Chapter 98
Matar Taj Part 2 Complete Hausa Novel. · about 30 min read
After 2 weeks..
Cikin sati biyun nan taj bai samu sukuni ba, duk wani registered agencies da ake kai yan aiki saida salim ya nemo masa sukaje neman ta, amma kwata kwata babu mai kamaninta a record dinsu, dukda haka baiyi giving up ba.
Shidai salim baisan dalilinsa na neman wadda yake nema ba don bai fada mashi ba amma ganin yanda ya dage sosai yasan cewa yarinyar is very important to him.
Amma me zaisa mai kudi kamarshi yana neman yar aiki? Anan nigeria? Ya tuna da lokacij daya taba tambayarshi meya kawoshi Nigeria ya shaida mashi its something personally important.
Fada mashi da babanshi yayi cewa taj din is someone that is very important to their business yasashi dagewa don neman yarinyar.
Yau ne last day of the semester, wanda ya kasance ranar da zasu gama last paper na exams dinsu.
Sabeeha tunda suka fara exams ta kebanci kanta da komai, da duk wani abu da zai jawo mata fitina da maya.
Tunda taga kiri kiri mayar ta tsaneta don tundaga lokacin datayi mata sharrin sata ta gane binta take da sharrin.
abun da sabeeha bata taba expecting ba shine anne data yarda cewa ba itace tayi satan ba, dukda bata fadi cewa maya ce tayi mata sharrin ba, da farko dataga reaction din maman maya da yanda ta yarda lokaci guda kan cewa itace tayi sata saiyata jin kowa ma yarda da hakan zaiyi, saitaga akasin haka
Wannan yasa ta kudurci duk avubda zai faru bazata taba bari tayi abun da zaisa anne ta zama disappointed da ita ba.
Misalin wajen karfe biyar na yamma hamad yazo ya daukesu daga school, gaba dayansu daga yanda suka fito zaka gane wxams din ta jijiga su, hamad ya tambayesu how was the exam laila ce kawia ta iya amsa shi.
Yana tuki ya juyo ya kalli sabeeha ganin yanda ta rakube tayi shuru, ba tun yanxu ba ya lura gaba daya ta chanza, yanda take ada yanxu dukta daina, abunda ke hadashi da ita gaisuwa ne kawai daga haka bata sake cewa komai, she’s trying to be invisible a gaban su gaba dayansu, daman don hamad na tsaya mata ne yasa maya ke jin haushi ita da ba kowan kowa ba.
Wannan abu na damunshi sosai ta dawo yanda ya fara saninta, babu walwala babu fara’a.
“Fatima how was your exam?”
Ya jefo mata tambaya,shuru bahu response saida ya sake cewa “fatimaa!”
Firgigi ta dawo daga dogon tunanin data fada, “naam”
“How was your exams?”
“Alhamdulillah” tana fadin haka ta maida kanta ga glass window din mota ta cigaba da tunanin datakeyi.
…….
Da daddare rabi ta shigo part din anne da sallama ta gaida anne kafin ta soma mata bayani.
“Hajiya daman bilki ce tace kawunta ya kira zata koma kauyensu don an saka ranar bikinta nanda sati biyu”
“Toh Masha Allah shine basu fada da wuri ba”
“Eh wai itama batasan an badata bane, kisan auran kauye basa neman shawraar yayan tun suna kananu suke bada auren su” rabi ta bata amsa cikin ladabi.
“Toh kice mata ta nace ta kira kawun nata yazo cikin satin nan kafin ta koma, karsu mata komai na kayan daki na dauki nauyin wannan”
Cikin murna rabi tace “toh allah ya saka da alkahiri hajiya allah ya buda”
Ta amsa da ameen.
Rabi na barin wajen anne ta sami bilki ta fada mata komai, a take ko ta kira kawunta ta shaida mashi komai.
Washe gari da safe kowa ya hallara kan dining, anne, nanna, maya sai laila data kwana a part din nasu don sun shirya yanxu ita da mutuniyar tata sai kuma hamad da shugowanshi kenan.
Karasowar taj yasa duk suka maida hankalinsu gareshi, maya da laila suka gaishesa, hamad ma haka shi kuma ya gaisheda nanna da anne kafin su fara karyawa.
Hira sukey jefi jefi kowa ya maida hankalinsa ga abuncin da yakeci banda maya data kureshi da ido, laila tana ankare da ita don ba tun yanxu ba ta lura da hakan.
Shine ma ya fara tashi ya futa bayan ya gama saboda kiranda salim ke mashi.
Nanna ga tambayeshi harya gana yace mata eh zai dan futa ne, bata tambayeshi ina ba saboda yanxu kam ay ya san gari kuma yanada nashi privacy din avubuwa shiyasa bata tambayehsi ba ya futa.
Yana barin wajen maya ta sauke ajiyar zuciya, lailanta kalleta da mamaki.
Bayan sun gama dinner laila da maya na zaune dakin maya laila ta kaleta tace “wai kallon nan da kikema uncle taj na menene?”
Kallonta maya tayi tace “is there a problem inna kalleshi?”
Dariya laila tayi tace “maya are you crushing on uncle taj? If you are kima ajeshi a gefe, he definitely has someone”
Rai a bace maya ta kalleta laila na ganin haka tasan cewa maya has feelings for him.
“Shi yace maki he has someone??”
“Ke yanxu kina ganin yanda ya hadu ya gaji da haduwa, gashi mai kudi sosai kuma daga saudi yake saiki yarda idan akace maki bashida wadda yakeso, balarabiya yar kasarsu?infact banajin akwai yar nigeria da zata iya zama on his league”
Cije lebe maya tayi har yana fashewa kadan jini ya futo lokaci guda yanayinta ya sauya, tace “karya ne wallahi, karya kikeyi banza dallah zoki futa karki bata min rai”
Yanda take magana kamar zata hau kan laila, laila tayi saurin cewa “it looks like ba crushing kadai kike ba maya, badai son uncle taj kike ba? Don’t start dreaming what’s impossible don wallahi yafi karfinki”
Wannan magana da laila tayi mata kamar ta chaka mata wuqa a wuya haka takeji, rai a bace ta kalleta tace “you wanna bet on him?”
Laila najin haka tace “uncle taj din? Bafa yaro bane”
“You wanna bet on him or not? Don ni zan nuna maki cewa idan har inason abu saina sameshi no matter what, karkiga wai yana da kudi kuma halfcast ne wallahi i will make him fall for me, you wanna bet??”
Dariya sosai laila ta tunda yi tana kallonta tace “okay..lets see”
….
Bayan futarshi bai tsaya ko’ina ba sai inda zasu hadu da salim, daga nan suka wuce inda zasuje.
Tun a mota salim ya soma mashi bayanin kananun agency din da yanda suke operating wajen, kuma a gaskia illegally suke shigar da mutane kasar waje don gaskia gomnati batasan da zamansu ba.
A tare suka shiga wajen, irin local agency ne haka duk wani hanya da akeyi ta cuku cuku sunayinta, duk kasar da kake son zuwa don har visa sunayi ma.
Yara ko kauye kauye suke zuwa daukansu ana masu training akaisu wata kasar don aikatau.
Da farko masu kula da wajen kin basu hadin kai sukayi saida salim ya basu maqudan kudade tukunna kafin su kaisu wajen ogansu.
Suna zuwa ba tare da wani bata lokaci ba suka mashi bayanı, kudi babu abunda baya saka mutun yi, koda suka bada sunanta da hotonta da kuma inda tayi aikatau da shekarar, a take mutumin yasa yaranshi suka fara bunciken yaran da suka tura saudiyya shekara biyu da suka wuce.
An samu fatima’s da yawa saidai kwata kwata babu mai kama da ita daga ciki, su da sukaga hoton sabeehar ma daya bayar sun dauka ko batan hanya yayi, suda suke kwaso yan qauye, kowacce yarinya idan zasu turata saisun dauki hotonta, information din iyayenta, gudun samun matsala.
Har zasu bar wajen wani tunani yazo mashi, tunda yake nemanta da fatima yake amfani bai taba kawowa ko ba sunan take amfani dashi ba sai yanxu da abun yayi clicking a mind dinshi, ya dubi salim yace su nemi idan akwi mai suna sabeeha.
Take salim ya fada masu suka fara dubawa, suna daga zaune yaron dake buncikowa ya shugo da file din mutun daya da aka samu da irin sunan, baisha wahalar samu ba saboda sunan is unique.
Da aka kawo file din saida gaban taj ya fadi, har sauri yake ya bude don ya tabbatar da ita dince, yana tabbatar da ita dince ya sauke wata ajiyar zuciya, duk yanda kamanninta ya banbanta da hoton daya nuna masu bai hana shi ganeta ba, lokacin gaba dayanta babu cimar kirki a tattare da ita tayi wani irin baqi sosai, gashi dukda ta rufe bakinta saida gatson nan ya futo.
“She’s the one” ya fada beneath his breath, ya dubi salim yace su fada mashi inda zasu sameta yanxu yanxun nan, zai basu ko nawa ne yanason su fada mashi komai game da ita.
Salim ya fada masu tare da ajiye masu kudade dayawa a gabansu.
Ogan dayaga kudade take yasa cikin yaronsa su nemo mashi yar wani gari ce, kuma ta dalilin waye aka kawota aikatau, masu daukosu sunada yawa don kowanne gari akwai agent dinsu.
“Wannan yarinyar oga jamilu ne ya kawota”
“Wani jamilun?” Ogan ya tambaya.
“Jamilun dake dutsen habuja, yar dan uwansa ce”
Salim ne ya fasaara masa abunda sukace, sannan ya buqaci sanin inda zasuga jamilu, ogan yace ay agent dinsu ne bari ma
Ya kira sa.
Yana kiran jamilu wajen saunuku bai dauka ba, taj ya buqaci address din jamilun ogan give su dawo zaisa jamilu yazo har office dunshi.
Taj baiso haka ba dan ya matsu sosai, yanajin kamar bazai iya jura har zuwa gobe ba.
Suna barin wajen daya daga cikin agent din yayi saurin kiran jamilu, aiko yayi saurin dauka, daman jiran kiransa yake tundaya kirashi yace mashi karya amsa kiran oga, akwai matsala.
yana dauka ya fada mashi komai sannan ya shaida mashi yanda suka sakarma oga maqudan kudi don neman yarinyar dakyar inba matsala aka samu ba.
Daman gaba dayansu baki daya agent din harma da ogannin shiyasa suke tsaka tsantsan don business dinsu illegal ne.
Da farko jamilu shi harya mance da wata sabeeha daya kawo agency din saidaga baya ya tunata yar hadiza kawar jamila matarshi, shifa gaba daya ya tsorata sosai jin ance masu kudi ne suka zo nemanta kuma harda balarabe saiyayi tunanin ko kisan kai tayi achan kasar ne ba a gano gaskia ba saida aka maidota nigeria,sai yanxu ake nemanta gashi ya shugarda sunansa a matsayin mariqinta.
Yana tsaka da buga bugarsa ya koma gida ya hau kan jamila da bala’i, “mun shiga uku jamila, yarinyar nan kisan kai tayi ake nemanta, ki kira uwarta wallahi tallahi babu ruwanmu, ke kikace mu taimaka masu a turata aikatau, yanxu danace ni marikinta ne idan ba a ganta ba aka kamani fa?”
Kokarin kwantar mashi da hankali jamila tayi harda kwada mata mari, “me gida dan allah ka kwantar da hankalinka”
“Ina zan iya kwnatar da hankalina shin kinma san inda suke? Wallahi jamila idan kika sani matsala igiyar aurenki ce zata tsinke, haka kikasani muka aurar da ba tare da sanin uwar tata ba, muka cinye kudin da aka bamu yanxu idan wani tsoho ne fa aka aura mata gidan aikin nata ta kasheshi ta gudo ba a sani ba sai yanxu? Shin kinma san inda uwar tata take kuwa? Idan hadiza ta gudu fa?”
Jamila na hawaye ta kalli mijin nata tace “wallahi mai gida zan nemota bazanma fada mata me ake ciki ba sainaje naga inda take”
“Toh wallahi tallahi kiyi hanzarin zuwgobe goben nan ki shaida mata yauwa ehe”
Tana fadin haka ya fuce.
Jamila jiki na bari ta soma dialing layin hadiza tana dauka ta soma magana “hadiza akwai matsala..”
“Wace iriyar matsala jamila”
“Ki tura min adireshin ki gobe zanzo muyi magana”
Hankali tashe hadiza tace “ki bari ni zanzo goben”
“Ah ah tunda nace maki ki bari zanzo kawai”
Da haka sukayi sallama.
Tunda taj ya koma gida gaba daya yaji ya kasa sukuni, ya rasa mai zaiji aranshi dadi ko rashinsa, zai iya fuskantarta kuwa? Da wani ido zai iya ganinta? Gaba daya abun ya addabeshi ya kasa cin komai.
Misalin wajen karfe tara na dare nanna ta kirashi ganin ko dinner baizo yayi ba tunda ya fita da safe, daga yanda yake amsata ta gane kamar yana cikin damuwa, ta tambayeshi ko baya jin dadi ya shiada mata yayi loosing appetite ne kawai and yayi dinner tare da abokinsa kafin ya dawo gida.
Hankalinta bai kwanta ba ta sashi yazo part dinta.
Dole ya shirya ya wuce main part, tunda ya shugo yakejin sautin kwanuka daga wajen dining da Alamu kamar tattara wajen akeyi, sai maganganu dake fitowa daga wajen,bai kalli wajenba ya tunkari hanyar stairs yana dora kafanshi kan stairs din farko ya tsaya chak
“Subhanallahi Ya akayi ya fashe?” Rabi data tunkaro wajen dining din tayi interrupting dinsu ,
maya data matsa gefe ta kalli rabi tace “ya kike kallona, ga wadda ta fasa nan saboda tana baqin cikin masu gida, tana bakin cikin ganin munaci da luxury plates bata taba ci akan irin plate dinba bari ta fasa dan mugun hali”
Sabeeha da ranta ya gama baci ga baqaqen maganganun data gama gaya mata ta watsa mata juice a jiki da gangan dukdan saboda ta buqaci a dafo mata indomie ta dafo sau uku tana cewa baiyi dadi ba sai an sake shine sabeehar tace taje ta dafo yanda zai mata tana shirin barin inda take ta watso mata plate din da indomie din a kasa plate din ya fashe.
Dukawa tayi ta soma kwashe plate din rabi ta karaso inda take kasa kasa da murya tace
“Garin yaya kika fasa? Kina menene?”
Amsanta sabeeha tayi itama yanda daga ita sai rabi ne zasuji tace.
“Wallahi anty rabi Itace ta fasa,”
“Barshi kije ki dauko tsintsiya karkiji ciwo a hannu”
Da toh ta amsata tare da nufar hanyar kitchen daidia nan ya karaso wajen dining din don tabbatar da muryar da yaji mai kama data sabeeha dayaji a kunneshi.
Saidai kashh yana isowa wajen ta shige kitchen sai dan glance din bacewarta a wajen daya gani.
Kallon rabi yayi dake tsaye sai maya tafayi saurin mikewa ganinshi ta sauke wani irij murmushi,
“Ina wuni yallabai” baijin hausa amma yanda rabi tayi magana ya gane gaishesa tayi, da mamakin kansa baima san ya iya kalmar ba yace “lafiya” ashe dai ya fara dan koya Kadan kadan.
Maya ta taho inda yake cikin kaudi kamar ba itace ta gama cin mutuncin sabeeha ba ta zauna tana harare harare itama rabi bata tsira ba don rashin kunya take mata
“Hey uncle taj….do you need anything?”
“No thanks” ya bata amsa ba tare da ya sake kallonta ba ya dauke kanshi ya juya, daidai nan sabeeha ta karaso”
Rabi ta girgiza kai tace “wannan yarinya akwai munafuka, ji yanda takeyi kamar ba yanxu ta gama sababi ba”
sabeeha data jita ta dago ta kalli inda rabin ke kallo, bayanshi kawai ta kurama idanu har suka bace kata daga gani, “ya kika tsaya? Tattare wajen” rabi ta mata magana.
Sama ya wuce maya ta bishi a baya tana karemashi kallo ta bayan, few steps ne tsakaninsu don yanajin takunta amma hankalinshi baya jikinsa yana ga muryar dayaji datake kama data sabeeha, toh kodai yawan tunaninta ne yasashi yakejin muryarta yanxu kuma?and he feels her presence a ko’in.
Daidai wajen shiga part din nanna ta dakata harya shige daga ciki kafin Ta koma daki tana murmushi.
Washe gari…
Tun wajejen karfe sha daya jamila ta kira hadiza ta tura mata adireshin gidan, sannan ta shaida mata tana nan tafe.
Hadiza fa bata kwana kalau ba don zuwan jamila da kiran da jamila ta mata dagaji ba na alkahiri bane.
Hadiza ta futo daga dakinsu ta rabi dake kitchen, “rabi dan Allah kiyi ma security magana yar uwata zata zo”
“Hajiya tasan da zuwan bakuwar taki?” Rabi ta tanbayeta
Rai a bace hadiza tace “yar uwatace zatazo kuma hajiya ta santa”
“Toh naji” rabi ta fada tare da cigaba da abunda take.
Hadiza kamar ta shaqeta dan baqin ciki.
Daga chan wajen security aka kira cikin gida, daman rabi ce sukeda access da ita suka tambayeta akwai mai expecting bakuwa tace eh, suka tambayi suna tace masu su barta ta shugo.
Jamila fa tundaga bakin gate idanu suka raina fata ta dunga wiki wiki dasu tana rarrabawa, aranta babu abunda take fadi sai lallai hadiza ta debo ruwa, kut…aljannar dubiya saimai rabo”
Futowar hadiza ta backyard ta hangota daga nesa cikin sauri ta karaso insa take, “jamilaaa…”
“Naam hadiza, anan kuke? , bura..ubanchan kaiii, lallai hadiza kinyi wuta, kunama mai zafin dafi”
“Muje daga ciki” hadiza ta fada tare da jan hannunta sukabi ta backyard.
Ta kitchen din suka wuce jamila suka gaisa da rabi kafin hadiza takaita dakinsu.
Suna shiga daga ciki hadiza ta karo kofa harda saka key jamila har an hau gadon zamani an zauna ga ac na buga dakin.
“Bamu gaisa ba ko? Hankalina yayi gaba naga duniyar arziki”
“Jamila ina magnar gaisuwa kin sani cikin tashin hankali? Ey?”
“Ay kya bari nasha ruwa ko? Ina yar taki?”
“Wacce daga ciki?” Hadiza tayi tambaya, jamila ta kyalkyale da dariya.
“Jamila yanxu ba lokacin dariya bane, ki fada kin meke tafe dake? Wace matsala ce ke tunkaro mu”
Gyara zama jamila tayi ta yaye mayafin dake kanta tace “wannan yarinyar nemanta ake,”
“Wa kenan?”
“Kinsan wa nake nufi, jiya jamilu yazo gida ya shaidamin wai wasu mutane masu kudi sunzo har agency dinnan nemanta, kuma da alamu yanda suke kakkashe kudi don ganin sun ganota babu tantama kisan kai tayi ko kuma sata tayi ake nemanta”
Dafe kirji hadiza tayi tace “na shiga uku ni hadiza? Kisan kai?”
“Kwarai kuwa, kuma kinsan cewa jamilu shine ya kaita wajennan a matsayin marikinta, duk wani abu datayi shi za a fara kamawa saboda haka wallahi tallahi kisan nayi,“
“Na shiga uku ni hadiza, kin tabbar kisan kai yace maki tayi?”
“Ah ah fa, hasashen mu ne inba haka ba meysa masu kudi haka zasu dunga nemanta eyy?”
“Jamila wallahi wallahi bazan dauki asara ba, tun ban cimma buri na ba a duniyar nan”
“Toh ya zakiyi? Daman dalilin zuwana kenan,dan wallahi igiyar aurena na hannunki, jamilu yace zai iya sauwwake min wallahi, ki kwasheta ku koma lafiya kawai inyaso saiki dawo”
“Jamila bazan iyaba,nayi kokarin yin haka tun ba yanxu ba”
“Toh kina nufin idan akazo a kama mu kenan?”
“Ah ah jamila zanyi tunani akai”
“Gwara dai kiyi tun wuri, ki debo mi dan abun kamusawa mana naci arziki kafin muyi arzikin?”
….
Sama rabi ta hau sai gata da anne sun sauko har kasa, zuwa sitting room.
Wani mutumi ne a zaune don ya dan manyanta, an aje mashi bottle water da snacks a gefe yana daga zaune a kasa.
Daga ganinshi zakasan anji jiki don yana sanye da wata riga yar shara da wando blue fatau an kure adaka, sai wage baki yake da yayi jaja saboda cin goro.
Gefenshi bilki ce zaune tana sanye da hijabi sai kayanta dake cikin jaka mai kyau, ka ganta fess fess tayi bulbul abunta.
Anne na karasowa ya sake gyara zaman babbar rigarshi dake kan yar sharar, “sannu hajiya sannu hajiya”
“Sannu dai” anne tayi magana kafij ta zauna
“Ina wuni hajiya? Mun sameku lafiya?”
“Lafiya lau alhamdulillahi ya mutan gida?“
“Lafiya kalau kalau kalau hajiya”
Kana ganinshi zakace wani burkitaccen mutun ne amma da hankalinsa tsabar duniya ta bugi idanunsa ce.
“Kaine kawun nata?”
“Ee nine hajiya”
“Toh Masha Allah”
Matsowa rabi tayi da kudade aqalla zasukai wajen 500k ta aje gabanshi anne tace “ga wannan ayi mata duk wani hidiman biki, idan akwai abunda yayi saura ma saita bilkin ta kira”
Kamar zai taugunna mata haka yake ji, sai faman gadiya yake kmar bai taba rike kudi kamar irin wannan ba.
“An gode hajiya an gode sosai, bilki marainiya bazatayi kukan maraici ba kun mata komai hajiya an gode an gode”
“Ba komai Toh bilki saduwar alkhairi allah ya bada zaman lafiya ya sanya alkahiri”
“Ameen duk suka amsa a tare bilki harda kukanta suka futo daga gidan bayan tayi sallama da kowa, basira harda hawaye, rabi ma saida taji wani iri haka sukayi sallama suka futa.
Suna fita ya chusa kudin cikn babbar riga ya zaro goro ya fara tauna.
“Wallahi idan baki kirani ba zaki ga daaowata hadiza na fada maki,”
“Kai jamila kamar babu yarda tsakanin mu?”
“Ke hadiza ba abar yarda bace ni kadai nasan koke wacece.
Dahiru har zai wuce ya dakata ya kare masu kallo musamman jamila.
“Jamilan zango???”
Jamila najin sunanta da ake kiranta dashi lokacin da suna en mata ana shan duniya ta juyo da mamaki,”
Tana ganin dahiru gabanta ya bada dan daran dammm, dariya ya kyakyace dashi irin ta manya yace “jamilan zangoo, ashe rai kanga rai? Ah madallah”
“Kin sanshi ne?” Hadiza tayi magana tana kallonta ganin gaba daya bata cikin hayyacinta hankalinta ya tashi.
“Koba jamila bace wannan?”
Ya sake tambaya ganin tana kakkauda kai, “ay ko barci nake na tashi dole in ganeki jamila ta”
Jin haka yasa jamila cije lebe ta juyo ta kalleshi tana yaqe tace “dahiru kenan, kana nan dai yanda kake an buga duniya an barta”
“Kwarai kuwa, yaushe gamo? Rabona dake shekara wajen ashirin da yan kai, har kinyi aure ko ay hikenan kin barni”
“Kaifa ka fiye hauka, an girma ba a san an girma ba mteww”
Kallon hadiza yayi har yana motse idanu kafin yace “wannan ba kawarki bace? Har yanxu kuna tare? Lallai amincinku mai karfi ne ba itace Wacce kika…”
“Dahiru.. me kazo yi nan ne?”
Tayi saurin dakatar dashi hankali tashe, “yar dan uwana ce take aiki anan zan aurar da ita kinga mun kwana biyu ko?” Ya fada yana yage baki.
“Kwarai na gani kuwa”
“Ke yama sunan masu gidan?” Ya tambayi bilki tace “gidan alhaji santuraki”
“Ku meya kawoku nan anguwar?”
“Bani lambarka zan kiraka anjima” jamila tayi cutting conversation din, ya zari wata yar nokia ya bata number.
Zasu wuce bilki tace “sai anjima hadiza na tafi”
“Toh bilki” ta amsa ta.
Suna barin wajen hadiza ta dubi jamila tace
“? Ina kika san wannan jemamman kamar wani dan wiwi”
“hadiza mun shiga uku dahiru ne,”
“Wani dahirin?”
“Ke amma jakace, shekaru ashirin da uku da suka wuce….”
Ay bata karasa ba hadiza ta kama haba tace “ke da shi?….”
“Shine, hadiza dahiru bashida kai wallahi, inata yi maki signal mubar wajen kika kasa ganewa, dan wiwi ne wallahi bashida kan gado, tunda har ya ganmu akwai matsala”
Haka suka tsaya kana ganinsu zakasan basuda gaskia kwata kwata.
Dahirun da bilki na barin wajen ya dubeta yace “ina kikasan wadda naji kik kurata da hadiza”
“A gidan da nake ayki suke ita da yarta”
“Yarta?”
“Eh kawu”
“Tun yaushe suke gidan?”
“Zasu kai wata shida a gidan” ta bashi amsa
“Ta manyanta da batada aure dana jarraba sa’a ta”
Dariya bilki tayi sanin yanda kawun nata yanda yake da son mata ga auri saki inya auri hadiza ay bala’i zasuyi, matar nan datake jin kanta kamar masu gidan harma ta fisi kafafa.
“Ay kuwa dai kawu, gashi batada miji don kamar ya mutu,”
“Toh ko yar zan nema ne? Tunda da kwari na zatayi kamarki?”
“Kawu na girmeta bazata wuce irin shekaru ashirin da uku ba haka”
Kyakyacewa yayi da dariya, sosai ba kadan ba “madallah..” ya fada yana tabo kudaden da anne ta basu daga aljihunsa.
Suna tafiya anne ta dubi rabi tace, “toh yanxu gashi yan matan wuya samu suke,“
“Va danuwa hajiya, tunda ga sabeeha ga basira sai a raba masu aikin kafin sabeehar ta koma makaranta nasan za a samu wata”
“Toh hakan yayi, naga fatimar nada tsafta ta dunga zuwa bangaren deeni tana gyarawa safe da yamma, duk abunda ya danganci bangarensa”
“Toh hajiya” rabi ta amsa ta.
Rabi na rabuwa da anne ta kira basira da sabeeha ta shaida masu kowa da aikinta, basira kamar ta kwada ihu, tanata murnar aikin bilki zai dawo hannunta, gyaran part din nanna da bangaren taj.
“Daga yau ke fatima zaki fara, bilki tayi na safe yamma nayi zakije ki gyara bangaren, shara mopping gyaran bandaki gyaran gado, komai, idan da lundry ma zaki dunga yi da goge.”
“Toh anty rabi”
“Dan allah banda kazanta, baya son kazanta ko kadan, yanayin rayuwarshi da tamu ba daya bace, kazanta kadan saita sashi amai abunka da ba dan nigeria ba”
Jinjina kai kawai sabeeha tayi, kwata kwata bata taba bada attention dinta gareshi ba sai yanxu, tadaiji ance dan anne kuma ba a kasar ya taso ba, amma bata taba sama ranta gani ko sanin wayeshi ba.
Jamila na tafiya hadiza ta koma gida gaba daya kamar ta burkice sabeeha na shigowa dakinsu ta taddata zaune
“Ke zo nan”
Karasowa sabeeha tayi cikin ladabi ta zauna kasa, “da kikace chan saudiyyar meya dawo dake? Meysa aka koroki? Karki sake kimin karya? Kisan kai kikayi ko sata? Wanne daga ciki”
Idanun sabeeha ya ciciko da hawaye ta kalli maman nata tace “mama wallahi…”
“Karki fara min rantse rantse munafuka, kisa kikayi ko sata wanne daga ciki? Don shi kadai zaisa azo ana nemanki”
Mamaki gaba daya da confusion ya cika sabeeha, hadiza ta zaro wuya tace “ko ki fada min kona kasheki anan na huta,iskanci kikaje kikayi ko wani kika kashe?”
“Mama wallahi banyi ko daya ba,”
“Meysa ake neman ki???? Ehhh????”
“Bansan wake nemana ba mama, wallahi ban sani ba”
“Wace iriyar rayuwa kikayi achan???”
Damm gabanta ya bada ta rasa ya zatayi, wace amsa zata bama mamanta? Ko karan hauka ke cinta bazata taba cewa aure tayi ba.
hadiza duk yanda taso ta tsorata da wuqa bata samu komai ba kwakwara dazai nuna cewa kisa tayi.
Wunin ranar cikin zulumi da kunci sabeeha tayi shi, tasha kukanta ta gaji ta hakura sannan ta fara tunanin maganganun mamanta, wake nemanta? Wazai nemeta? Babu mai bata amsa.
Yamma nayi wajen 4 ta shuga part din da zata dunga gyarawa, da sallama ta bude kofar kamshin diffusers ya bade ko’ina, bin ko’ina tayi da kallo wajen ya burgeta sosai ba kadan ba, har wani natsuwa takeji, haka ta fara gyaran parlor da babu datti kwata kwata ta share dakin shima ta sauya bedings ta wanke bathroom kal kal kamar ba a taba shiga ba sannan ta futo ta rufo kofar.
Tana futawa ta samu dakali daga chan wajen compound din ta bama wajen baya tana tunani da nazari.
Tunda ta zauna babu tunanin wanda yake circulating a ranta saina taj,duk iya kokari da take na ganin ta yakice shi ta kasa data fara ma take hana kanta ta hanyar tunawa da abunda ya mata yau ko ta kasa hana kanta.
Misalin wajen karfe shida da rabi ya shugo compund din wajen parking spot yayi parking motarshi kafin ya nufi hanyar part dinshi, kamar ance ya juyo ya kalli wajen da take zaune kuwa ya juyo ya ganta tana kokarin miqewa, take gabanshi ya soma bugawa fat fat fat, ya kasa daga idanunshi allah allah yake kawai ta juyo yaga ko wacece a wajen da zuciyarshi ta dakatar dashi babu dalili, tana miqewa kamar zata juyo kuma saita tsaya tare da daukan slippers dinta daya tainke ta dauka adaidai lokacin ya dawo hayyacinshi ya wuce cikin part dinshi ita kuma ta juyo.
Sallah ta shiga tayi taci abunci sannan suka fara prepping shirin aje dinner.
Yana shiga part dinshi yabi ko’ina da kallo, duk guaran da ake mashi sai yaga na yau is times 10 of it, sai yaji dadi aranshi soaai, komai anyi organinzing to his taste.
A tare sukayi aikin kitchen ana gama cin abunci suka tattara, harda sabeehar suka wanke ita da basira rabi kuma ta wuce don hidimar anne.
Wayar landline dake kitchen aka kira basira ta dauka kafin tace “gata”
“Tohm hajiya”
Kallon sabeeha tayi tace “hajiya nanna na kiranki, tace a yanka fruit”
Murmushi sabeeha tayi tace toh, ta fidda komai ta yayyanka yanda ya kamata ta zuba zuma a bowl ta jera kan tray sannan ta wuce sama.
Babu hijab a jikinta tana sanye da doguwar riga kuma ta mata kyau sosai daidai jikinta, ta dan rame saboda damuwa saidai kuma dirin na nan yanda yake gata yar gajeruwa.
Da sallama ta bude kofar part din bayan an bata izini ta shiga, nanna na zaune sitting room ta dubeta tace “sannu yar albarka,”
“Nanna ina wuni?”
“Lafiya lau my dear, how are you? Ya exams dinku an gama ko? Ina fata anyi abun arziki”
Dariya tayi tace “eh nanna”
“Aje fruit din akan dining, tajudeen zaizo yasha yanxu”
Dammmm gabanta ya bada badan ta rike tray din da kyau ba zai iya subuce mata.
“Tajudeennnn” kai ina zata iya mantawa da wannan suna a rayuwar nan.
Aje wa tayi tace “akwai wani abun da ake buqata?” Babu yarinyar kirki, nagode, rabi tace kin karbi aikin bilki ko? Gyaran part din tajudeen ya dawo hannunki”
“Eh, dazu ma naje part din na gyara”
“Toh Masha allah,”
“Saida safe nanna”
“Toh allah ya kaimu”
Sabeeha ta futa, koda ta futo ta wuce sama.
Washe gari wajen karfe goma ta shiga part din nashi, already harya futa wannan ya bata damar kimtsa ko’ina, yanda ya kamata, kayan data gani a closet a ajiye a kasa kamar cikin gaggawa aka ciresu ba a tattare ba ta kwaso ta sakasu laudry, ta taaftace wajen sannan ta nufi hanyar futa, har zata futa ta dakata idanunta ya sauka kan wani wrist watch, komawa tayi tana kallon watch din da mamaki, runtse idanunta tayi tana tunanin maisa komai yake reminding dinta da taj, kauda tunanin tayi ta duta daga part din.
Bangaren taj ya da sassafe ya futa ya koma agency,tun ana neman jamilu har aka kasa daina nemansa, salim ya gane wala wala suke masu, wata dabara tazo kashi cikin yaran wajen ya samu daya ya shaqe shi da kudi sosai ya fada mashi inda jamilu yake ayko bai tsaya wasa ba ya nemo mashi address dun jamilu.
A ranar suka dauki hanyar wajen gari habuja sai dutsen habuja, suna zuwa basusha wahala ba sukayi lokacin gidan jamilu, taj yayi mamaki sosai ganin anguwar, zuciyarshi kawia saita fara breaking sosai.
Akayi sallama da jamilu, jamila ta fito don jin ko waye, tana ganin jibgegeiyar kota gabanta ya soma faduwa, salim ya futo taj ma haka, ay sumewa ne kawai jamila batayi ba gar zata kulle gidanta salil ya mata sallama yace “dan allah hajiya ki dan saurare mu, muna neman jamilu ne”
“Mei sa kuke neman mijina me zai maku? Kamashi zakuyi?”
“Ah ah hajiya, babu ko daya cikin abunda kika fada, bai mana komai ba, wannan ogana ne, muna neman wata yarinya mai suna sabeeha, kuma an Shaida mana shine marikinta.
“Babu wata sabeeha a gidan nan, bamu santa ba, wata qila kunyi mistake ne, nice matar jamilu kuma bamuda ya mace yayanmu duk maza ne, dan allah ku daina neman mijina,”
“Amma Hajiya dakin saurare mi”
“Dallah nace maka babu wata sabeeha gidan nan” tana fadin haka ta banko kofar gidan gabanta na faduwa, jamilu dake zaune a daki yana ganin ta yace sune ko? Kamani zasuyi? Ke jamila wallahi tallahi taki ta kare na rantse da Allah”
*…
Tana rufe kofar salim ya fada ma taj komai, da yanda tayi dening, gaba daya everything doesn’t seems right, shi kanshi salim din ya gane basuda gaskia kwata kwata daga jamilun har wannan dake ikirarin matarsa ce.
Taj fa bai hakura ba yasa salim ya tambayi mutanen dake wucewa, wajen mutane hudu suka tambaya kowa sai yace bai santa ba.
Wani dan yaro daya taso daga islamiyya yana wasanshi dayaga an zagaye wayar da salim ke nunawa shima ya karasa wajen don ganin me ake gani, yana ganin sabeeha yace “kai wannan na santa”
Salim yayi saurin cewa “ina ka santa?”
“Ga gidan su chan kasan gangare, kudi salim ya bashi gar 5k yace zoka rakamu, aiko ya rakasu a kafa, gaba daya anguwar so disgusting, ko ina duk wari, taj dai bai taba zuwa iri waje haka ba baima san it exist ba sai yau, daudai gidan hayansu sabeeha ya tsaya yace “nan ne”
Tuni landlord dake ciki ya futo tare da yaron, irin igbo man dinnan ne sai bala’i yake yazo karban kudin wata yana ganin balarabe kawai ya soma washe baki.
“Oga please do you know this girl? We heard that she live here?”
“Ah yessoo, this girl and her mother, they never pay my rent they ran away, useless and wicked people”
“Mind your words please” taj ya fada rai adan bace.
“Where can we find them?”
“How would i know? Shey i told you they never pay me my rent”
“How much is your rent, “50k” ya bashi amsa
Taj yayi tsuka, rai a bace jijiyoyin kanshi na tashi, kamar yaui hauka haka yakeji, salim ya bama landlord 100k suka bar wajen saboda hamami.
Tund asuka shugo mota taj ya dage kanshi, daga jiya zuw ayau salim ya gane wannan binciken yarinyar badan komai bane saidai so, duk yanda akayi mutumin nan son yarinyar yake, kuma ya hadu da ita a kasarshi ne.
“Sir zamu sameta insha allah, i still dont trust that jamilu, he definitely knows where to find her, ko kanaso musa hukuma a ciki?”
“No need for that, lets calm it a day”
Salim yaja motar sukabar wajen.
Suna cikin tafiya salim yace “sir ive assigned you the membership of the best gymnastic close to your home you can start anytime”
“Thank” taj ya amsashi gaba daya hes fed up, ya kasa thinking straightforward.
Wajen karfe hudu suka iso, salim ya saukeshi ya shiga ciki jiki a mace.
Laila data shugo part din anne ta a zuwa direct kitcen ta wuce wajen anty rabi, tana isowa tace “anty rabi ga lunch din uncle taj mami tace a kawo”
“Toh bari akai mashi”
Sabeeha dake tsaye tana yankan naman sa da aka kawo za a saka a fridge rabi ta kalla tacebar naman zamu cigaba nida basira kije ki kai wannan chan part din”
“Toh anty rabi”
Ta bata ansa tare da karbar tray din basira ta bita da harara, ita maisa baza ace takai ba.
Akan idanun laila sabeeha ta wuce part din taj, sai kawai tayi murmushi ta wuce part dinsu tare da daukan wayarta ta kura maya, “baby girl, kina ina ne? What are you doing?”
“Sleeping..”
Ta amsata kai tsaye, “ya muke ciki ne da bet dinmu? Banga wani sauyi ba?”
“Kina doubting dina ne?”
“No kawai dai na tambaya ne, naje part din anne nakai Favourite abunci sa da mami ta zuba mashi shine na tuna da bet dinmu”
“Meysa baki kirani ba????”
“Woo, kai masa zakiyi?“
“Yea…”
“Haba dai…you’ll not do that, irin waennan abubuwan ba kince yan aiki ne ya kamata sunayi ba,”
Banza tayi da ita amma ta qulu sosai ba kadan ba, “waye kika bama zai kai?”
“Sabeeha, i heard that aykin part dinshi ya koma hannunta,“
Kitt maya ta kashe wayar jikinta na bari ko dankwali bata saka ba daga ita sai wata yar vest da tight tayi packing shegen gashinta da ko ribbom din bai kamasu sosai.
Kamar zata fadi haka take tafiya gaf gaf gaf har zuwa part din, ko knocking batayi ba ta bankade kofar, adaidai lokacin ta tadda sabeeha na jera abuncin a dining, maya na ganinta ta daka mata tsawa “keeee me kikeyi anan?”
Da mamaki sabeeha ke kallonta, “bake nakema magana ba yar matsiyara me kike anan?”
Banza tayi da ita maya ta hasala “dan…”
“Karki sake ki zageni,aikina ya kawo ni nan ba fada dake ba,”
Daga yau karki sake shugowa nan?”
“Idan ke nakema aiki ki hanani”
Tana fadin haka ta juya abunta ta futa daga gidan kota kanta batabi ba, maya kamar ta shaqo ta ta kashe haka takeji, lokaci gida taji shes insecured gaba daya.
Sabeeha na futa sai gashi ya sauko kasan, sanye da armless riga da gajeran dogon wando kamar zaije gym, tundaga sama yake kallonta da mamaki,”wannan yarinyar is she okay?” Ya tambayi kanshi.
“What are you doing here?”
Ya tambayeta babu wasa, “uhm uncle taj, daman mami ne tace na kawo maka breakfast”
Tund aya mata kallo daya bai sake kallonta haka ba badan komai ba saidai kwata kwata babu abun burgewa a tattare da kallon nata,
“You may find your way”
Murmushi tayi tana gyara tsayiwarta harda kwarkwasa oho shi baima san tanayi ba,
“Uncle taj, are you going to gym? Can i come along?”
Ay baiyi tunanin anan ma akwai marasa kunya ba sai yanxu,,
“You may find your way” ya sake fada yana mata nuni da hanya this time around babu wasa, jiki a mace ta juya ta futa.
Sai yaji abuncin ma ya fita aranshi baici ba ya fuce.
Da daddare kowa ya hallara for dinner, hamad da nanna da maya banda anne data kasa suakowa saboda kafa.
Daga kitchen rabi ta dubi sabeeha tace “dan allah jeki kai pepper soup dinnan nan,“
“Toh” sabeeha ta fada tana kokari daukan warmer din, ta tunkari dining area din.
Da sallama dauke a bakinta ta karaso, hamad ne ya fara dagowa jin muryanta mai sanyi, ya dade bai ganta sai yaga ta sauya gaba daya tunda sukayi hutun school.
“Sannu ku da hidima” nanna tayi magana tana kallonta.
Murmushi kawai sabeeha tayi ta aje abuncin kan dining, harta juya ta tsaya chak kamar ruwa yacita “taj, ga pepper soup a zuba maka?”
“No nanna, this is okay” ya fada da larabci.
Kirjin sabeeha kamar ana lugude, yanda kasan ana buga guduma haaka take ji, ta kasaa juyowa ta wuce kitchen jikinta na bari, so take ta juya amma ta kasa, kafafunta kamar ba a jikinta suke, muryan taj taji ko kuwa kunenta ne da kwalwalwarta ke kokarin yi mata wasa da hankali.
“Kai its impossible mai ze kawo taj nan gidan? Shida yake saudi She must be mistaken”
Basira ce ta kalleta dataga shugowanta tace “kizo mu karasa kin barni ni kadai inata fama da tukwane, duk wani abun arziki sai a wani sakaki aikin banza saikace ance ni bazan iyaba,”
“Yi hakuri basira”
“Ki daina ban hakuri dan allah, kizo mu cigaba na gaji zan kwanta,”
Hannu sabeeha ta sa mata hankalinta baya jikinta kwata kwata.
Basira dake kallonta ta gefen ido ce tace “kinga balaraben nan? Dan nanna yanada kyau ko?”
Balarabe? Sabeeha ta nanata aranta, “kai wallahi allah yayi mashi kyau, inama ace zai aureni wayyo, hmm bari na daina haukan nan nasan achan kasarsu saudiyya akwai zillaziyas hadaddu ba kamar ni ba gaja” harda yar dariyarta
Chak sabeeha ta tsaya da scrubbing din da take jikinta har tsuma yake ta juya ta nufi wajen futa daga kitcehn din, daidai wajen walkway din barrier din dayayi iyaka da kitchen din ta tsaya don tana iya hango duk wanda ke dining din, adaidai lokacin ya moqe tsaye bayan yayi ma nanna sallama zai koma part dinshi.
Wani irin jiri ta soma ji kamar zata fadi tsabar shock, babu abunda take sai “innalilahi wa inna ialaihi rajiun, “ har muryanta na dan futowa, she’s shock and confuse at the same time, juyowa yayi da hanzari don yaji tayi saurin shigewa saqon wajen ta boye fuskanta…
✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊
MATAR TAJ (destined with you🩵 🤍)
Written by
Queenmarh✍️
Book2
PAID
Cikin sati biyun nan taj bai samu sukuni ba, duk wani registered agencies da ake kai yan aiki saida salim ya nemo masa sukaje neman ta, amma kwata kwata babu mai kamaninta a record dinsu, dukda haka baiyi giving up ba.
Shidai salim baisan dalilinsa na neman wadda yake nema ba don bai fada mashi ba amma ganin yanda ya dage sosai yasan cewa yarinyar is very important to him.
Amma me zaisa mai kudi kamarshi yana neman yar aiki? Anan nigeria? Ya tuna da lokacij daya taba tambayarshi meya kawoshi Nigeria ya shaida mashi its something personally important.
Fada mashi da babanshi yayi cewa taj din is someone that is very important to their business yasashi dagewa don neman yarinyar.
Yau ne last day of the semester, wanda ya kasance ranar da zasu gama last paper na exams dinsu.
Sabeeha tunda suka fara exams ta kebanci kanta da komai, da duk wani abu da zai jawo mata fitina da maya.
Tunda taga kiri kiri mayar ta tsaneta don tundaga lokacin datayi mata sharrin sata ta gane binta take da sharrin.
abun da sabeeha bata taba expecting ba shine anne data yarda cewa ba itace tayi satan ba, dukda bata fadi cewa maya ce tayi mata sharrin ba, da farko dataga reaction din maman maya da yanda ta yarda lokaci guda kan cewa itace tayi sata saiyata jin kowa ma yarda da hakan zaiyi, saitaga akasin haka
Wannan yasa ta kudurci duk avubda zai faru bazata taba bari tayi abun da zaisa anne ta zama disappointed da ita ba.
Misalin wajen karfe biyar na yamma hamad yazo ya daukesu daga school, gaba dayansu daga yanda suka fito zaka gane wxams din ta jijiga su, hamad ya tambayesu how was the exam laila ce kawia ta iya amsa shi.
Yana tuki ya juyo ya kalli sabeeha ganin yanda ta rakube tayi shuru, ba tun yanxu ba ya lura gaba daya ta chanza, yanda take ada yanxu dukta daina, abunda ke hadashi da ita gaisuwa ne kawai daga haka bata sake cewa komai, she’s trying to be invisible a gaban su gaba dayansu, daman don hamad na tsaya mata ne yasa maya ke jin haushi ita da ba kowan kowa ba.
Wannan abu na damunshi sosai ta dawo yanda ya fara saninta, babu walwala babu fara’a.
“Fatima how was your exam?”
Ya jefo mata tambaya,shuru bahu response saida ya sake cewa “fatimaa!”
Firgigi ta dawo daga dogon tunanin data fada, “naam”
“How was your exams?”
“Alhamdulillah” tana fadin haka ta maida kanta ga glass window din mota ta cigaba da tunanin datakeyi.
…….
Da daddare rabi ta shigo part din anne da sallama ta gaida anne kafin ta soma mata bayani.
“Hajiya daman bilki ce tace kawunta ya kira zata koma kauyensu don an saka ranar bikinta nanda sati biyu”
“Toh Masha Allah shine basu fada da wuri ba”
“Eh wai itama batasan an badata bane, kisan auran kauye basa neman shawraar yayan tun suna kananu suke bada auren su” rabi ta bata amsa cikin ladabi.
“Toh kice mata ta nace ta kira kawun nata yazo cikin satin nan kafin ta koma, karsu mata komai na kayan daki na dauki nauyin wannan”
Cikin murna rabi tace “toh allah ya saka da alkahiri hajiya allah ya buda”
Ta amsa da ameen.
Rabi na barin wajen anne ta sami bilki ta fada mata komai, a take ko ta kira kawunta ta shaida mashi komai.
Washe gari da safe kowa ya hallara kan dining, anne, nanna, maya sai laila data kwana a part din nasu don sun shirya yanxu ita da mutuniyar tata sai kuma hamad da shugowanshi kenan.
Karasowar taj yasa duk suka maida hankalinsu gareshi, maya da laila suka gaishesa, hamad ma haka shi kuma ya gaisheda nanna da anne kafin su fara karyawa.
Hira sukey jefi jefi kowa ya maida hankalinsa ga abuncin da yakeci banda maya data kureshi da ido, laila tana ankare da ita don ba tun yanxu ba ta lura da hakan.
Shine ma ya fara tashi ya futa bayan ya gama saboda kiranda salim ke mashi.
Nanna ga tambayeshi harya gana yace mata eh zai dan futa ne, bata tambayeshi ina ba saboda yanxu kam ay ya san gari kuma yanada nashi privacy din avubuwa shiyasa bata tambayehsi ba ya futa.
Yana barin wajen maya ta sauke ajiyar zuciya, lailanta kalleta da mamaki.
Bayan sun gama dinner laila da maya na zaune dakin maya laila ta kaleta tace “wai kallon nan da kikema uncle taj na menene?”
Kallonta maya tayi tace “is there a problem inna kalleshi?”
Dariya laila tayi tace “maya are you crushing on uncle taj? If you are kima ajeshi a gefe, he definitely has someone”
Rai a bace maya ta kalleta laila na ganin haka tasan cewa maya has feelings for him.
“Shi yace maki he has someone??”
“Ke yanxu kina ganin yanda ya hadu ya gaji da haduwa, gashi mai kudi sosai kuma daga saudi yake saiki yarda idan akace maki bashida wadda yakeso, balarabiya yar kasarsu?infact banajin akwai yar nigeria da zata iya zama on his league”
Cije lebe maya tayi har yana fashewa kadan jini ya futo lokaci guda yanayinta ya sauya, tace “karya ne wallahi, karya kikeyi banza dallah zoki futa karki bata min rai”
Yanda take magana kamar zata hau kan laila, laila tayi saurin cewa “it looks like ba crushing kadai kike ba maya, badai son uncle taj kike ba? Don’t start dreaming what’s impossible don wallahi yafi karfinki”
Wannan magana da laila tayi mata kamar ta chaka mata wuqa a wuya haka takeji, rai a bace ta kalleta tace “you wanna bet on him?”
Laila najin haka tace “uncle taj din? Bafa yaro bane”
“You wanna bet on him or not? Don ni zan nuna maki cewa idan har inason abu saina sameshi no matter what, karkiga wai yana da kudi kuma halfcast ne wallahi i will make him fall for me, you wanna bet??”
Dariya sosai laila ta tunda yi tana kallonta tace “okay..lets see”
….
Bayan futarshi bai tsaya ko’ina ba sai inda zasu hadu da salim, daga nan suka wuce inda zasuje.
Tun a mota salim ya soma mashi bayanin kananun agency din da yanda suke operating wajen, kuma a gaskia illegally suke shigar da mutane kasar waje don gaskia gomnati batasan da zamansu ba.
A tare suka shiga wajen, irin local agency ne haka duk wani hanya da akeyi ta cuku cuku sunayinta, duk kasar da kake son zuwa don har visa sunayi ma.
Yara ko kauye kauye suke zuwa daukansu ana masu training akaisu wata kasar don aikatau.
Da farko masu kula da wajen kin basu hadin kai sukayi saida salim ya basu maqudan kudade tukunna kafin su kaisu wajen ogansu.
Suna zuwa ba tare da wani bata lokaci ba suka mashi bayanı, kudi babu abunda baya saka mutun yi, koda suka bada sunanta da hotonta da kuma inda tayi aikatau da shekarar, a take mutumin yasa yaranshi suka fara bunciken yaran da suka tura saudiyya shekara biyu da suka wuce.
An samu fatima’s da yawa saidai kwata kwata babu mai kama da ita daga ciki, su da sukaga hoton sabeehar ma daya bayar sun dauka ko batan hanya yayi, suda suke kwaso yan qauye, kowacce yarinya idan zasu turata saisun dauki hotonta, information din iyayenta, gudun samun matsala.
Har zasu bar wajen wani tunani yazo mashi, tunda yake nemanta da fatima yake amfani bai taba kawowa ko ba sunan take amfani dashi ba sai yanxu da abun yayi clicking a mind dinshi, ya dubi salim yace su nemi idan akwi mai suna sabeeha.
Take salim ya fada masu suka fara dubawa, suna daga zaune yaron dake buncikowa ya shugo da file din mutun daya da aka samu da irin sunan, baisha wahalar samu ba saboda sunan is unique.
Da aka kawo file din saida gaban taj ya fadi, har sauri yake ya bude don ya tabbatar da ita dince, yana tabbatar da ita dince ya sauke wata ajiyar zuciya, duk yanda kamanninta ya banbanta da hoton daya nuna masu bai hana shi ganeta ba, lokacin gaba dayanta babu cimar kirki a tattare da ita tayi wani irin baqi sosai, gashi dukda ta rufe bakinta saida gatson nan ya futo.
“She’s the one” ya fada beneath his breath, ya dubi salim yace su fada mashi inda zasu sameta yanxu yanxun nan, zai basu ko nawa ne yanason su fada mashi komai game da ita.
Salim ya fada masu tare da ajiye masu kudade dayawa a gabansu.
Ogan dayaga kudade take yasa cikin yaronsa su nemo mashi yar wani gari ce, kuma ta dalilin waye aka kawota aikatau, masu daukosu sunada yawa don kowanne gari akwai agent dinsu.
“Wannan yarinyar oga jamilu ne ya kawota”
“Wani jamilun?” Ogan ya tambaya.
“Jamilun dake dutsen habuja, yar dan uwansa ce”
Salim ne ya fasaara masa abunda sukace, sannan ya buqaci sanin inda zasuga jamilu, ogan yace ay agent dinsu ne bari ma
Ya kira sa.
Yana kiran jamilu wajen saunuku bai dauka ba, taj ya buqaci address din jamilun ogan give su dawo zaisa jamilu yazo har office dunshi.
Taj baiso haka ba dan ya matsu sosai, yanajin kamar bazai iya jura har zuwa gobe ba.
Suna barin wajen daya daga cikin agent din yayi saurin kiran jamilu, aiko yayi saurin dauka, daman jiran kiransa yake tundaya kirashi yace mashi karya amsa kiran oga, akwai matsala.
yana dauka ya fada mashi komai sannan ya shaida mashi yanda suka sakarma oga maqudan kudi don neman yarinyar dakyar inba matsala aka samu ba.
Daman gaba dayansu baki daya agent din harma da ogannin shiyasa suke tsaka tsantsan don business dinsu illegal ne.
Da farko jamilu shi harya mance da wata sabeeha daya kawo agency din saidaga baya ya tunata yar hadiza kawar jamila matarshi, shifa gaba daya ya tsorata sosai jin ance masu kudi ne suka zo nemanta kuma harda balarabe saiyayi tunanin ko kisan kai tayi achan kasar ne ba a gano gaskia ba saida aka maidota nigeria,sai yanxu ake nemanta gashi ya shugarda sunansa a matsayin mariqinta.
Yana tsaka da buga bugarsa ya koma gida ya hau kan jamila da bala’i, “mun shiga uku jamila, yarinyar nan kisan kai tayi ake nemanta, ki kira uwarta wallahi tallahi babu ruwanmu, ke kikace mu taimaka masu a turata aikatau, yanxu danace ni marikinta ne idan ba a ganta ba aka kamani fa?”
Kokarin kwantar mashi da hankali jamila tayi harda kwada mata mari, “me gida dan allah ka kwantar da hankalinka”
“Ina zan iya kwnatar da hankalina shin kinma san inda suke? Wallahi jamila idan kika sani matsala igiyar aurenki ce zata tsinke, haka kikasani muka aurar da ba tare da sanin uwar tata ba, muka cinye kudin da aka bamu yanxu idan wani tsoho ne fa aka aura mata gidan aikin nata ta kasheshi ta gudo ba a sani ba sai yanxu? Shin kinma san inda uwar tata take kuwa? Idan hadiza ta gudu fa?”
Jamila na hawaye ta kalli mijin nata tace “wallahi mai gida zan nemota bazanma fada mata me ake ciki ba sainaje naga inda take”
“Toh wallahi tallahi kiyi hanzarin zuwgobe goben nan ki shaida mata yauwa ehe”
Tana fadin haka ya fuce.
Jamila jiki na bari ta soma dialing layin hadiza tana dauka ta soma magana “hadiza akwai matsala..”
“Wace iriyar matsala jamila”
“Ki tura min adireshin ki gobe zanzo muyi magana”
Hankali tashe hadiza tace “ki bari ni zanzo goben”
“Ah ah tunda nace maki ki bari zanzo kawai”
Da haka sukayi sallama.
Tunda taj ya koma gida gaba daya yaji ya kasa sukuni, ya rasa mai zaiji aranshi dadi ko rashinsa, zai iya fuskantarta kuwa? Da wani ido zai iya ganinta? Gaba daya abun ya addabeshi ya kasa cin komai.
Misalin wajen karfe tara na dare nanna ta kirashi ganin ko dinner baizo yayi ba tunda ya fita da safe, daga yanda yake amsata ta gane kamar yana cikin damuwa, ta tambayeshi ko baya jin dadi ya shiada mata yayi loosing appetite ne kawai and yayi dinner tare da abokinsa kafin ya dawo gida.
Hankalinta bai kwanta ba ta sashi yazo part dinta.
Dole ya shirya ya wuce main part, tunda ya shugo yakejin sautin kwanuka daga wajen dining da Alamu kamar tattara wajen akeyi, sai maganganu dake fitowa daga wajen,bai kalli wajenba ya tunkari hanyar stairs yana dora kafanshi kan stairs din farko ya tsaya chak
“Subhanallahi Ya akayi ya fashe?” Rabi data tunkaro wajen dining din tayi interrupting dinsu ,
maya data matsa gefe ta kalli rabi tace “ya kike kallona, ga wadda ta fasa nan saboda tana baqin cikin masu gida, tana bakin cikin ganin munaci da luxury plates bata taba ci akan irin plate dinba bari ta fasa dan mugun hali”
Sabeeha da ranta ya gama baci ga baqaqen maganganun data gama gaya mata ta watsa mata juice a jiki da gangan dukdan saboda ta buqaci a dafo mata indomie ta dafo sau uku tana cewa baiyi dadi ba sai an sake shine sabeehar tace taje ta dafo yanda zai mata tana shirin barin inda take ta watso mata plate din da indomie din a kasa plate din ya fashe.
Dukawa tayi ta soma kwashe plate din rabi ta karaso inda take kasa kasa da murya tace
“Garin yaya kika fasa? Kina menene?”
Amsanta sabeeha tayi itama yanda daga ita sai rabi ne zasuji tace.
“Wallahi anty rabi Itace ta fasa,”
“Barshi kije ki dauko tsintsiya karkiji ciwo a hannu”
Da toh ta amsata tare da nufar hanyar kitchen daidia nan ya karaso wajen dining din don tabbatar da muryar da yaji mai kama data sabeeha dayaji a kunneshi.
Saidai kashh yana isowa wajen ta shige kitchen sai dan glance din bacewarta a wajen daya gani.
Kallon rabi yayi dake tsaye sai maya tafayi saurin mikewa ganinshi ta sauke wani irij murmushi,
“Ina wuni yallabai” baijin hausa amma yanda rabi tayi magana ya gane gaishesa tayi, da mamakin kansa baima san ya iya kalmar ba yace “lafiya” ashe dai ya fara dan koya Kadan kadan.
Maya ta taho inda yake cikin kaudi kamar ba itace ta gama cin mutuncin sabeeha ba ta zauna tana harare harare itama rabi bata tsira ba don rashin kunya take mata
“Hey uncle taj….do you need anything?”
“No thanks” ya bata amsa ba tare da ya sake kallonta ba ya dauke kanshi ya juya, daidai nan sabeeha ta karaso”
Rabi ta girgiza kai tace “wannan yarinya akwai munafuka, ji yanda takeyi kamar ba yanxu ta gama sababi ba”
sabeeha data jita ta dago ta kalli inda rabin ke kallo, bayanshi kawai ta kurama idanu har suka bace kata daga gani, “ya kika tsaya? Tattare wajen” rabi ta mata magana.
Sama ya wuce maya ta bishi a baya tana karemashi kallo ta bayan, few steps ne tsakaninsu don yanajin takunta amma hankalinshi baya jikinsa yana ga muryar dayaji datake kama data sabeeha, toh kodai yawan tunaninta ne yasashi yakejin muryarta yanxu kuma?and he feels her presence a ko’in.
Daidai wajen shiga part din nanna ta dakata harya shige daga ciki kafin Ta koma daki tana murmushi.
Washe gari…
Tun wajejen karfe sha daya jamila ta kira hadiza ta tura mata adireshin gidan, sannan ta shaida mata tana nan tafe.
Hadiza fa bata kwana kalau ba don zuwan jamila da kiran da jamila ta mata dagaji ba na alkahiri bane.
Hadiza ta futo daga dakinsu ta rabi dake kitchen, “rabi dan Allah kiyi ma security magana yar uwata zata zo”
“Hajiya tasan da zuwan bakuwar taki?” Rabi ta tanbayeta
Rai a bace hadiza tace “yar uwatace zatazo kuma hajiya ta santa”
“Toh naji” rabi ta fada tare da cigaba da abunda take.
Hadiza kamar ta shaqeta dan baqin ciki.
Daga chan wajen security aka kira cikin gida, daman rabi ce sukeda access da ita suka tambayeta akwai mai expecting bakuwa tace eh, suka tambayi suna tace masu su barta ta shugo.
Jamila fa tundaga bakin gate idanu suka raina fata ta dunga wiki wiki dasu tana rarrabawa, aranta babu abunda take fadi sai lallai hadiza ta debo ruwa, kut…aljannar dubiya saimai rabo”
Futowar hadiza ta backyard ta hangota daga nesa cikin sauri ta karaso insa take, “jamilaaa…”
“Naam hadiza, anan kuke? , bura..ubanchan kaiii, lallai hadiza kinyi wuta, kunama mai zafin dafi”
“Muje daga ciki” hadiza ta fada tare da jan hannunta sukabi ta backyard.
Ta kitchen din suka wuce jamila suka gaisa da rabi kafin hadiza takaita dakinsu.
Suna shiga daga ciki hadiza ta karo kofa harda saka key jamila har an hau gadon zamani an zauna ga ac na buga dakin.
“Bamu gaisa ba ko? Hankalina yayi gaba naga duniyar arziki”
“Jamila ina magnar gaisuwa kin sani cikin tashin hankali? Ey?”
“Ay kya bari nasha ruwa ko? Ina yar taki?”
“Wacce daga ciki?” Hadiza tayi tambaya, jamila ta kyalkyale da dariya.
“Jamila yanxu ba lokacin dariya bane, ki fada kin meke tafe dake? Wace matsala ce ke tunkaro mu”
Gyara zama jamila tayi ta yaye mayafin dake kanta tace “wannan yarinyar nemanta ake,”
“Wa kenan?”
“Kinsan wa nake nufi, jiya jamilu yazo gida ya shaidamin wai wasu mutane masu kudi sunzo har agency dinnan nemanta, kuma da alamu yanda suke kakkashe kudi don ganin sun ganota babu tantama kisan kai tayi ko kuma sata tayi ake nemanta”
Dafe kirji hadiza tayi tace “na shiga uku ni hadiza? Kisan kai?”
“Kwarai kuwa, kuma kinsan cewa jamilu shine ya kaita wajennan a matsayin marikinta, duk wani abu datayi shi za a fara kamawa saboda haka wallahi tallahi kisan nayi,“
“Na shiga uku ni hadiza, kin tabbar kisan kai yace maki tayi?”
“Ah ah fa, hasashen mu ne inba haka ba meysa masu kudi haka zasu dunga nemanta eyy?”
“Jamila wallahi wallahi bazan dauki asara ba, tun ban cimma buri na ba a duniyar nan”
“Toh ya zakiyi? Daman dalilin zuwana kenan,dan wallahi igiyar aurena na hannunki, jamilu yace zai iya sauwwake min wallahi, ki kwasheta ku koma lafiya kawai inyaso saiki dawo”
“Jamila bazan iyaba,nayi kokarin yin haka tun ba yanxu ba”
“Toh kina nufin idan akazo a kama mu kenan?”
“Ah ah jamila zanyi tunani akai”
“Gwara dai kiyi tun wuri, ki debo mi dan abun kamusawa mana naci arziki kafin muyi arzikin?”
….
Sama rabi ta hau sai gata da anne sun sauko har kasa, zuwa sitting room.
Wani mutumi ne a zaune don ya dan manyanta, an aje mashi bottle water da snacks a gefe yana daga zaune a kasa.
Daga ganinshi zakasan anji jiki don yana sanye da wata riga yar shara da wando blue fatau an kure adaka, sai wage baki yake da yayi jaja saboda cin goro.
Gefenshi bilki ce zaune tana sanye da hijabi sai kayanta dake cikin jaka mai kyau, ka ganta fess fess tayi bulbul abunta.
Anne na karasowa ya sake gyara zaman babbar rigarshi dake kan yar sharar, “sannu hajiya sannu hajiya”
“Sannu dai” anne tayi magana kafij ta zauna
“Ina wuni hajiya? Mun sameku lafiya?”
“Lafiya lau alhamdulillahi ya mutan gida?“
“Lafiya kalau kalau kalau hajiya”
Kana ganinshi zakace wani burkitaccen mutun ne amma da hankalinsa tsabar duniya ta bugi idanunsa ce.
“Kaine kawun nata?”
“Ee nine hajiya”
“Toh Masha Allah”
Matsowa rabi tayi da kudade aqalla zasukai wajen 500k ta aje gabanshi anne tace “ga wannan ayi mata duk wani hidiman biki, idan akwai abunda yayi saura ma saita bilkin ta kira”
Kamar zai taugunna mata haka yake ji, sai faman gadiya yake kmar bai taba rike kudi kamar irin wannan ba.
“An gode hajiya an gode sosai, bilki marainiya bazatayi kukan maraici ba kun mata komai hajiya an gode an gode”
“Ba komai Toh bilki saduwar alkhairi allah ya bada zaman lafiya ya sanya alkahiri”
“Ameen duk suka amsa a tare bilki harda kukanta suka futo daga gidan bayan tayi sallama da kowa, basira harda hawaye, rabi ma saida taji wani iri haka sukayi sallama suka futa.
Suna fita ya chusa kudin cikn babbar riga ya zaro goro ya fara tauna.
“Wallahi idan baki kirani ba zaki ga daaowata hadiza na fada maki,”
“Kai jamila kamar babu yarda tsakanin mu?”
“Ke hadiza ba abar yarda bace ni kadai nasan koke wacece.
Dahiru har zai wuce ya dakata ya kare masu kallo musamman jamila.
“Jamilan zango???”
Jamila najin sunanta da ake kiranta dashi lokacin da suna en mata ana shan duniya ta juyo da mamaki,”
Tana ganin dahiru gabanta ya bada dan daran dammm, dariya ya kyakyace dashi irin ta manya yace “jamilan zangoo, ashe rai kanga rai? Ah madallah”
“Kin sanshi ne?” Hadiza tayi magana tana kallonta ganin gaba daya bata cikin hayyacinta hankalinta ya tashi.
“Koba jamila bace wannan?”
Ya sake tambaya ganin tana kakkauda kai, “ay ko barci nake na tashi dole in ganeki jamila ta”
Jin haka yasa jamila cije lebe ta juyo ta kalleshi tana yaqe tace “dahiru kenan, kana nan dai yanda kake an buga duniya an barta”
“Kwarai kuwa, yaushe gamo? Rabona dake shekara wajen ashirin da yan kai, har kinyi aure ko ay hikenan kin barni”
“Kaifa ka fiye hauka, an girma ba a san an girma ba mteww”
Kallon hadiza yayi har yana motse idanu kafin yace “wannan ba kawarki bace? Har yanxu kuna tare? Lallai amincinku mai karfi ne ba itace Wacce kika…”
“Dahiru.. me kazo yi nan ne?”
Tayi saurin dakatar dashi hankali tashe, “yar dan uwana ce take aiki anan zan aurar da ita kinga mun kwana biyu ko?” Ya fada yana yage baki.
“Kwarai na gani kuwa”
“Ke yama sunan masu gidan?” Ya tambayi bilki tace “gidan alhaji santuraki”
“Ku meya kawoku nan anguwar?”
“Bani lambarka zan kiraka anjima” jamila tayi cutting conversation din, ya zari wata yar nokia ya bata number.
Zasu wuce bilki tace “sai anjima hadiza na tafi”
“Toh bilki” ta amsa ta.
Suna barin wajen hadiza ta dubi jamila tace
“? Ina kika san wannan jemamman kamar wani dan wiwi”
“hadiza mun shiga uku dahiru ne,”
“Wani dahirin?”
“Ke amma jakace, shekaru ashirin da uku da suka wuce….”
Ay bata karasa ba hadiza ta kama haba tace “ke da shi?….”
“Shine, hadiza dahiru bashida kai wallahi, inata yi maki signal mubar wajen kika kasa ganewa, dan wiwi ne wallahi bashida kan gado, tunda har ya ganmu akwai matsala”
Haka suka tsaya kana ganinsu zakasan basuda gaskia kwata kwata.
Dahirun da bilki na barin wajen ya dubeta yace “ina kikasan wadda naji kik kurata da hadiza”
“A gidan da nake ayki suke ita da yarta”
“Yarta?”
“Eh kawu”
“Tun yaushe suke gidan?”
“Zasu kai wata shida a gidan” ta bashi amsa
“Ta manyanta da batada aure dana jarraba sa’a ta”
Dariya bilki tayi sanin yanda kawun nata yanda yake da son mata ga auri saki inya auri hadiza ay bala’i zasuyi, matar nan datake jin kanta kamar masu gidan harma ta fisi kafafa.
“Ay kuwa dai kawu, gashi batada miji don kamar ya mutu,”
“Toh ko yar zan nema ne? Tunda da kwari na zatayi kamarki?”
“Kawu na girmeta bazata wuce irin shekaru ashirin da uku ba haka”
Kyakyacewa yayi da dariya, sosai ba kadan ba “madallah..” ya fada yana tabo kudaden da anne ta basu daga aljihunsa.
Suna tafiya anne ta dubi rabi tace, “toh yanxu gashi yan matan wuya samu suke,“
“Va danuwa hajiya, tunda ga sabeeha ga basira sai a raba masu aikin kafin sabeehar ta koma makaranta nasan za a samu wata”
“Toh hakan yayi, naga fatimar nada tsafta ta dunga zuwa bangaren deeni tana gyarawa safe da yamma, duk abunda ya danganci bangarensa”
“Toh hajiya” rabi ta amsa ta.
Rabi na rabuwa da anne ta kira basira da sabeeha ta shaida masu kowa da aikinta, basira kamar ta kwada ihu, tanata murnar aikin bilki zai dawo hannunta, gyaran part din nanna da bangaren taj.
“Daga yau ke fatima zaki fara, bilki tayi na safe yamma nayi zakije ki gyara bangaren, shara mopping gyaran bandaki gyaran gado, komai, idan da lundry ma zaki dunga yi da goge.”
“Toh anty rabi”
“Dan allah banda kazanta, baya son kazanta ko kadan, yanayin rayuwarshi da tamu ba daya bace, kazanta kadan saita sashi amai abunka da ba dan nigeria ba”
Jinjina kai kawai sabeeha tayi, kwata kwata bata taba bada attention dinta gareshi ba sai yanxu, tadaiji ance dan anne kuma ba a kasar ya taso ba, amma bata taba sama ranta gani ko sanin wayeshi ba.
Jamila na tafiya hadiza ta koma gida gaba daya kamar ta burkice sabeeha na shigowa dakinsu ta taddata zaune
“Ke zo nan”
Karasowa sabeeha tayi cikin ladabi ta zauna kasa, “da kikace chan saudiyyar meya dawo dake? Meysa aka koroki? Karki sake kimin karya? Kisan kai kikayi ko sata? Wanne daga ciki”
Idanun sabeeha ya ciciko da hawaye ta kalli maman nata tace “mama wallahi…”
“Karki fara min rantse rantse munafuka, kisa kikayi ko sata wanne daga ciki? Don shi kadai zaisa azo ana nemanki”
Mamaki gaba daya da confusion ya cika sabeeha, hadiza ta zaro wuya tace “ko ki fada min kona kasheki anan na huta,iskanci kikaje kikayi ko wani kika kashe?”
“Mama wallahi banyi ko daya ba,”
“Meysa ake neman ki???? Ehhh????”
“Bansan wake nemana ba mama, wallahi ban sani ba”
“Wace iriyar rayuwa kikayi achan???”
Damm gabanta ya bada ta rasa ya zatayi, wace amsa zata bama mamanta? Ko karan hauka ke cinta bazata taba cewa aure tayi ba.
hadiza duk yanda taso ta tsorata da wuqa bata samu komai ba kwakwara dazai nuna cewa kisa tayi.
Wunin ranar cikin zulumi da kunci sabeeha tayi shi, tasha kukanta ta gaji ta hakura sannan ta fara tunanin maganganun mamanta, wake nemanta? Wazai nemeta? Babu mai bata amsa.
Yamma nayi wajen 4 ta shuga part din da zata dunga gyarawa, da sallama ta bude kofar kamshin diffusers ya bade ko’ina, bin ko’ina tayi da kallo wajen ya burgeta sosai ba kadan ba, har wani natsuwa takeji, haka ta fara gyaran parlor da babu datti kwata kwata ta share dakin shima ta sauya bedings ta wanke bathroom kal kal kamar ba a taba shiga ba sannan ta futo ta rufo kofar.
Tana futawa ta samu dakali daga chan wajen compound din ta bama wajen baya tana tunani da nazari.
Tunda ta zauna babu tunanin wanda yake circulating a ranta saina taj,duk iya kokari da take na ganin ta yakice shi ta kasa data fara ma take hana kanta ta hanyar tunawa da abunda ya mata yau ko ta kasa hana kanta.
Misalin wajen karfe shida da rabi ya shugo compund din wajen parking spot yayi parking motarshi kafin ya nufi hanyar part dinshi, kamar ance ya juyo ya kalli wajen da take zaune kuwa ya juyo ya ganta tana kokarin miqewa, take gabanshi ya soma bugawa fat fat fat, ya kasa daga idanunshi allah allah yake kawai ta juyo yaga ko wacece a wajen da zuciyarshi ta dakatar dashi babu dalili, tana miqewa kamar zata juyo kuma saita tsaya tare da daukan slippers dinta daya tainke ta dauka adaidai lokacin ya dawo hayyacinshi ya wuce cikin part dinshi ita kuma ta juyo.
Sallah ta shiga tayi taci abunci sannan suka fara prepping shirin aje dinner.
Yana shiga part dinshi yabi ko’ina da kallo, duk guaran da ake mashi sai yaga na yau is times 10 of it, sai yaji dadi aranshi soaai, komai anyi organinzing to his taste.
A tare sukayi aikin kitchen ana gama cin abunci suka tattara, harda sabeehar suka wanke ita da basira rabi kuma ta wuce don hidimar anne.
Wayar landline dake kitchen aka kira basira ta dauka kafin tace “gata”
“Tohm hajiya”
Kallon sabeeha tayi tace “hajiya nanna na kiranki, tace a yanka fruit”
Murmushi sabeeha tayi tace toh, ta fidda komai ta yayyanka yanda ya kamata ta zuba zuma a bowl ta jera kan tray sannan ta wuce sama.
Babu hijab a jikinta tana sanye da doguwar riga kuma ta mata kyau sosai daidai jikinta, ta dan rame saboda damuwa saidai kuma dirin na nan yanda yake gata yar gajeruwa.
Da sallama ta bude kofar part din bayan an bata izini ta shiga, nanna na zaune sitting room ta dubeta tace “sannu yar albarka,”
“Nanna ina wuni?”
“Lafiya lau my dear, how are you? Ya exams dinku an gama ko? Ina fata anyi abun arziki”
Dariya tayi tace “eh nanna”
“Aje fruit din akan dining, tajudeen zaizo yasha yanxu”
Dammmm gabanta ya bada badan ta rike tray din da kyau ba zai iya subuce mata.
“Tajudeennnn” kai ina zata iya mantawa da wannan suna a rayuwar nan.
Aje wa tayi tace “akwai wani abun da ake buqata?” Babu yarinyar kirki, nagode, rabi tace kin karbi aikin bilki ko? Gyaran part din tajudeen ya dawo hannunki”
“Eh, dazu ma naje part din na gyara”
“Toh Masha allah,”
“Saida safe nanna”
“Toh allah ya kaimu”
Sabeeha ta futa, koda ta futo ta wuce sama.
Washe gari wajen karfe goma ta shiga part din nashi, already harya futa wannan ya bata damar kimtsa ko’ina, yanda ya kamata, kayan data gani a closet a ajiye a kasa kamar cikin gaggawa aka ciresu ba a tattare ba ta kwaso ta sakasu laudry, ta taaftace wajen sannan ta nufi hanyar futa, har zata futa ta dakata idanunta ya sauka kan wani wrist watch, komawa tayi tana kallon watch din da mamaki, runtse idanunta tayi tana tunanin maisa komai yake reminding dinta da taj, kauda tunanin tayi ta duta daga part din.
Bangaren taj ya da sassafe ya futa ya koma agency,tun ana neman jamilu har aka kasa daina nemansa, salim ya gane wala wala suke masu, wata dabara tazo kashi cikin yaran wajen ya samu daya ya shaqe shi da kudi sosai ya fada mashi inda jamilu yake ayko bai tsaya wasa ba ya nemo mashi address dun jamilu.
A ranar suka dauki hanyar wajen gari habuja sai dutsen habuja, suna zuwa basusha wahala ba sukayi lokacin gidan jamilu, taj yayi mamaki sosai ganin anguwar, zuciyarshi kawia saita fara breaking sosai.
Akayi sallama da jamilu, jamila ta fito don jin ko waye, tana ganin jibgegeiyar kota gabanta ya soma faduwa, salim ya futo taj ma haka, ay sumewa ne kawai jamila batayi ba gar zata kulle gidanta salil ya mata sallama yace “dan allah hajiya ki dan saurare mu, muna neman jamilu ne”
“Mei sa kuke neman mijina me zai maku? Kamashi zakuyi?”
“Ah ah hajiya, babu ko daya cikin abunda kika fada, bai mana komai ba, wannan ogana ne, muna neman wata yarinya mai suna sabeeha, kuma an Shaida mana shine marikinta.
“Babu wata sabeeha a gidan nan, bamu santa ba, wata qila kunyi mistake ne, nice matar jamilu kuma bamuda ya mace yayanmu duk maza ne, dan allah ku daina neman mijina,”
“Amma Hajiya dakin saurare mi”
“Dallah nace maka babu wata sabeeha gidan nan” tana fadin haka ta banko kofar gidan gabanta na faduwa, jamilu dake zaune a daki yana ganin ta yace sune ko? Kamani zasuyi? Ke jamila wallahi tallahi taki ta kare na rantse da Allah”
*…
Tana rufe kofar salim ya fada ma taj komai, da yanda tayi dening, gaba daya everything doesn’t seems right, shi kanshi salim din ya gane basuda gaskia kwata kwata daga jamilun har wannan dake ikirarin matarsa ce.
Taj fa bai hakura ba yasa salim ya tambayi mutanen dake wucewa, wajen mutane hudu suka tambaya kowa sai yace bai santa ba.
Wani dan yaro daya taso daga islamiyya yana wasanshi dayaga an zagaye wayar da salim ke nunawa shima ya karasa wajen don ganin me ake gani, yana ganin sabeeha yace “kai wannan na santa”
Salim yayi saurin cewa “ina ka santa?”
“Ga gidan su chan kasan gangare, kudi salim ya bashi gar 5k yace zoka rakamu, aiko ya rakasu a kafa, gaba daya anguwar so disgusting, ko ina duk wari, taj dai bai taba zuwa iri waje haka ba baima san it exist ba sai yau, daudai gidan hayansu sabeeha ya tsaya yace “nan ne”
Tuni landlord dake ciki ya futo tare da yaron, irin igbo man dinnan ne sai bala’i yake yazo karban kudin wata yana ganin balarabe kawai ya soma washe baki.
“Oga please do you know this girl? We heard that she live here?”
“Ah yessoo, this girl and her mother, they never pay my rent they ran away, useless and wicked people”
“Mind your words please” taj ya fada rai adan bace.
“Where can we find them?”
“How would i know? Shey i told you they never pay me my rent”
“How much is your rent, “50k” ya bashi amsa
Taj yayi tsuka, rai a bace jijiyoyin kanshi na tashi, kamar yaui hauka haka yakeji, salim ya bama landlord 100k suka bar wajen saboda hamami.
Tund asuka shugo mota taj ya dage kanshi, daga jiya zuw ayau salim ya gane wannan binciken yarinyar badan komai bane saidai so, duk yanda akayi mutumin nan son yarinyar yake, kuma ya hadu da ita a kasarshi ne.
“Sir zamu sameta insha allah, i still dont trust that jamilu, he definitely knows where to find her, ko kanaso musa hukuma a ciki?”
“No need for that, lets calm it a day”
Salim yaja motar sukabar wajen.
Suna cikin tafiya salim yace “sir ive assigned you the membership of the best gymnastic close to your home you can start anytime”
“Thank” taj ya amsashi gaba daya hes fed up, ya kasa thinking straightforward.
Wajen karfe hudu suka iso, salim ya saukeshi ya shiga ciki jiki a mace.
Laila data shugo part din anne ta a zuwa direct kitcen ta wuce wajen anty rabi, tana isowa tace “anty rabi ga lunch din uncle taj mami tace a kawo”
“Toh bari akai mashi”
Sabeeha dake tsaye tana yankan naman sa da aka kawo za a saka a fridge rabi ta kalla tacebar naman zamu cigaba nida basira kije ki kai wannan chan part din”
“Toh anty rabi”
Ta bata ansa tare da karbar tray din basira ta bita da harara, ita maisa baza ace takai ba.
Akan idanun laila sabeeha ta wuce part din taj, sai kawai tayi murmushi ta wuce part dinsu tare da daukan wayarta ta kura maya, “baby girl, kina ina ne? What are you doing?”
“Sleeping..”
Ta amsata kai tsaye, “ya muke ciki ne da bet dinmu? Banga wani sauyi ba?”
“Kina doubting dina ne?”
“No kawai dai na tambaya ne, naje part din anne nakai Favourite abunci sa da mami ta zuba mashi shine na tuna da bet dinmu”
“Meysa baki kirani ba????”
“Woo, kai masa zakiyi?“
“Yea…”
“Haba dai…you’ll not do that, irin waennan abubuwan ba kince yan aiki ne ya kamata sunayi ba,”
Banza tayi da ita amma ta qulu sosai ba kadan ba, “waye kika bama zai kai?”
“Sabeeha, i heard that aykin part dinshi ya koma hannunta,“
Kitt maya ta kashe wayar jikinta na bari ko dankwali bata saka ba daga ita sai wata yar vest da tight tayi packing shegen gashinta da ko ribbom din bai kamasu sosai.
Kamar zata fadi haka take tafiya gaf gaf gaf har zuwa part din, ko knocking batayi ba ta bankade kofar, adaidai lokacin ta tadda sabeeha na jera abuncin a dining, maya na ganinta ta daka mata tsawa “keeee me kikeyi anan?”
Da mamaki sabeeha ke kallonta, “bake nakema magana ba yar matsiyara me kike anan?”
Banza tayi da ita maya ta hasala “dan…”
“Karki sake ki zageni,aikina ya kawo ni nan ba fada dake ba,”
Daga yau karki sake shugowa nan?”
“Idan ke nakema aiki ki hanani”
Tana fadin haka ta juya abunta ta futa daga gidan kota kanta batabi ba, maya kamar ta shaqo ta ta kashe haka takeji, lokaci gida taji shes insecured gaba daya.
Sabeeha na futa sai gashi ya sauko kasan, sanye da armless riga da gajeran dogon wando kamar zaije gym, tundaga sama yake kallonta da mamaki,”wannan yarinyar is she okay?” Ya tambayi kanshi.
“What are you doing here?”
Ya tambayeta babu wasa, “uhm uncle taj, daman mami ne tace na kawo maka breakfast”
Tund aya mata kallo daya bai sake kallonta haka ba badan komai ba saidai kwata kwata babu abun burgewa a tattare da kallon nata,
“You may find your way”
Murmushi tayi tana gyara tsayiwarta harda kwarkwasa oho shi baima san tanayi ba,
“Uncle taj, are you going to gym? Can i come along?”
Ay baiyi tunanin anan ma akwai marasa kunya ba sai yanxu,,
“You may find your way” ya sake fada yana mata nuni da hanya this time around babu wasa, jiki a mace ta juya ta futa.
Sai yaji abuncin ma ya fita aranshi baici ba ya fuce.
Da daddare kowa ya hallara for dinner, hamad da nanna da maya banda anne data kasa suakowa saboda kafa.
Daga kitchen rabi ta dubi sabeeha tace “dan allah jeki kai pepper soup dinnan nan,“
“Toh” sabeeha ta fada tana kokari daukan warmer din, ta tunkari dining area din.
Da sallama dauke a bakinta ta karaso, hamad ne ya fara dagowa jin muryanta mai sanyi, ya dade bai ganta sai yaga ta sauya gaba daya tunda sukayi hutun school.
“Sannu ku da hidima” nanna tayi magana tana kallonta.
Murmushi kawai sabeeha tayi ta aje abuncin kan dining, harta juya ta tsaya chak kamar ruwa yacita “taj, ga pepper soup a zuba maka?”
“No nanna, this is okay” ya fada da larabci.
Kirjin sabeeha kamar ana lugude, yanda kasan ana buga guduma haaka take ji, ta kasaa juyowa ta wuce kitchen jikinta na bari, so take ta juya amma ta kasa, kafafunta kamar ba a jikinta suke, muryan taj taji ko kuwa kunenta ne da kwalwalwarta ke kokarin yi mata wasa da hankali.
“Kai its impossible mai ze kawo taj nan gidan? Shida yake saudi She must be mistaken”
Basira ce ta kalleta dataga shugowanta tace “kizo mu karasa kin barni ni kadai inata fama da tukwane, duk wani abun arziki sai a wani sakaki aikin banza saikace ance ni bazan iyaba,”
“Yi hakuri basira”
“Ki daina ban hakuri dan allah, kizo mu cigaba na gaji zan kwanta,”
Hannu sabeeha ta sa mata hankalinta baya jikinta kwata kwata.
Basira dake kallonta ta gefen ido ce tace “kinga balaraben nan? Dan nanna yanada kyau ko?”
Balarabe? Sabeeha ta nanata aranta, “kai wallahi allah yayi mashi kyau, inama ace zai aureni wayyo, hmm bari na daina haukan nan nasan achan kasarsu saudiyya akwai zillaziyas hadaddu ba kamar ni ba gaja” harda yar dariyarta
Chak sabeeha ta tsaya da scrubbing din da take jikinta har tsuma yake ta juya ta nufi wajen futa daga kitcehn din, daidai wajen walkway din barrier din dayayi iyaka da kitchen din ta tsaya don tana iya hango duk wanda ke dining din, adaidai lokacin ya moqe tsaye bayan yayi ma nanna sallama zai koma part dinshi.
Wani irin jiri ta soma ji kamar zata fadi tsabar shock, babu abunda take sai “innalilahi wa inna ialaihi rajiun, “ har muryanta na dan futowa, she’s shock and confuse at the same time, juyowa yayi da hanzari don yaji tayi saurin shigewa saqon wajen ta boye fuskanta…
✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊
MATAR TAJ (destined with you🩵 🤍)
Written by
Queenmarh✍️
Book2
PAID