asalin dan uwanta, fadwa ce outcast cikin su, ta haramtacciyar hanya ma aka sameta, mahaifiyar tasu da suke duk waennan abubuwan saboda ita ashe itace aje masu abun kunya.
wannan babbar ishara ce a garesu gaba dayansu musamman hidayar data dauka tsanar duniya ta dorama taj, ta wulaqanta rayuwarshi ta kusa salwantar da rayuwarshi saboda tsana, bai tsareta da komai ba, yanxu gashi komai ya juye mata, yar uwar datake tunanin itace jininta ta kasance batada alakar ubantaka da ita kuma ta zame mata babbar barazanar.
Shima kanshi bata barshi ba, dukdan sabod aya tsayama taj, yayi protecting dinshi, saboda hakan ta maidashi kamar wani enemy dinta yana matsayin mijinta.
Tunda ya samu paralyze kuwa ya zame mata mara amfani ta fiddashi daga gidan nan ta turashi kasar waje neman lafiya bata sake waiwayarsa ba, Batama san yanda akayi ya samu lafiya ba har yazo gareta yanxu haka, duk tsawon wannan lokacin bashida tunanin daya wuce na taj da sabeeha, saboda shi kadai zai iya fadin wahalar da suka sha a wajenta, makirci iri iri daban daban dukdan akan abun duniya, dukdan saboda taj karya gajesu.
Babu irin maganganun da jamid bai fada mata ba cikin bacin rai sosai, ta kasa magana kwata kwata gaba daya saboda she’s guilty of everything, he vent so much of his anger akanta sannan ya nuna mata ay bataga komai ba, kamar yanda ya fada mata bazata taba sanin zafin abunda tayi ma taj ba sai ya samu nata gashi nan ba a je ko’ina ba saboda abubuwan datayi a baya zai shafi dansu, an innocent child daman duk abunda kayi sai anyi ma naka,, a karshe ma dai fada mata yayi idan har wani abu ya samu dansu bazai taba yafe mata ba.
Aranar daya dawo yaji labarin kamata da akayi tunda abune ba boyayye ba kama ga matsayinta a kasar, ko’ina zai dauka don zai shafi kamfanin su, yayi mamaki sosai, wannan ne yasa yazo don ya tabbatar ma idanunshi don hidaya can never give up so easily he wanted to see why tayi sanyi batayi amfani da tricky connections dinta ba, don zata iya yin komai akan kamfaninsu da kuma ganin duk wasu abubuwa da takeyi bai fito idon duniya ba, ashe ashe ga dalili, ga kuma labarin bacewar taj.
Haka ya futa yabarta zaune, jiki a mace tayi la’asar kamar ba hidaya ba, ta kasa tabuka komai, komai ya juye mata gaba daya bata cikin natsuwarta saboda danta, da tanada hanyar maida hannun Agogo baya da batayi abunda tayi ba a baya, sai hankalinta ya sake tashi sosai, don tabbas fadwa zata iya illatar mata da danta dukda ta bata abunda take nema.
Jamid na barin detention center din, gabanshi na faduwa sosai ya wuce school dinsu direct.
Gaba daya school din yau is busy saboda hutun end of the terms da akayi kuma iyaye nata zuwa daukan yaransu.
Dukda yasan makarantar akwai tsaro sosai wannan baisa gabanshi faduwa ba,at the same time har zuwa lokacin he’s in so much shock.
Ay bai gama samun shock of his life ba saida aka nemi barad a school sama da kasa aka rasa, home school teacher dake kula dashi ta shaida yana zaune a visiting area, don tun safe ake zuwa daukan student, on a blink of eye aka nemeshi aka rasa, jamid kamar zaiyi hauka, school gaba daya ta rikici aka fara duban cctv, abunda suka gani ne ya sake tadama jamid hankali, don footage din ya nuna wani mutumi ne ya shugarda barad din cikin wata baqar mota, home school teacher data gane ko wanene ta shaida masu ay driver din dake zuwa daukansa ne lokacin da yake zuwa day kafin a maidashi prep border…
Jamid was so confused don a lokacin yana kwance baisan meke faruwa ba, baima san wanenene driver ba, tsoronshi daya karya kasance driver nada sa hannu da fadwa…
Waya mutallib ya dauka yayi typing message kafin ya aje wayar ya maida dubanshi ga barad dake zaune, yaron yayi shuru baice qala ba,har suka isa hideout suna isowa mutallib ya bude mashi kofa ya futo.
Dauko yaron baiyi ma mutallib wuya ba saboda yaron ya sanshi, ciki suka shiga yana fatan kar yaron ya tsorata idan yaga khaal don yanada wayo.
Cikin ikon allah Koda yaron yaga khaal bai nuna yaji tsoron ganin shi ba, saima tambayar khaal din yayi how is he alive? Mamanshi tace ya mutu bazai dawo ba, gashi kuma yanxu yana raye that means mamanshi karya ta mashi kenan? khaal ya rasa wani answer zai bashi…
Kallon khaal yaron ya sakeyi Sai kawai ya fara kuka sosai yana tambayar khaal da gaske an kama mamanshi? Friends dinshi sunce mamanshi is a kidnapper an nunota a tv, har bullying dinshi aka fara yi.
Tausayin yaron ya gama babaibayeshi,idan ya taso yaji abubuwan da mahaifiyarsa tayi a baya abun zaiyi affecting dinshi sosai…
Call din taj yasa mutallib futa daga inda suke don ya amsa, gaisawa sukayi kafin mutallib ya soma magana.
“Na kawoshi yana tare da khaal yanxu.”
Shuru akayi daga chan mutallib na jin yanda ya sauke ajiyar zuciya, “please take care of him”
Da mamaki mutallib ya soma magana, “duk abunda mamanshi tayi maka baisa kayi abandoning dinshi ba? Why?”
Daga chan taj ya bashi amsa kamar haka, “saboda he’s innocent,“
Murmushi kawai mutallib yayi yace “kamar yanda kayi hasashe, an saka kamfanin a kasuwa, next week za ayi bidding akan, kuma darajarshi ta sauka akwai possibility kamfanin B&B ne sukeson su saya saboda su kadaine tayi partning dasu kafin wannan scandal din,”
Shuru taj din yayi yana wani dogon nazari akai, saida mutallib ya sake magana kafin yace “i will call you back” ya kashe wayar ya soma dilaing number merk, yana daukan wayan ya soma mashi proper bayanin yanda abubuwan ke wakana a kamfanin, already yasan fadwa has take over tunda daman itace next to hidaya, at first ya dauka agenda dinsu daya da Hidayar tunda duk wasu abubuwa da sukeyi akan karya gaji kamfanin mahaifin nasu ne, kuma zasu iyayin komai akanshi sai yanxu ya fuskanshi ba hakan bane, nata plans din dabanne, daman he never trusted her tunda har ta iya cin amanar yar uwar tata, dubaga lokacin da aka kama hidayar ta futo ta nuna cewa kwata kwata basusan komai gameda abunda yar uwarsu keyi ba, kuma dalilin dayasa ta hanasu su kansu yan uwanta su shiga harkar business, ta juya komai akan hidayar, yanda dai sukayi ma khaal, lokacin da aka ce yana amfani da kamfanin wajen yin illegal abubuwa, ashe ita sayarda kamfanin ma takesonyi, kuma ga competitors dinsu.
Jamid na barin school fadwa ta karaso itama, tana zuwa neman barad din aka shaida mata ay driver yazo ya daukeshi, tana barin wajen ta shiga mota taja da mugun speed, tayi mugun sake da bata daukeshi ba tuntuni tun kafin ma tayi threatening hidaya dashi, dole hidaya will not sit still zatayi komai akan danta, musamman yanzu data gano komai tasan wacece asalin fadwar, hidaya has so much influence da zata iya yin hakan,ko zaman sati biyun nan datayi a detention center dinnan fadwa ce tasan yanda tayi duk wani lawyer yaqi daukan case din hidayar, dole hidaya ta zauna a ciki don tasan sirrinsu ita da mahaifinta, kuma idan har ta fito zata iya zame masu barazana shiyas ayanxu tayi deciding daukan barad don tasan shine weakness din hidayar shi zaisa taqi making any moves.
Nigeria…
Baze university abuja…
Suna gama debate presentation kowa ya futo daga class, excitedly, musamman haya da sabeeha sai wasu maza biyu da suka kasance a group dinsu suke.
Sune overall best a cikin group dinsu kuma sabeeha ta kasance leader dinsu don itace jagaban, beauty and brains.
Tunda suka fito daga auditorium din class mates dinsu da waenda suka zauna akayi presentation din dasu babu abunda suke ce mata sai “nice presentation,”
Lokaci guda saita zama kamar wata celeb, babu abunda yafi burge kowa sai yanda ta dunga debating lecturers din da aka ajiye for questioning.
Tunda suka fito hamad yake kallonta, gaba daya ya shagala da murmushin da takeyi, duk wanda ya ganta yasan she’s so excited.
Gefenta ya kalla yaga samarin da suke tafe tare dasu sai kawai ya hade rai ya kauda kai.
Dan tureta haya tayi ta dago ta kalleta chan kasa kasa tace “ga admirer dinki chan”
Cikin saurin ta dago kanta idanunta ya sauka kan nashi, tayi saurin dauke idanunta ta dubi haya tace “ki bari dan Allah”
Dariya haya tayi ta tsaida samarin da suka fito tare dasu ita kuma sabeeha tayi saurin karasawa inda yake ya wani hade hannayenshi a kirjinshi.
“Ya hamad! Ina wuni, kazo da wuri yau”
Bai amsa ta ba yace “how was the presentation?”
“Alhamdulillah”
“Good” ya bata amsa kai tsaye sukayi shuru gaba dayan su aka rasa wazai magana, “su waye waenchan? “ ya sake tambayanta yana kallon wajensu haya.
“That’s haya, my friend,”
“I know!”
Ya bata amsa kai tsaye and still looking into her eyes yana jiran amsar da yake nema.
Wani iri taji ganin irin kallon da yake mata saita samun kanta da cewa “group members dinmu ne sauran”
Dan tabe baki kawai yayi kamar bazaiyi magana ba yace “are they also your friends?”
“No ya hamad, kawai munyi presentation ne tare”
“Okay!!” Ya fada kai tsaye, daidai nan su maya suka tunkaro inda suke tsaye, ko kallon inda take batayi ba ta shiga mota, laila tayi mata murmushi ta shiga itama.
Ganin haka yasa sabeeha kallonshi don yana tsaye har zuwa lokacin, ganin yanayinsa har zuwa lokacin yana nan yanda ta taddashi yasa ta bude baki zatayi magana kenan ya juya ya shiga motar.
Bude motar tayi itama ta zauna yaja motar suka bar harabar school din bayan ta tura ma haya message din cewa ta tafi.
Around wajen 3:30pm suka iso gida, maya ce ta fara fita kafin laila, ya rage dagashi sai ita, tana kokarin futa daga motar ya tsaidata.
“Male friends are prohibited islamically, don’t make one”
Tana jin haka tasan me yake nufi wannan yasa babu gaddama tace mashi “Insha Allah”
Laptop dinshi daya bata aro ta aje mashi “thank you” ta fada kafin ta futa daga motar.
Ya sauke ajiyar zuciya kafin ya wuce airport da motar.
Cikin gida gaba daya sai hada hada akeyi, a sauke wannan a dora wannan, gaba daya ma’aikatan nata aiki.
Dakinsu ta fara zuwa ta aje littafanta sannan ta dauro alwala tayi sallah kafin ta futo kitchen din.
Da sallama ta shugo rabi ta dubeta tace “har kun dawo da wuri haka?”
“Eh anty rabi, sannunku da aiki”
“Yan mata dake wajen suka amsa da yauwa sabeeha.
Gefen inda hadiza ke tsaye ta nufa tace “ina wuni mama”
Ganin ido yasa hadiza cewa lafiya ta tsake hannunta daga veggies da suke gyarawa ta fita daga kitchen din.
“Zauna ki taya su yankawa” rabi tayi magana sabeeha ta zauna ta soma yankan veggies din.
Yanda aketa fidda sabun warmers yasa sabeeha tunanin kodai baqi za ayi ne bata gama tunanin ba cikin yan matan dake yankan veggies sahura da bintu suka soma magana kasa kasa.
“Ay naji ance manyan baqi za ayi,”
“Harkar masu kudi zakaga abu allah ka mana arziki, aure a cikin gidan nan ay daula ce”
Dariya sukayi kasa kasa sabeeha batace masu tak ba don bata yawan shiga cikinsu saboda irin gulma da tsegumin nan da basa rabo dashi, shiyasa suke ce mata wani sa’in tanada girman kai, uwarta kuwa batada mutunci, ji take kamar a gidan aka haifeta.
Misalin karfe takwas daidai hamad yayi packing motarsa daidai main house, daga baya aka budo kofar, wata kyakyawa mata ce ta futo da dan cikinta daya futo, farace tass Masha allah, zagayowa sufyan yayi hamad ya bude booth suka kwaso kayansu.
“Sannu maman baby” hamad yayi magana yana mai dubanta.
Murmushi ta danyi cikin kunya tace “yauwa!”
Kallonsa sufyan yayi yace “bari na aje kayanmu a part din mummy ka shiga da ita part din anne.
“Ah ah kuje ciki bari nakai maku kayan chan”
“Thank buddy” sufyan ya fada yana mumrushi suka shiga main house shi kuma ya wuce part din anty laila da kayansu.
Da sallama suka shugo antu fadila dake saukowa daga part din anne tana hangosu ta fara murmushi.
“What a surprise…ango ango…masha allah saukan yaushe”
Dariya yayi ya kalleta yace “yanxu fa mami, ina wuni”
Cikin sauri ta karaso kasan ta rungume matar sufyan din tace “bari na fara gaisawa da sirilata tukunna, how are you my dear? Masha Allah,allah ya raba lafiya”
Tsabar kunya taqi dagowa ta kalleta ta sunkuyar dakai tace “mami ina wuni mun sameku lafiya?”
“Lafiya lau alhamdulillah”
Laila dake saukowa daga dakin maya ta biyo mami tana jin muryar ya sufyan tayi saurin saukowa, “ya sufyan…”
“Princess…” tayi saurin saukowa jikinta har tsuma yake batama lura da matarshi ba tace “yanxu kuka iso? Ina wuni”
“Lpy lau princess how are you?”
“Im fine yaya” tana fadin haka ta dubi matarshi tace “ina wuni”
“Lafiya ta amsata anty fadila tace “ kuje anne na sama, gashi ana kiran salla saiku huta”
Suka wuce saman itama suka wuce part dinsu.
8pm
Nanna na zaune kan sallaya bayan ta idar da sallah ta nade abun salla kenan akayi knocking kofa daga waje.
“Yes come in”
Ta amsa don duk a tunaninta sabeeha ce, rabonta da ita yau tun safe data tafi school ko lekowa batayi ba da yamma.
Nanna na kokarin juyowa wadda ta bude kofar tayi saurin cewa “nannna!!!!”
Tana jin muryar bahijja tayi saurin dagowa da mamaki karara akan fuskarta, “bahijja, is that you?”
“Ni ce dai bahijjan ki nanna!”
Cikin hanzari bahijja ta karaso cikin dakin ta rungume nanna, nanna ta kasa magana tace” saukan yaushe? Shine baki fada min ba ko jiya da mukayi waya”
“I was so excited nazo nayi surprising dinki,”
“Oh my god, what a surprise…kuma babu wandaya fada min”
“Ay babu wanda yasan da zuwan nawa ma, Happy 60th birthday nanna,”
Murmushi nanna tayi don ta manta gaba daya banda yanxu da bahijjar ta fada.
“Oh kudai baku mantuwa, ni nama manta da wani abu wai shi birthday,no wonder business partners dina keta kirana yau, i wanted to take a rest for the day naki dauka”
Dariya bahijja tayi tace “yanxu dai ki shirya mu fita, please don’t ask me ina zamuje its a surprise”
Dariya kawai nanna tayi tace “toh”
Kusan a tare suka fito ita da nanna, nanna ta saka wani lace na alfarma mai kyau peach color sai mayafi kusan same color da lace din, ta zuba dankunne masu kyan gaske sai Yalqi suke kamar diamond, tunda ta sauko from the look of yanda gidan yayi shuru tasan cewa babu kowa, duk sun fita kenan, koda suka karaso mota hamad na tsaye na jiransu.
Yana ganin nanna yayi saurin rungumeta dake yanada tsayi saida ya dan rankwafo sosai yace “happy birthday nanna”
Dabbing bayanshi tayi fararen haqoranta suka fito rass tace “thank you hamadudu, yaushe ka kara tsayi ne haka”
Dariya sukayi gaba dayansu ya bude masu kofa suka zauna ya shiga mazaunin driver ya tuqa motar.
Bahijja ta kalli nanna, wani irin farın ciki ne gaba daya ya gama lullubeta, yau zatayi testifying wannan rana kamar ta yau, abunda ta dade tana addua akai.
“Ina majeed din? Na ganki ke daya”
“Yana chan nanna, ni kadai nazo, ay dole ma nazo saboda rana irin ta yau”
Nanna bata gane me take nufi ba kawai dai ta murmusa har suka iso wajen, hamad na parking ya futo ya bude ma nanna anty bahijja ta futo ta kama hannunta.
Wani dan kyalle ta karba hannun hamad abu kamar abun yara fa suka rufe mata fuska, abunka da yan boko masu wayewa saita tafi da abun nasu suka shiga wajen din.
Suna isowa wajen hamad ya fara shiga daga ciki bahijja zare mata abun fuskan nata aka kunna haske bauu ko’ina.
Kananun yaran suka fara ihu…
“Surprise!!!!!!!!!”
Saida nanna ta kifta ido ta sake bude kafin ta fara ganin mutanen dake tsaye a wajen, anyi decorating wajen yanda kasan za ayi dan mini event, an kawata wajen da decorations na zamani, ga banners din hotonta a kafa an rubuta happy 60ths birthday, family and friends kowa ya halarta, kai waje dai masha allah duk wanda ke wajen is close to her harda business partners dinta.
Gaba daya wajen ya dauka da “Happy birthday to you..”
wani irin breath taking murmushi takeyi, kamar zatayi kwalla tsabar farin ciki, ga iyalansu kowa ya hallara, sameer ne da nashi iyalan duka, harda yan makaranta abal dake karatu a dubai, ga sufyan da matarshi, kowa dai ya hallara.
Babu abunda take fada sai “Alhamdulillah alhamdulillah, thank you so much thank you thank you, when did you plan all if this?”
Tayi tambayar bakinta ya kasa rufuwa, kowa nata kokarin hugging dinta, aka bama anne waje ta nufi inda take ta rungumeta itama tace “Allah ya karo shekaru masu albarka”
“Ameen ya Allah yaya”
Gaba daya hankalinsu bai kaiga anty bahijja ba don tana daga bayan nanna saida fadila ta hangota tukunna tace “bahijjaaaa,kamar bahijja nake gani”-
“Anne tace ba kama bane itace,”
Kyakyacewa da dariya anty fadila tayi ta rungumeta tace “wai daman zaki dawo nija yau shine baki fada min ba?”
“Wanted to Surprise everyone shiyasa nace anne karta fadama kowa, ya sameer ne kawai da nanna suka san zanzo”
Kallon ya sameer fadila tayi tace “kofa dazu saida mukayi mganarki dashi baice min komai ba akan zuwanki”
Dariya akayi gaba daya, aka fara gaggaisawa,
Maya dake zaune chan wajen da aka zazzauna kwata kwata bata tasoba tunda hamad ya shugo ya shaida masu isowar nanna, tanajin muryar mummynta kamar a mafarki tayi saurin mikewa ta tunkaro wajen,
Tana karasowa wajen sai hawaye ta taho a guje ta rungume mummyta “mummyyyyyyyyy!!!!!!”
Bahijja na jinta a jikinta tace “babyyyyyy!”
“Mummy yaushe kika dawo? Meysa baki fada min zakizo ba,”
“Daman zanyi surprising dinki ne babyn mummy, how are you?”
“Im fine mummy ina dady?”
“Daddy yana chan baizoba”
Gyaran murya anne tayi wanda yasa hankalin kowa ya koma gareta tace “lets have dinner ko”
Aka zazzauna gaba daya, masu serving suka soma zagaye da casserole shaqe da abunci kala kala, aka ajiya, wani abunma saika rantse ba cikar yan kasar bane.
Tunda suka zauna table din family gaba daya babu abunda ake sai hira, bini bini anne zata kalli nanna daketa faman murmushi tana kallon kowa dake wajen, kana ganinta kasan tana cikin farin ciki, its been long rabonda ta ganta cikin farin ciki haka.
Kananun jikoki nata yawo a waje gwanin ban sha’awa, fadila da bahijja ko nata faman hira don seat daya suka zauna, gefenta kuwa maya ce ta wani maqale mata kai kace zata sha mama, yar shagwaba kenan, laila ko me zatayi banda yi mata dariya.
Hamad da sufyan sunata hira gwanin birgewa, amaryar sufyan ko tana gefen anty mubina don akwai yar kunya tsakaninta da anty laila wato maman sufyan kenan sirikarta.
Sameer ko sai faman magana yake da mutane da aka gayyata family friends.
Ana tsaka da cin abunci ana hirarrakin yaushe gamo anne ta miqe tsaye tayi gyaran murya.
Duk kowa ya maida attention dinsu gareta, bude taron tayi da sunan Allah sannan ta fara godiya ga waenda suka halarta, sannan tayi godiya ga allah daya azurtasu da arziki mai albarka da iyalai.
Sannan ta dora da tana son tayi introducing addition to their family wanda ba kowane yasanshi ba.
Maganarta ta karshe yayi daidai da budewar kofar wajen da securities din wajen sukayi, ya sanyo kafarshi cikin wajen kowa ya juyo don ganin ko wanene, kwata kwata baisan da yawan jama’a a wajen, yana sanye da jallab fara khaal yayi nadin kundura akanshi, sai ya zamo kamar wani tauraro daya haske wajen aka bishi da kallo.
Nanna na ganinshi sai kawai murmushin dake fuskarta ya kara tsananta, anne na ganin fuskarta tayi hamdala aranta don wannan na tabbatar mata da hajara ta hakura da komai kenan.
Dakawata anne tayi da magana ta dubi anne sannan tace “bismillah hajara, bani ya kamata nayi introducing dinshi ga kowa ba face ke”
Wasu hawaye ne masu zafi suka sauko mata akan fuskarta na farin ciki tayi saurin sharesu ta miqe tsaye ta nufi inda taj yake gabanshi na dukan uku uku ya kasa dagowa ya kalli oummi dinshi.
Tana karasowa ta kama hannunshi da babu jakar daya riko a ciki yayi saurin dagowa ya kalleta ta sauke mashi murmushi ta juyo tana duban kowa dake wajen kafin ta soma magana.
“This is my one and only son Tajudeen Abdullah Taheel allah has unite us after we got separated for more than 40years Alhamdulillah”
Tana fadin haka ta maida dubanta ga taj tace “Meet my co workers and your cousins, your family”
Murmushin da zaice ya dade rabon da yayi shi da farin cikin daya manta da yinshi ne ya bayyana a fili, gaba daya sai yaji kamar an sauya mashi da duniyarshi gaba daya, haske ya bayyana a gabanshi.
Hannu nanna ta bude mashi ya rungumeta hawaye na sauka a idanunshi tana ta hamdala, its was an emotional moment kowa nata nanata 40years aranshi, wallahi abun ban tausayi da ban sha’awa, shima dai dakyar ya iya danne emotions dinshi kamar wanda ke tsoron magana muryarshi na karkarwa yace “Ighfiri li ya oummi, i will always be by your side”
“I’m sorry my son, ka yafemin”
Dagowa yayi ya kalleta yace “hawayenki masifa ne a gareni ya oumi, please karki nemi yafita ni zan nemi yafiyarki, I’m so sorry for..”
“Ya isa haka” ta dakatar dashi, “komai ya rigada ya wuce,”
Girgiza kai yayi har zuwa lokacin hannunshi na cikin nata,anne daketa faman murmushi babu abunda take sai hamdala, kowa ya kasa daina kallonsu,Bahijja tafi kowa farin ciki, shiyasa da anne ta fada mata komai ta kasa hakura dole ta nemi excuse tabi jirgi ta taho, saurin goge kwallar fuskarta tayi tana hamdala.
Maya da laila sai sakin baki, ita laila ranar da yazo ta gane shine saidai batasan da maganar cewa dan nanna bane ita kuwa maya yaza ayi ta manta da wanna Fuskar da take mararin gani koda a mafarki ne?…spoon din data duaka zatakai bakinta yafi minti biyu a haka bata saukesui ba bata kaishi bakinta ba.
Laila ta tabota tace “kinganshi ko? Shine shine wanda nake fada maki, he’s our uncle..oh my godddddd”
Gaggaisawa da kowa nanna tasa yayi, ta dunga introducing dinshi ga partners dinta, kana ganinta kasan tana cikin farin ciki da annushuwa.
Karasowa wajen anne sukayi ya kama hannunta ya sumbaceta irin yanda larabawa keyi sannan ya gaisheta, ta sa mashi Albarka, ya gaisa da ya sameer dasu anty bahijja da anty fadila, anne tayi introducing dun kowa,sauran yaran kowa ya dunga gaishesa anne tasa ya zauna kusa da seat dun nanna dake kusa da nata.
Kai wannan family saidai ace masha allah, duk wanda ya gansu sai yayi alfahari dasu, don allah ya albarkacesu da komai, zuri’a ta gari, kwanciyar hankali babu fita babu tashi hankali ga hadin kai.
Hira sosai ta karade, dukda bashida yawan magana haka suka dunga janshi da surutu, amla na jikinshi tana kama gemushi, sauran samarin ko duk haduwarsi da ji da kudi da suke dashi suna arba dashi suka raina kansu, ya sameer ne ana cikin hira ya jefo mashi tambaya trying to get to know him, “what do you study?”
“Mechanical engineering” ya bashi amsa kai tsaye yana murmushi, gaba daya duk kallonshi sukeyi wannan yasa ya kasa sakewa.
“Wow thats very interesting, kana aiki?”
“Yes..I’m into manufacturing of cars” ya bashi amsa
“Masha Allah,” ya sameer ya fada, abal dakeda interest akan motoci yayi saurin cewa “wow, uncle taj, are you a developer?”
Dan murmusawa taj yayi ya dubeshi ganin yanda yake kallonshi yana ganinshi ya gane bazai wuce irin 22 dinnan ba, saiya tuna mashi lokacin da yana kamarshi.
“Yes i am, i’m the founder of Fords motor”
Baki sake abal ya bude duk suka bishi da idanu harda sameer, abal kamar zai rungumoshi tsabar excitement yace “oh myyyyyy… you’re the founder of fords???? The whole fords?, T-ford?”
Dariya taj ya danyi don shi ya fada ne kamar irin ay ba wani abu bane, ganin how interested he is yasa taj cewa “looks like you’re interested in this field”
“Yes i am, wow thats hugeeee, dady kasan kamfanin fords? Motocin fords fa? That one of the best cars around the globe,”
Sai a lokacin anne ta dubeshi tace “that’s impressive, at the age of 33 you have achieved this? Wow…I’m so proud of you masha Allah”
Murmushi kawai yayi ya dubi nanna daketa kallonshi kamar ta maidashi ciki ahankali tace “i’m so so proud of you”
Kamar an tsundumashi a aljanna haka yaji, bai taba sanin cewa akwai wanda zasuyi murnar daukakarshi ba sai yanxu…he feels like boyewar identity dinshi batada amfani yanxu.
Maya fa har zuwa lokacin ta kasa dawowa hayyacinta, babu abunda take sai kallonshi, sau daya ya dago ya kalleta lokacin da kowa ke intoducing kanshi, tundaga lokacin bai sake kallonta ba.
“Uncle taj why haven’t you visited us?” Laila tayi tambayar dayasa kowa kallonta, honestly tayi tambayar amma ganin yanda kowa yake mata wani irin kallon yasa tayi shuru ta suake kanta kasa maminta kuwa me zatayi banda harararta, taj ko ya kasa cewa komai nanna ma jikinta yayi sanyi.
Anne ce tayi gyaran murya tace “ya kamata mu koma gida haka nan its past 10pm.”
Shirye shiryen komawa gida aka somayi aka fito gaba daya, yawanci waenda aka gayyata duk sun tafi, sai yan gida.
Katuwan lexus din gidan guda biyu kowa ya shishiga,anne ta dubi taj tace “ina fata ka gama clearing da chan masaukinka don bazaka koma hotel dinnan ba”
Murmushi yayi yace “insha allah anne”
Abal dake zaune mazaunin gaba yanajin haka yayi saurin fitowa yace “can i join you uncle taj?”
“Yes sure!” Ya bashi amsa tare da rufe kofar da anne ke zaune ya zagayo inda nanna ke zaune yace “allah ya kiyaye zan biku a baya”
Murmushi nanna ta mashi, lallai haihuwa nada rana, bakinta kamar baka farin cikinta baya misaltuwa tace “allah yayi maka albarka”
Wani irin dadi yaji aranshi mara misaltuwa ya amsa da ameen driver yaja suka bar wajen.
Shida abal suka nufi wajen zabgegeiyar motarshi, ya tada suka bisy a baya.
Abal ya dunga mashi hira kamar ba gobe kafin sukai dai saida taj ya gane yanda abal ke son motoci kamarshi, gashi he’s so smart.
Lokacin da suka iso kowa ya rigada ya shiga cikin main house, booth dinshi ya bude abal ya dauko mashi classy LV luggage dunshi, daidai nan hamad ya futo daga cikin gidan, yana hangosu ya karaso inda suke sannan ya jagoranci taj din zuwa masaukinsa.
apartment din dake gefe kusa dana anty bahijja hamad ya bude,yawanci irinshi ne ma aka bama sufyan da amaryarsa duk sanda sukazo hutu anan zasu dunga sauka.
Duk apartment din sun zagaye main house, saboda ahalain ya dunga expanding yasa akayi part part din, tunda gashi duk samarin tasowa sukeyi kuma zasuyi aure duk me so zai iya zuwa yayi zamanshi.
Suna shiga abal ya shiga da luggae dinshi har ciki, an suya komai na ciki apartment din, interior din part din black and white, so esthetic babu wani abun hayaniya, parlor ne a kasa dayasha english kujeru sai dining wajen kitchen sai kuma sama bedrooms guda biyu, daya master dayan kuma second bedroom, suma dai Masha allah.
Kafin su futa hamad ya shaida mashi nanna tace he should settle in and rest zuwa gobe saiya shugo main house sannan idan yana buqatar wani abu ya nemi hamad din, nan sukayi exchanging contacts, abal kam tuni ya karbi nashi number din tun a mota, Suna futa ya sauke wata ajiyar zuciya yabi ko’ina da kallo, komai goes to his taste dayake shi bamaisan hayaniya bane.
Sama ya wuce zuwaga bedroom din shima ko’ina fess fess a gyare babu kazanta ko kadan.
Setting in ya soma yi kafin ya shiga bathroom ya watsa ruwa ya fito ya saka jallab, lokacin wajen karfe sha daya ya tada kabbarar sallah, tunda ya fara sallah abi zauna ba har wajen karfe uku babu abund ayake zai godiya ga Allah daya nuna mashi wannan raya, ta bangaren nanna ma bata iya barshi ba haka ta kwana tana godiya ga Allah, gaba daya a ranar babu wand atakema addua kamar taj.
Sai wajen karfe uku da rabi ya iya tashi ya kwanta kan kace me wani irin ni’imataccen barcin da ya mance rabon da yayi tun bayan tafiyar sabeeha yayi shi.
He sleeps peacefully kamar wani baby, gaba daya ji yake kamar an cire mashi 90% of damuwarshi.
Kiran sallar farko a kunneshi, koda ya bude idanunshi ya dauka mafarkin komai yayi sai yaga zahiri ne, this is the life he dream for him self,yanajinshi kamar he’ss complete, a take zuciyarshi ta raya mashi how he can’t be complete without her, tunaninta da yake hana kanshi saiya kasa gaba daya, memories dinsu ya dawo mashi kamar anyi rewinding, daman ance sai an samu kwnaciyar hankali ake wani tunani, don har steamy moments dinsu saida ya dunga zuwa mashi, ya mafi tsaya mashi arai don gaba daya yasa jikin shi yayi wani irin sanyi, akanta yasan he’s a man, very needy man infact theres a needy monster inside him that makes him crave for her presence, her scent, her breath and her boobs.
Shagalcewa fa yayi ya kasa tashi gaba daya yana tunanin sabeeha, watanni nawa kenan ya kasa cireta aranshi, kai dukyanda za ayi dole ya nemota.
Kiran sallah na biyu ne yasashi tashi dakyar ya wuce bathroom kamar wani mara lafiya, ya sakarma kanshi ruwan zafi sosai kafin ya danji dama dama sannan ya futo a gaggauce ya saka jallab da wani cute ovy black slippers ya sauko kasa lokacin har an fara tada kabbara.
Da suka shugo estate din gidan ya hango masallaci daga gefe wannan yasa yana futowa ya nufi wajen,yana dab da shuga ya sameer dasu abal da sufyan harma da hamad suma suka karaso gaba daya suka shiga masallacin sukabi sallah.
Suna idarwa bayan sun fitfito ya gaggaisa da kowa, ya sameer ya bashi hannu su abal da sufyan suka gaishesa hamad ma ya gaishesa a mutunce kafin ya koma part dinshi.
Barcin da bai koma ba kenan ya bude laptop dinshi ya fara aiki, da duban report din da merk ya tura mashi.
Karfe takwas daidai wayanshi tayi ringing, number anne ya gani wannan yasashi saurin dauka ba tare da wani tunani ba yayi sallama ya gaisheta cikin natsuwa.
Ta tambayeshi ya kwanan sabon waje? Sannan yana buqatar wani abu ko wajen bai mashi ba ko yana san a sauya abubuwan da aka saka mashi, yace mata ah ah, babu komai, kuma hes so grateful for everything.
Nunfasawa tayi sanna tace mashi ya shugo main house yayi breakfast yanxu yace mata toh.
A gurguje ya shiga wanka ya fito ya kintsa cikin jallabiyanshi this time around black jallab ce ta amshi skin dinsa sosai kunsan ance black and white idan aka hadu bade kyau ba, gashi morning face dinshi is so breathtaking.
Wayanshi kawai ya dauka ya saka black slippers dinshi da suka fidda yatsun kafarshi doyage sannan ya futo ya tunkari main house, babu wani nisa baifi taku ashirin ba yakai aka bude kofa ya shiga daga ciki, rabi dake jera abunci a dining tana hangoshi ta kasa dauke idanunta,har chokalin hannunta da take jerawa a dining ya subuce, “allah gamu gareka,” ta furta a hankali hadiza ta bita da ido, kafin ta maida dubanta ga taj wanda rabi ke kallo, ay saita fi ma rabi rudewa, cha take “wannan waye kuma kamar balarabe a gidannan”
Rabi ta juyo tace “zaki zubarda coffee din, ta galla mata harara.
Maya dake zaune hadiza na zuba mata coffee tana jin abunda tace yasa tayi saurin miqewa da cup din coffee din a hannunta ta nufi inda suke tsaye ta hangoshi a taaye a wajen ya taaya ganin babu kowa a kasan.
Maya uwar kaudi tayi saurin karasowa inda yake kamar zata fadi har tana hardewa gab da inda yake nesa dashi kadan coffee din ya subce mata ya fadi kasa cup din ya fashe, daidai wajen yatsun kafafunshi dake bayyane tayi saurin cewa “oh my god im so sorry…”
Muryarta ce da yanda event din ya faru yasashi ganseta lokaci guda, the girl that split mocktail on him that very day”
Yi yayi kamar baisan da ita a wajen ba harta tsugunna daidai nan anne ta sauko ya karasa inda take ya kama hannunta ya sumbaceta, wannan alada taqi rabuwa dashi mufa nan bama haka a nigeria lol…
“Good morning Deen, how was your night?”
“Hamdullah!’” Ya bata amsa,
“Kaje sama kayi breakfast wajen oummin ka,”
Murmushi yayi mata shidai kamar bashida baki yace “okay an…ne”
Kiran rabi anne tayi tasata ta kaishi har part din nanna, ta jagoranshi bayan ta gaishesa har zuwa oart din sannan tayi sallama da
Nanna a bedroom dinta ta shaida mata da zuwanshi, yana daga zaune sitting room din
Tunda ya shigo gabansa ke faduwa dab dab dab ya rasa dalili amma yana alaqantashi da wani abu da yake jinshi mafi kusanci da zuciyarsa, futowa rabi tayi tace mashi ya shiga ciki, yana shiga daidai nan sabeeha ta fito daga dakin da take kwana tun lokacin da rabi ta nuna mata.
Rabi na ganin futowarta don tana gab da futa tace “baku tafi ba?”
“Eh yanxu zamu tafi ina kwana anty rabi”
“Lafiya ta amsa ta”
Ta dauka kasan zata sauko sai taga ta nufi bedroom din nanna har zatayi kncking rabi ta dakatar da ita tace “me zakiyi?”
“Daman zan ce mata na tafi ne?”
“tanada baqo a ciki, ki tafiyarki kawai”
Da toh sabeeha ta amsa mata sannan ta bi bayan rabi suka sauko kasa tana dafe kirjinta.
Tun jiya da daddare gabanta ke faduwa ta rasa dalili
,nanna na zaune kan carpet an jera breakfast hannunta rike da coffee sai news papers dake hannunta ta dago ta kalleshi ta sauke murmushi tace “come in bismillah” ta mashi nuni da gefenta wajen carpet din.
Zama yayi cikin biyayya ya gaisheta irin gaisuwarsu, nanna ta tambayeshi how was his night yace mata alhamdulillah sannan da kanta ta mashi serving abunci tace bismillah.
Yanajin abun kamar a mafarki ba gaskia ba, yau gashi ga mahaifiyarsa, bini bini nanna ke dagowa tana kallonshi tana murmushi, harya cinye tass baima san ya cinye ba tunda yazo baici abunda ya mashi dadi ba kamar wannan.
✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊
MATAR TAJ (destined with you🩵🤍)
Written by
QueenmarhBook2
PAID
Jamid baibar detention center dinnan ba saida hidaya ta fada mashi komai, asalin fadwa yanda ta kashe tareeq saboda shine ya fara sanin sirrinta da kuma bacewar taj, da yanda ta dunga amfani da ita don cinma burinta, dukda itama tana da nata kason a cikin duk abubuwan da suka faruwa.
Abunda yafi bama jamid mamaki shine asalin fadwar, ba yar taheel bace? All those years haka suka dunga venting akan taj, Hating on him, ganging up on him, suka kusa salwantar da rayuwarshi, kuma ba kowa bane kan gaba sai hidayar, ashe shine asalin dan uwanta, fadwa ce outcast cikin su, ta haramtacciyar hanya ma aka sameta, mahaifiyar tasu da suke duk waennan abubuwan saboda ita ashe itace aje masu abun kunya.
wannan babbar ishara ce a garesu gaba dayansu musamman hidayar data dauka tsanar duniya ta dorama taj, ta wulaqanta rayuwarshi ta kusa salwantar da rayuwarshi saboda tsana, bai tsareta da komai ba, yanxu gashi komai ya juye mata, yar uwar datake tunanin itace jininta ta kasance batada alakar ubantaka da ita kuma ta zame mata babbar barazanar.
Shima kanshi bata barshi ba, dukdan sabod aya tsayama taj, yayi protecting dinshi, saboda hakan ta maidashi kamar wani enemy dinta yana matsayin mijinta.
Tunda ya samu paralyze kuwa ya zame mata mara amfani ta fiddashi daga gidan nan ta turashi kasar waje neman lafiya bata sake waiwayarsa ba, Batama san yanda akayi ya samu lafiya ba har yazo gareta yanxu haka, duk tsawon wannan lokacin bashida tunanin daya wuce na taj da sabeeha, saboda shi kadai zai iya fadin wahalar da suka sha a wajenta, makirci iri iri daban daban dukdan akan abun duniya, dukdan saboda taj karya gajesu.
Babu irin maganganun da jamid bai fada mata ba cikin bacin rai sosai, ta kasa magana kwata kwata gaba daya saboda she’s guilty of everything, he vent so much of his anger akanta sannan ya nuna mata ay bataga komai ba, kamar yanda ya fada mata bazata taba sanin zafin abunda tayi ma taj ba sai ya samu nata gashi nan ba a je ko’ina ba saboda abubuwan datayi a baya zai shafi dansu, an innocent child daman duk abunda kayi sai anyi ma naka,, a karshe ma dai fada mata yayi idan har wani abu ya samu dansu bazai taba yafe mata ba.
Aranar daya dawo yaji labarin kamata da akayi tunda abune ba boyayye ba kama ga matsayinta a kasar, ko’ina zai dauka don zai shafi kamfanin su, yayi mamaki sosai, wannan ne yasa yazo don ya tabbatar ma idanunshi don hidaya can never give up so easily he wanted to see why tayi sanyi batayi amfani da tricky connections dinta ba, don zata iya yin komai akan kamfaninsu da kuma ganin duk wasu abubuwa da takeyi bai fito idon duniya ba, ashe ashe ga dalili, ga kuma labarin bacewar taj.
Haka ya futa yabarta zaune, jiki a mace tayi la’asar kamar ba hidaya ba, ta kasa tabuka komai, komai ya juye mata gaba daya bata cikin natsuwarta saboda danta, da tanada hanyar maida hannun Agogo baya da batayi abunda tayi ba a baya, sai hankalinta ya sake tashi sosai, don tabbas fadwa zata iya illatar mata da danta dukda ta bata abunda take nema.
Jamid na barin detention center din, gabanshi na faduwa sosai ya wuce school dinsu direct.
Gaba daya school din yau is busy saboda hutun end of the terms da akayi kuma iyaye nata zuwa daukan yaransu.
Dukda yasan makarantar akwai tsaro sosai wannan baisa gabanshi faduwa ba,at the same time har zuwa lokacin he’s in so much shock.
Ay bai gama samun shock of his life ba saida aka nemi barad a school sama da kasa aka rasa, home school teacher dake kula dashi ta shaida yana zaune a visiting area, don tun safe ake zuwa daukan student, on a blink of eye aka nemeshi aka rasa, jamid kamar zaiyi hauka, school gaba daya ta rikici aka fara duban cctv, abunda suka gani ne ya sake tadama jamid hankali, don footage din ya nuna wani mutumi ne ya shugarda barad din cikin wata baqar mota, home school teacher data gane ko wanene ta shaida masu ay driver din dake zuwa daukansa ne lokacin da yake zuwa day kafin a maidashi prep border…
Jamid was so confused don a lokacin yana kwance baisan meke faruwa ba, baima san wanenene driver ba, tsoronshi daya karya kasance driver nada sa hannu da fadwa…
Waya mutallib ya dauka yayi typing message kafin ya aje wayar ya maida dubanshi ga barad dake zaune, yaron yayi shuru baice qala ba,har suka isa hideout suna isowa mutallib ya bude mashi kofa ya futo.
Dauko yaron baiyi ma mutallib wuya ba saboda yaron ya sanshi, ciki suka shiga yana fatan kar yaron ya tsorata idan yaga khaal don yanada wayo.
Cikin ikon allah Koda yaron yaga khaal bai nuna yaji tsoron ganin shi ba, saima tambayar khaal din yayi how is he alive? Mamanshi tace ya mutu bazai dawo ba, gashi kuma yanxu yana raye that means mamanshi karya ta mashi kenan? khaal ya rasa wani answer zai bashi…
Kallon khaal yaron ya sakeyi Sai kawai ya fara kuka sosai yana tambayar khaal da gaske an kama mamanshi? Friends dinshi sunce mamanshi is a kidnapper an nunota a tv, har bullying dinshi aka fara yi.
Tausayin yaron ya gama babaibayeshi,idan ya taso yaji abubuwan da mahaifiyarsa tayi a baya abun zaiyi affecting dinshi sosai…
Call din taj yasa mutallib futa daga inda suke don ya amsa, gaisawa sukayi kafin mutallib ya soma magana.
“Na kawoshi yana tare da khaal yanxu.”
Shuru akayi daga chan mutallib na jin yanda ya sauke ajiyar zuciya, “please take care of him”
Da mamaki mutallib ya soma magana, “duk abunda mamanshi tayi maka baisa kayi abandoning dinshi ba? Why?”
Daga chan taj ya bashi amsa kamar haka, “saboda he’s innocent,“
Murmushi kawai mutallib yayi yace “kamar yanda kayi hasashe, an saka kamfanin a kasuwa, next week za ayi bidding akan, kuma darajarshi ta sauka akwai possibility kamfanin B&B ne sukeson su saya saboda su kadaine tayi partning dasu kafin wannan scandal din,”
Shuru taj din yayi yana wani dogon nazari akai, saida mutallib ya sake magana kafin yace “i will call you back” ya kashe wayar ya soma dilaing number merk, yana daukan wayan ya soma mashi proper bayanin yanda abubuwan ke wakana a kamfanin, already yasan fadwa has take over tunda daman itace next to hidaya, at first ya dauka agenda dinsu daya da Hidayar tunda duk wasu abubuwa da sukeyi akan karya gaji kamfanin mahaifin nasu ne, kuma zasu iyayin komai akanshi sai yanxu ya fuskanshi ba hakan bane, nata plans din dabanne, daman he never trusted her tunda har ta iya cin amanar yar uwar tata, dubaga lokacin da aka kama hidayar ta futo ta nuna cewa kwata kwata basusan komai gameda abunda yar uwarsu keyi ba, kuma dalilin dayasa ta hanasu su kansu yan uwanta su shiga harkar business, ta juya komai akan hidayar, yanda dai sukayi ma khaal, lokacin da aka ce yana amfani da kamfanin wajen yin illegal abubuwa, ashe ita sayarda kamfanin ma takesonyi, kuma ga competitors dinsu.
Jamid na barin school fadwa ta karaso itama, tana zuwa neman barad din aka shaida mata ay driver yazo ya daukeshi, tana barin wajen ta shiga mota taja da mugun speed, tayi mugun sake da bata daukeshi ba tuntuni tun kafin ma tayi threatening hidaya dashi, dole hidaya will not sit still zatayi komai akan danta, musamman yanzu data gano komai tasan wacece asalin fadwar, hidaya has so much influence da zata iya yin hakan,ko zaman sati biyun nan datayi a detention center dinnan fadwa ce tasan yanda tayi duk wani lawyer yaqi daukan case din hidayar, dole hidaya ta zauna a ciki don tasan sirrinsu ita da mahaifinta, kuma idan har ta fito zata iya zame masu barazana shiyas ayanxu tayi deciding daukan barad don tasan shine weakness din hidayar shi zaisa taqi making any moves.
Nigeria…
Baze university abuja…
Suna gama debate presentation kowa ya futo daga class, excitedly, musamman haya da sabeeha sai wasu maza biyu da suka kasance a group dinsu suke.
Sune overall best a cikin group dinsu kuma sabeeha ta kasance leader dinsu don itace jagaban, beauty and brains.
Tunda suka fito daga auditorium din class mates dinsu da waenda suka zauna akayi presentation din dasu babu abunda suke ce mata sai “nice presentation,”
Lokaci guda saita zama kamar wata celeb, babu abunda yafi burge kowa sai yanda ta dunga debating lecturers din da aka ajiye for questioning.
Tunda suka fito hamad yake kallonta, gaba daya ya shagala da murmushin da takeyi, duk wanda ya ganta yasan she’s so excited.
Gefenta ya kalla yaga samarin da suke tafe tare dasu sai kawai ya hade rai ya kauda kai.
Dan tureta haya tayi ta dago ta kalleta chan kasa kasa tace “ga admirer dinki chan”
Cikin saurin ta dago kanta idanunta ya sauka kan nashi, tayi saurin dauke idanunta ta dubi haya tace “ki bari dan Allah”
Dariya haya tayi ta tsaida samarin da suka fito tare dasu ita kuma sabeeha tayi saurin karasawa inda yake ya wani hade hannayenshi a kirjinshi.
“Ya hamad! Ina wuni, kazo da wuri yau”
Bai amsa ta ba yace “how was the presentation?”
“Alhamdulillah”
“Good” ya bata amsa kai tsaye sukayi shuru gaba dayan su aka rasa wazai magana, “su waye waenchan? “ ya sake tambayanta yana kallon wajensu haya.
“That’s haya, my friend,”
“I know!”
Ya bata amsa kai tsaye and still looking into her eyes yana jiran amsar da yake nema.
Wani iri taji ganin irin kallon da yake mata saita samun kanta da cewa “group members dinmu ne sauran”
Dan tabe baki kawai yayi kamar bazaiyi magana ba yace “are they also your friends?”
“No ya hamad, kawai munyi presentation ne tare”
“Okay!!” Ya fada kai tsaye, daidai nan su maya suka tunkaro inda suke tsaye, ko kallon inda take batayi ba ta shiga mota, laila tayi mata murmushi ta shiga itama.
Ganin haka yasa sabeeha kallonshi don yana tsaye har zuwa lokacin, ganin yanayinsa har zuwa lokacin yana nan yanda ta taddashi yasa ta bude baki zatayi magana kenan ya juya ya shiga motar.
Bude motar tayi itama ta zauna yaja motar suka bar harabar school din bayan ta tura ma haya message din cewa ta tafi.
Around wajen 3:30pm suka iso gida, maya ce ta fara fita kafin laila, ya rage dagashi sai ita, tana kokarin futa daga motar ya tsaidata.
“Male friends are prohibited islamically, don’t make one”
Tana jin haka tasan me yake nufi wannan yasa babu gaddama tace mashi “Insha Allah”
Laptop dinshi daya bata aro ta aje mashi “thank you” ta fada kafin ta futa daga motar.
Ya sauke ajiyar zuciya kafin ya wuce airport da motar.
Cikin gida gaba daya sai hada hada akeyi, a sauke wannan a dora wannan, gaba daya ma’aikatan nata aiki.
Dakinsu ta fara zuwa ta aje littafanta sannan ta dauro alwala tayi sallah kafin ta futo kitchen din.
Da sallama ta shugo rabi ta dubeta tace “har kun dawo da wuri haka?”
“Eh anty rabi, sannunku da aiki”
“Yan mata dake wajen suka amsa da yauwa sabeeha.
Gefen inda hadiza ke tsaye ta nufa tace “ina wuni mama”
Ganin ido yasa hadiza cewa lafiya ta tsake hannunta daga veggies da suke gyarawa ta fita daga kitchen din.
“Zauna ki taya su yankawa” rabi tayi magana sabeeha ta zauna ta soma yankan veggies din.
Yanda aketa fidda sabun warmers yasa sabeeha tunanin kodai baqi za ayi ne bata gama tunanin ba cikin yan matan dake yankan veggies sahura da bintu suka soma magana kasa kasa.
“Ay naji ance manyan baqi za ayi,”
“Harkar masu kudi zakaga abu allah ka mana arziki, aure a cikin gidan nan ay daula ce”
Dariya sukayi kasa kasa sabeeha batace masu tak ba don bata yawan shiga cikinsu saboda irin gulma da tsegumin nan da basa rabo dashi, shiyasa suke ce mata wani sa’in tanada girman kai, uwarta kuwa batada mutunci, ji take kamar a gidan aka haifeta.
Misalin karfe takwas daidai hamad yayi packing motarsa daidai main house, daga baya aka budo kofar, wata kyakyawa mata ce ta futo da dan cikinta daya futo, farace tass Masha allah, zagayowa sufyan yayi hamad ya bude booth suka kwaso kayansu.
“Sannu maman baby” hamad yayi magana yana mai dubanta.
Murmushi ta danyi cikin kunya tace “yauwa!”
Kallonsa sufyan yayi yace “bari na aje kayanmu a part din mummy ka shiga da ita part din anne.
“Ah ah kuje ciki bari nakai maku kayan chan”
“Thank buddy” sufyan ya fada yana mumrushi suka shiga main house shi kuma ya wuce part din anty laila da kayansu.
Da sallama suka shugo antu fadila dake saukowa daga part din anne tana hangosu ta fara murmushi.
“What a surprise…ango ango…masha allah saukan yaushe”
Dariya yayi ya kalleta yace “yanxu fa mami, ina wuni”
Cikin sauri ta karaso kasan ta rungume matar sufyan din tace “bari na fara gaisawa da sirilata tukunna, how are you my dear? Masha Allah,allah ya raba lafiya”
Tsabar kunya taqi dagowa ta kalleta ta sunkuyar dakai tace “mami ina wuni mun sameku lafiya?”
“Lafiya lau alhamdulillah”
Laila dake saukowa daga dakin maya ta biyo mami tana jin muryar ya sufyan tayi saurin saukowa, “ya sufyan…”
“Princess…” tayi saurin saukowa jikinta har tsuma yake batama lura da matarshi ba tace “yanxu kuka iso? Ina wuni”
“Lpy lau princess how are you?”
“Im fine yaya” tana fadin haka ta dubi matarshi tace “ina wuni”
“Lafiya ta amsata anty fadila tace “ kuje anne na sama, gashi ana kiran salla saiku huta”
Suka wuce saman itama suka wuce part dinsu.
8pm
Nanna na zaune kan sallaya bayan ta idar da sallah ta nade abun salla kenan akayi knocking kofa daga waje.
“Yes come in”
Ta amsa don duk a tunaninta sabeeha ce, rabonta da ita yau tun safe data tafi school ko lekowa batayi ba da yamma.
Nanna na kokarin juyowa wadda ta bude kofar tayi saurin cewa “nannna!!!!”
Tana jin muryar bahijja tayi saurin dagowa da mamaki karara akan fuskarta, “bahijja, is that you?”
“Ni ce dai bahijjan ki nanna!”
Cikin hanzari bahijja ta karaso cikin dakin ta rungume nanna, nanna ta kasa magana tace” saukan yaushe? Shine baki fada min ba ko jiya da mukayi waya”
“I was so excited nazo nayi surprising dinki,”
“Oh my god, what a surprise…kuma babu wandaya fada min”
“Ay babu wanda yasan da zuwan nawa ma, Happy 60th birthday nanna,”
Murmushi nanna tayi don ta manta gaba daya banda yanxu da bahijjar ta fada.
“Oh kudai baku mantuwa, ni nama manta da wani abu wai shi birthday,no wonder business partners dina keta kirana yau, i wanted to take a rest for the day naki dauka”
Dariya bahijja tayi tace “yanxu dai ki shirya mu fita, please don’t ask me ina zamuje its a surprise”
Dariya kawai nanna tayi tace “toh”
Kusan a tare suka fito ita da nanna, nanna ta saka wani lace na alfarma mai kyau peach color sai mayafi kusan same color da lace din, ta zuba dankunne masu kyan gaske sai Yalqi suke kamar diamond, tunda ta sauko from the look of yanda gidan yayi shuru tasan cewa babu kowa, duk sun fita kenan, koda suka karaso mota hamad na tsaye na jiransu.
Yana ganin nanna yayi saurin rungumeta dake yanada tsayi saida ya dan rankwafo sosai yace “happy birthday nanna”
Dabbing bayanshi tayi fararen haqoranta suka fito rass tace “thank you hamadudu, yaushe ka kara tsayi ne haka”
Dariya sukayi gaba dayansu ya bude masu kofa suka zauna ya shiga mazaunin driver ya tuqa motar.
Bahijja ta kalli nanna, wani irin farın ciki ne gaba daya ya gama lullubeta, yau zatayi testifying wannan rana kamar ta yau, abunda ta dade tana addua akai.
“Ina majeed din? Na ganki ke daya”
“Yana chan nanna, ni kadai nazo, ay dole ma nazo saboda rana irin ta yau”
Nanna bata gane me take nufi ba kawai dai ta murmusa har suka iso wajen, hamad na parking ya futo ya bude ma nanna anty bahijja ta futo ta kama hannunta.
Wani dan kyalle ta karba hannun hamad abu kamar abun yara fa suka rufe mata fuska, abunka da yan boko masu wayewa saita tafi da abun nasu suka shiga wajen din.
Suna isowa wajen hamad ya fara shiga daga ciki bahijja zare mata abun fuskan nata aka kunna haske bauu ko’ina.
Kananun yaran suka fara ihu…
“Surprise!!!!!!!!!”
Saida nanna ta kifta ido ta sake bude kafin ta fara ganin mutanen dake tsaye a wajen, anyi decorating wajen yanda kasan za ayi dan mini event, an kawata wajen da decorations na zamani, ga banners din hotonta a kafa an rubuta happy 60ths birthday, family and friends kowa ya halarta, kai waje dai masha allah duk wanda ke wajen is close to her harda business partners dinta.
Gaba daya wajen ya dauka da “Happy birthday to you..”
wani irin breath taking murmushi takeyi, kamar zatayi kwalla tsabar farin ciki, ga iyalansu kowa ya hallara, sameer ne da nashi iyalan duka, harda yan makaranta abal dake karatu a dubai, ga sufyan da matarshi, kowa dai ya hallara.
Babu abunda take fada sai “Alhamdulillah alhamdulillah, thank you so much thank you thank you, when did you plan all if this?”
Tayi tambayar bakinta ya kasa rufuwa, kowa nata kokarin hugging dinta, aka bama anne waje ta nufi inda take ta rungumeta itama tace “Allah ya karo shekaru masu albarka”
“Ameen ya Allah yaya”
Gaba daya hankalinsu bai kaiga anty bahijja ba don tana daga bayan nanna saida fadila ta hangota tukunna tace “bahijjaaaa,kamar bahijja nake gani”-
“Anne tace ba kama bane itace,”
Kyakyacewa da dariya anty fadila tayi ta rungumeta tace “wai daman zaki dawo nija yau shine baki fada min ba?”
“Wanted to Surprise everyone shiyasa nace anne karta fadama kowa, ya sameer ne kawai da nanna suka san zanzo”
Kallon ya sameer fadila tayi tace “kofa dazu saida mukayi mganarki dashi baice min komai ba akan zuwanki”
Dariya akayi gaba daya, aka fara gaggaisawa,
Maya dake zaune chan wajen da aka zazzauna kwata kwata bata tasoba tunda hamad ya shugo ya shaida masu isowar nanna, tanajin muryar mummynta kamar a mafarki tayi saurin mikewa ta tunkaro wajen,
Tana karasowa wajen sai hawaye ta taho a guje ta rungume mummyta “mummyyyyyyyyy!!!!!!”
Bahijja na jinta a jikinta tace “babyyyyyy!”
“Mummy yaushe kika dawo? Meysa baki fada min zakizo ba,”
“Daman zanyi surprising dinki ne babyn mummy, how are you?”
“Im fine mummy ina dady?”
“Daddy yana chan baizoba”
Gyaran murya anne tayi wanda yasa hankalin kowa ya koma gareta tace “lets have dinner ko”
Aka zazzauna gaba daya, masu serving suka soma zagaye da casserole shaqe da abunci kala kala, aka ajiya, wani abunma saika rantse ba cikar yan kasar bane.
Tunda suka zauna table din family gaba daya babu abunda ake sai hira, bini bini anne zata kalli nanna daketa faman murmushi tana kallon kowa dake wajen, kana ganinta kasan tana cikin farin ciki, its been long rabonda ta ganta cikin farin ciki haka.
Kananun jikoki nata yawo a waje gwanin ban sha’awa, fadila da bahijja ko nata faman hira don seat daya suka zauna, gefenta kuwa maya ce ta wani maqale mata kai kace zata sha mama, yar shagwaba kenan, laila ko me zatayi banda yi mata dariya.
Hamad da sufyan sunata hira gwanin birgewa, amaryar sufyan ko tana gefen anty mubina don akwai yar kunya tsakaninta da anty laila wato maman sufyan kenan sirikarta.
Sameer ko sai faman magana yake da mutane da aka gayyata family friends.
Ana tsaka da cin abunci ana hirarrakin yaushe gamo anne ta miqe tsaye tayi gyaran murya.
Duk kowa ya maida attention dinsu gareta, bude taron tayi da sunan Allah sannan ta fara godiya ga waenda suka halarta, sannan tayi godiya ga allah daya azurtasu da arziki mai albarka da iyalai.
Sannan ta dora da tana son tayi introducing addition to their family wanda ba kowane yasanshi ba.
Maganarta ta karshe yayi daidai da budewar kofar wajen da securities din wajen sukayi, ya sanyo kafarshi cikin wajen kowa ya juyo don ganin ko wanene, kwata kwata baisan da yawan jama’a a wajen, yana sanye da jallab fara khaal yayi nadin kundura akanshi, sai ya zamo kamar wani tauraro daya haske wajen aka bishi da kallo.
Nanna na ganinshi sai kawai murmushin dake fuskarta ya kara tsananta, anne na ganin fuskarta tayi hamdala aranta don wannan na tabbatar mata da hajara ta hakura da komai kenan.
Dakawata anne tayi da magana ta dubi anne sannan tace “bismillah hajara, bani ya kamata nayi introducing dinshi ga kowa ba face ke”
Wasu hawaye ne masu zafi suka sauko mata akan fuskarta na farin ciki tayi saurin sharesu ta miqe tsaye ta nufi inda taj yake gabanshi na dukan uku uku ya kasa dagowa ya kalli oummi dinshi.
Tana karasowa ta kama hannunshi da babu jakar daya riko a ciki yayi saurin dagowa ya kalleta ta sauke mashi murmushi ta juyo tana duban kowa dake wajen kafin ta soma magana.
“This is my one and only son Tajudeen Abdullah Taheel allah has unite us after we got separated for more than 40years Alhamdulillah”
Tana fadin haka ta maida dubanta ga taj tace “Meet my co workers and your cousins, your family”
Murmushin da zaice ya dade rabon da yayi shi da farin cikin daya manta da yinshi ne ya bayyana a fili, gaba daya sai yaji kamar an sauya mashi da duniyarshi gaba daya, haske ya bayyana a gabanshi.
Hannu nanna ta bude mashi ya rungumeta hawaye na sauka a idanunshi tana ta hamdala, its was an emotional moment kowa nata nanata 40years aranshi, wallahi abun ban tausayi da ban sha’awa, shima dai dakyar ya iya danne emotions dinshi kamar wanda ke tsoron magana muryarshi na karkarwa yace “Ighfiri li ya oummi, i will always be by your side”
“I’m sorry my son, ka yafemin”
Dagowa yayi ya kalleta yace “hawayenki masifa ne a gareni ya oumi, please karki nemi yafita ni zan nemi yafiyarki, I’m so sorry for..”
“Ya isa haka” ta dakatar dashi, “komai ya rigada ya wuce,”
Girgiza kai yayi har zuwa lokacin hannunshi na cikin nata,anne daketa faman murmushi babu abunda take sai hamdala, kowa ya kasa daina kallonsu,Bahijja tafi kowa farin ciki, shiyasa da anne ta fada mata komai ta kasa hakura dole ta nemi excuse tabi jirgi ta taho, saurin goge kwallar fuskarta tayi tana hamdala.
Maya da laila sai sakin baki, ita laila ranar da yazo ta gane shine saidai batasan da maganar cewa dan nanna bane ita kuwa maya yaza ayi ta manta da wanna Fuskar da take mararin gani koda a mafarki ne?…spoon din data duaka zatakai bakinta yafi minti biyu a haka bata saukesui ba bata kaishi bakinta ba.
Laila ta tabota tace “kinganshi ko? Shine shine wanda nake fada maki, he’s our uncle..oh my godddddd”
Gaggaisawa da kowa nanna tasa yayi, ta dunga introducing dinshi ga partners dinta, kana ganinta kasan tana cikin farin ciki da annushuwa.
Karasowa wajen anne sukayi ya kama hannunta ya sumbaceta irin yanda larabawa keyi sannan ya gaisheta, ta sa mashi Albarka, ya gaisa da ya sameer dasu anty bahijja da anty fadila, anne tayi introducing dun kowa,sauran yaran kowa ya dunga gaishesa anne tasa ya zauna kusa da seat dun nanna dake kusa da nata.
Kai wannan family saidai ace masha allah, duk wanda ya gansu sai yayi alfahari dasu, don allah ya albarkacesu da komai, zuri’a ta gari, kwanciyar hankali babu fita babu tashi hankali ga hadin kai.
Hira sosai ta karade, dukda bashida yawan magana haka suka dunga janshi da surutu, amla na jikinshi tana kama gemushi, sauran samarin ko duk haduwarsi da ji da kudi da suke dashi suna arba dashi suka raina kansu, ya sameer ne ana cikin hira ya jefo mashi tambaya trying to get to know him, “what do you study?”
“Mechanical engineering” ya bashi amsa kai tsaye yana murmushi, gaba daya duk kallonshi sukeyi wannan yasa ya kasa sakewa.
“Wow thats very interesting, kana aiki?”
“Yes..I’m into manufacturing of cars” ya bashi amsa
“Masha Allah,” ya sameer ya fada, abal dakeda interest akan motoci yayi saurin cewa “wow, uncle taj, are you a developer?”
Dan murmusawa taj yayi ya dubeshi ganin yanda yake kallonshi yana ganinshi ya gane bazai wuce irin 22 dinnan ba, saiya tuna mashi lokacin da yana kamarshi.
“Yes i am, i’m the founder of Fords motor”
Baki sake abal ya bude duk suka bishi da idanu harda sameer, abal kamar zai rungumoshi tsabar excitement yace “oh myyyyyy… you’re the founder of fords???? The whole fords?, T-ford?”
Dariya taj ya danyi don shi ya fada ne kamar irin ay ba wani abu bane, ganin how interested he is yasa taj cewa “looks like you’re interested in this field”
“Yes i am, wow thats hugeeee, dady kasan kamfanin fords? Motocin fords fa? That one of the best cars around the globe,”
Sai a lokacin anne ta dubeshi tace “that’s impressive, at the age of 33 you have achieved this? Wow…I’m so proud of you masha Allah”
Murmushi kawai yayi ya dubi nanna daketa kallonshi kamar ta maidashi ciki ahankali tace “i’m so so proud of you”
Kamar an tsundumashi a aljanna haka yaji, bai taba sanin cewa akwai wanda zasuyi murnar daukakarshi ba sai yanxu…he feels like boyewar identity dinshi batada amfani yanxu.
Maya fa har zuwa lokacin ta kasa dawowa hayyacinta, babu abunda take sai kallonshi, sau daya ya dago ya kalleta lokacin da kowa ke intoducing kanshi, tundaga lokacin bai sake kallonta ba.
“Uncle taj why haven’t you visited us?” Laila tayi tambayar dayasa kowa kallonta, honestly tayi tambayar amma ganin yanda kowa yake mata wani irin kallon yasa tayi shuru ta suake kanta kasa maminta kuwa me zatayi banda harararta, taj ko ya kasa cewa komai nanna ma jikinta yayi sanyi.
Anne ce tayi gyaran murya tace “ya kamata mu koma gida haka nan its past 10pm.”
Shirye shiryen komawa gida aka somayi aka fito gaba daya, yawanci waenda aka gayyata duk sun tafi, sai yan gida.
Katuwan lexus din gidan guda biyu kowa ya shishiga,anne ta dubi taj tace “ina fata ka gama clearing da chan masaukinka don bazaka koma hotel dinnan ba”
Murmushi yayi yace “insha allah anne”
Abal dake zaune mazaunin gaba yanajin haka yayi saurin fitowa yace “can i join you uncle taj?”
“Yes sure!” Ya bashi amsa tare da rufe kofar da anne ke zaune ya zagayo inda nanna ke zaune yace “allah ya kiyaye zan biku a baya”
Murmushi nanna ta mashi, lallai haihuwa nada rana, bakinta kamar baka farin cikinta baya misaltuwa tace “allah yayi maka albarka”
Wani irin dadi yaji aranshi mara misaltuwa ya amsa da ameen driver yaja suka bar wajen.
Shida abal suka nufi wajen zabgegeiyar motarshi, ya tada suka bisy a baya.
Abal ya dunga mashi hira kamar ba gobe kafin sukai dai saida taj ya gane yanda abal ke son motoci kamarshi, gashi he’s so smart.
Lokacin da suka iso kowa ya rigada ya shiga cikin main house, booth dinshi ya bude abal ya dauko mashi classy LV luggage dunshi, daidai nan hamad ya futo daga cikin gidan, yana hangosu ya karaso inda suke sannan ya jagoranci taj din zuwa masaukinsa.
apartment din dake gefe kusa dana anty bahijja hamad ya bude,yawanci irinshi ne ma aka bama sufyan da amaryarsa duk sanda sukazo hutu anan zasu dunga sauka.
Duk apartment din sun zagaye main house, saboda ahalain ya dunga expanding yasa akayi part part din, tunda gashi duk samarin tasowa sukeyi kuma zasuyi aure duk me so zai iya zuwa yayi zamanshi.
Suna shiga abal ya shiga da luggae dinshi har ciki, an suya komai na ciki apartment din, interior din part din black and white, so esthetic babu wani abun hayaniya, parlor ne a kasa dayasha english kujeru sai dining wajen kitchen sai kuma sama bedrooms guda biyu, daya master dayan kuma second bedroom, suma dai Masha allah.
Kafin su futa hamad ya shaida mashi nanna tace he should settle in and rest zuwa gobe saiya shugo main house sannan idan yana buqatar wani abu ya nemi hamad din, nan sukayi exchanging contacts, abal kam tuni ya karbi nashi number din tun a mota, Suna futa ya sauke wata ajiyar zuciya yabi ko’ina da kallo, komai goes to his taste dayake shi bamaisan hayaniya bane.
Sama ya wuce zuwaga bedroom din shima ko’ina fess fess a gyare babu kazanta ko kadan.
Setting in ya soma yi kafin ya shiga bathroom ya watsa ruwa ya fito ya saka jallab, lokacin wajen karfe sha daya ya tada kabbarar sallah, tunda ya fara sallah abi zauna ba har wajen karfe uku babu abund ayake zai godiya ga Allah daya nuna mashi wannan raya, ta bangaren nanna ma bata iya barshi ba haka ta kwana tana godiya ga Allah, gaba daya a ranar babu wand atakema addua kamar taj.
Sai wajen karfe uku da rabi ya iya tashi ya kwanta kan kace me wani irin ni’imataccen barcin da ya mance rabon da yayi tun bayan tafiyar sabeeha yayi shi.
He sleeps peacefully kamar wani baby, gaba daya ji yake kamar an cire mashi 90% of damuwarshi.
Kiran sallar farko a kunneshi, koda ya bude idanunshi ya dauka mafarkin komai yayi sai yaga zahiri ne, this is the life he dream for him self,yanajinshi kamar he’ss complete, a take zuciyarshi ta raya mashi how he can’t be complete without her, tunaninta da yake hana kanshi saiya kasa gaba daya, memories dinsu ya dawo mashi kamar anyi rewinding, daman ance sai an samu kwnaciyar hankali ake wani tunani, don har steamy moments dinsu saida ya dunga zuwa mashi, ya mafi tsaya mashi arai don gaba daya yasa jikin shi yayi wani irin sanyi, akanta yasan he’s a man, very needy man infact theres a needy monster inside him that makes him crave for her presence, her scent, her breath and her boobs.
Shagalcewa fa yayi ya kasa tashi gaba daya yana tunanin sabeeha, watanni nawa kenan ya kasa cireta aranshi, kai dukyanda za ayi dole ya nemota.
Kiran sallah na biyu ne yasashi tashi dakyar ya wuce bathroom kamar wani mara lafiya, ya sakarma kanshi ruwan zafi sosai kafin ya danji dama dama sannan ya futo a gaggauce ya saka jallab da wani cute ovy black slippers ya sauko kasa lokacin har an fara tada kabbara.
Da suka shugo estate din gidan ya hango masallaci daga gefe wannan yasa yana futowa ya nufi wajen,yana dab da shuga ya sameer dasu abal da sufyan harma da hamad suma suka karaso gaba daya suka shiga masallacin sukabi sallah.
Suna idarwa bayan sun fitfito ya gaggaisa da kowa, ya sameer ya bashi hannu su abal da sufyan suka gaishesa hamad ma ya gaishesa a mutunce kafin ya koma part dinshi.
Barcin da bai koma ba kenan ya bude laptop dinshi ya fara aiki, da duban report din da merk ya tura mashi.
Karfe takwas daidai wayanshi tayi ringing, number anne ya gani wannan yasashi saurin dauka ba tare da wani tunani ba yayi sallama ya gaisheta cikin natsuwa.
Ta tambayeshi ya kwanan sabon waje? Sannan yana buqatar wani abu ko wajen bai mashi ba ko yana san a sauya abubuwan da aka saka mashi, yace mata ah ah, babu komai, kuma hes so grateful for everything.
Nunfasawa tayi sanna tace mashi ya shugo main house yayi breakfast yanxu yace mata toh.
A gurguje ya shiga wanka ya fito ya kintsa cikin jallabiyanshi this time around black jallab ce ta amshi skin dinsa sosai kunsan ance black and white idan aka hadu bade kyau ba, gashi morning face dinshi is so breathtaking.
Wayanshi kawai ya dauka ya saka black slippers dinshi da suka fidda yatsun kafarshi doyage sannan ya futo ya tunkari main house, babu wani nisa baifi taku ashirin ba yakai aka bude kofa ya shiga daga ciki, rabi dake jera abunci a dining tana hangoshi ta kasa dauke idanunta,har chokalin hannunta da take jerawa a dining ya subuce, “allah gamu gareka,” ta furta a hankali hadiza ta bita da ido, kafin ta maida dubanta ga taj wanda rabi ke kallo, ay saita fi ma rabi rudewa, cha take “wannan waye kuma kamar balarabe a gidannan”
Rabi ta juyo tace “zaki zubarda coffee din, ta galla mata harara.
Maya dake zaune hadiza na zuba mata coffee tana jin abunda tace yasa tayi saurin miqewa da cup din coffee din a hannunta ta nufi inda suke tsaye ta hangoshi a taaye a wajen ya taaya ganin babu kowa a kasan.
Maya uwar kaudi tayi saurin karasowa inda yake kamar zata fadi har tana hardewa gab da inda yake nesa dashi kadan coffee din ya subce mata ya fadi kasa cup din ya fashe, daidai wajen yatsun kafafunshi dake bayyane tayi saurin cewa “oh my god im so sorry…”
Muryarta ce da yanda event din ya faru yasashi ganseta lokaci guda, the girl that split mocktail on him that very day”
Yi yayi kamar baisan da ita a wajen ba harta tsugunna daidai nan anne ta sauko ya karasa inda take ya kama hannunta ya sumbaceta, wannan alada taqi rabuwa dashi mufa nan bama haka a nigeria lol…
“Good morning Deen, how was your night?”
“Hamdullah!’” Ya bata amsa,
“Kaje sama kayi breakfast wajen oummin ka,”
Murmushi yayi mata shidai kamar bashida baki yace “okay an…ne”
Kiran rabi anne tayi tasata ta kaishi har part din nanna, ta jagoranshi bayan ta gaishesa har zuwa oart din sannan tayi sallama da
Nanna a bedroom dinta ta shaida mata da zuwanshi, yana daga zaune sitting room din
Tunda ya shigo gabansa ke faduwa dab dab dab ya rasa dalili amma yana alaqantashi da wani abu da yake jinshi mafi kusanci da zuciyarsa, futowa rabi tayi tace mashi ya shiga ciki, yana shiga daidai nan sabeeha ta fito daga dakin da take kwana tun lokacin da rabi ta nuna mata.
Rabi na ganin futowarta don tana gab da futa tace “baku tafi ba?”
“Eh yanxu zamu tafi ina kwana anty rabi”
“Lafiya ta amsa ta”
Ta dauka kasan zata sauko sai taga ta nufi bedroom din nanna har zatayi kncking rabi ta dakatar da ita tace “me zakiyi?”
“Daman zan ce mata na tafi ne?”
“tanada baqo a ciki, ki tafiyarki kawai”
Da toh sabeeha ta amsa mata sannan ta bi bayan rabi suka sauko kasa tana dafe kirjinta.
Tun jiya da daddare gabanta ke faduwa ta rasa dalili
,nanna na zaune kan carpet an jera breakfast hannunta rike da coffee sai news papers dake hannunta ta dago ta kalleshi ta sauke murmushi tace “come in bismillah” ta mashi nuni da gefenta wajen carpet din.
Zama yayi cikin biyayya ya gaisheta irin gaisuwarsu, nanna ta tambayeshi how was his night yace mata alhamdulillah sannan da kanta ta mashi serving abunci tace bismillah.
Yanajin abun kamar a mafarki ba gaskia ba, yau gashi ga mahaifiyarsa, bini bini nanna ke dagowa tana kallonshi tana murmushi, harya cinye tass baima san ya cinye ba tunda yazo baici abunda ya mashi dadi ba kamar wannan.
✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊
MATAR TAJ (destined with you🩵🤍)
Written by
QueenmarhBook2
PAID