Chapter 91
Matar Taj Part 2 Complete Hausa Novel. · about 48 min read
Abuja nigeriaa…
Tun daga nesa ya hango su biyu,kowacce na rike da jaka a hannu sai faman yanga akeyi, maya kam tafi kowa yauqi kamar bazata taka kasa ba.
Duban agogon hannunshi yayi ganin 4 daidai, da yasan yauqi zasu fara da yayi sallar sa kafin ma ya karaso school din, ganin babu sabeeha a tare dasu yayi mamaki sosai, don yawanci ma da zarar sun futo take yin gaba tabarsu, itadai badai sauqin kaiba, ya lura kwata kwata batason a bata mashi lokaci.
Gashi dagashi har ita ba ma’abotan son magana ba amma yanxu sun dan saba sama sama, he’s picking interest on her, yanda take da kamewa da sanin darajar dan adam wannan yafi burgeshi game da ita sosai ga biyayya.
“Hello ya hamad..”laila tayi magana suna karasowa inda yake.
Bai kalleta don suna isowa ya kauda idanunshi akansu, da mamaki yaji muryar maya tace “Hi”
Bai amsa masu ba don sallama yayi expecting daga garesu kamar yanda sabeeha ke mashi da zarar ta ganshi sannan ta gaishesa.
“Wa’alaikum salam, tunda baku iya sallama ba, “sorry ya hamad assalamu alaikum”
Banza yayi da ita maya ko ta wani irin tabe baki suka bude kofar baya.
Ya tsaya bai motsa ba yana jiran isowar sabeeha, maya tayi winding glass din tace “mu tafi mana tana da extra class yau sai anjima zata dawo”
Ko kallon inda take baiba saida laila tace “ya hamad da gaske, dazu munyi class din statistics da ita lecturer yace duk wanda is left behind baiyi catching up da lectures din yau ba ya tsaya za ayi extra classes, probably ta tsaya ne for the class”
“Ke maisa bazaki tsaya ba?”
“Ya hamad bazan iyaba marana yana min ciwo, sabeeha will help me out”
Girgiza kai kawai yayi ya zagaya mazaunin driver ya kunna matar tare da barin wajen.
Yana saukesu gida yasa laila ta fada ma anne asa daya daga cikin driver suje su dauko ta zuwa anjima don zai koma office bazai samu dawowa ba sai dare.
Ko minti biyar basuyi ba da barin wajen ba ta fito cikin sauri ganin 4:15 saboda tasan hamad by 4 yake isowa gashi batason bata mashi lokaci kwata kwata, gaba daya tayi wani iri, fitowanta kenan daga office din lecturer da akace yana kiranta koda taje office din nashi ya shaida mata bai nemeta maybe wani lecturer din ake nufi ba shi.
Hakanan ta fito jiki a mace, gashi class rep din ya tafi shine daman yace ana kiranta.
Haka nan ta tsaya wajen minti talatin babu ya hamad wajen inda yake parking, tayi mamaki sosai ba kadan ba wata dabara tazo mata ta wuce inda tasan su laila na zama ko zata gansu, koda tace nanma babu su, haka nan ta juya zuwa masallaci tayi sallah sannan ta fito ta zauna wajen inda yake parking gudun kar yazo suna nemanta don bata neman abun magana.
Tana nan zaune abubuwan da suka faru dazu suka dunga mata flashing a kwakwalwa, hankalinta ya tashi sosqi ba kadan ba, abu daya za ayi mata dake tayar mata da hankali shine qazafi, tana jin zafin abun sosai, dukda anyi clearing komai hakan baisa taji wani iri ba don har toilet ta shiga tasha kukanta ta godema allah yanda maya ta tsaya kyam tana kallon cikin idanunta tana attacking dinta da sata, batajiba bata ganiba, daa allah yaso class din basuda yawa sosai don da irin general class ne idan akaji wannan wani ba lallai ya yarda ba itace tayi satar ba.
A zuciyarta ta soma magana “banajin inada rabon jin dadi a duniya ne shiyasa”
Hawaye mai dumi ya sauko akan fuskarata tayi saurin gogewa tare da dago kanta jin alamun mutun a wajen.
Irin patrol securities dinnan ne dake assisting wajen parking.
“Baki tafi ba?”
“Ina wuni” tayi saurin gaishesa ganin babba ne.
“Lpy lau, inace kece ake zuwa daukan ku a wata katuwar bakar mota keda yan uwanki? Ay sun tafi tun dazu? Ya akayi baki bisu ba?”
“Wallahi ban sani ba, qila sun jirani ne ban fito ba da wuri” ta bashi amsa.
“Toh ki kirasu a waya,”
“Tohm nagode”ta amsashi ya kara gaba.
Wayar ta zaro tana kallonta, tama rasa me zatayi, what if da gaske sun jirata bata fitoba suka tafi? Ita a wacece zasu zauna jiranta ita da ba kowan kowa ba?” Da wannan tunanin ta aje wayar kawai ta kasa kira, nan ta fara tunanin ya zatayi, yoh ta ina ma zatayi kiran babu kati a wayar.
Jikinta yayi sanyi sosai kalau ta zama stranded gaba daya.
Acahn gida suna isowa kowacce tayi hanyar part dinsu, fadila ta wuce nasu while maya ta wuce na anne, zansu dabarar da takeyi duk welends take kwana wajen anty laila donta samu damar fita son ranta.
Kuma anne bata hana ba don ya sameer yayima anne magana akan ta dunga barinta tunda tana taya laila hira don batada yar budurwa kamar laila.
Anne batayi jayyayya dashi ba don babu wani abun kawai dai daman so take ana sa ido akanta tunda nanna ta ganta a hotel.
Shi ko ya sameer anty laila ce ta sashi gaba da mita da qananun maganganun yanda ta saba ay ba’a sonta a gidan da anty mubina ce baza ace maya ta bar part dinta ba dayake ita aka tsana itace yar agola wadda keda bakin jini shiyasa ake kyamatarta, wannan qananun maganganun nata yasashi zuwa wajen anne ya roki abarta tana zuwa tayata hira tunda duk an zama daya.
Lokacin data shugo part din anne babu kowa a kasan sai hadiza da sukayi kicibus hannunta rike da iced squeeze orange, kamar ta daidaici lokacin dawowarta kuwa.
“Sannu da dawowa hajiya”
Ko kallonta maya batayi ba ta wuce sama, hadiza tabi bayanta.
Tana gab da shiga bedroom dinta hadiza ta cimmata “in shugo?”
Dan dakatawa maya tayi sai kuma tace “shugo”
Rufo kofar hafiza tayi tana duban mayar data watsar da takalmanta da handbag dinta a kasa ta yaye yalolom gyalen data rikeshi a hannu sannan ta fada gadonta tana sauke ajiyar zuciya.
“Sannu kin gaji ko? Ga juice nan mai sanyi yanxun nan akayi juicing dinshi”
Hannu maya ta miqa mata ta karba sannan ta zauna tasha juice din kadan ta miqa ma hadiza, a tunanin fita zata yi saiyaga akasin haka, “in hada maki ruwan wanka?”
“Hada” ta amsata da gadara.
Jiki na tsuma hadiza ta shiga bathroom ta hada mata ruwa mai zafi sosai a jacuzzi ta watsa mata liquid bath soap dake wajen masu kamshi sannan ta fito.
Miqewa maya tayi ta wuce hanyar bathroom tana rage kayan jikinta ta watsar anan kasan.
Haka hadiza tabi kayan tana tattaresu ta saka a laudry basket sannan ta futo ta gyara mata gadon fess fess kamar ba a haushi ba sannan ta tsaya don jiran fitowarta.
Takai wajen 30mins cikin bathroom bata futo ba hadiza dai na tsaye ta fito.
Da mamaki maya ke kallonta, cikin rashin iya magana tace “ke kuma zaman me kikemin a daki? Ko dan hannu za amin ne ban sani ba?like mother like daughter?”
“Yo hakuri hajiya maya, daman na tsaya ne naji ko kina buqatar wani abun? Ko zakici abunci? Ko kinason a dafa maki wani abun da kikeso”
Wajen dresser maya ta nufa tana daukan man ta zata shafa tace “kije ki kawo min pepper soup din kaza, amma thighs din kawai nakeso, karki cika yaci sosai”
Murmushi hadiza tayi tsabar jin dadi tace “toh sai me kuma kikeso, fada kin duk abunda kikeso zan maki”
“Shiknen, idan kin gama kizo ki wanken undies dina sai bathroom dina ba a wankeshi da kyau ba”
“An gama hajiya maya, ay babu abunda baza a yi maki ba gimbiyar gidan nan”
Maya ji tayi kanta kamar zai fashe sosai ba kadan ba, hadiza na fita tayi smirking “lallai wannan anyi bagidajiya,”
Fitar hadiza daga saman taci karo da rabi data futo daga part din anne da sauran yan matan dake hauro mata da abunci sama.
Rabin ce ke assigning dinsu inda zasu dinga aiki kuma tayi mamakin ganin hadiza a sama don aikace aikacen ta bai shafi sama ba wannan yasa tabi hadiza da kallo suna saukowa kasa tayi kicibus da ita a kitchen tana kokarin daura abunci.
“Hadiza meya kaiki sama inace aikin ki a kasa kawai yake.”
Rai a bace hadiza tace “banida ikon yin aikin daya wuce na kasa ne? Ke kinsan matsayina kuwa a gidan nan?”
“Menene matsayin naki? Inace aiki kikazo yi ana biyanki? Kinada wani matsayin ne bayan wannan bamu sani ba? Ki fada min dalilinki na zuwa sama inva haka ba na sanarwa da hajiya, babu amsu zuwa saman sai wanda aka yarje masu kuma bana jin kina cikin waenda akace su dunga hidima a sama”
Hadizq tajji zafin maganar rabi amma haka ta hadiye ta danne tace “ba komai ne ya kaini dama ba, jikar hajiya ce ta buqaci a kawo mata juice da parpesun kaji shine na hau saman”
“Ba aikinki bane idan tana buqatar wani abu zata nema wajen masu girki ko ta kirani”
“Ke kuma asuwa?? “
Suka jiyo muryar maya daga bakin kitchen din, juyowa rabi tayi ta kalleta, tana daure da towel a kirjinta ko me tazo dauka a kitchen din allah kadai ya sani,
“Daga yau duk abunda ya shafeni ita ce zatayi min, karki sake questionining dinta, banason iyayin banza da wofi, kema ba yar aikin bace ba har kinada ikon fadin yanda za ayi da abunda baza ayi ba”
Sunkuyar dakai rabi tayi, gaba dayansu zasu haifi uku ta wallahi amma yanda take magana kwata kwata babu respect a ciki.
“Mteww…ke yama sunanki?”
Ta nuna hadiza da hannu, binta da ido hadiza tayi, sai kawai wani murmushi ya kufce mata ta kasa magana saida mayan ta kara cewa “baki..”
Cikin sauri hadiza ta katse ta “hadiza..sunana hadiza”
“Inason smoothie yanxu kafin ki gama pepper soup din”
“Tohm an gama yanxun nan kuwa za ayi maki sai kuma me kikeso? Ki fada kin ayi maki yanxun nan”
Dan tabe baki maya tayi tana jin wani irin dadi aranta amma ta basar tace “ya isa”
Ta futa rabi ta girgiza kai aranta tace “futsararriyar yarinya”
Hadiza kuwa ta bi rabi da kallo tayi kwafa sannan ta fara kokarin yi mata smoothie data buqata.
Ahankali akayi knocking kofar kafin a shugo da sallama, nanne ce zaune akan gado cikin irin maroocan gowns dinnan mai hula, tana ganin anne tayi saurin sauke kafafunta daga kan gado ta aje takardun dake gabanta da glass din dake hannunta.
“Wa alaikum salam! Anne!! Lafiya dai dakin bari nazo ay keda kike fama da kafa” nanna tayi magana tana kallon yayar tata.
Takowa anne tayi ta zauna gefen gado inda nanna ke zaune tace “nazo dubaki ne, ya zazzabin?”
“Alhamdulillah anne doctor yazo dazu ay dan zazzabine fa, alhamdulillah ya sauka ma, ina wuni ya fama da iyali”
“Toh alhamdulillahi,”
Shuru ne ya dan biyo baya kafin anne tace “hajara!”
Nanna najin yanda ta kira sunanta tasan akwai magana.
“Na’am yaya”
“Nayi magana da doctor dazu, ba zazzabi kadai ke damunki ba harda hawan jini kuma nasan damuwa ce tasa maki shi, Hajara ina ganin lokaci yayi daya kamata ki waiwayo rayuwarki ta baya….”
Murmushi nanna tayi ta kalli anne tace “wallahi babu abunda ke damuna babu wata damuwa anne, kawai stress din aiki ne ba wani abu ba, ina gab da retire nima na huta abarma yara suyi”
“Hajara kinsan abunda nake nufi, bazanyi forcing dinki ba tunda kin nuna bakyason ayi maganar, bazan iya sanin abunda kike ji aranki ba amma inaso ki sani ni yar uwarki ce hajara bakida kamarni, nice uwa a gareki kuma nice uba, bana fatan rasaki hajara don ayanxu ne nafi kowa buqatarki, babu wanda yasan gobe da abunda ke cikinta, kiyi hkuri hajara, bazan fasa baki hkurin nan ba kinji, ki aje komai a gefe ki nemi…”
Hawaye ne suka fara neman ambaliya akan fuskarta tace “Anne please..dan allah dan allah badan halina ba mubar zancen nan,”
Shuru anne tayi sannan ta kama hannunta tace “shikenan hajara na bari, allah ya rufa asiri allah ya sawaqe, tunda kince ba damuwa bane, amma kiyi kokari kina gujema stress din”
“Insha Allah.. ya kafan ki?”
“Kufa kuke wani damuwa da kafa, wallahi garau nakejinta yanxu, abun kunya ni ban samu hawan jini ba da shekaruna gashi ke saboda tunani zaki jefa kanki a halaka”
Girgiza kai kawai nanna tayi don yayar tata tasanta ciki dabai, duk falewar da zatayi bazata taba yarda ba don ta san duk wani condition da take ciki.
“Toh anne za a rage tunanin,”
Mumrushi tayi mata sannan sukayi sallama anne ta fita.
Wata nayyayyiyar ajiyar zuciya nanna ta sauke,idanunta sunyi jaa sosai take taji kirjinta na mata wani irin nauyi, tayi hanzarin daukan pills dinta ta sha sannan ta kwanta.
Daki anne ta koma ana mata tausa hamad ya shugo suka gaisa, wuraren past 7 don anan idar da sallah ya shugo, hira suka danyi jefi jefi ya danci tuwon da aka kawo ma anne sannan ya mata sallama kan zai dawo anjima.
Yana sauka kasan yaga yan aikin gidan nata faman shirya dinner a dining duk bai buqata saiyaje ya diba.
Sai a lokacin sabeeha ta fado mashi yasan by this time an daukota, amma rashin ganinta da baiyi ba dazu sai yaji babu dadi gaba daya, gashi bazai iya sqwa a kirata ba, toh akirata yace mata mene? Saboda mene? A wani dalili kenan? Saurin watsar da zancen yayi ya wuce gida.
Yana parking a part dinsu ya shiga daga ciki.
Kai masha allah, gaskia anty fadila badai gayu ba, itama gidanta mansion ne mai zaman kanshi baikai nasu anne ba don shine family house dinsu amma shima badai girma ba gari guda.
Ko’ina yasha adon gold and off white, parlor ga wani katin frame na hoton su su hudu, laila hamad then babansu sai mamansu.
Daidai zai shugo yaci karo da laila data debo abunci zata wuce sama, hartasa yar aikinsu ta kawo mata tanajin sallamarshi ta karbe karyayi mata fada, irin waennan kananun abubuwan kamar irinsu gyaran gadonta da gyaran wardrops dinta ita keyi, ba’ayarda yar aiki tayi ba saidai wanke toilets da shara, saboda kar shagwabewar tayi yawa, sometimes ma itake girki a gidan, dakin mamansu kuwa itake gyarashi tass.
Gaskia an basu tarbiyya kam mai kyau, babu raina na gaba musamman na kasa dasu.
“Hello ya hamad!”
“The next time kika kara cemin hello saina mareki, baki iya gaisuwa bane”
“Sorry ina wuni how was your day”
“Alhamdulillah ya amsa ta” ta turo baki tare na bin hanyar stairs ya dakatar da ita.
“Kinje ta koya maki?” Ya jefa mata tambaya daman yanason yaji ko yaushe sabeehan ta dawo.
Damn gabanta ya bada, tsakani da allah dazun nan ciwon mara ya riketa sosai tunda ta kwanta take barci bata tashi ba sai yanxu shaf ta mance da batun driver daya kamata ta fada ma anne.
Ganin yanda tayi tsuru tsuru yasan bata da gaskia, “are you dumb?”
“Innalillahi wallahil azeem yaya ciwon mara nake dazu sai yanxu na iya tashi”
“Is that the question that i asked you?”
Ganin ta sunkuyar dakai yasa shi zaro ido don sai yanxu ya fuskanci inda ta dosa, “what!!!!!! Bakida hankali???? “
“Yaya wallahi mantawa nayi”
Ko sauraron baiba don kamar ya kwada mata mari haka ykeji ya fuce daga gidan a fusace kamar zai tashi, yayi hanzarin shiga motarshi ya juya akalar motar.
Gudu yake sosai gabanshi na faduwa, yanajin kamar yayima laila dan banzan duka, ya za’aui ta manta and ya bata strict instructions akan ta fadama anne asa cikin drivers available one yaje ya daukota, gaba daya saiya fara jin wani irin rashin dadi da tausayi sabeehar yanxu haka shes stranded batasan ya zatayi ba innalillahi wa inna ilaihi rajiun.
Yana isowa school din ya wuce direct wajen department dinsu hankali a tashe, duban duniya yayi mata bai ganta ba, gashi duk securities daya tambaya sai suce basu ganta ba don ana yi shifting na rana sun tafi.
Haka nan ya zagaye school dinnan gaba daya da securities ana nemanta, har akayi sallar isha’i, cikin ikon allah wani tunani yazo masa ya nufi masallacin mata, bai shiga ba yasa daya daga cikin securities mata suka shiga ko za a ganta.
Tana shiga saigata kuw sun fito tare, tana daga kwance chan sakon masallaci ta jigata sosai ga gajiya ga yunwa, sallah kawai takeyi ta koma kwance.
Tana ganin hamad ta sunkuyar da kanta feeling so sad, wallahi yarinyar nan ba karamin kashe mashi jiki take ba haka kawai yake jin tausayinta bayason ganin ta cikin kunci ko kdan, yana hango tsananin damuwa da rashin farin ciki cikin idanunta, kamar someone that is lonely and longing for something.
“Dauko littafanki”
Komawa tayi jiki a mace ta dauko ta fito suka wuce taba biye dashi a baya har suka iso mota ya bude mata seat din baya ta shiga ta zauna ya rufe
Kunna motar yayi ya saka ac kadan sannan yayi reversing ya futa daga school din.
Shi shuru ita shuru aka rasa wanda zaiyi magana.
Shi wani irin rashin dadi yakeji, how can he be so careless, dayayi tunanin kiranta yayi confirming kota dawo da duk haka bata kasance ba.
“Kayi hakuri ya hamad, ka dawo saboda ni, wallahi ba laifina bane, bansan kazo da wuri ba dazun da bazan bata maka lokaci ba,”ta fada cikin sanyi, zuciyar sa kam ta karaya dajin furucinta sannan ga abunda ya biyo baya da bai fuskanta ba.
“Why are you sorry? Daman ba extra lectures kika tsaya yi ba?”
Nanata abun tayi a ranta batason cewa komai yanxu data fuskanci kamar akwai dan misunderstanding.
Ganin taqi cewa komai yasashi cewa
“Now tell me meysa kika bata min lokacin”
“Daman class rep dinmu ne yace min lecturer dinmu na nemana shine naje, bayan naje kuma yace min ba nemana yake ba saidai ko wani lecturer ne bashi ba,“
“And sai kuma akayi yaya? Ya nemi karin bayani.
“Shine na sauko kasan don banga rep dinmu ba kamar ya tafi, anan ne naji wajen wani security cewa kazo kun jirani harkun tafi, kayi hkuri hakan bazata kara faruwa ba”
Shru yayi bayan ya gama sauraronta tass, a cikin maganganun nata ya fuskanci abubuwa biyu, na daya babu wani extra class datace ma laila da maya zasuyi, secondly kuma batasan cewa shima kanshi da wannan wrong info din yabi ba.
“Bakiyi laifi ba, but next time ki dunga kirana idan abu ya faru dake, kamar yanxu this is very wrong for a lady ki zauna, and im sorry bansan cewa driver bai biyo sahunki ba yazo daukanki i should have called you naji ko an maidoki”
“Insha allah”
Suna karasowa gida yayi parking ta wuce bayan sunyi sallama sannan ya wuce part dinsu.
Yana parking ya wuce ciki dirwct zuwa dakin laila yana shiga yayi knocking tana zaune tayi zuru avun tausayi don tasan yau zai sauke mata, kuma harga allah bata kyauta how can she forget this.
Yana shugow ata moqe tsaye kamar zatayi kuka “yaya don girman allah kayi hkuri wallahil azeem banqi fada ba da gangan”
Tass ya kwashe ta da mari, “meysa kikamin karyan extra class da kikace zasuyi?”
“Answer me” ya daka mata tsawa ganin tayi shuru, ta fara daburdabur, “wallahi ban maka karya ba, meysa zan maka karya yaya, tare mukayi statistics class da ita kuma a gabana lecturer yace zaiyi extra class”
“Ita da bakinki tace maki zata tsaya yi?”
“Ah ah,”
“Then how did you conclude zatayi?”
“To ay naji maya tace zatayi extra class ne sainayi tunanin class din zatayi”
Saida ta fadi hakan ya gane inda gaba daya akayi misleading dinsu, wannan kafurar yarinyar futsararriyar ce, kuma saiya koya mata hankali.
“The next time kika kara bani wrong information saina tattakaki”
Hamad nada sauqin kai sosai amma in aka taboshi bashida sauqi.
Yana kaiwa nan ya fuce ya barta da kama kunci, anty fadila data fito daga part dinsu ita da oga don su ne a sama da maya kasan is for hamad tana ganin yanda ya futa tasan sunyi rikici kenan da qanwar tasa.
Bedroom din laila ta shiga ta taddata tana kuka shabe shabe.
“Menene kuma me kika masa? Nasan kece mara gaskia”
Cikin shesheka tace “mami wallahi ba laifina bane, kinga maya ce tace wai sabeeha zatayi extra class shine nayi tunanin class din zatayi ashe bashi zatayi ba shine shine muka tafi muka barta a school, toh dazun daya dawo damu yace na fada ma anne asa driver yakaita ni kuma bayan nasha maganin ciwon mara yasa ni barci na manta gabadaya shine yazo yanxu..”
Tun kafin takai aya fadila tace “innalillahi wa inna ilaihi rajiun karkice kin yarinyar nan kuka vari a makaranta tun da yamma har zuwa yanxu, amma bakida hanklai, are you mad?what sorr of nonsense is this? Eh”
Haka ta dunga balbaleta itama hankalinta ya tashi, abun babu dadi.
Sabeeha na shiga part dinsu ta tadda dakin kacha kacha, daman ita ke gyara wa duk sanda ta dawo daga school to yau ko zanin gado hadiza bata daga ba.
Wata iriyar yunwa takeji wannan yasa ta fuce zuwa kitchen ko zata samu wani abun da zata kaima cikinta.
Tana shugowa taci karo dasu rabi da hadiza a kitchen din anata faman gyare gyaren kwanuka na dinner da akayi.
Gaishesu sabeeha tayi sai a lokacin hadiza ta tuna da ita, batace mata komai ba sai binta take da ido tana girgiza kai.
Ganin irin kallon da hadiza ke mata na tuhuma yasa taji yunwar ma ta tafi gaba daya ta juya zata cire kayan jikinta dan tazo ayi aikin da ita daidai nan sukayi karo da maya data sauko kamar zata tashi sama, a kufule saboda yanda hamad yazo saura kiris ya mareta akan wannan yar wanke wanken.
Wani irin turata baya maya tayi kamar zata fadi ta daidaita tsayuwarta, “wallahil azeem da ya hamad ya mareni saboda ke wulaqantacciya yau da sainaga jini a bakinki, haka kawai saboda kin tafi yawanki na iskanci sai yazo ya balbaleni? Banza barauniya, asarraru, yar wanke wanke, gaba dayanku wahalace ta maku yawa tsabar Samun wajen har kin isa kisa yazo kamar zai dukeni? Ke a wa? Who’s your father? Ke yar uban wacece? Wataqila ma wajenshi kika gado sata”
Rabi dataga abun yayi yawa ne yasa tace “haba maya, me ta maki? Ya zaki mata kazafin sata?”
Hadiza na daga tsaye tana wanke wankenta ko tak bata ce ba ranta in yayi dubu yayi mugun baci sosai, saida taji anyi batun sata ne yasa ta juyo ta kalli sabeeha, maya dataga haka tace, “ki daina yi mata wani kallo, inta sato ke zata kawowa ay ba wani ba mteww rubbish”
Tana fadin haka ta juya tabar wajen hadiza ta fizgi hannun sabeeha zuwa backyard, ta kama hannunta sosai kamar zata ballata tace “dan abu kaza kaza…..”ta kundumo mata ashariya tace “koda na tura ki chan wata kasa daman sata kika koyo??? Eh????”
Tana shekar kuka tace “wallahi mama ban taba yi ba, wallahi da gaske nake”
“Zata maki karya ne???? Wallahi bazaki Jawo min magana ba, gwraa na tattaraki gaba daya ki koma chan wajen dangin ubanki lafia”
Tana kaiwa nan ta bar wajen kamar zata tashi sama.
Tana barin wajen sabeeha ta duka anan dakalin wajen ta saka kanta tsakanin cinyoyinta sai hawaye, kuka take sosai bakajin sautin ma sosai sai kadan kadan.
Jin alamun an dafata ne yasa tayi saurin dagowa ta miqe tsaye, nanna ta kalleta ganin tana saurin goge hawayen dake fuskarta kar a gani.
Saukowanta kenan kasa, daman tana zama ne a balcony dinta dake sama saiya kasance yana daga wajen backyard din, kaf conversation dinsu taji, wannan yasa ta sauko.
“Ina wuni Hajiya akwai abunda kike buqata”
Kallon fuskanta nanna tayi hawayen sun kasa tsayawa, ba karamin tausayinta taji ba ga muryanta ya soma dishewa, irin wannan ba tuhumar mutun akeba zama ake dashi a tambayesa akan komai bawai a yanke mar hukunci ba,
Hannu nanna tasa ta share mata hawayen a maimakon ta daina sai kawai ta fashe da hawayen sosai, nanna batasan lokacin data rungumeta ba ta soma padding bayanta, “shiii, ya isa haka”
Tana fadin haka ta zarota daga jikinta sannan tace “share hawayen”
Ta gogesu tass sannan tace “now tell me
Meya faru?meysa akace kinyi sata?
Kujerun dake wajen nanna taja masu suka zauna tana fuskantar sabeeha.
“Wallahi hajiya banyi ba, sharri ne,”
“Zan yarda dake idan kika fada min meya faru”
Ajiyar zuciya sabeeha ta sauke tana jin wani irin sanyi aranta tace”Daman dazu ne a school muna zaune ana lectures sai kawai maya tace anyi mata sata, tayi reporting to lecturer din saiyace duk wanda ya dauka ya futo dashi ko yasa a shigarda report, duk sai naga suna kallona bansan meya faruba wallahi, sai wata daga cikin students tace wai a duba jakana,im the suspect,nace masu ni banida jaka ma don littafaina ma a hannu nake rikesu,sai lecturer yace na fito zuwa stage zaiyi questioning dina, wallahi hajiya ina tashi bansan ta inda agogo yafito ba sai kawai suka fara ihu wai gashi nan nice na dauka, shine aka kira securities, sukazo za akaini disciplinary, sai wata sabuwar student ta dakatar dasu ta fidda same watch din tace ay wanda ya fito a jikina ita ta bani na aje mata ga nasu nan a wajenta lokacin data shugo class ta tsinta, toh kinji yanda akayi”
“Toh ita din da gaske ta baki ki ake mata?”
“Wallahi ah ah, banka santa ba wallahi ranar na fara ganinta a class din”
“She saved you?
Da mamaki sabeeha ke kallonta “yes she saved you, duk yanda akayi na hannunta shine nata na asali wanchan dayan kuma its possible ko wani ne yaso yayi maki sharri, you should be thankful to her”
Sabeeha tayi mamakin maganar nanna sosai don sai yanxu ta fuskanci hakan, “sunanki fatima ko?”
Ta girgiza mata kai alamun eh, “na yarda bake kika dauka ba kinji, sannan next time ki dunga lura da mutanen dake kusa dake, wanda ke kusa dakai shike da damar cutar dakai”
“Tohm hajiya nagode sosai”
“Karki sake yin kuka kinji ko? Tunda bakiyi ba me zaisa kiyi kuka, now give me a big smile”
Take kuwa ta sauke mata murmuhshin ta mai kyan gaske, nanna ta dunga kallon idanunta tana tunanin ina ta taba ganin ta ko me kama da ita.
Kallonta da nanna keyi yasa itama ta kura mata idanu tana tunanin ina ta taba ganin ta, sai kawai tayi zumbur ta miqe tsaye “laa hajiya kece wallhi kece, kece wadda kika taba bani kudi da yawa dana baki jakarki da kika yadda a masallaci”
Tunani nanna ta farayi yaushe event haka ya faru, “hajiya wallahi kece, wajen masallacin gidan man salbas dake kan Hanyar wajen gari? Shekara biyu da suka wuce? Kika mance purse dinki a masallaci harna biyoki da jakar lokacin zaki wuce”
Kama baki nanna tayi set of hakoranta suka fito rass tace “allahu akbar kece wannan yarinyar? Yar amana? Kece mai robar kwai ko?”
“Eh nice hajiya ni ce wallahi”
“Allah sarki, wani ikon allah kenan?”
Dariya sabeeha tayi ashe har hannunta ta kama tsabar excitement, don har yau batajin zata taba manta nanna, saboda matar lokaci guda ta shiga ranta,
“Wallahi Har kika yadda wani dan hotonki ina dashi ma na ajiye shi cikin kayana kafin na tafi saudi”
“Saudi? Meya kaiki saudi?”
Shuru sabeeha tayi ta dan dakata batason tuna abunda ya faru a baya kwata kwata,
“Aikatau naje yi achan”
For few seconds babu wanda ya sake magana, yanayin nanna ya sauya gaba daya, “allah sarki yanxu na kara yarda bazaki taba yima kowa sata ba saboda kinada amana, dare yayi yanxu jeki kwanta”
“Nagode sosai hajiya saida safe”
Sukayi sallama nanna ta bita da kallo.
Hilton….
Misalin karfe tara da rabi daidaiya shigo, dakin bayan sunyi sallama da salim daya saukeshi, workers din wajen suka biyoshi da shopping dayayi ma kanshi na abubuwan da zai buqata na zamn da zaiyi.
Fuskanshi na kalla, ya shanza hair cut kuma ya amshe sa sosai don yayi kyauba kadan ba, ga gashin bakinsa daketa fama kyalli yasha gyara.
Agogon hannunshi ya zame a je gefe sannan ya shiga ya watsa ruwa mai zafin gaske sannan yayi ordern brunch na dare aka kawo mashi yaci kadan saboda tashin zuciya dayakeji sama sama.
Nan yasa akazo aka kwashi abunci don bai wani ci na kirki ba.
Yana zaune laptop dinshi nakan cinyanshi yana aiki da yan dube dube call ya shugo mashi, kallon screen dinshi nayi to my surprise kawai naga wani hoton sabiha da fuskatan yayi zooming sosai, tayi murmushi, skin dinta kamar madara ga dan v lips dinta yayi wani irin jaa gashi idanunta sun fito zara zara, ya dade yana kallon wayar bawai mai kiran yake kallo ba sai fuskarta daya kasa dalilin saka hotonta da yayi akan screen dinshi, ya dade sosai har call din ya katse kafin wani ya shugo ya dauka yasa speaker.
“Hello sir!!”
“Yes saalem?”
“How are you feeling now sir? Ko nazo muje asibiti?”
“No its just minor headache, will feel much better by tomorrow”
“Okay sir please let me know idan kana buqatar wani abun at anytime”
“Thank saalem” taj ya amsa shi don haka yake kiranshi.
Yana kashe wayar ya shiga messages din da merk ya tura mashi, yana dubawa, reports ne ya turura mashi na avubuwan da suka faru tsakanin jiya da yau.
Dayaga labaran dake circulating akan hidaya sai yaji zuciyar na karaya, wallahi wholeheartedly ya dauketa a matsayin daya bata kafin tayi watsi dashi tayi disappointing dinshi, kuma yana tausayin barad da jamid, albarkacinsu ne kawai zaisa bazai saka hannunshi ba cikin almarin don idan yayi haka she will be behind bars forever, yanxu ana trail ne da da ita kuma taqi bada hadin kai.
On the other hand baiyi mamakin ganin live press release din fadwa ba, he never trusted her and he will never, yasan this will be the out omen yanda sukayi ma khaal suka cireshi daga family saboda laifinshi haka tayi ma hidaya ta nuna kwata kwata kamar ba yar uwarta ba,ta nunawa duniya basusan haka hidaya take ba ta juya mata ba, wannan shine tsantsar cin amana, kuma company will not be responsible for hidayas wrong doings.
Kashe laptop din yayi jin gaba daya wani zazzabi ya saukar mashi gaba daya.
5am..da kyar ya iya bude idanunshi, rabin daren nan ko barcin kirki baiba kwata kwata, he feels so weak, sai faman bayan gida yake shiga, yayi stooling akalla sau goma a daren, dakyar ya iya runtsawa bayan sallar asuba yayi barcin wahala.
Around 10am jikin dak sai faman zafi yake dole ya kira salem akan yazo ya kaishi asibiti.
10:30 saleem yazo suka wuce asibiti, sai daurewa yakeyi don inka ganshi bazakace bashida lafiya ba karfin hali.
Tuna isowa deda hospital saleem yayi parking sannan suka shiga shi ya zauna a reception salim kuma ya bude mashi file yayi duk wani payment da zaiyi, yana gama wa ya buqaci ganin one of the best doctor immediately,wata nurse ta mashi jagowara zuwa office din.
Asibitin irin asibitocin kasar wajene, standard dinshi da komai.
Lift suka shiga zuwa 3rd floor inda office din yake, ya shiga yaga doctor, sannan yasa a mashi test sannan ya mashi allurai don ya samu karfin jikinshi for now.
Kuma yaji dan dama dama sannan ya sauko kasa akayi test ya zauna don jiran result.
Vip Consultation room 3
Cikin dakin doctor ne zaune yana duban screen dinshi, ga patient dake zaune tana fuskantarshi.
Cire glasses dinshi yayi wannan yasa tace “dr barau akwai wani matsala ne?”
Sauke ajiyar zuciya yayi ya kalleta baima san ta yanda zai fara mata bayani ba, he has been her specialty for over the years kuma shike traking conditions dinta koda yaushe, yayi mamaki how he missed on this important issue.
“Karka cemin hawan jini ne fa? Don ga magunguna na nan na chanye su”
“Hajiya akwai matsala..”
“Wace matsala kenan?”
“You’re having a brain turmo hajiya ”
Dan murmushinsu na manya anne tayi tace “thats an expensive joke doctor barau, har lokaci na yayi kenan?”
Shuru ya danyi kafin yace “hajiya we’ve been turning blind eye on this, it has reach to a point that zai iya…”
“Zai iya zamowa ajalina?”
“Yes hajiya, we need to operate on you as soon as possible”
“Kanada assurance din zanyi surviving ne?”
“20%”
Tanajin haka kawai ta miqe, “hajiya listen to me,”
“Babu abunda zan tsaya naji fa barau, and ina baka umarin karka shaida ma kowa wannan, i want to keep it from everyone”
“Hajiya your family needs to know cause you will need them the most now”
“No barau, bazaka fadama kowa ba, i want to keep it confidential.”
Girgiza kai kawai yayi yace “hajiya please”
Batama tsaya sauraronsa ba ta fuce daga office din kirjinta na bugawa sosai, kafarta ya rike kyam sosai kamar ana rarraba kashushuwanta.
Hanyar lift ta nufa masu maintenance na daga tsaye suna aiki saboda lift din ta tsaya chak, dole mutane aka koma wajen private escalator, saida ta tsaya duk mutanen wajen suka hau tukunna kafin ta hau bata ganin gabanta haka ta hau escalator dinnan.
Zuciyanta ya karaya,it feels so heavy,kamar rock, ga wani jiri jiri da takeji, idan manyance yazo yana zuwa da kalubale iri iri wannan yasa ta fidda hope kawai idan ajalinta ne wannan babu wanda ya isa ya hana.
Baifi few steps ba ya rage ta sauko kasa kawai ta kasa daga kafarta taji ta wani sandare ta kasa daukanta.
Taj dake zaune reception tun daga sama ya hangota, kuma mistakenly ya dago idanunshi ya hangita saiya kasa daukewa kamar wanda ke karantar ta, kamar wanda keyi wani calculation ko ya karanci halun da take ciki yayi hanzari miqewa a guje kamar zai tashi sama aka bishi da kallo daidai inda ya kamata ta sauka kawai kafarta yayi trumbling jiri ya kwasheta tayo gaba cikin ikon allah ya taro saidai wani hanzari ba gudu ba dukda ya tarota hakan baisa mayafinta ya shige cikin lift dinba ya nemi shaqe mata wuya, fadin irin tashin hankalin da yake ciki bata lokaci ne,tuni security suka karaso aka kashe escalator din, kamar zai hauka haka ya soma warware wuyanta daya shaqe sosai don kanar zatayi passing out yana gama cirewa kawai ya kalli fuskanta, wani irin tsoro shock ya dabaibayeshi, baima san sanda ya furtaa..
“Ammi!!!!!!!!” Ba…..
Sama sama anne ke ganin mutanen dake wajen kafin ta sume akayi gaggawar wucewa da uta dakin gaggawa aka kwantar da ita aka bata taimakon gaggawa.
Abun ya ahde masu biyu, ga situation dinta ga shock dayasa tayi passing out ga hawan jini datake dashi amma ta boya familyn gaba daya don ko sameer bai sani ba.
Da taj aka tafi da ita emergency ya kada zaune ya kasa tsaye, yama manta da tashi rashin lafiyar, wani irin fargaba da tsoro yakeji, yana tsaye doctors da nurse na shige da fice.
About 30mins later wata nurse ta ya futo daya kasa hkura saiya tareta yace “whats going on in there? Hows she? Mwke damunta?”
“Please what are you to the patient”
Daburcewa yayi ya rasa answer da zai bata “excuse me sir? Who are you to the patient?”
“I’m her son now tell me what is going on? Meke damunta?”
Yanda yake magana zaka san hankalinshi baya jikinshi.
“I’m sorry sir, she’s in shock rn, and jininta ya hau sosai probabbly saboda news din daya risketa”
“Wani news kenan? Meke damunta?”
“She has a stage 3 brain turmo”
“Nurse betty” wata ta kirata daga ciki ta wuce ta barshi a tsaye
Baya ya danyi, yanajin wani irin abu gaba daya ya kasa controlling kanshi, first of all akan idanunshi ta kusa faduwa kuma irin faduwa kamar wannan can lead to shanyewar jiki secondly, ya rasa dalilin dayasa yakejin wani irin tattare da ita.
Yana nan zaune doctors biyu suka fito doctor barau ya kalleshi ya miqa mashi hannu yace “thank you so much for saving my patients, you have really a saving grace, badan kaiba komai zai iya faruwa were really grateful”
Girgiza mashi kawai taj yayi tace “hows she? Is she going to survive this?”
Da mamaki doctor ke kallonshi yace “survive?”
“Brain tumor??”
“I guess you had from the nurses?”
“Yes im sorry, hankalina ya tashi ne i wanted to know wani condition take ciki”
“Well shes safe now, but i dont think she will be tomorrow?”
“Why???” Taj ya tambayeshi, “it’s confidential information”
Hannu suka kara gaisawa sannan doctor ya wuce shi kuma taj ya shiga dakin,
A zaune ya tadda anne ta fizge drip da aka saka mata yanxu, kokarin saukowa tayi yayi hanzarin karasowa inda take yace “ma’am please don’t”
Kallonshi anne tayi ta kasa duake idanunta akanshi sai kawai murmushi ya kubce mata ta koma ta zauna shima ya zauna a gefenta yace “how are you feeling? Did you get hurt in any way ma’am”
Hannunshi anne ta kama ta rike ganin kamar ba bahaushe ba don appearance dinshi ya nuna hakan kuma musulmi ne don yayi mata sallama yasa tace tace “whats your name?”
“Tajudeen!!!”
Saida ta nanata sunan aranta sannan tace “thank you so much tajudeen may allah bless you for me”
Jinjina kai kawai yayi sannan yace “karkisa damuwa aranki ma’am, you have your family, they will stay with you and stand by you i promise,”
“I don’t have….”
Bai bari yaji mai zatace ba don yaui tsammanin zatace mashi batada family itako so take tace mashi batada courage din fada masu.
“You have one now! I will stand with you,”
Da mamaki take kallonshi tana hango yanda jikinshi yayi sanyi, wannan shi ake kira da pure mutun, ya ceceta daga halaka a lokacin da kowa ne zai iya hakan ba, ta lura da gefen hannunshi daya kurje ma shi bai lura ba.
“Duk wadda ta haifeta tayi haihuwa mai amfani ga alumma, allah ya baka abunda kake nema duniya da lahira, ko na mutu yanxu i have achieved everything”
“No ma’am bazaki mutu ba.. i promise, sai lokacinki yayi”
“Toh ay lokacin ne yayi tajudeen, zan iya mutuwa koda yaushe”
Idanunshi sunyi jaa sosai jiniyoyin kanshi na futowa ridu ridu kamar shine yake sharing pains dinta yace “no ma’am, i promise you zaki samu lafiya, cuta ba mutuwa bace, kuma duk wata cuta nada magani, mutuwa kuma sai lokaci yayi”
Hannunshi ta rike gam sosai tace “okay okay I believe you okay???”
Tana fadin haka ta moqe tsaye ya taimaka mata, yanajin kamar sunyi sharing relations haka itama takeji game dashi, doctor ya shugo daidai lokacin ya bata magangun dayayi prescribing sannan ya roki next ganin da zaiyi its for her acceptance don ayi mata aiki.
Tadai girgiza mashi kai kawai sannan ta fita.
Taj na rike da magungunanta suka karaso wajen lift zata shiga yyi hanzarin kama hannunta ganin zata dafe, suka shiga lift din.
Duk sukayi shuru anne ita tasan tunanin da take akanshi, don irinsu ne one in a million.
Har waje suka fita saleem na zaune cikin mota yanajin kida baisan sun fito ba.
Har bakin motarta ya rakata sannan driver ya bude baya “ma’am”
“Call me anne”
Dan sunkuyar da kanshi yayi sannan ya dago ya kalleta yace “An..ne, please promise me youll be fine,?”
“I will insha allah tajudeen”
Yanason ya karba contact dinta amma bayason zaqewa wannan yasa ya juya ta dakatar dashi ya dawo da sauri ta miqa mashi wayarta tace, “samun number ka anan”
Wani irin farin ciki ne ya bayyana akan fuskanshi ya rubuta yayi dialing number ya shigo wayarshi sannan ya mata sallama anne na yaba halayyanshi, very nice and gentle man.
Yana nan tsaye sukabar wajen ya koma mota ya zauna saleem ya karbo mashi magungunan da aka bashi da result dinshi, its just food poisoning, cimar da yake bata amshi cikinsa ba tukunna.
Jiki a mace anne ta koma gida tana tuna tajudeen, yanayin yanda yake very soft kanar hamad favorite jikanta sai takejinshi kamar jikanta shima.
Gaskia duk wadda ta haifesa ta iya haihuwar alkahiri, well mannered and respected young man, baisanta ba bata sanshi ba amma lokaci guda ya shiga ranta.
The next morning..
Su sabeeha suka koma school, ita da maya saidai harara, laila kuwa wani irin kunyanta takeji sai take ganin kamar sun hada bakine da maya, sabeeha kuwa batada riko, bata kawo komai aranta ba kwata kwata.
Nanna ta bata wani irin confidence, datakejin she can stand for her self a ko wanne lokaci.
Suna shiga first class awa daya da rabi suka fito suka shiga next one.
Ana gamawa ta tattara littafanta as usual saida kowa ya futa ta tashi.
“Hiii” taji daga bayanta.
Dakatawa tayi ta juyo karaf idanunta ya sauka kan wanda ta taimaketa jiya.
Excitedly sabeeha ta karaso inda take tace “hey…ya kike? Inata nemanki”
Dariya haya tayi tace “toh gani”
“Thank you so much for yesterday”
“Don’t thank me okay nasan bake kika dauka ba ay, nasan wacece ta aje maki ba tare da saninki ba”
Da mamaki sabeeha ke kallonta, hannu haya ta miqa mata tace “Haya”
Sabeeha itama ta miqa mata hannu tace “sabeeha”
“Nice,can we be friends?”
“Yes sure we can”
Haya kyakyawace sosai masha Allah, kuma farace saidai siririyace don batada qiba.
Gata yar gaye don dressing dinta kadai abun kallo ne masha allah, decently.
Aranar dai kawance ya kullu kamar an dade da sanin juna,haya ta jasu cafe ta saya masu abubuwa sosai sabeeha ta rasa bakin godiya, sukaci suka sha suka koma class, lokacin tashi nayi Haya ta wuce motarta maya ta tsaya jiran ya hamad, yana isowa su maya ma suka fito.
Tana komawa gida nanna tasa a kirata, lokacin hadiza batanan tana baya tana wankin kaya da maya ta bata.
Wato shakuwa wani abu ne da baka sanin lokacin dake shiga taakanin mutun da mutun, lokaci guda ta shiga tsakanin nanna da sabeeha, sabeehar da bata da sakewa saita sake sosai da nanna harda taya ninke kaya, ta gyara mata gadonta.
Abun yayi ma nanna dadi sosai don yarinyar tun lokacin nan ta gama shiga ranta.
Washe gari ta kama friday, its a short day, bayan first class da suka fito second one din lecturer din yayi delaying dole suka tsaya jiranshi wasu suka fito bakin auditorium suka tsayatsaya.
Sabeeha da Haya na tsaye suna hira some ither student ma na tsaye, click dinsu maya sukazo wucewa, kamar bataga sabeeha ba haka tazo ta gefen wajen other end din stairs din wajen ta watso mata books dinta akai, duk akan idanun haya kuma wasu daga ciki student sun gansu
“Oppsss sorrieee”
Kauda kai kawai sabeeha tayi maya ta miqo mata hannu alamun ta dauko mata books dinta, kamar bata ganta ba haka sabeeha tayi ta kauda ido maya ta kufulu soaai kamar zata tashi sama kuma ta kudiri niyar kunsasa mata, rai a bace ta duqa ta dauki littafan daidai lokacin haya ta gama cin bananas data dauko daga jakarta, ta wulla wajen hanyar stairs din ta kauda ido kamar batayi ba har wani counting takeyi don tason dole maya ta taka bananas din.
“One two three four..”
Tun kafin tace five ji kake timmmmm a kasa tayo baya kan duwawunta ta dunga sauka daga benenen a haka, me za ayi banda dariya, so embarrassing, maya kamar ta nitse harma masu video, kamar tayi kuka kawayenta sukazo suka taimaka mata ta mike ta bar wajen a guje tana kiran wayar saleem.
Sabeeha dake dariya kasa kasa tana dagowa taga haya na daga mata hannu suka tafa.
Haya tace “serves her right..no one dares to mess up with my friends”
Anatse sabeeha tace “thank you haya”
“Fadamim meysa take treating dinki haka? Meysa baki ramawa? Ki koya mata hankali mana”
“I çant haya”
“Meysa?”
“Saboda ni yar aiki ce a gidansu, ni ba kowan kowa bace banida gata banida kowa”
“Kinada gata sabeeha, and i promise to stand by u okay”
“Thank you haya.”
“Zanyi maganin ta ne idan naga dama bazata kara tako kafa school dinnan ba”
Da mamaki saveeha ke kallonta haya ta ja hannunta tace “bakisan koni wacece ba ko? Bana fada ne, nice first and only daughter na founder din makarantar nan, Haya baba Datti”
Baki sabeeha ta kama tsabar shock yanxu wannan yar me makarantar ce? Ba girman kai babu dagawa? Ikon allah.
“Aje wannan shock din naki ga lecturer yazo muje class”
Transcorp hiltons hotels…
Kallon wayar yake da mamaki, yanxu nan ya gama tunanin ta saiga call dinta ya shugo unexpectedly.
Jiya sun dade sosai a waya, kuma duk tsawon wayar nan encouraging dinta yakeyi yana nuna mata cewa she’s not alone,he understands her fear saboda tsufanta and he wants to help her through the journey, yanajinta kamar uwa, kuma wallahi duk a tunaninshi batada kowa.
Sannan daga baya ta tambayeshi about himself ya fada mata komai bai boye mata ba, kasar mahaifarshi da inda ya taso da abu daya ne bai fada mata ba rayuwar da yayi a baya da dalilinshi na zuwa nigeria kawai dai yace mata wasu ayyuka ne suka kawoshi nan, dake macece wadda tasan harkar business sosai and she has interests in the field tunda hannunta yayi aiki a ciki over the years, taji dadin iin yanda yakeda nashi experience din.
Abunka da wayyayu sai suka zama very close lokaci guda, ita kanta tana mamakin yanda ya shiga ranta lokaci guda.
Dagawa yayi cikin hanzari bakinsa dauke da sallama.
“Walaikum salam tajudeen, how are you my dear”
“Hamdullah, how are you feeling? Kinasha medication? Akwai avunda ke damunki?”
“I’m fine tajudeen, thank you for your concern, i will like to invite you for dinner this evening”
Murmushi yayi ya dubi agogon hannunshi, hopefully zai gama abunda yake kafin lokacin.
“Tajudeen are you there?”
“Yes anne i am…”
“Please inason kazo, I will like to treat you dinner with my family to thank you enough for helping me”
“Insha Allah zanzo..zan aje duk wani plans dina for the day”
Wani irin dadi anne keji ganin yanda yake answer ta with so much respect.
“See you then may Allah blessings be with you as always”
“Insha Allah”
Sukayi sallama ta kashe wayar shima ya aje.
Yana gama shiryawa ya fito inda saleem ke jiranshi.
Suka gaisa asual suka fara zagayen da zasuyi, sun dade sosai kafin suyi branching a company baban salim na motocin ford da yake karban dealers.
Salim ya sanar ma babannashi daman taj din ya buqaci zuwa wajen, shi baban nasa baya kasar yayi tafiya so ya bama salim go ahead don yasan mahimmancin taj din tunda yaji daga inda yake dukda baisan shi din waye ba.
Sun zagaye wajen and taj is so impressed with yanayin yanda suke tafiyar da wajen, don ya banbanta da yanda sukeyi achan company, kuma duk varieties of different collections akwai saidai karancin colors ga pending orders da mutane keyi suggesting, a take yayi waya da merk yasa suyi approving duka collection din da baban salim ya nema daga kamfani.
Lokacin da wannan abun alkairi yazoma alhaji buba yayi murna kwarai ya kara tabbatar da zuwan taj alkairi ne, abunda sai a dauka shekaru kafin ayi approving sai gashi cikin awanni kadan ya samu kai abun yayi mashi dadi sosai.
Salim fa zuru yayi da idanu ganin yanda taj din yake zayyano wani turanci yana waya a take yayi signing wani deal dasu yayi approving a bude wani companying anan.
Wani abun mamaki daya kara gigita salim lokcin da suke zagayen motocin ya nuna interest akan wata ford sprt car, take taj yace mashi “are you into drift?”
Yace mashi yes, daga yes dinnan kawai yace “take it”
Salim kamar yayi tsalle don ko a mafarki bai taba tsammani ba, take wata natsuwa ta shigeshi yayi murna ba kadan ba kamar zai tsugunnama taj.
Shi taj dinma mamaki ya dungayi yanda yake mashi godiya don motar ba komai bace compare to latest collections dinsu na yanxu.
A haka sukabar wajen aka biyo taj din da wata dankararriyar mota daga cikin motocin.
Sai wajen 5 suka dawo gida, yayi sallah yayi wanka, baibi takan abunci wajen ba kwata kwata don yanxu ba komai yake ci ba.
Yana zaune mesaage din mutallib ya shugo mashi kamar haka.
“This is khaal, idan kayi receiving mesaage dinnan inason ka kira ni”
Take yayi dialing back tare da wani dogon tunani ba.
Call din na shiga akayi saurin dauka, taj yayi sallama.
Suka gaisa sannan suka dan tattauna, sun dade sosai suna magana kafin suyi sallama.
Har zai katse wayar khaal yaui saurin dakatar dashi.
“Tajudeen!!!” Khaal ya kirashi.
“Ka nemi mahaifiyar???”
Dam yaji gabanshi ya bada yayi saurin runtse idanunshi.
“This is the right time taj, shakarun da suka wuce a baya bazaka iya dawo dasu ba,its high time ka nemi mahaifiyarka, what you should have done years ago”
Jiki a mace ya dafe kanshi dayaji ya sara mashi jikinshi ya mutu yace “I don’t deserve to be with her, khaal,ban chanchanci bayyana a gabanta ba khaal,nayi babban kuskuren da bazai gogu ba khaal”
“Allah yana mana laifi munyafe masa, she will Accept you happily, HAJAR is one of a kind, and halinta ka biyo, baka da kamarta ayanxu, so face the consequences ka nemi yafiyarta, ka nemi albarkacinta saboda rayuwarka tayi albarka, saboda rayiwar ta inganta”
“Kodan hakkinta banajin zan taba samun kwanciyar hankali a rayuwata khaal, banida bakin kiranta a matsayin mahaifiyata, na cireta daga babin rayuwa ta nayi dana sani khaal, i was foolish and stupid and manipulated into thinking bata buqata na a rayuwarta”
“Ba laifinka bane taj, ba laifinka bane..KADDARARKA kenan,bazamu iya maida hannu agogo baya ba, so try and fix your past, try and clean your relationship with your mother, ka gyara alaqarka da mahaifiyarka, nasan guilt ke dakatar dakai, amma inason ka sani lokaci na kurewa karkazo kayi regretting”
“Insha Allah khaal” da haka sukayi sallama ya kashe wayar
Ya zauna yana tunanin rayuwarshi ta baya, wallahi babu ranar da zata gifta a rayuwarshi da kalmar mahaifiyarshi bazatayi crossing kind dinshi ba, wallahi an cuceshi matuqa, ace kana raye kuma mahaifiyarka na raye wadda ta tsugunna ta haifeka amma anyi distancing dinku, kuma bai gani laifin kowa sai laifin kanshi, bai ganin na iyayenshi da suka rabu a daidai lolacin dayafi kowa buqatarsu har hakan yayi sanadiyar gurbata rayuwarshi ya shiga wani traumatic stage at a very young age.
Sai yaji wani irin dumm a kanshi, hoton ta daya karba wajen khaal har yanxu yana jikinshi akoda yaushe duk inda yake.
Maganganunsu da khaal ya kara bashi wani irin courage.
Har wajen magrib yana zaune jiki a
Mace kafin ya tashi ya shiga bathroom yayi wanka ya fito da alwala yayi sallah, cikinshi ya soma qugi amma yaqi cin komai.
Yana zaune yana addu’oi akayi sallahr isha’i ya tashi yayi sallah yana idarwa a gaggauce ya shirya cikin irin farar jallabiyan nan ya saka kundura akanshi ya nadota saiya dawo sak balarabenshi dashi Masha allah.
Kai masha allah masha allah…tsarki ya tabbata ga wanda yayi wannan halitta, sai buga kamshi yake yalwatacce, ya dora agogo a hanunshi da zobunan azurfa a yatsunsa.
Yana gamawa ya fito daga dakin cikin kamewa ya sauka kasan, yana sauka kasan ya karba keys din sabuwar motar daga wajen valley keepers sannan ya shiga ciki, wajen dashboard ya bude kamar yanda ya buqaci permit da documentation duk an hada mashi a ciki karkashin sunan alhaji buba incase.
Kunna motar yayi sannan ya kunna wayarshi tare da dialing number anne, ana dagawa ya buqaci address ta fado mashi sannan yasa a map ya kama hanya.
Lokacin wajen karfe takwas da yan mintuna kadan, anatse yake driving yanabin map dukda baisan hanyar ba cikin ikon allah cikin abunda baifi 20 mins ba ya iso gwarinpa.
Daga nanma ya dunga bin map din har zuwa santuraki’s creasent avenue, yana shugowa lighing din wajen ya bade ko’ina ya soma slowing motar ganin securities at ko wanne end, bakinsa ya soma matsawa a hankali don banjin abunda yake fada harya karasowa gate din tafkeken mansion din.
Yayi bayanin inda zaije da sunansa kai tsaye babu wani tambaya aka barshi ya shiga, saiyama rasa ina zaibi wanne part zaije, daidai babban dake tsakiya ya tsaya wajen parking lots yayi parking.
Hamad dayayi parking shima yana kokarin kwasar paper bags din dinkunan dayayi tun daga shugowar motar yabita da ido.
This is the first time yaga irin motar a cikin compound din.
Ya dauka wajen minti biyu bayan ya kashe motar bakinsa na motsawa kafin ya sauke ajiyar zuciya ya fito daga motar yabi ko’ina da kallo har idanunshi ya sauka kan hamad dake shirin shiga main house.
Dan dakatawa yayi ya karaso inda taj din yake ya miqa mashi hannu da mamaki suna kallon juna.
“Asaalamu alaikum”
“Wa alaikum salam wa rohmatullah”ta ya amsa shi fuskansa ba yabo ba fallasa sai yalqi take Masha allah, ga wani cikar haiba da annuri dake kwance kan fuskar.
Hamad kwata kwata bai kawo shine baqon anne ba wanda tabi ta ishesa da zancensa da take cewa kusan halinsu daya very soft and calm guy.
“Hamad Abdullah”
“Tajudeen abdullah taheel”
Suida yaji sunansa tukunna hamad ya gane shine expected guest din kenan, shine wanda ya tafi karba kaya da anne tasa ayi masa daga babban kamfanin the boss ateliar suna dinkin manyan kaya da yadidika hadaddu.
Murmushi hamad ya mashi sannan ya mashi iso suka nufi hanyar main entrance.
Har cikin babban parlor hamad ya jagoranceshi ya zauna, babu kowa cikin parlor din sai kamshi yake ga sanyi ac.
Gaban taj daketa faduwa tun amota sai yayi doubling kamar ana lugude, and its something different da bai taba experiencing ba kwata kwata.
Har yana dafe kirjin nashi don kamar zai fito, yanajin kusancin wani abu daidai da bugun zuciyarshi.
Saukowa hamad yayi ya zauna tare dashi suka sake gaisawa sannan ya shaida mashi ya sanar ma da anne zata sakko yanxu.
Jinjina kai kawai taj yayi shi kadai yasan me yakeji.
Cikin yan sekanni kadan sai ga anne ta sakko cikin shiga ta alfarma, idanunta sanye da farin glass ga fara’a kwance a fuskanta.
Daidai nan anty fadila ta shugo tare da laila don anne tace yau duk anan za ayi dinner, (mijin anty fadila baya nan yayi tafiya)
Yana ganin saukowar anne yayi saurin miqewa murmushi kan fuskarshi shima ta karaso parlor ta zauna ya tako har inda take ya kama hannunta kamar yanda yakema ammu da khaal ya sumbacu hannunta cikin larabci ya gaisheta ta amsa.
Su anty fadila sai suka zama yan kallo, wannan ne baqon anne din, tsantagwaran balarabe? Shin ina ta san shi kuma? Meya hadashi da ita tambayoyin da suka dunga yima ka su kenan.
Su laila sai aka fara sunne kai anga kyakyawa, ta kasa daina kallonshi don baka iya resisting, allah allah take maya tazo ta ganshi, ita ta rikice qila maya sai sumewa.
“Zauna tajudeen”
Ta mashi nuni da kujera ya zauna.
Daidai nan uncle sameer ya shugo shima, shida anty mubina da yan yayanta, anty laila ko itada batasan shiga cikin dangin miji cewa tayi zazzabi takeji bata iya futowa, sai su abal ne suka biyo bayan daddyn nasu.
Gana daya yaran wajen cikin harshen turanci suka gaishesa ya amsa masu da yar fara ar shi.
Anty fadila ma ya gaisheta, uncle sameer ko musabaha sukayi.
“Masha allah tajudeen welcome to my home, and waennan family na ne”
Da mamaki sosai yake kallonsu su duka don wallahi bai taba tsammanin shes blessed with such a wonderful family ba.
“This is my first sameer, and this is my second fadila, thats her kids i have one more, she’s in london”
“Masha Allah” ya furta ahankali yana murmushi.
Su uncle sameer sai jinjina shi suke aransu don abun mamaki ne ace anne ta kawo stranger to their home definately yayi mata wani abunda bazata manta ba.
“Laila ja yaran nan kuje dining”
Laila ta jasu su duka ya rage sai iyayen nasu kadai.
“Sameer wannan shine tajudeen, shine wanda ya taimakeni badan jiba da tuni bana nan zaune a kusa daku”
Da mamaki duka suka juyo suka kallon anne meysa zatayi wannan furucin,….duk suka zuba mata idanu gaba dayansu suna jiran amsa.
“Muje muyi dinner ko”
Tasan son karin bayani suke amma ta katse su suka miqe tayi gaba suka bita a baya.
Aka zazzauna, what a happy family daya shiga cikinsu sai yaji kamar he’s among.
Uncle sameer ya dunga janshi da hira don yana kusa dashi.
Anne babu abunda take sai murmushin jin dadi kawai.
Ana gama cin dinner suka dawo sitting room, anne taso fada masu komai amma saitaji this is not the perfect timing gashi nanna bata nan, taj daya lura da hakan shima baiyi kokarin cewa komai ba.
“Anne tace daga saudi kake? Meysa kawo ka nigeria? I must say business right?”
“Yea business..and some personal stuff”
“Masha allah what are you into?” Sameer ya sake tambayarshi.
“Cars..i am the founder of…”
“Assalamu alaikum…”
Daga ciki da sukajiyo sallamar suka amsa da “wa alaikum salam..nanna”
Driver ya biyota da akwatin nata, duk suka juyo suka kalleta don bata idasa karasowa ba hamad yayi saurin karban box din anty fadila tace “ah ah baki tafi ba?”
“Uhm fadila bazan iya ba da delays din flight dinku na nan nigeria, ive been stranded for about 3 hours, sun gama zaunar damu hamad yayi min booking wani flig…”
Chak ta tsaya tana karasowa sitting room din, kuma a daidai lokacin idanunta ya sauka akanshi, bugunda kirjinta keyi lokacin data shugo estate din bana wasa bane.
Daga kan wayarta zuwa files din dake hannunta duk wani abu daya kasance yana hannunta gaba daya sakinshi tayi kasa wanwas ji kake passs pass a kasa, take idanunta yayi jaa sosai ta soma yin baya baya jikinta na karkarwa jininta ya soma yin kasa sai jiri daya soma dibanta, fadila data lura da yanayinta tace “nanna!!!! Nanna!!!!” A daidai lokacin ya dago da idanunshi ya sauke cikin nata mug din tea din dake hannunshi ya sake gaba daya ya malale a kafanshi gashi da zafi sosai, shima cup din ya fashe.
Jikin nanna ya fara vibration kamar wadda zata shide tayi luuuuuuuu ji kake timmm a kasa.
“Innalillahi wa inna ialaihi raji’un suka miqe gaba dayansu sukayo kanta harma da taj da baisan ya taka mug dinnan ba ya karasa fashashi ya fasa mashi kafa, yana zuwa gab da ita ya kasa karasawa hotonta na flashing a fuskanshi yayi saurin rintse idanunshi ya bude ya sauke akan fuskanta da idanunta ke rufe, ya wani irin dafe kanshi cikin hanzari ya tura hannunshi cikin aljihunsa ya zaro hoton nata, duk kachaniyar da suka a gabamta duk sun zagayeta bayajin kwata kwata abunda suke fada abu kamar an
Toshe mashi kunne da basira ya kasa tabuka komai sai kallon hotonta da yake da fuskarta wani irin zazzabin ya saukar mashi mai zafi sosai ba kadan ba.
Ruwa aka yayyafa mata amma ta kasa dawowa daidai karshe ma nunfashinta daukewa yayi gaba daya.
Sameer yayi saurin cewa “anne bata nunfashi, bata nunfashi”
“Innalillahi wa inna ilaihi rajiun sameer ku kira barau ku kira ambulance karna rasa yar uwata, innalillahi wa inna ialaihi rajiun” ta dafe kanta daya soma sara mata.
Sai a lokacin taj ya dawo hayyacinsa wallahi bayaji baya ganinsu gaba dayansu, gaba daya ya koma kamar jan kosai, jijiyoyinsa suka fito rado rado.
Ya tsugunna ya dauko nanna gaba daya ya rungumeta zuciyarshi na kuna, wasu irin strong mixed feelings na shigarshi ga radadin da yakeji a zuciyarshi, ya nufi hanyar fita da ita.
Bata nunfashi inaga maganar kiran ambulance, wallahi bayajin me suke cewa kwata kwata yayi reverse da motar baibi takan kowa ba ya figi moatar, allah yaso akwai keys a jikin hamad wannan yasa suka shigiga cikin moatar sukabi bayan tashi.
Gudu yake ba karamin gudu ba kamar zai tashi sama,kiris ya rage baiyi causing accident ba har suka iso deeda.
Suna isowa ya zagaya baya kamar his life depend on her ya daukota ya shiga da ita, take nurses suka karaso da gado a da sauri aka sakata yabisu, aka dakatar dashi.
Aka kira doctors har uku don ta shiga critical condition, dasun shiga sun fito saiya miqe daidai nan su anne suka karaso, wani doctor ya sake futowa taj ya riko hannunshi kamar zai ballashi sai zufa yake gaba daya ya futa hayyacinsa yace “please save her…dan allah ku ceceta, i need her in my life”
Gaba daya kallonshi suka dunga yi, ya gama shiga tashi hankali gaba daya.
Anne da sameer da fadila suka karaso harda hamad suka zagaye doctor din anne tace “barau whats going on? Me yar uwata ke ciki? Ku rifa min asirin don allah ku ceceta”
“Hajiya calm down.. you need to make her calm down saboda idan hankalinta ya tashi its risky” barau ya karashe yana kallon sameer, anne tace “barau explain to me what is happening to my sister”
“Hajiya shock ne, which result to jininta ya sauka, yanxu nurses zasu kawo blood daga blood bank na asibiti, insha allah babu abunda zai sameta ku mata addua”
Daidai nan nurse ta karaso jiki na bari tace “sir can i have a minute with you”
Yadan matsa ta mashi magana kafin ya juyo, idan har ya bayyana masu babu blood type dinta a asibitin nan zai iya zame masu matsala don a gaskia family santuraki manyan client dinsu ne.
With the kind of look da yake basu yasa taj cewa “take my blood..”
Gaba daya juyowa sukayi suna kalonshi, with annoyance hamad yace “please stay on your limit, allow them to do thier work”
Ko kallo inda yake baiba yace “i said take my damn bloood…idan wani abu ya sameta saboda delay dinku i will Make sure that asibitin nan bai sake anfanuwa ba”
“Bubu yanda za ayi a diba blood dinka bamusan kokai waye ba”
Sameer yayi magana cikin bacin rai don shi tun daya dauki nanna ya fice da ita ranshi ya baci.
Wallahi baima san sunayi ba kwata kwata ji yake kamar ya shaqe doctor din.
Anne ta katse su tace “doctor barau what is the issue”
“Hajiya im sorry bamuda blood tupe dinta”
“Ku diba nawa”
“You’re not compatible hajiya batada wani da ko jika? Wanda blood dinshi A ne?”
“Please take my blood and save her”
Sai a lokacin barau ya kalleshi yace “qre you related to her and what’s your blood group sir?”
“I AM HER SON!!!!!”
Dammmm gaban anne ya bada, ay itama saita samu wani hawan ruwa a take.
Fadila da sameer banda kallonshi babu ahunda suke with so much shock.
“Doctor doctor the patient is having pulsing tana jijiga”
Wata nurse ta fito hankali a tashe.
Ay ko kallon inda suke taj baiba ya afka dakin doctor barau yabi bayanshi.
Yabar su uncle sameer da anty fadila da suman tsaye, uncle sameer zai bishi don a tunanin shi ko ya haukace ne anne ta dakatar dashi.
“Tabbas dan hajara ne wannan babu makawa, tajudeen dan nanna ne ita din mahaifiyarshi ce, wadda ta tsugunna ta haifeshi tayi rainon cikinsa wata tara allahu akbar” sai hawayeeee😭😭😭😭😭
✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊
MATAR TAJ (destined with you🩵🤍)
Written by
Queenmarh✍️
Book2
PAID
Tun daga nesa ya hango su biyu,kowacce na rike da jaka a hannu sai faman yanga akeyi, maya kam tafi kowa yauqi kamar bazata taka kasa ba.
Duban agogon hannunshi yayi ganin 4 daidai, da yasan yauqi zasu fara da yayi sallar sa kafin ma ya karaso school din, ganin babu sabeeha a tare dasu yayi mamaki sosai, don yawanci ma da zarar sun futo take yin gaba tabarsu, itadai badai sauqin kaiba, ya lura kwata kwata batason a bata mashi lokaci.
Gashi dagashi har ita ba ma’abotan son magana ba amma yanxu sun dan saba sama sama, he’s picking interest on her, yanda take da kamewa da sanin darajar dan adam wannan yafi burgeshi game da ita sosai ga biyayya.
“Hello ya hamad..”laila tayi magana suna karasowa inda yake.
Bai kalleta don suna isowa ya kauda idanunshi akansu, da mamaki yaji muryar maya tace “Hi”
Bai amsa masu ba don sallama yayi expecting daga garesu kamar yanda sabeeha ke mashi da zarar ta ganshi sannan ta gaishesa.
“Wa’alaikum salam, tunda baku iya sallama ba, “sorry ya hamad assalamu alaikum”
Banza yayi da ita maya ko ta wani irin tabe baki suka bude kofar baya.
Ya tsaya bai motsa ba yana jiran isowar sabeeha, maya tayi winding glass din tace “mu tafi mana tana da extra class yau sai anjima zata dawo”
Ko kallon inda take baiba saida laila tace “ya hamad da gaske, dazu munyi class din statistics da ita lecturer yace duk wanda is left behind baiyi catching up da lectures din yau ba ya tsaya za ayi extra classes, probably ta tsaya ne for the class”
“Ke maisa bazaki tsaya ba?”
“Ya hamad bazan iyaba marana yana min ciwo, sabeeha will help me out”
Girgiza kai kawai yayi ya zagaya mazaunin driver ya kunna matar tare da barin wajen.
Yana saukesu gida yasa laila ta fada ma anne asa daya daga cikin driver suje su dauko ta zuwa anjima don zai koma office bazai samu dawowa ba sai dare.
Ko minti biyar basuyi ba da barin wajen ba ta fito cikin sauri ganin 4:15 saboda tasan hamad by 4 yake isowa gashi batason bata mashi lokaci kwata kwata, gaba daya tayi wani iri, fitowanta kenan daga office din lecturer da akace yana kiranta koda taje office din nashi ya shaida mata bai nemeta maybe wani lecturer din ake nufi ba shi.
Hakanan ta fito jiki a mace, gashi class rep din ya tafi shine daman yace ana kiranta.
Haka nan ta tsaya wajen minti talatin babu ya hamad wajen inda yake parking, tayi mamaki sosai ba kadan ba wata dabara tazo mata ta wuce inda tasan su laila na zama ko zata gansu, koda tace nanma babu su, haka nan ta juya zuwa masallaci tayi sallah sannan ta fito ta zauna wajen inda yake parking gudun kar yazo suna nemanta don bata neman abun magana.
Tana nan zaune abubuwan da suka faru dazu suka dunga mata flashing a kwakwalwa, hankalinta ya tashi sosqi ba kadan ba, abu daya za ayi mata dake tayar mata da hankali shine qazafi, tana jin zafin abun sosai, dukda anyi clearing komai hakan baisa taji wani iri ba don har toilet ta shiga tasha kukanta ta godema allah yanda maya ta tsaya kyam tana kallon cikin idanunta tana attacking dinta da sata, batajiba bata ganiba, daa allah yaso class din basuda yawa sosai don da irin general class ne idan akaji wannan wani ba lallai ya yarda ba itace tayi satar ba.
A zuciyarta ta soma magana “banajin inada rabon jin dadi a duniya ne shiyasa”
Hawaye mai dumi ya sauko akan fuskarata tayi saurin gogewa tare da dago kanta jin alamun mutun a wajen.
Irin patrol securities dinnan ne dake assisting wajen parking.
“Baki tafi ba?”
“Ina wuni” tayi saurin gaishesa ganin babba ne.
“Lpy lau, inace kece ake zuwa daukan ku a wata katuwar bakar mota keda yan uwanki? Ay sun tafi tun dazu? Ya akayi baki bisu ba?”
“Wallahi ban sani ba, qila sun jirani ne ban fito ba da wuri” ta bashi amsa.
“Toh ki kirasu a waya,”
“Tohm nagode”ta amsashi ya kara gaba.
Wayar ta zaro tana kallonta, tama rasa me zatayi, what if da gaske sun jirata bata fitoba suka tafi? Ita a wacece zasu zauna jiranta ita da ba kowan kowa ba?” Da wannan tunanin ta aje wayar kawai ta kasa kira, nan ta fara tunanin ya zatayi, yoh ta ina ma zatayi kiran babu kati a wayar.
Jikinta yayi sanyi sosai kalau ta zama stranded gaba daya.
Acahn gida suna isowa kowacce tayi hanyar part dinsu, fadila ta wuce nasu while maya ta wuce na anne, zansu dabarar da takeyi duk welends take kwana wajen anty laila donta samu damar fita son ranta.
Kuma anne bata hana ba don ya sameer yayima anne magana akan ta dunga barinta tunda tana taya laila hira don batada yar budurwa kamar laila.
Anne batayi jayyayya dashi ba don babu wani abun kawai dai daman so take ana sa ido akanta tunda nanna ta ganta a hotel.
Shi ko ya sameer anty laila ce ta sashi gaba da mita da qananun maganganun yanda ta saba ay ba’a sonta a gidan da anty mubina ce baza ace maya ta bar part dinta ba dayake ita aka tsana itace yar agola wadda keda bakin jini shiyasa ake kyamatarta, wannan qananun maganganun nata yasashi zuwa wajen anne ya roki abarta tana zuwa tayata hira tunda duk an zama daya.
Lokacin data shugo part din anne babu kowa a kasan sai hadiza da sukayi kicibus hannunta rike da iced squeeze orange, kamar ta daidaici lokacin dawowarta kuwa.
“Sannu da dawowa hajiya”
Ko kallonta maya batayi ba ta wuce sama, hadiza tabi bayanta.
Tana gab da shiga bedroom dinta hadiza ta cimmata “in shugo?”
Dan dakatawa maya tayi sai kuma tace “shugo”
Rufo kofar hafiza tayi tana duban mayar data watsar da takalmanta da handbag dinta a kasa ta yaye yalolom gyalen data rikeshi a hannu sannan ta fada gadonta tana sauke ajiyar zuciya.
“Sannu kin gaji ko? Ga juice nan mai sanyi yanxun nan akayi juicing dinshi”
Hannu maya ta miqa mata ta karba sannan ta zauna tasha juice din kadan ta miqa ma hadiza, a tunanin fita zata yi saiyaga akasin haka, “in hada maki ruwan wanka?”
“Hada” ta amsata da gadara.
Jiki na tsuma hadiza ta shiga bathroom ta hada mata ruwa mai zafi sosai a jacuzzi ta watsa mata liquid bath soap dake wajen masu kamshi sannan ta fito.
Miqewa maya tayi ta wuce hanyar bathroom tana rage kayan jikinta ta watsar anan kasan.
Haka hadiza tabi kayan tana tattaresu ta saka a laudry basket sannan ta futo ta gyara mata gadon fess fess kamar ba a haushi ba sannan ta tsaya don jiran fitowarta.
Takai wajen 30mins cikin bathroom bata futo ba hadiza dai na tsaye ta fito.
Da mamaki maya ke kallonta, cikin rashin iya magana tace “ke kuma zaman me kikemin a daki? Ko dan hannu za amin ne ban sani ba?like mother like daughter?”
“Yo hakuri hajiya maya, daman na tsaya ne naji ko kina buqatar wani abun? Ko zakici abunci? Ko kinason a dafa maki wani abun da kikeso”
Wajen dresser maya ta nufa tana daukan man ta zata shafa tace “kije ki kawo min pepper soup din kaza, amma thighs din kawai nakeso, karki cika yaci sosai”
Murmushi hadiza tayi tsabar jin dadi tace “toh sai me kuma kikeso, fada kin duk abunda kikeso zan maki”
“Shiknen, idan kin gama kizo ki wanken undies dina sai bathroom dina ba a wankeshi da kyau ba”
“An gama hajiya maya, ay babu abunda baza a yi maki ba gimbiyar gidan nan”
Maya ji tayi kanta kamar zai fashe sosai ba kadan ba, hadiza na fita tayi smirking “lallai wannan anyi bagidajiya,”
Fitar hadiza daga saman taci karo da rabi data futo daga part din anne da sauran yan matan dake hauro mata da abunci sama.
Rabin ce ke assigning dinsu inda zasu dinga aiki kuma tayi mamakin ganin hadiza a sama don aikace aikacen ta bai shafi sama ba wannan yasa tabi hadiza da kallo suna saukowa kasa tayi kicibus da ita a kitchen tana kokarin daura abunci.
“Hadiza meya kaiki sama inace aikin ki a kasa kawai yake.”
Rai a bace hadiza tace “banida ikon yin aikin daya wuce na kasa ne? Ke kinsan matsayina kuwa a gidan nan?”
“Menene matsayin naki? Inace aiki kikazo yi ana biyanki? Kinada wani matsayin ne bayan wannan bamu sani ba? Ki fada min dalilinki na zuwa sama inva haka ba na sanarwa da hajiya, babu amsu zuwa saman sai wanda aka yarje masu kuma bana jin kina cikin waenda akace su dunga hidima a sama”
Hadizq tajji zafin maganar rabi amma haka ta hadiye ta danne tace “ba komai ne ya kaini dama ba, jikar hajiya ce ta buqaci a kawo mata juice da parpesun kaji shine na hau saman”
“Ba aikinki bane idan tana buqatar wani abu zata nema wajen masu girki ko ta kirani”
“Ke kuma asuwa?? “
Suka jiyo muryar maya daga bakin kitchen din, juyowa rabi tayi ta kalleta, tana daure da towel a kirjinta ko me tazo dauka a kitchen din allah kadai ya sani,
“Daga yau duk abunda ya shafeni ita ce zatayi min, karki sake questionining dinta, banason iyayin banza da wofi, kema ba yar aikin bace ba har kinada ikon fadin yanda za ayi da abunda baza ayi ba”
Sunkuyar dakai rabi tayi, gaba dayansu zasu haifi uku ta wallahi amma yanda take magana kwata kwata babu respect a ciki.
“Mteww…ke yama sunanki?”
Ta nuna hadiza da hannu, binta da ido hadiza tayi, sai kawai wani murmushi ya kufce mata ta kasa magana saida mayan ta kara cewa “baki..”
Cikin sauri hadiza ta katse ta “hadiza..sunana hadiza”
“Inason smoothie yanxu kafin ki gama pepper soup din”
“Tohm an gama yanxun nan kuwa za ayi maki sai kuma me kikeso? Ki fada kin ayi maki yanxun nan”
Dan tabe baki maya tayi tana jin wani irin dadi aranta amma ta basar tace “ya isa”
Ta futa rabi ta girgiza kai aranta tace “futsararriyar yarinya”
Hadiza kuwa ta bi rabi da kallo tayi kwafa sannan ta fara kokarin yi mata smoothie data buqata.
Ahankali akayi knocking kofar kafin a shugo da sallama, nanne ce zaune akan gado cikin irin maroocan gowns dinnan mai hula, tana ganin anne tayi saurin sauke kafafunta daga kan gado ta aje takardun dake gabanta da glass din dake hannunta.
“Wa alaikum salam! Anne!! Lafiya dai dakin bari nazo ay keda kike fama da kafa” nanna tayi magana tana kallon yayar tata.
Takowa anne tayi ta zauna gefen gado inda nanna ke zaune tace “nazo dubaki ne, ya zazzabin?”
“Alhamdulillah anne doctor yazo dazu ay dan zazzabine fa, alhamdulillah ya sauka ma, ina wuni ya fama da iyali”
“Toh alhamdulillahi,”
Shuru ne ya dan biyo baya kafin anne tace “hajara!”
Nanna najin yanda ta kira sunanta tasan akwai magana.
“Na’am yaya”
“Nayi magana da doctor dazu, ba zazzabi kadai ke damunki ba harda hawan jini kuma nasan damuwa ce tasa maki shi, Hajara ina ganin lokaci yayi daya kamata ki waiwayo rayuwarki ta baya….”
Murmushi nanna tayi ta kalli anne tace “wallahi babu abunda ke damuna babu wata damuwa anne, kawai stress din aiki ne ba wani abu ba, ina gab da retire nima na huta abarma yara suyi”
“Hajara kinsan abunda nake nufi, bazanyi forcing dinki ba tunda kin nuna bakyason ayi maganar, bazan iya sanin abunda kike ji aranki ba amma inaso ki sani ni yar uwarki ce hajara bakida kamarni, nice uwa a gareki kuma nice uba, bana fatan rasaki hajara don ayanxu ne nafi kowa buqatarki, babu wanda yasan gobe da abunda ke cikinta, kiyi hkuri hajara, bazan fasa baki hkurin nan ba kinji, ki aje komai a gefe ki nemi…”
Hawaye ne suka fara neman ambaliya akan fuskarta tace “Anne please..dan allah dan allah badan halina ba mubar zancen nan,”
Shuru anne tayi sannan ta kama hannunta tace “shikenan hajara na bari, allah ya rufa asiri allah ya sawaqe, tunda kince ba damuwa bane, amma kiyi kokari kina gujema stress din”
“Insha Allah.. ya kafan ki?”
“Kufa kuke wani damuwa da kafa, wallahi garau nakejinta yanxu, abun kunya ni ban samu hawan jini ba da shekaruna gashi ke saboda tunani zaki jefa kanki a halaka”
Girgiza kai kawai nanna tayi don yayar tata tasanta ciki dabai, duk falewar da zatayi bazata taba yarda ba don ta san duk wani condition da take ciki.
“Toh anne za a rage tunanin,”
Mumrushi tayi mata sannan sukayi sallama anne ta fita.
Wata nayyayyiyar ajiyar zuciya nanna ta sauke,idanunta sunyi jaa sosai take taji kirjinta na mata wani irin nauyi, tayi hanzarin daukan pills dinta ta sha sannan ta kwanta.
Daki anne ta koma ana mata tausa hamad ya shugo suka gaisa, wuraren past 7 don anan idar da sallah ya shugo, hira suka danyi jefi jefi ya danci tuwon da aka kawo ma anne sannan ya mata sallama kan zai dawo anjima.
Yana sauka kasan yaga yan aikin gidan nata faman shirya dinner a dining duk bai buqata saiyaje ya diba.
Sai a lokacin sabeeha ta fado mashi yasan by this time an daukota, amma rashin ganinta da baiyi ba dazu sai yaji babu dadi gaba daya, gashi bazai iya sqwa a kirata ba, toh akirata yace mata mene? Saboda mene? A wani dalili kenan? Saurin watsar da zancen yayi ya wuce gida.
Yana parking a part dinsu ya shiga daga ciki.
Kai masha allah, gaskia anty fadila badai gayu ba, itama gidanta mansion ne mai zaman kanshi baikai nasu anne ba don shine family house dinsu amma shima badai girma ba gari guda.
Ko’ina yasha adon gold and off white, parlor ga wani katin frame na hoton su su hudu, laila hamad then babansu sai mamansu.
Daidai zai shugo yaci karo da laila data debo abunci zata wuce sama, hartasa yar aikinsu ta kawo mata tanajin sallamarshi ta karbe karyayi mata fada, irin waennan kananun abubuwan kamar irinsu gyaran gadonta da gyaran wardrops dinta ita keyi, ba’ayarda yar aiki tayi ba saidai wanke toilets da shara, saboda kar shagwabewar tayi yawa, sometimes ma itake girki a gidan, dakin mamansu kuwa itake gyarashi tass.
Gaskia an basu tarbiyya kam mai kyau, babu raina na gaba musamman na kasa dasu.
“Hello ya hamad!”
“The next time kika kara cemin hello saina mareki, baki iya gaisuwa bane”
“Sorry ina wuni how was your day”
“Alhamdulillah ya amsa ta” ta turo baki tare na bin hanyar stairs ya dakatar da ita.
“Kinje ta koya maki?” Ya jefa mata tambaya daman yanason yaji ko yaushe sabeehan ta dawo.
Damn gabanta ya bada, tsakani da allah dazun nan ciwon mara ya riketa sosai tunda ta kwanta take barci bata tashi ba sai yanxu shaf ta mance da batun driver daya kamata ta fada ma anne.
Ganin yanda tayi tsuru tsuru yasan bata da gaskia, “are you dumb?”
“Innalillahi wallahil azeem yaya ciwon mara nake dazu sai yanxu na iya tashi”
“Is that the question that i asked you?”
Ganin ta sunkuyar dakai yasa shi zaro ido don sai yanxu ya fuskanci inda ta dosa, “what!!!!!! Bakida hankali???? “
“Yaya wallahi mantawa nayi”
Ko sauraron baiba don kamar ya kwada mata mari haka ykeji ya fuce daga gidan a fusace kamar zai tashi, yayi hanzarin shiga motarshi ya juya akalar motar.
Gudu yake sosai gabanshi na faduwa, yanajin kamar yayima laila dan banzan duka, ya za’aui ta manta and ya bata strict instructions akan ta fadama anne asa cikin drivers available one yaje ya daukota, gaba daya saiya fara jin wani irin rashin dadi da tausayi sabeehar yanxu haka shes stranded batasan ya zatayi ba innalillahi wa inna ilaihi rajiun.
Yana isowa school din ya wuce direct wajen department dinsu hankali a tashe, duban duniya yayi mata bai ganta ba, gashi duk securities daya tambaya sai suce basu ganta ba don ana yi shifting na rana sun tafi.
Haka nan ya zagaye school dinnan gaba daya da securities ana nemanta, har akayi sallar isha’i, cikin ikon allah wani tunani yazo masa ya nufi masallacin mata, bai shiga ba yasa daya daga cikin securities mata suka shiga ko za a ganta.
Tana shiga saigata kuw sun fito tare, tana daga kwance chan sakon masallaci ta jigata sosai ga gajiya ga yunwa, sallah kawai takeyi ta koma kwance.
Tana ganin hamad ta sunkuyar da kanta feeling so sad, wallahi yarinyar nan ba karamin kashe mashi jiki take ba haka kawai yake jin tausayinta bayason ganin ta cikin kunci ko kdan, yana hango tsananin damuwa da rashin farin ciki cikin idanunta, kamar someone that is lonely and longing for something.
“Dauko littafanki”
Komawa tayi jiki a mace ta dauko ta fito suka wuce taba biye dashi a baya har suka iso mota ya bude mata seat din baya ta shiga ta zauna ya rufe
Kunna motar yayi ya saka ac kadan sannan yayi reversing ya futa daga school din.
Shi shuru ita shuru aka rasa wanda zaiyi magana.
Shi wani irin rashin dadi yakeji, how can he be so careless, dayayi tunanin kiranta yayi confirming kota dawo da duk haka bata kasance ba.
“Kayi hakuri ya hamad, ka dawo saboda ni, wallahi ba laifina bane, bansan kazo da wuri ba dazun da bazan bata maka lokaci ba,”ta fada cikin sanyi, zuciyar sa kam ta karaya dajin furucinta sannan ga abunda ya biyo baya da bai fuskanta ba.
“Why are you sorry? Daman ba extra lectures kika tsaya yi ba?”
Nanata abun tayi a ranta batason cewa komai yanxu data fuskanci kamar akwai dan misunderstanding.
Ganin taqi cewa komai yasashi cewa
“Now tell me meysa kika bata min lokacin”
“Daman class rep dinmu ne yace min lecturer dinmu na nemana shine naje, bayan naje kuma yace min ba nemana yake ba saidai ko wani lecturer ne bashi ba,“
“And sai kuma akayi yaya? Ya nemi karin bayani.
“Shine na sauko kasan don banga rep dinmu ba kamar ya tafi, anan ne naji wajen wani security cewa kazo kun jirani harkun tafi, kayi hkuri hakan bazata kara faruwa ba”
Shru yayi bayan ya gama sauraronta tass, a cikin maganganun nata ya fuskanci abubuwa biyu, na daya babu wani extra class datace ma laila da maya zasuyi, secondly kuma batasan cewa shima kanshi da wannan wrong info din yabi ba.
“Bakiyi laifi ba, but next time ki dunga kirana idan abu ya faru dake, kamar yanxu this is very wrong for a lady ki zauna, and im sorry bansan cewa driver bai biyo sahunki ba yazo daukanki i should have called you naji ko an maidoki”
“Insha allah”
Suna karasowa gida yayi parking ta wuce bayan sunyi sallama sannan ya wuce part dinsu.
Yana parking ya wuce ciki dirwct zuwa dakin laila yana shiga yayi knocking tana zaune tayi zuru avun tausayi don tasan yau zai sauke mata, kuma harga allah bata kyauta how can she forget this.
Yana shugow ata moqe tsaye kamar zatayi kuka “yaya don girman allah kayi hkuri wallahil azeem banqi fada ba da gangan”
Tass ya kwashe ta da mari, “meysa kikamin karyan extra class da kikace zasuyi?”
“Answer me” ya daka mata tsawa ganin tayi shuru, ta fara daburdabur, “wallahi ban maka karya ba, meysa zan maka karya yaya, tare mukayi statistics class da ita kuma a gabana lecturer yace zaiyi extra class”
“Ita da bakinki tace maki zata tsaya yi?”
“Ah ah,”
“Then how did you conclude zatayi?”
“To ay naji maya tace zatayi extra class ne sainayi tunanin class din zatayi”
Saida ta fadi hakan ya gane inda gaba daya akayi misleading dinsu, wannan kafurar yarinyar futsararriyar ce, kuma saiya koya mata hankali.
“The next time kika kara bani wrong information saina tattakaki”
Hamad nada sauqin kai sosai amma in aka taboshi bashida sauqi.
Yana kaiwa nan ya fuce ya barta da kama kunci, anty fadila data fito daga part dinsu ita da oga don su ne a sama da maya kasan is for hamad tana ganin yanda ya futa tasan sunyi rikici kenan da qanwar tasa.
Bedroom din laila ta shiga ta taddata tana kuka shabe shabe.
“Menene kuma me kika masa? Nasan kece mara gaskia”
Cikin shesheka tace “mami wallahi ba laifina bane, kinga maya ce tace wai sabeeha zatayi extra class shine nayi tunanin class din zatayi ashe bashi zatayi ba shine shine muka tafi muka barta a school, toh dazun daya dawo damu yace na fada ma anne asa driver yakaita ni kuma bayan nasha maganin ciwon mara yasa ni barci na manta gabadaya shine yazo yanxu..”
Tun kafin takai aya fadila tace “innalillahi wa inna ilaihi rajiun karkice kin yarinyar nan kuka vari a makaranta tun da yamma har zuwa yanxu, amma bakida hanklai, are you mad?what sorr of nonsense is this? Eh”
Haka ta dunga balbaleta itama hankalinta ya tashi, abun babu dadi.
Sabeeha na shiga part dinsu ta tadda dakin kacha kacha, daman ita ke gyara wa duk sanda ta dawo daga school to yau ko zanin gado hadiza bata daga ba.
Wata iriyar yunwa takeji wannan yasa ta fuce zuwa kitchen ko zata samu wani abun da zata kaima cikinta.
Tana shugowa taci karo dasu rabi da hadiza a kitchen din anata faman gyare gyaren kwanuka na dinner da akayi.
Gaishesu sabeeha tayi sai a lokacin hadiza ta tuna da ita, batace mata komai ba sai binta take da ido tana girgiza kai.
Ganin irin kallon da hadiza ke mata na tuhuma yasa taji yunwar ma ta tafi gaba daya ta juya zata cire kayan jikinta dan tazo ayi aikin da ita daidai nan sukayi karo da maya data sauko kamar zata tashi sama, a kufule saboda yanda hamad yazo saura kiris ya mareta akan wannan yar wanke wanken.
Wani irin turata baya maya tayi kamar zata fadi ta daidaita tsayuwarta, “wallahil azeem da ya hamad ya mareni saboda ke wulaqantacciya yau da sainaga jini a bakinki, haka kawai saboda kin tafi yawanki na iskanci sai yazo ya balbaleni? Banza barauniya, asarraru, yar wanke wanke, gaba dayanku wahalace ta maku yawa tsabar Samun wajen har kin isa kisa yazo kamar zai dukeni? Ke a wa? Who’s your father? Ke yar uban wacece? Wataqila ma wajenshi kika gado sata”
Rabi dataga abun yayi yawa ne yasa tace “haba maya, me ta maki? Ya zaki mata kazafin sata?”
Hadiza na daga tsaye tana wanke wankenta ko tak bata ce ba ranta in yayi dubu yayi mugun baci sosai, saida taji anyi batun sata ne yasa ta juyo ta kalli sabeeha, maya dataga haka tace, “ki daina yi mata wani kallo, inta sato ke zata kawowa ay ba wani ba mteww rubbish”
Tana fadin haka ta juya tabar wajen hadiza ta fizgi hannun sabeeha zuwa backyard, ta kama hannunta sosai kamar zata ballata tace “dan abu kaza kaza…..”ta kundumo mata ashariya tace “koda na tura ki chan wata kasa daman sata kika koyo??? Eh????”
Tana shekar kuka tace “wallahi mama ban taba yi ba, wallahi da gaske nake”
“Zata maki karya ne???? Wallahi bazaki Jawo min magana ba, gwraa na tattaraki gaba daya ki koma chan wajen dangin ubanki lafia”
Tana kaiwa nan ta bar wajen kamar zata tashi sama.
Tana barin wajen sabeeha ta duka anan dakalin wajen ta saka kanta tsakanin cinyoyinta sai hawaye, kuka take sosai bakajin sautin ma sosai sai kadan kadan.
Jin alamun an dafata ne yasa tayi saurin dagowa ta miqe tsaye, nanna ta kalleta ganin tana saurin goge hawayen dake fuskarta kar a gani.
Saukowanta kenan kasa, daman tana zama ne a balcony dinta dake sama saiya kasance yana daga wajen backyard din, kaf conversation dinsu taji, wannan yasa ta sauko.
“Ina wuni Hajiya akwai abunda kike buqata”
Kallon fuskanta nanna tayi hawayen sun kasa tsayawa, ba karamin tausayinta taji ba ga muryanta ya soma dishewa, irin wannan ba tuhumar mutun akeba zama ake dashi a tambayesa akan komai bawai a yanke mar hukunci ba,
Hannu nanna tasa ta share mata hawayen a maimakon ta daina sai kawai ta fashe da hawayen sosai, nanna batasan lokacin data rungumeta ba ta soma padding bayanta, “shiii, ya isa haka”
Tana fadin haka ta zarota daga jikinta sannan tace “share hawayen”
Ta gogesu tass sannan tace “now tell me
Meya faru?meysa akace kinyi sata?
Kujerun dake wajen nanna taja masu suka zauna tana fuskantar sabeeha.
“Wallahi hajiya banyi ba, sharri ne,”
“Zan yarda dake idan kika fada min meya faru”
Ajiyar zuciya sabeeha ta sauke tana jin wani irin sanyi aranta tace”Daman dazu ne a school muna zaune ana lectures sai kawai maya tace anyi mata sata, tayi reporting to lecturer din saiyace duk wanda ya dauka ya futo dashi ko yasa a shigarda report, duk sai naga suna kallona bansan meya faruba wallahi, sai wata daga cikin students tace wai a duba jakana,im the suspect,nace masu ni banida jaka ma don littafaina ma a hannu nake rikesu,sai lecturer yace na fito zuwa stage zaiyi questioning dina, wallahi hajiya ina tashi bansan ta inda agogo yafito ba sai kawai suka fara ihu wai gashi nan nice na dauka, shine aka kira securities, sukazo za akaini disciplinary, sai wata sabuwar student ta dakatar dasu ta fidda same watch din tace ay wanda ya fito a jikina ita ta bani na aje mata ga nasu nan a wajenta lokacin data shugo class ta tsinta, toh kinji yanda akayi”
“Toh ita din da gaske ta baki ki ake mata?”
“Wallahi ah ah, banka santa ba wallahi ranar na fara ganinta a class din”
“She saved you?
Da mamaki sabeeha ke kallonta “yes she saved you, duk yanda akayi na hannunta shine nata na asali wanchan dayan kuma its possible ko wani ne yaso yayi maki sharri, you should be thankful to her”
Sabeeha tayi mamakin maganar nanna sosai don sai yanxu ta fuskanci hakan, “sunanki fatima ko?”
Ta girgiza mata kai alamun eh, “na yarda bake kika dauka ba kinji, sannan next time ki dunga lura da mutanen dake kusa dake, wanda ke kusa dakai shike da damar cutar dakai”
“Tohm hajiya nagode sosai”
“Karki sake yin kuka kinji ko? Tunda bakiyi ba me zaisa kiyi kuka, now give me a big smile”
Take kuwa ta sauke mata murmuhshin ta mai kyan gaske, nanna ta dunga kallon idanunta tana tunanin ina ta taba ganin ta ko me kama da ita.
Kallonta da nanna keyi yasa itama ta kura mata idanu tana tunanin ina ta taba ganin ta, sai kawai tayi zumbur ta miqe tsaye “laa hajiya kece wallhi kece, kece wadda kika taba bani kudi da yawa dana baki jakarki da kika yadda a masallaci”
Tunani nanna ta farayi yaushe event haka ya faru, “hajiya wallahi kece, wajen masallacin gidan man salbas dake kan Hanyar wajen gari? Shekara biyu da suka wuce? Kika mance purse dinki a masallaci harna biyoki da jakar lokacin zaki wuce”
Kama baki nanna tayi set of hakoranta suka fito rass tace “allahu akbar kece wannan yarinyar? Yar amana? Kece mai robar kwai ko?”
“Eh nice hajiya ni ce wallahi”
“Allah sarki, wani ikon allah kenan?”
Dariya sabeeha tayi ashe har hannunta ta kama tsabar excitement, don har yau batajin zata taba manta nanna, saboda matar lokaci guda ta shiga ranta,
“Wallahi Har kika yadda wani dan hotonki ina dashi ma na ajiye shi cikin kayana kafin na tafi saudi”
“Saudi? Meya kaiki saudi?”
Shuru sabeeha tayi ta dan dakata batason tuna abunda ya faru a baya kwata kwata,
“Aikatau naje yi achan”
For few seconds babu wanda ya sake magana, yanayin nanna ya sauya gaba daya, “allah sarki yanxu na kara yarda bazaki taba yima kowa sata ba saboda kinada amana, dare yayi yanxu jeki kwanta”
“Nagode sosai hajiya saida safe”
Sukayi sallama nanna ta bita da kallo.
Hilton….
Misalin karfe tara da rabi daidaiya shigo, dakin bayan sunyi sallama da salim daya saukeshi, workers din wajen suka biyoshi da shopping dayayi ma kanshi na abubuwan da zai buqata na zamn da zaiyi.
Fuskanshi na kalla, ya shanza hair cut kuma ya amshe sa sosai don yayi kyauba kadan ba, ga gashin bakinsa daketa fama kyalli yasha gyara.
Agogon hannunshi ya zame a je gefe sannan ya shiga ya watsa ruwa mai zafin gaske sannan yayi ordern brunch na dare aka kawo mashi yaci kadan saboda tashin zuciya dayakeji sama sama.
Nan yasa akazo aka kwashi abunci don bai wani ci na kirki ba.
Yana zaune laptop dinshi nakan cinyanshi yana aiki da yan dube dube call ya shugo mashi, kallon screen dinshi nayi to my surprise kawai naga wani hoton sabiha da fuskatan yayi zooming sosai, tayi murmushi, skin dinta kamar madara ga dan v lips dinta yayi wani irin jaa gashi idanunta sun fito zara zara, ya dade yana kallon wayar bawai mai kiran yake kallo ba sai fuskarta daya kasa dalilin saka hotonta da yayi akan screen dinshi, ya dade sosai har call din ya katse kafin wani ya shugo ya dauka yasa speaker.
“Hello sir!!”
“Yes saalem?”
“How are you feeling now sir? Ko nazo muje asibiti?”
“No its just minor headache, will feel much better by tomorrow”
“Okay sir please let me know idan kana buqatar wani abun at anytime”
“Thank saalem” taj ya amsa shi don haka yake kiranshi.
Yana kashe wayar ya shiga messages din da merk ya tura mashi, yana dubawa, reports ne ya turura mashi na avubuwan da suka faru tsakanin jiya da yau.
Dayaga labaran dake circulating akan hidaya sai yaji zuciyar na karaya, wallahi wholeheartedly ya dauketa a matsayin daya bata kafin tayi watsi dashi tayi disappointing dinshi, kuma yana tausayin barad da jamid, albarkacinsu ne kawai zaisa bazai saka hannunshi ba cikin almarin don idan yayi haka she will be behind bars forever, yanxu ana trail ne da da ita kuma taqi bada hadin kai.
On the other hand baiyi mamakin ganin live press release din fadwa ba, he never trusted her and he will never, yasan this will be the out omen yanda sukayi ma khaal suka cireshi daga family saboda laifinshi haka tayi ma hidaya ta nuna kwata kwata kamar ba yar uwarta ba,ta nunawa duniya basusan haka hidaya take ba ta juya mata ba, wannan shine tsantsar cin amana, kuma company will not be responsible for hidayas wrong doings.
Kashe laptop din yayi jin gaba daya wani zazzabi ya saukar mashi gaba daya.
5am..da kyar ya iya bude idanunshi, rabin daren nan ko barcin kirki baiba kwata kwata, he feels so weak, sai faman bayan gida yake shiga, yayi stooling akalla sau goma a daren, dakyar ya iya runtsawa bayan sallar asuba yayi barcin wahala.
Around 10am jikin dak sai faman zafi yake dole ya kira salem akan yazo ya kaishi asibiti.
10:30 saleem yazo suka wuce asibiti, sai daurewa yakeyi don inka ganshi bazakace bashida lafiya ba karfin hali.
Tuna isowa deda hospital saleem yayi parking sannan suka shiga shi ya zauna a reception salim kuma ya bude mashi file yayi duk wani payment da zaiyi, yana gama wa ya buqaci ganin one of the best doctor immediately,wata nurse ta mashi jagowara zuwa office din.
Asibitin irin asibitocin kasar wajene, standard dinshi da komai.
Lift suka shiga zuwa 3rd floor inda office din yake, ya shiga yaga doctor, sannan yasa a mashi test sannan ya mashi allurai don ya samu karfin jikinshi for now.
Kuma yaji dan dama dama sannan ya sauko kasa akayi test ya zauna don jiran result.
Vip Consultation room 3
Cikin dakin doctor ne zaune yana duban screen dinshi, ga patient dake zaune tana fuskantarshi.
Cire glasses dinshi yayi wannan yasa tace “dr barau akwai wani matsala ne?”
Sauke ajiyar zuciya yayi ya kalleta baima san ta yanda zai fara mata bayani ba, he has been her specialty for over the years kuma shike traking conditions dinta koda yaushe, yayi mamaki how he missed on this important issue.
“Karka cemin hawan jini ne fa? Don ga magunguna na nan na chanye su”
“Hajiya akwai matsala..”
“Wace matsala kenan?”
“You’re having a brain turmo hajiya ”
Dan murmushinsu na manya anne tayi tace “thats an expensive joke doctor barau, har lokaci na yayi kenan?”
Shuru ya danyi kafin yace “hajiya we’ve been turning blind eye on this, it has reach to a point that zai iya…”
“Zai iya zamowa ajalina?”
“Yes hajiya, we need to operate on you as soon as possible”
“Kanada assurance din zanyi surviving ne?”
“20%”
Tanajin haka kawai ta miqe, “hajiya listen to me,”
“Babu abunda zan tsaya naji fa barau, and ina baka umarin karka shaida ma kowa wannan, i want to keep it from everyone”
“Hajiya your family needs to know cause you will need them the most now”
“No barau, bazaka fadama kowa ba, i want to keep it confidential.”
Girgiza kai kawai yayi yace “hajiya please”
Batama tsaya sauraronsa ba ta fuce daga office din kirjinta na bugawa sosai, kafarta ya rike kyam sosai kamar ana rarraba kashushuwanta.
Hanyar lift ta nufa masu maintenance na daga tsaye suna aiki saboda lift din ta tsaya chak, dole mutane aka koma wajen private escalator, saida ta tsaya duk mutanen wajen suka hau tukunna kafin ta hau bata ganin gabanta haka ta hau escalator dinnan.
Zuciyanta ya karaya,it feels so heavy,kamar rock, ga wani jiri jiri da takeji, idan manyance yazo yana zuwa da kalubale iri iri wannan yasa ta fidda hope kawai idan ajalinta ne wannan babu wanda ya isa ya hana.
Baifi few steps ba ya rage ta sauko kasa kawai ta kasa daga kafarta taji ta wani sandare ta kasa daukanta.
Taj dake zaune reception tun daga sama ya hangota, kuma mistakenly ya dago idanunshi ya hangita saiya kasa daukewa kamar wanda ke karantar ta, kamar wanda keyi wani calculation ko ya karanci halun da take ciki yayi hanzari miqewa a guje kamar zai tashi sama aka bishi da kallo daidai inda ya kamata ta sauka kawai kafarta yayi trumbling jiri ya kwasheta tayo gaba cikin ikon allah ya taro saidai wani hanzari ba gudu ba dukda ya tarota hakan baisa mayafinta ya shige cikin lift dinba ya nemi shaqe mata wuya, fadin irin tashin hankalin da yake ciki bata lokaci ne,tuni security suka karaso aka kashe escalator din, kamar zai hauka haka ya soma warware wuyanta daya shaqe sosai don kanar zatayi passing out yana gama cirewa kawai ya kalli fuskanta, wani irin tsoro shock ya dabaibayeshi, baima san sanda ya furtaa..
“Ammi!!!!!!!!” Ba…..
Sama sama anne ke ganin mutanen dake wajen kafin ta sume akayi gaggawar wucewa da uta dakin gaggawa aka kwantar da ita aka bata taimakon gaggawa.
Abun ya ahde masu biyu, ga situation dinta ga shock dayasa tayi passing out ga hawan jini datake dashi amma ta boya familyn gaba daya don ko sameer bai sani ba.
Da taj aka tafi da ita emergency ya kada zaune ya kasa tsaye, yama manta da tashi rashin lafiyar, wani irin fargaba da tsoro yakeji, yana tsaye doctors da nurse na shige da fice.
About 30mins later wata nurse ta ya futo daya kasa hkura saiya tareta yace “whats going on in there? Hows she? Mwke damunta?”
“Please what are you to the patient”
Daburcewa yayi ya rasa answer da zai bata “excuse me sir? Who are you to the patient?”
“I’m her son now tell me what is going on? Meke damunta?”
Yanda yake magana zaka san hankalinshi baya jikinshi.
“I’m sorry sir, she’s in shock rn, and jininta ya hau sosai probabbly saboda news din daya risketa”
“Wani news kenan? Meke damunta?”
“She has a stage 3 brain turmo”
“Nurse betty” wata ta kirata daga ciki ta wuce ta barshi a tsaye
Baya ya danyi, yanajin wani irin abu gaba daya ya kasa controlling kanshi, first of all akan idanunshi ta kusa faduwa kuma irin faduwa kamar wannan can lead to shanyewar jiki secondly, ya rasa dalilin dayasa yakejin wani irin tattare da ita.
Yana nan zaune doctors biyu suka fito doctor barau ya kalleshi ya miqa mashi hannu yace “thank you so much for saving my patients, you have really a saving grace, badan kaiba komai zai iya faruwa were really grateful”
Girgiza mashi kawai taj yayi tace “hows she? Is she going to survive this?”
Da mamaki doctor ke kallonshi yace “survive?”
“Brain tumor??”
“I guess you had from the nurses?”
“Yes im sorry, hankalina ya tashi ne i wanted to know wani condition take ciki”
“Well shes safe now, but i dont think she will be tomorrow?”
“Why???” Taj ya tambayeshi, “it’s confidential information”
Hannu suka kara gaisawa sannan doctor ya wuce shi kuma taj ya shiga dakin,
A zaune ya tadda anne ta fizge drip da aka saka mata yanxu, kokarin saukowa tayi yayi hanzarin karasowa inda take yace “ma’am please don’t”
Kallonshi anne tayi ta kasa duake idanunta akanshi sai kawai murmushi ya kubce mata ta koma ta zauna shima ya zauna a gefenta yace “how are you feeling? Did you get hurt in any way ma’am”
Hannunshi anne ta kama ta rike ganin kamar ba bahaushe ba don appearance dinshi ya nuna hakan kuma musulmi ne don yayi mata sallama yasa tace tace “whats your name?”
“Tajudeen!!!”
Saida ta nanata sunan aranta sannan tace “thank you so much tajudeen may allah bless you for me”
Jinjina kai kawai yayi sannan yace “karkisa damuwa aranki ma’am, you have your family, they will stay with you and stand by you i promise,”
“I don’t have….”
Bai bari yaji mai zatace ba don yaui tsammanin zatace mashi batada family itako so take tace mashi batada courage din fada masu.
“You have one now! I will stand with you,”
Da mamaki take kallonshi tana hango yanda jikinshi yayi sanyi, wannan shi ake kira da pure mutun, ya ceceta daga halaka a lokacin da kowa ne zai iya hakan ba, ta lura da gefen hannunshi daya kurje ma shi bai lura ba.
“Duk wadda ta haifeta tayi haihuwa mai amfani ga alumma, allah ya baka abunda kake nema duniya da lahira, ko na mutu yanxu i have achieved everything”
“No ma’am bazaki mutu ba.. i promise, sai lokacinki yayi”
“Toh ay lokacin ne yayi tajudeen, zan iya mutuwa koda yaushe”
Idanunshi sunyi jaa sosai jiniyoyin kanshi na futowa ridu ridu kamar shine yake sharing pains dinta yace “no ma’am, i promise you zaki samu lafiya, cuta ba mutuwa bace, kuma duk wata cuta nada magani, mutuwa kuma sai lokaci yayi”
Hannunshi ta rike gam sosai tace “okay okay I believe you okay???”
Tana fadin haka ta moqe tsaye ya taimaka mata, yanajin kamar sunyi sharing relations haka itama takeji game dashi, doctor ya shugo daidai lokacin ya bata magangun dayayi prescribing sannan ya roki next ganin da zaiyi its for her acceptance don ayi mata aiki.
Tadai girgiza mashi kai kawai sannan ta fita.
Taj na rike da magungunanta suka karaso wajen lift zata shiga yyi hanzarin kama hannunta ganin zata dafe, suka shiga lift din.
Duk sukayi shuru anne ita tasan tunanin da take akanshi, don irinsu ne one in a million.
Har waje suka fita saleem na zaune cikin mota yanajin kida baisan sun fito ba.
Har bakin motarta ya rakata sannan driver ya bude baya “ma’am”
“Call me anne”
Dan sunkuyar da kanshi yayi sannan ya dago ya kalleta yace “An..ne, please promise me youll be fine,?”
“I will insha allah tajudeen”
Yanason ya karba contact dinta amma bayason zaqewa wannan yasa ya juya ta dakatar dashi ya dawo da sauri ta miqa mashi wayarta tace, “samun number ka anan”
Wani irin farin ciki ne ya bayyana akan fuskanshi ya rubuta yayi dialing number ya shigo wayarshi sannan ya mata sallama anne na yaba halayyanshi, very nice and gentle man.
Yana nan tsaye sukabar wajen ya koma mota ya zauna saleem ya karbo mashi magungunan da aka bashi da result dinshi, its just food poisoning, cimar da yake bata amshi cikinsa ba tukunna.
Jiki a mace anne ta koma gida tana tuna tajudeen, yanayin yanda yake very soft kanar hamad favorite jikanta sai takejinshi kamar jikanta shima.
Gaskia duk wadda ta haifesa ta iya haihuwar alkahiri, well mannered and respected young man, baisanta ba bata sanshi ba amma lokaci guda ya shiga ranta.
The next morning..
Su sabeeha suka koma school, ita da maya saidai harara, laila kuwa wani irin kunyanta takeji sai take ganin kamar sun hada bakine da maya, sabeeha kuwa batada riko, bata kawo komai aranta ba kwata kwata.
Nanna ta bata wani irin confidence, datakejin she can stand for her self a ko wanne lokaci.
Suna shiga first class awa daya da rabi suka fito suka shiga next one.
Ana gamawa ta tattara littafanta as usual saida kowa ya futa ta tashi.
“Hiii” taji daga bayanta.
Dakatawa tayi ta juyo karaf idanunta ya sauka kan wanda ta taimaketa jiya.
Excitedly sabeeha ta karaso inda take tace “hey…ya kike? Inata nemanki”
Dariya haya tayi tace “toh gani”
“Thank you so much for yesterday”
“Don’t thank me okay nasan bake kika dauka ba ay, nasan wacece ta aje maki ba tare da saninki ba”
Da mamaki sabeeha ke kallonta, hannu haya ta miqa mata tace “Haya”
Sabeeha itama ta miqa mata hannu tace “sabeeha”
“Nice,can we be friends?”
“Yes sure we can”
Haya kyakyawace sosai masha Allah, kuma farace saidai siririyace don batada qiba.
Gata yar gaye don dressing dinta kadai abun kallo ne masha allah, decently.
Aranar dai kawance ya kullu kamar an dade da sanin juna,haya ta jasu cafe ta saya masu abubuwa sosai sabeeha ta rasa bakin godiya, sukaci suka sha suka koma class, lokacin tashi nayi Haya ta wuce motarta maya ta tsaya jiran ya hamad, yana isowa su maya ma suka fito.
Tana komawa gida nanna tasa a kirata, lokacin hadiza batanan tana baya tana wankin kaya da maya ta bata.
Wato shakuwa wani abu ne da baka sanin lokacin dake shiga taakanin mutun da mutun, lokaci guda ta shiga tsakanin nanna da sabeeha, sabeehar da bata da sakewa saita sake sosai da nanna harda taya ninke kaya, ta gyara mata gadonta.
Abun yayi ma nanna dadi sosai don yarinyar tun lokacin nan ta gama shiga ranta.
Washe gari ta kama friday, its a short day, bayan first class da suka fito second one din lecturer din yayi delaying dole suka tsaya jiranshi wasu suka fito bakin auditorium suka tsayatsaya.
Sabeeha da Haya na tsaye suna hira some ither student ma na tsaye, click dinsu maya sukazo wucewa, kamar bataga sabeeha ba haka tazo ta gefen wajen other end din stairs din wajen ta watso mata books dinta akai, duk akan idanun haya kuma wasu daga ciki student sun gansu
“Oppsss sorrieee”
Kauda kai kawai sabeeha tayi maya ta miqo mata hannu alamun ta dauko mata books dinta, kamar bata ganta ba haka sabeeha tayi ta kauda ido maya ta kufulu soaai kamar zata tashi sama kuma ta kudiri niyar kunsasa mata, rai a bace ta duqa ta dauki littafan daidai lokacin haya ta gama cin bananas data dauko daga jakarta, ta wulla wajen hanyar stairs din ta kauda ido kamar batayi ba har wani counting takeyi don tason dole maya ta taka bananas din.
“One two three four..”
Tun kafin tace five ji kake timmmmm a kasa tayo baya kan duwawunta ta dunga sauka daga benenen a haka, me za ayi banda dariya, so embarrassing, maya kamar ta nitse harma masu video, kamar tayi kuka kawayenta sukazo suka taimaka mata ta mike ta bar wajen a guje tana kiran wayar saleem.
Sabeeha dake dariya kasa kasa tana dagowa taga haya na daga mata hannu suka tafa.
Haya tace “serves her right..no one dares to mess up with my friends”
Anatse sabeeha tace “thank you haya”
“Fadamim meysa take treating dinki haka? Meysa baki ramawa? Ki koya mata hankali mana”
“I çant haya”
“Meysa?”
“Saboda ni yar aiki ce a gidansu, ni ba kowan kowa bace banida gata banida kowa”
“Kinada gata sabeeha, and i promise to stand by u okay”
“Thank you haya.”
“Zanyi maganin ta ne idan naga dama bazata kara tako kafa school dinnan ba”
Da mamaki saveeha ke kallonta haya ta ja hannunta tace “bakisan koni wacece ba ko? Bana fada ne, nice first and only daughter na founder din makarantar nan, Haya baba Datti”
Baki sabeeha ta kama tsabar shock yanxu wannan yar me makarantar ce? Ba girman kai babu dagawa? Ikon allah.
“Aje wannan shock din naki ga lecturer yazo muje class”
Transcorp hiltons hotels…
Kallon wayar yake da mamaki, yanxu nan ya gama tunanin ta saiga call dinta ya shugo unexpectedly.
Jiya sun dade sosai a waya, kuma duk tsawon wayar nan encouraging dinta yakeyi yana nuna mata cewa she’s not alone,he understands her fear saboda tsufanta and he wants to help her through the journey, yanajinta kamar uwa, kuma wallahi duk a tunaninshi batada kowa.
Sannan daga baya ta tambayeshi about himself ya fada mata komai bai boye mata ba, kasar mahaifarshi da inda ya taso da abu daya ne bai fada mata ba rayuwar da yayi a baya da dalilinshi na zuwa nigeria kawai dai yace mata wasu ayyuka ne suka kawoshi nan, dake macece wadda tasan harkar business sosai and she has interests in the field tunda hannunta yayi aiki a ciki over the years, taji dadin iin yanda yakeda nashi experience din.
Abunka da wayyayu sai suka zama very close lokaci guda, ita kanta tana mamakin yanda ya shiga ranta lokaci guda.
Dagawa yayi cikin hanzari bakinsa dauke da sallama.
“Walaikum salam tajudeen, how are you my dear”
“Hamdullah, how are you feeling? Kinasha medication? Akwai avunda ke damunki?”
“I’m fine tajudeen, thank you for your concern, i will like to invite you for dinner this evening”
Murmushi yayi ya dubi agogon hannunshi, hopefully zai gama abunda yake kafin lokacin.
“Tajudeen are you there?”
“Yes anne i am…”
“Please inason kazo, I will like to treat you dinner with my family to thank you enough for helping me”
“Insha Allah zanzo..zan aje duk wani plans dina for the day”
Wani irin dadi anne keji ganin yanda yake answer ta with so much respect.
“See you then may Allah blessings be with you as always”
“Insha Allah”
Sukayi sallama ta kashe wayar shima ya aje.
Yana gama shiryawa ya fito inda saleem ke jiranshi.
Suka gaisa asual suka fara zagayen da zasuyi, sun dade sosai kafin suyi branching a company baban salim na motocin ford da yake karban dealers.
Salim ya sanar ma babannashi daman taj din ya buqaci zuwa wajen, shi baban nasa baya kasar yayi tafiya so ya bama salim go ahead don yasan mahimmancin taj din tunda yaji daga inda yake dukda baisan shi din waye ba.
Sun zagaye wajen and taj is so impressed with yanayin yanda suke tafiyar da wajen, don ya banbanta da yanda sukeyi achan company, kuma duk varieties of different collections akwai saidai karancin colors ga pending orders da mutane keyi suggesting, a take yayi waya da merk yasa suyi approving duka collection din da baban salim ya nema daga kamfani.
Lokacin da wannan abun alkairi yazoma alhaji buba yayi murna kwarai ya kara tabbatar da zuwan taj alkairi ne, abunda sai a dauka shekaru kafin ayi approving sai gashi cikin awanni kadan ya samu kai abun yayi mashi dadi sosai.
Salim fa zuru yayi da idanu ganin yanda taj din yake zayyano wani turanci yana waya a take yayi signing wani deal dasu yayi approving a bude wani companying anan.
Wani abun mamaki daya kara gigita salim lokcin da suke zagayen motocin ya nuna interest akan wata ford sprt car, take taj yace mashi “are you into drift?”
Yace mashi yes, daga yes dinnan kawai yace “take it”
Salim kamar yayi tsalle don ko a mafarki bai taba tsammani ba, take wata natsuwa ta shigeshi yayi murna ba kadan ba kamar zai tsugunnama taj.
Shi taj dinma mamaki ya dungayi yanda yake mashi godiya don motar ba komai bace compare to latest collections dinsu na yanxu.
A haka sukabar wajen aka biyo taj din da wata dankararriyar mota daga cikin motocin.
Sai wajen 5 suka dawo gida, yayi sallah yayi wanka, baibi takan abunci wajen ba kwata kwata don yanxu ba komai yake ci ba.
Yana zaune mesaage din mutallib ya shugo mashi kamar haka.
“This is khaal, idan kayi receiving mesaage dinnan inason ka kira ni”
Take yayi dialing back tare da wani dogon tunani ba.
Call din na shiga akayi saurin dauka, taj yayi sallama.
Suka gaisa sannan suka dan tattauna, sun dade sosai suna magana kafin suyi sallama.
Har zai katse wayar khaal yaui saurin dakatar dashi.
“Tajudeen!!!” Khaal ya kirashi.
“Ka nemi mahaifiyar???”
Dam yaji gabanshi ya bada yayi saurin runtse idanunshi.
“This is the right time taj, shakarun da suka wuce a baya bazaka iya dawo dasu ba,its high time ka nemi mahaifiyarka, what you should have done years ago”
Jiki a mace ya dafe kanshi dayaji ya sara mashi jikinshi ya mutu yace “I don’t deserve to be with her, khaal,ban chanchanci bayyana a gabanta ba khaal,nayi babban kuskuren da bazai gogu ba khaal”
“Allah yana mana laifi munyafe masa, she will Accept you happily, HAJAR is one of a kind, and halinta ka biyo, baka da kamarta ayanxu, so face the consequences ka nemi yafiyarta, ka nemi albarkacinta saboda rayuwarka tayi albarka, saboda rayiwar ta inganta”
“Kodan hakkinta banajin zan taba samun kwanciyar hankali a rayuwata khaal, banida bakin kiranta a matsayin mahaifiyata, na cireta daga babin rayuwa ta nayi dana sani khaal, i was foolish and stupid and manipulated into thinking bata buqata na a rayuwarta”
“Ba laifinka bane taj, ba laifinka bane..KADDARARKA kenan,bazamu iya maida hannu agogo baya ba, so try and fix your past, try and clean your relationship with your mother, ka gyara alaqarka da mahaifiyarka, nasan guilt ke dakatar dakai, amma inason ka sani lokaci na kurewa karkazo kayi regretting”
“Insha Allah khaal” da haka sukayi sallama ya kashe wayar
Ya zauna yana tunanin rayuwarshi ta baya, wallahi babu ranar da zata gifta a rayuwarshi da kalmar mahaifiyarshi bazatayi crossing kind dinshi ba, wallahi an cuceshi matuqa, ace kana raye kuma mahaifiyarka na raye wadda ta tsugunna ta haifeka amma anyi distancing dinku, kuma bai gani laifin kowa sai laifin kanshi, bai ganin na iyayenshi da suka rabu a daidai lolacin dayafi kowa buqatarsu har hakan yayi sanadiyar gurbata rayuwarshi ya shiga wani traumatic stage at a very young age.
Sai yaji wani irin dumm a kanshi, hoton ta daya karba wajen khaal har yanxu yana jikinshi akoda yaushe duk inda yake.
Maganganunsu da khaal ya kara bashi wani irin courage.
Har wajen magrib yana zaune jiki a
Mace kafin ya tashi ya shiga bathroom yayi wanka ya fito da alwala yayi sallah, cikinshi ya soma qugi amma yaqi cin komai.
Yana zaune yana addu’oi akayi sallahr isha’i ya tashi yayi sallah yana idarwa a gaggauce ya shirya cikin irin farar jallabiyan nan ya saka kundura akanshi ya nadota saiya dawo sak balarabenshi dashi Masha allah.
Kai masha allah masha allah…tsarki ya tabbata ga wanda yayi wannan halitta, sai buga kamshi yake yalwatacce, ya dora agogo a hanunshi da zobunan azurfa a yatsunsa.
Yana gamawa ya fito daga dakin cikin kamewa ya sauka kasan, yana sauka kasan ya karba keys din sabuwar motar daga wajen valley keepers sannan ya shiga ciki, wajen dashboard ya bude kamar yanda ya buqaci permit da documentation duk an hada mashi a ciki karkashin sunan alhaji buba incase.
Kunna motar yayi sannan ya kunna wayarshi tare da dialing number anne, ana dagawa ya buqaci address ta fado mashi sannan yasa a map ya kama hanya.
Lokacin wajen karfe takwas da yan mintuna kadan, anatse yake driving yanabin map dukda baisan hanyar ba cikin ikon allah cikin abunda baifi 20 mins ba ya iso gwarinpa.
Daga nanma ya dunga bin map din har zuwa santuraki’s creasent avenue, yana shugowa lighing din wajen ya bade ko’ina ya soma slowing motar ganin securities at ko wanne end, bakinsa ya soma matsawa a hankali don banjin abunda yake fada harya karasowa gate din tafkeken mansion din.
Yayi bayanin inda zaije da sunansa kai tsaye babu wani tambaya aka barshi ya shiga, saiyama rasa ina zaibi wanne part zaije, daidai babban dake tsakiya ya tsaya wajen parking lots yayi parking.
Hamad dayayi parking shima yana kokarin kwasar paper bags din dinkunan dayayi tun daga shugowar motar yabita da ido.
This is the first time yaga irin motar a cikin compound din.
Ya dauka wajen minti biyu bayan ya kashe motar bakinsa na motsawa kafin ya sauke ajiyar zuciya ya fito daga motar yabi ko’ina da kallo har idanunshi ya sauka kan hamad dake shirin shiga main house.
Dan dakatawa yayi ya karaso inda taj din yake ya miqa mashi hannu da mamaki suna kallon juna.
“Asaalamu alaikum”
“Wa alaikum salam wa rohmatullah”ta ya amsa shi fuskansa ba yabo ba fallasa sai yalqi take Masha allah, ga wani cikar haiba da annuri dake kwance kan fuskar.
Hamad kwata kwata bai kawo shine baqon anne ba wanda tabi ta ishesa da zancensa da take cewa kusan halinsu daya very soft and calm guy.
“Hamad Abdullah”
“Tajudeen abdullah taheel”
Suida yaji sunansa tukunna hamad ya gane shine expected guest din kenan, shine wanda ya tafi karba kaya da anne tasa ayi masa daga babban kamfanin the boss ateliar suna dinkin manyan kaya da yadidika hadaddu.
Murmushi hamad ya mashi sannan ya mashi iso suka nufi hanyar main entrance.
Har cikin babban parlor hamad ya jagoranceshi ya zauna, babu kowa cikin parlor din sai kamshi yake ga sanyi ac.
Gaban taj daketa faduwa tun amota sai yayi doubling kamar ana lugude, and its something different da bai taba experiencing ba kwata kwata.
Har yana dafe kirjin nashi don kamar zai fito, yanajin kusancin wani abu daidai da bugun zuciyarshi.
Saukowa hamad yayi ya zauna tare dashi suka sake gaisawa sannan ya shaida mashi ya sanar ma da anne zata sakko yanxu.
Jinjina kai kawai taj yayi shi kadai yasan me yakeji.
Cikin yan sekanni kadan sai ga anne ta sakko cikin shiga ta alfarma, idanunta sanye da farin glass ga fara’a kwance a fuskanta.
Daidai nan anty fadila ta shugo tare da laila don anne tace yau duk anan za ayi dinner, (mijin anty fadila baya nan yayi tafiya)
Yana ganin saukowar anne yayi saurin miqewa murmushi kan fuskarshi shima ta karaso parlor ta zauna ya tako har inda take ya kama hannunta kamar yanda yakema ammu da khaal ya sumbacu hannunta cikin larabci ya gaisheta ta amsa.
Su anty fadila sai suka zama yan kallo, wannan ne baqon anne din, tsantagwaran balarabe? Shin ina ta san shi kuma? Meya hadashi da ita tambayoyin da suka dunga yima ka su kenan.
Su laila sai aka fara sunne kai anga kyakyawa, ta kasa daina kallonshi don baka iya resisting, allah allah take maya tazo ta ganshi, ita ta rikice qila maya sai sumewa.
“Zauna tajudeen”
Ta mashi nuni da kujera ya zauna.
Daidai nan uncle sameer ya shugo shima, shida anty mubina da yan yayanta, anty laila ko itada batasan shiga cikin dangin miji cewa tayi zazzabi takeji bata iya futowa, sai su abal ne suka biyo bayan daddyn nasu.
Gana daya yaran wajen cikin harshen turanci suka gaishesa ya amsa masu da yar fara ar shi.
Anty fadila ma ya gaisheta, uncle sameer ko musabaha sukayi.
“Masha allah tajudeen welcome to my home, and waennan family na ne”
Da mamaki sosai yake kallonsu su duka don wallahi bai taba tsammanin shes blessed with such a wonderful family ba.
“This is my first sameer, and this is my second fadila, thats her kids i have one more, she’s in london”
“Masha Allah” ya furta ahankali yana murmushi.
Su uncle sameer sai jinjina shi suke aransu don abun mamaki ne ace anne ta kawo stranger to their home definately yayi mata wani abunda bazata manta ba.
“Laila ja yaran nan kuje dining”
Laila ta jasu su duka ya rage sai iyayen nasu kadai.
“Sameer wannan shine tajudeen, shine wanda ya taimakeni badan jiba da tuni bana nan zaune a kusa daku”
Da mamaki duka suka juyo suka kallon anne meysa zatayi wannan furucin,….duk suka zuba mata idanu gaba dayansu suna jiran amsa.
“Muje muyi dinner ko”
Tasan son karin bayani suke amma ta katse su suka miqe tayi gaba suka bita a baya.
Aka zazzauna, what a happy family daya shiga cikinsu sai yaji kamar he’s among.
Uncle sameer ya dunga janshi da hira don yana kusa dashi.
Anne babu abunda take sai murmushin jin dadi kawai.
Ana gama cin dinner suka dawo sitting room, anne taso fada masu komai amma saitaji this is not the perfect timing gashi nanna bata nan, taj daya lura da hakan shima baiyi kokarin cewa komai ba.
“Anne tace daga saudi kake? Meysa kawo ka nigeria? I must say business right?”
“Yea business..and some personal stuff”
“Masha allah what are you into?” Sameer ya sake tambayarshi.
“Cars..i am the founder of…”
“Assalamu alaikum…”
Daga ciki da sukajiyo sallamar suka amsa da “wa alaikum salam..nanna”
Driver ya biyota da akwatin nata, duk suka juyo suka kalleta don bata idasa karasowa ba hamad yayi saurin karban box din anty fadila tace “ah ah baki tafi ba?”
“Uhm fadila bazan iya ba da delays din flight dinku na nan nigeria, ive been stranded for about 3 hours, sun gama zaunar damu hamad yayi min booking wani flig…”
Chak ta tsaya tana karasowa sitting room din, kuma a daidai lokacin idanunta ya sauka akanshi, bugunda kirjinta keyi lokacin data shugo estate din bana wasa bane.
Daga kan wayarta zuwa files din dake hannunta duk wani abu daya kasance yana hannunta gaba daya sakinshi tayi kasa wanwas ji kake passs pass a kasa, take idanunta yayi jaa sosai ta soma yin baya baya jikinta na karkarwa jininta ya soma yin kasa sai jiri daya soma dibanta, fadila data lura da yanayinta tace “nanna!!!! Nanna!!!!” A daidai lokacin ya dago da idanunshi ya sauke cikin nata mug din tea din dake hannunshi ya sake gaba daya ya malale a kafanshi gashi da zafi sosai, shima cup din ya fashe.
Jikin nanna ya fara vibration kamar wadda zata shide tayi luuuuuuuu ji kake timmm a kasa.
“Innalillahi wa inna ialaihi raji’un suka miqe gaba dayansu sukayo kanta harma da taj da baisan ya taka mug dinnan ba ya karasa fashashi ya fasa mashi kafa, yana zuwa gab da ita ya kasa karasawa hotonta na flashing a fuskanshi yayi saurin rintse idanunshi ya bude ya sauke akan fuskanta da idanunta ke rufe, ya wani irin dafe kanshi cikin hanzari ya tura hannunshi cikin aljihunsa ya zaro hoton nata, duk kachaniyar da suka a gabamta duk sun zagayeta bayajin kwata kwata abunda suke fada abu kamar an
Toshe mashi kunne da basira ya kasa tabuka komai sai kallon hotonta da yake da fuskarta wani irin zazzabin ya saukar mashi mai zafi sosai ba kadan ba.
Ruwa aka yayyafa mata amma ta kasa dawowa daidai karshe ma nunfashinta daukewa yayi gaba daya.
Sameer yayi saurin cewa “anne bata nunfashi, bata nunfashi”
“Innalillahi wa inna ilaihi rajiun sameer ku kira barau ku kira ambulance karna rasa yar uwata, innalillahi wa inna ialaihi rajiun” ta dafe kanta daya soma sara mata.
Sai a lokacin taj ya dawo hayyacinsa wallahi bayaji baya ganinsu gaba dayansu, gaba daya ya koma kamar jan kosai, jijiyoyinsa suka fito rado rado.
Ya tsugunna ya dauko nanna gaba daya ya rungumeta zuciyarshi na kuna, wasu irin strong mixed feelings na shigarshi ga radadin da yakeji a zuciyarshi, ya nufi hanyar fita da ita.
Bata nunfashi inaga maganar kiran ambulance, wallahi bayajin me suke cewa kwata kwata yayi reverse da motar baibi takan kowa ba ya figi moatar, allah yaso akwai keys a jikin hamad wannan yasa suka shigiga cikin moatar sukabi bayan tashi.
Gudu yake ba karamin gudu ba kamar zai tashi sama,kiris ya rage baiyi causing accident ba har suka iso deeda.
Suna isowa ya zagaya baya kamar his life depend on her ya daukota ya shiga da ita, take nurses suka karaso da gado a da sauri aka sakata yabisu, aka dakatar dashi.
Aka kira doctors har uku don ta shiga critical condition, dasun shiga sun fito saiya miqe daidai nan su anne suka karaso, wani doctor ya sake futowa taj ya riko hannunshi kamar zai ballashi sai zufa yake gaba daya ya futa hayyacinsa yace “please save her…dan allah ku ceceta, i need her in my life”
Gaba daya kallonshi suka dunga yi, ya gama shiga tashi hankali gaba daya.
Anne da sameer da fadila suka karaso harda hamad suka zagaye doctor din anne tace “barau whats going on? Me yar uwata ke ciki? Ku rifa min asirin don allah ku ceceta”
“Hajiya calm down.. you need to make her calm down saboda idan hankalinta ya tashi its risky” barau ya karashe yana kallon sameer, anne tace “barau explain to me what is happening to my sister”
“Hajiya shock ne, which result to jininta ya sauka, yanxu nurses zasu kawo blood daga blood bank na asibiti, insha allah babu abunda zai sameta ku mata addua”
Daidai nan nurse ta karaso jiki na bari tace “sir can i have a minute with you”
Yadan matsa ta mashi magana kafin ya juyo, idan har ya bayyana masu babu blood type dinta a asibitin nan zai iya zame masu matsala don a gaskia family santuraki manyan client dinsu ne.
With the kind of look da yake basu yasa taj cewa “take my blood..”
Gaba daya juyowa sukayi suna kalonshi, with annoyance hamad yace “please stay on your limit, allow them to do thier work”
Ko kallo inda yake baiba yace “i said take my damn bloood…idan wani abu ya sameta saboda delay dinku i will Make sure that asibitin nan bai sake anfanuwa ba”
“Bubu yanda za ayi a diba blood dinka bamusan kokai waye ba”
Sameer yayi magana cikin bacin rai don shi tun daya dauki nanna ya fice da ita ranshi ya baci.
Wallahi baima san sunayi ba kwata kwata ji yake kamar ya shaqe doctor din.
Anne ta katse su tace “doctor barau what is the issue”
“Hajiya im sorry bamuda blood tupe dinta”
“Ku diba nawa”
“You’re not compatible hajiya batada wani da ko jika? Wanda blood dinshi A ne?”
“Please take my blood and save her”
Sai a lokacin barau ya kalleshi yace “qre you related to her and what’s your blood group sir?”
“I AM HER SON!!!!!”
Dammmm gaban anne ya bada, ay itama saita samu wani hawan ruwa a take.
Fadila da sameer banda kallonshi babu ahunda suke with so much shock.
“Doctor doctor the patient is having pulsing tana jijiga”
Wata nurse ta fito hankali a tashe.
Ay ko kallon inda suke taj baiba ya afka dakin doctor barau yabi bayanshi.
Yabar su uncle sameer da anty fadila da suman tsaye, uncle sameer zai bishi don a tunanin shi ko ya haukace ne anne ta dakatar dashi.
“Tabbas dan hajara ne wannan babu makawa, tajudeen dan nanna ne ita din mahaifiyarshi ce, wadda ta tsugunna ta haifeshi tayi rainon cikinsa wata tara allahu akbar” sai hawayeeee😭😭😭😭😭
✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊
MATAR TAJ (destined with you🩵🤍)
Written by
Queenmarh✍️
Book2
PAID