← Book details Matar Taj Part 2 Complete Hausa Novel. Local reading mode
CHAPTER 54 OF 66

Chapter 107

Matar Taj Part 2 Complete Hausa Novel. · about 21 min read

Akan idanunta bahijja ta futo da sabeeha kuma taga komai daga farko har karshe, bata samu damar magana ba sai yanxu.

Hadiza dake daki bayan fitar jamila haka kawai jikinta ya bata ta biyo bayan jamilar taga kota futa, don makircin jamila ya wuce tunani, don kuwa zata iya komai koda kuwa tana kan gabar mutuwa ne, bata tashi biyota ba saida har suka iso, dake tsakanin backyard din zuwa compund din akwai nisa sosai wannan yasa bata hango abunda ke faruwa ba, kamar ance ta dago karaf idanunta ya sauka kan anne dake zaune kan wheel chair.

take gabanta ya fadi ganin jamila tsaye daga gefe ta kure su da ido, tuni hankalinta ya tashi.a tunaninta ta rigada ta futa don neman yanda zata tseratar da kanta,

hankalinta bai gama tashi ba saida taji maganar da jamila tayi don da karfi take magana, ay batasan sanda ta taho a guje ba kamar zakanya, daidai lokacin kuma allah ya bama jamila nasarar hangota daga nesa tayi wani makirin murmushi ta janye mayafin datake rike dashi a hannunta ta daure a kugunta dashi, ta fara taunar chewing gum, ji kake kass kass.

“Jamilaaaaa jamilaaaaa !!!!!” Hadiza ta kwalo mata kira tana gudu, harda tuntube ta fadi kasa, jamila ko me zatayi banda dariya kamar mahaukaciyar sabon kamu, ta sauke wani makirin murmushin mugunta tana taunar chewing sautin nan na futa ji kake qas qas ta tuge daurin ta zuwa gaba, Ta dubi hadiza dake kokarin tashi zata cigaba da gudun duk don ta dakatar da ita tace 
“Da kin daina gudu kin taho ahankali, don babu abunda zai hana yau dinan na tona asirinki da kika kwashe shekaru ashirin da uku kina binnewa”

 Gaba daya sai suka maida attention dinsu ga sabuwar dramar da suke gani, taj na daga zaune a mota, waya yake mai amfani dayasa ya kasa katsewa amma idanunshi nakan abunda ke faruwa a tsakar gidan.

Duban bahijja jamila tayi sannan tace “kafin ki illatata inaso ki sani cewa yarki ta asali zaki illata saboda yar da ba taki ba, don wacchrr” tayi nuni ga maya “wachar ba yarki bace, yar hadiza ce”

Dammmmm, gaban bahijja ya fadi, bama ita kadai ba hatta daddy da fadila da nann, kai kowa ma dake tsaye a wajen.


Anne dai na daga gefe, basu kaiga karasawa ba tun maganar da jamila tayi ta farko ta dakatar da hamad ya tsaida wheel din ta dafe kanta, yau gaba daya tunda ta tashi bata iya magana da kowa ba, sunmayi tunanin ko ciwonta ne, har fadila na cewa kar ayi discharging dinsu don gaba daya yanayinta ya sauya gashi taqi fadama kowa komenene ke damunta, saima insisting datayi dole yau ayi discharging dinta haka kuwa akayi don yanxu dole a lallabata saboda yanayinta baason ta shiga wani state na damuwa.
“Wacece wannan mahaukaciyar??” Fadila tayi magana cikin bacin rai,
“Kinga da hankalina, ga uwarku nan tasan maganar da nake ay”

“Keeee!!!!! Kinsha kwaya ne? Who allowed this insolent woman in here????” sameer ya daka tsawa, jamila ko a jikinta, saima taunar chewing gums dinta data keyi hankali kwance, daidai nan hadiza ta karaso, tana yaqe kamar zautacciya, sai faman haki take, jikinta ko sai kyarma tsabar tashin hankali ''karku saurari abunda take fada, yar kwaya ce a buge take ma, makociyarmu ce achan anguwarmu, bashinta naci ban biyata ba, shine tazo na biyata, saboda ban cika mata sauran ba shine take kokarin bina da sharri don a koreni anan dan allah kusa a futar da ita''
''ai idan batasa an koreki ba yau dinnan zaku bar gidan nan keda wannan shedaniyar yar taki, mugaye wanda babu allah a ransu, a maku alkahiri ku sakawa mutun da sharri,har yarki nada guts din daukan wuka zata illata maya, idan har zata iya daukan wuka ta yanke ta to tabbas zata iya kisa''

hadiza najin an anbato maya hankalinta ya tashi, daidai lokacin idanunta ya sauka kan maya data rike hannunta daya baci da jini haka zalika rigarta, har zuwa lokacin hawaye takeyi fuskar nan yayi jaga jaga sai faman tabe fuska take tana washh,

da har ranta ya fara baci ganin wannan matar data gani a dakin hadiza daxu na kokarin bata mata shiri sai kuma yanxu da fadila ta dawo da maganar yankata da sabeeha tayi saitaji dadi, so take kawai a koresu daga gidan.
hadiza harda tuntube tsabar rudewa ta nufi inda maya ke tsaye hankalinta a tashe har tana bangaje bahijja dake gefen mayan tace ''innalillahi wa inna ialaihi rajiun, jinin menene wannan a jikinki? wa ya maki haka? ina kikaji ciwo?, jini ne wannan?, na shiga uku, da zafi?, waya maki haka? wallahi bazan bar koma waye ya maki haka ba''
gaba daya ta susuce tama manta da batun jamila gaba daya, saboda ganin mayan datayi da riga duk jini, kamar dai yanda hankalin kowa ya tashi saima nata yafi na su.
sai suka zama yan kallo, yanda ta rude ko bahijja batayi irin rudewar ba, sai faman tattaba maya take tana kokarin ganin inda taji ciwo, mayan kuma sai faman tureta take.
duk sai suka tsaya sororo suna kallon ikon allah, …Bahijja ko babu abunda take sai kallon hadiza da mayar, magnagnun da jamila tayi dazu na yawo a kwakwalwarta.

jamila na ganin haka kawai ta soma tafawa,''wato shifa sharrin jini ko, baya taba buya, sannan yau na kara tabbatar da hankali ke gani ba ido ba,koda yake bazanga laifinku ba tunda bata barku haka ba harda aikin asiri,''

chak hadiza ta tsaya tare da sakin maya, sai a lokacin hankalinta ya dawo jikinta, kwata kwata bata lura da abunda take shirin yi ba sai yanxu, ta fara kame kame.

fadila ce dai ta sake magana a karo na biyu ''wannan wani irin maganan banza ne wacece ke da har zaki shugo cikin gidan nan kina fadin magnagnun da basuda fasali? ku fitar da su daga gidan nan''… ta fada rai a bace tana instructing guards din
daman tana da zafi sosai don tafi bahijja zafi.
''kafin kisa a futar dani inason ki sani….''


hadiza na jin haka batayi wata wata ba kawai tayo kan jamila iya karfinta, duk ta burkice gaba daya, har dan kwalinta na neman faduwa kasa, kamar wadda zatayi hauka, jamila tayi wani irin kukan kura ta turata ta fadi kasa kamar kayan wanki, ta dubeta tace;

''duk fa abunda zakiyi bazaisa na fasa tona maki asiri ba, a tunanin ki wai guba kika bani daxu ko? toh bari kiji, a shirye nazo gidan nan yau dinan, ni bana rufa rufa, daman na fada maki indai har kika ci amanata saina wulaqantaki hadiza, kuma nice zan zama ta farko da zan kwance maki zani a baynar nasi, wannan annamimiyar da kuke gani idan har kukaji abunda tayi maku to wallahi bazaku kara barinta tayi yawo a doran kasa ba don…..

a daidai lokacin wani karfi ya sake zuwanma hadiza ta fara kokarin tashi kamar zautacciya ganin dai da gaske jamila tona asirin ta zatayi, inda da akwai wuqa a kusa da hadiza babu abunda zai hana ta daba mata adai dai wannan lokacin duk don kar asirinta ya tonu, ga idanun kowa a wajen, da asirinta ya tonu gwara ta kasheta inyaso itama a kasheta, don bazata taba bari asan cewa maya ce yarta ba sabeeha kuma itace yarsu, tunda har ta kawo e yanxu bazata bari komai ya wargaje ba, bazata taba bari yarta ta dandan talaucin rayuwa ba, sannan yar bahijja kuwa saidai ta kare rayuwarta a wulaqance wannan alkawari ne ta daukarma kanta.

daidai nan idanunta ya sauka kan irin manya manyan grass sweeper machine da ake gyaran grass dasu, kamar mahaukaciya haka ta dauko sandar karfen abun ta taho da gudu, ko tsoron manya manyan guards dinnan bataji ba, bataji bata gani, “jamilaaaaaaaa,…saina kasheki, saina kashekiiiiiii!!!”

kafin kace komai sai kawai suka biqe da bugun juna, basuyi aune ba sai ganin waennan guard din sukayi akansu, hankali tashe hadiza tace ''wallahi mahaukaciya ce, mahaukaciya ce karku saurari maganganunta''

Ya sameer ne ya dubi securities din ya bada umarnin a fidda jamila daga gidan, ganin haka yasa hadiza ta soma washe baki.

“ku saketa''!!!!!” Anne tayi magana wanda yasa duk kowa ya maida hankalinshi gareta.

tuni dariyar kan fuskar hadiza ta koma da furgici…“Hajiya hajiya wallahi mahaukaciya ce, cutar haukace da ita karku tsaya bata lokacin ku wajen sauraron maganganunta na banza, yama wannan zancen zai zama na hankali???” Hadiza ta fada tana ihu duk bakinta ya fafashe saboda bugun juna da suka dungayi ita da jamilar.

jamila ko me zatayi banda dariyar yan bariki, ta sake maida daurinta gaba, kafin tace
“A karamar kwakwalwarki kina tunanin zanzo da magana ta baki ne kawai? Da shedu na nake tafe…, nii jamila da kaina na chanza yar bahijja da yar hadiza, ranar 24th ga watan October shekarar dubu 2001 a ranar da aka haifesu..”

Wani irin dummm bahijja taji akanta kamar an buga mata guduma, fadin irin shock din da kowa ya shiga a daidai wannan lokacin bata lokaci ne, daddyn maya ko idanunshi bai kaiga ko'ina ba sai kan sabeeha dake tsugunne, sabeeha ko in banda kuka babu abunda take, tsabar rikicewar datayi tunda taga wannan guards din sun zagayeta, tsabar rudewar datayi batama san maganar me akeyi ba.
Maya ko da ba maida hankali tayi ba wajen magnagnun da sukeyi akai, burinta kawai so take a futar da sabeeha.

“Karyaaa ne karya ne wallHi karya ne karya ne, karku saurari wannan mahaukaciyar, yar kwaya ce, ba tun yanxu take kwaya ba har taohon mijinta ta kashe, yar kwaya ce yar tasha ce ku fitar da ita daga nan” hadiza sai kawai ta fara soshe soshe ta dora hannu aka tana neman guduwa, kamar jamila tasan me take shirin yi wannan yasa tayi saurin damqo hannunta, ta kalleta cikin ido tace
''karma ki fara soshe soshen munafurci, wallahi taki ta kare yau hadiza,''
duk yanda hadiza taso ta kwace ma jamila kasawa tayi don riko ta mata na mu mutu tare, kowa ma ya rasa.


''baiwar allah wannan wani irin magana ne?kinsan abunda kike fada kuwa?'' nanna ta fada tana dafe kirjinta, don dakyar ne idan jininta bai hau ba.
''idan baku yarda da maganganun danayi ba zaku iya tambayar hajiya'' jamila tayi nuni da anne.
gaba daya sai suka maida dubansu ga anne, da mamaki sukaga tana zubda hawaye, tuni hankali sameer ya tashi, bama shi kadai ba harda fadila.
''allah ya tsine maki jamila, allah ya tsinema ubanda ya kawoki duniya, wallahi karya takey..''

ay gaba daya hankalinsu baya ga hadizar ma gaba daya, sun maidashi ga anne data kasa hada ido da kowa, kuma ta kasa cewa komai.

Bahijja data sandare, lokaci guda nunfashinta ya nemi daukewa, ta kafama anne idanu,ANNEN ma kallonta take, tuni taji gaba daya kafafunta na neman qin daukanta tayi baya zata fadi maya ta tarota.
bahijja na cikin wannan state din na furgici ta dubi hannunta inda aka deba jininta jiya da anne tasata zuwa asibiti da gaggawa, tuni ta soma jujuya kanta, ganin abun take kamar a mafarki, ay har gwara ace mafarki takeyi wata qila inta farka zataji sauqin abunda takeji.

kasa kallon inda sabeeha ke tsugunne anne tayi, don zuciyarta ta karaya, yau akwai babban tashin hankali a cikin gidan innalillahi wa inna ilaihi rajiun.
''anne? kodai jikinta ne? mu koma asibiti'' sameer yayi magana cikin tashin hankali, ko sauraron abunda yake fada batayi ba tace
“rabi dagata ku shigo ciki''

tana fadin haka ta dubi sameer, ''ku shigo min dasu suma” tana gama fadin haka hamad ya tura wheel dinta zuwa ciki, rabi tayi gaggawar taimakawa sabeeha ta tashi tsaye, gaba daya ta galabaita, ba karamin duka bahijja ta mata ba da wannan wire, tuni hankalin maya ya tashi ganin ana kokarin komawa da sabeeha cikin gida, sai a yanxu ta fara fuskantar abunda ke faruwa, daxu dai bawai ta maida hankali bane kan magnganun da akeyi.

hadiza na tirjewa haka jamila ta kankame hannunta guards dinan suka tasa su a gaba, hadiza babu damar guduwa, tayi tsuru tsuru, bata taba tsammanin asirinta zai tonu cikin sauqi haka ba, tayi dana sanin sanin haduwarta da jamila, zagi kuwa babu irin wanda batayi ma jamila ba, gaba daya ta susuce, bata sanin me take fada ita kanta.

Bahijja dai bata san yanda akayi ta shugo parlorn ba don ta shiga wani yanayi mai tafe da furgici da tashin hankali da fargaba, bin kowa kawai take da idanu gabanta na faduwa, har idanunta ya sauka kan sabeeha da tun shugowarsu ta sulale kasa sai faman kuka take kasa kasa tana shesheqa.
duk sun zazzauna kan kujera kamar waenda aka kawowa saqon mutuwa, duk sun zubama anne idanu, nanna na gefenta ta dafe kirjinta saboda yanda yake mata nauyi. daddyn maya ko gaba daya idanunshi sunyi jaa sosai.
ga su jamila da hadiza a zaune, har zuwa lokacin jamila fa bata saki hannun hadiza ba da har lokacin zage zage take, gaba daya ta zama kamar burkitattciya,sameer ya doka mata tsawa wanda hakan yasa ta yi shuru.

Daidai nan taj ya shugo gidan da sallama, da kyar sameer ya iya amsa mashi, ganin yanayin kowa yasa shi tambayar ko lafiya?
nanna ce kawai ta iya cewa ya samu waje ya zauna.
Ganin anne ma ta kasa cewa komai yasa nanna cewa ''yaya…ki mana bayanin abunda ke faruwa?''

Dakyar anne ta samu ta danne zafi da dacin da takeji aranta ta kalli rabi, wanda hakan yasa rabi ta soma magana kamar haka, ''jiya misalin wajen karfe sha biyu aka kirani daga security post kan cewa wata bakuwa tazo tana nema, ina futa sai naga wannan''
tayi nuni da jamila, ''kawar hadiza ce, don ta taba zuwa sau daya gidan nan, saina tambayeta dalilin nemana da take sai tace wai tanason na kaita wajen anne, ni kuma nace indai bata bani kwakwaran dalili ba babu abunda zaisa na kaita, nan ne take shaida min rayuwar yar hadiza wato sabeeha na cikin hadari, kuma ba kowa ne ke kokarin sata cikin hadari ba sai hadizar, wadda ta kasance ba mahaifiyarta ta asali ba a cewar jamilar, jin wannan yasa na amince muka dauki drop zuwa ga asibiti wajen hajiya, muna zuwa na kaita har wajen hajiya''
tana fadin haka ta dakata, fadila ta dubi jamila sai a lokacin ta tuna da, ta ganta asibiti kuwa tabbas lokacin ta futo daga dakin anne ita kuma a lokacin taje ganin doctor kan prescription din anne…

A day before (Abunda ya faru a jiya).
rabi da jamila na isowa asibiti da sallama rabi ta bude kofar bedroom din anne jamila na biye da ita, lokacin kuwa anne ce kawai a dakin, cikin sauri rabi ta karaso cikin ladabi ta gaishe da anne, jamila ko tana daga tsaye, saida rabin ta gama gaisheta kafin ta gaishe da annen itama cikin mutunci baza kace tazo da wani abu aranta ba.
jamila bata bama rabi damar yima anne bayanin ko ita wace ba da dalilin zuwanta kai tsaye ta fada mata yanda take da hadiza sannan tace mata tazo ne wajenta da magana mai nauyi kuma mahimmiya wadda ta shafi ahalinta, anne najin haka da mamaki ta buqaci rabi ta futa ta basu waje, rabi na futa jamila ta dubi anne sannan tace.
''ba komai ne ya kawo ni ba sai dan na fada maki wani sirrin da ba kowa ya sani ba dagani sai hadiza.''
Jamila ta danyi shuru kafin ta cigaba, ''dalilin dayasa nace ya shafi ahalinki kuwa shine, fatima wato yar hadiza ba yarta bace ta asali yar bahijja ce''
confusely anne ta kalleta, jamila na ganin haka tace ''nasan bazaki manta da ranar da hadiza da bahijja suka haihu ba, tabbas a wannan ranar muka sauya yaran ba tare da sanin kowa ba… idan baki yarda ba zaki iya yin bincike akai saiki nemeni don ni banida da asara''
jamila na kaiwa nan ta tashi sannan ta mata sallama ta futa, ko tsayawa taji me anne zatace batayi ba, zabi ne tabarta dashi kota yarda ko kar ta yarda.
fadin irin tashin hankalin da anne ta shiga bata lokaci ne,sai kawai ta tuna ranar da aka haifesu.
jamila na futowa ko jiran rabi batayi ba ta kama hanyarta, rabi ta koma dakin anne ta mata sallam lokacin fadila ta dawo daga wajen doc so batasan meya faru ba, rabi na komawa gida anne ta kirata a waya, tana dagawa ta umarceta data nemo mata gashin sabeeha ko kuma brush na wanke baki, rabi batayi qestioning dinta ba tayi abunda tace, tana daukan brush din sabeehar ta taho asibitin,yanda anne ta umarceta kan cewa karta bari kowa ya sani hakan tayi kuwa.
bayan barin asibiti da rabi tayi a daidai lokacin ne kuma bahijja ta iso, saboda kiran gaggawa da anne tayi mata, itama dai tana zuwa anne tasa doctor ya deba jininta, bahijja was so confuse bama ita kadai ba hatta fadila, saidai ganin yanayin annen yasa basuyi questioning dinta ba.
A ranar anne tasa ayi maternity DNA test, test din dake daukan kwana biyu kafin result ya futo a ranar anne tasa ayi cikin gaggawa, misalin wajen karfe sha biyun dare kuwa dr barau yayi mata presenting result, gabanta na faduwa ta bude result din, tabbas sabeeha yar bahijja ce ta asali, a daren dai anne kasa barci tayi tana hawaye, tashin hankalin data shiga yasa jininta hawa sosai, dakyar aka samu yayi regulating, washe gari kuwa tayi insisting dole a sallameta daman a ranar ya kamata a sallamota.
''hadiza ta cucesu ta cucesu cutar da har abada batajin bahijja zata iya yafema kanta, tana rike da yarda ba tata ba while tata na rayuwar wulaqanci, don ba tun yanxu anne ta lura da yanda hadiza ke treating yarinyar ba, ta rabata da iyayenta tun daga haihuwarta innalillahi wa inna ialihi rajiun, hadiza ta cucesu ta cucesu, gaba daya ahalin gidan, har zuwa lokacin anne ta kasa gane wani dalili ne zaisa hadiza ta chanza yar bahijja da tata,''


cigaban labari….
anne na hawaye ta soma magana ''tabbas fatima yar bahijja ce wadda suka sauya ta da maya lokacin da aka haifesu''
take kowa ya zaro ido in so much shock, tuni maya ta nemi natsuwarta ta rasa, tama kasa gane inda gabar maganr take, wannan wani irin magan banza sukeyi? ta tambayi kanta.
hamad ko da sameer babu abunda suke sai kallon anne baki a bude, jamila ko babu abunda take sai murmushi.

Hankali a tashe fadila ta soma magana ''ya zaayi ta zama yar bahijja anne?'' bata kaiga karasawa ba ta dakata tunawa da ranar da aka haifi maya, tabbas in bata manta ba tare suka kai bahijja da hadiza asibiti, don ranar a tare suka fara naquda.


Jikin bahijja na tsuma ta miqe tsaye, ta tunkari inda anne ke zaune ga envelop a hannunta, tayi saurin karba jikinta na rawa, tundaga lokacin da anne ta soma magana ta shiga tashin hankalinda gaba daya ji take dama nunfashinta yabar jikinta.
idanunta na cike da kwalla hannunta na rawa ta bude papers din, bata gama bude takardar ba duka idanunta ya sauka kan sunanta, ''DNA maternity test result, Name; Hajiya bahijja santuraki, and ''Fatima,''
tana kai idanunta kasan paper din inda aka rubuta result taga an rubuta probability of maternity test 99.9%''
tana ganin haka ta soma jin wani juyayi kunenta ya toshe gaba daya kanta yayi dummm, a take paper ta sulale, majeed dake zaune gefenta yayi saurin mikewa ya dauki papers din ya bude shima yana karanta bai kaiga dagowa ba sai jin bahijja yayi ta soma cewa ''innalillahi wa inna ilihi rajiun….innalillahi wa inna ilaihi rajiun, na shiga uku, innalillahi wa inna iliahi rajiun, majeed yatace da gaske, yatace…what have i done???? tana fadin haka ta sulale kasa.
shima dai takardar faduwa tayi daga hannunshi, gaba daya hannunshi sai faman karkarwa yake yana kallon sabeeha, tabbas tundaga ranar daya sanyata a idanunsa yaji wani abu game da ita.
Tuni nanna ta runtse idanunta sai hawaye, hadiza ko dora hannu kawai tayi aka tana kukan munafurci.

Tuni hankalin maya ya tashi tana daga zaune tana kallon mummynta dake hawaye tana kuka, me mummy ke magana akai?, wacece yar hadiza? wai meke faruwa ne?'' haka ta dunga tambayar kanta.

fadila da taga yanayin da suka shiga itama miqewar tayi ta dauka takardar ta soma karantowa, tuni hawaye ya soma sulalo mata ta miqawa sameer dake gefenta takardar, tayo kan hadiza a guje, ta soma bugunta kamar an aikota, nanna na hawaye ta soma kiran fadila, ''fadila fadila '' amma ina bataji bataji bata gani,

taj da tun shugowarshi idanunshi ya kaiga sabeeha ganin yanayin daya ganta yasa ya kasa natsuwa, controlling kanshi kawai yake saboda ita, saboda bayanson ya nuna akwai wani abu tsakaninsu badan haka ba, bayajin zai iya zama yana ganinta tana hawaye gashi baisan dalili ba, gashi babu wanda ya bashi damar sanin abunda ke faruwa sai binsu kawai yake da ido.
karban takardar dake hannun sameer yayi shima ya soma karantawa, yana gama karantawa ya dago da kanshi ya kalli sabeeha, sannan ya maida dubanshi ga bahijja in so much shock, gaba daya yafi shiga confusion don baisan meke faruwa ba.

''me muka maki?me muka maki?, duk abunda muka maki ta hanyar nan zaki saka mana?'' fadila ta fada tana ihu tana dukan hadiza.

hadiza fa saida ta rasa natsuwarta saboda irin dukan da fadila ke mata jamila na daga gefe sai faman taunar gums dinta take hankali kwance, kwata kwata bata ma tunanin ko zasu sa a kamata ita da hadizar kai ko an kamata wallahi tasha don burinta ya cika,

''ya isa fadilaaa ya isa'' nanna tayi magana dakyar tana kukan tausayin bahijja da sabeeha data fashe da sabon kuka dukda tana cikin rudu da tashin hankali magnagnunsu na zuwa kunenta, kuma ta kasa yarda da hakan.

''ki barni nanna, ki barni na kashe tsinanniyar nan, kin cucemu kin cucemu,yau shekaru ashirin da biyu kenan, muna barci cikin kwanciyar hankali ba tare da sanin yarmu na chan wata duniyar ba? a wulaqance?, ke kuma taki tana nan cikin jin dadin rayuwa? ba a rageta da komai ba? wannan wani irin baqin zalinci ne, wallahi bazaki taba samun rahamar allah ba hadiza wallahi saikin gwammaci baki taba sanin ahalinnan ba''

anne dai na daga zaune ta kasa cewa komai sai hawayen da takeyi,tanajin guilt din komai, tabbas a lokacin da aka sauyasu allah ya nuna mata ta wata sigarda dan abu kadan zatayi da zaiyi preventing sauyasun da sukayi, saidai kuma saboda yanda bason auran majeed din da bahijjan take ba yasa kwata kwata bata maida hankali ba musamman akan abunda ya shafesu, ko haihuwar ma bawai nuna jin dadinta tayi ba lokacin da bahijjar ta haihu, amma tabbas a lokacin da aka sauyasu allah ya nuna mata amma taqi yin komai akai, she choose to turn a blind eye on it.

fadila na tsaka da jibgarta suka soma jin jiniyar motocin DSS,
Jikin maya na rawa ta miqe hankali a tashe sai yanxu kwakwalwarta ta fayyace mata komai, suna nufin an sauyata da sabeeha? sabeeha ce yar asalin daddy da mummy ita kuma itace yar mai aikin nan hadiza?'' bakinta na karkarwa ta dubi hadizar sannan ta dubi sabeehar ta dubi daddy da mummy, ta fashe da kuka tana juya kanta, ina bazai yuwu ba bazai yuwu ba, bazai taba yuwuwa ba ta kasance yar mai aiki,

bakinta ra rawa ta soma magana ''wallahi karya ne, ni ce yar mummy, ni ba yar mai aiki bace, karya ne wallahi, ni kadai ce yar mummy naa'' tuni ta furgice hawaye na sauka kan fuskarta harda majina, duk suka bita da ido, bahijja ko kasa kallon kowa tayi musamman sabeeha, ya zata kalli yarta? da wani irin ido zata kalli yarta ta asali?, innalillahi wa inna ilaihi rajiun, da kanta ta so illata yarta,da kanta ta nuna tsana mafi muni gareta, ?? take ta tuna yanda ta dunga treating sabeeha tunda ta fara ganinta, da yanda ta dunga dukanta dazu, inama ace zata iya maida hannun agogo baya?, inama ace zata bude idanunta taga mafarki takeyi, Ya allah, this is so unbearable to her, yarta tayi treating hka ba tare da saninta ba, maya kuma ba yarta bace?, ba asalin yarta bace yar hadiza ce, yarta ta asali takema kallon yar iska kuma barauniya? duk dan saboda zalincin hadiza???

Bahijja na kuka tana kankame da majeed tana hawaye shima sai girgiza kanshi kawai yake, idanunshi sunyi jaa sosai, hadiza ta cucesu ta cucesu, cutarda har abada bazasu taba mancewa ba, ta rabasu da yarsu, yarinyar da bataji ba bata gani ba, saboda wani dalili nata daban da basu san ko menene ba? shima kanshi kasa kallon sabeehar yayi, he raised yarinyar da ba tashi ba all those years, tashi kuma tana chan uwa duniya.

Babu wanda ya lura da sumewar da maya tayi sai nanna'tayi saurin miqewa ta tunkari inda take a kwance ta tallabo kanta tausayin yarinyar ya cikata, dole zata shiga shock itama.

dakyar hadiza ta kwace daga hannun fadila bakinta duk a faffashe ta miqe tsaye tana zare zaren ido ta fashe dariya ''kona mutu yanxu naci galaba akanki bahijja kodan saboda yarki dana juyawa rayuwa kuma na tabbatar rayuwarta ta wulaqanta tun haihuwarta,kin ganta nan saida na tabbatar batasan wani abu waishi gata ba balle jin dadin rayuwa,kima godewa allah ban watsa ta duniya ba ta zama kwantacciyar karuwa mai lasisi koba komai na dandana maki zafin cin amanata da kikayi, ay wallahi duk abunda na maki baikai kwatankwacin abunda kikayi min ba, wallahi wallahi bahijja indai ina nunfashi bazan taba bari ki samu farin ciki ba ke bake kadai ba duka ahalin nan''
tana cikin magana batayi auni ba saiji tayi an kwasheta da mari, dagowan dazatayi sameer ya sake sauke mata wani marin, a daidai lokacin kuma wasu samudawan DSS officers suka shugo, su kusan biyar rida rida dasu, baqaqe suna sanye da baqaqen kaya da bindigu abun tsoro.

daman musamman anne ta kira general director dinsu tun kafin su dawo gida, ta shiada mashi crime din hadizar da jamilar, daman kwana tayi da tunanin wani hukunci ne ya dace dasu,don duk abunda zatasa ayi masu batajin zai wanke laifukan abunda hadiza tayi.
Anne na daga zaune tayi instructing a fita dasu, take hankalin jamila ya tashi don batayi tsammanin harda ita za a hada ba amma ta dake don koba komai dai ta tona asirin hadiza hankalinta ya kwanta.
kafin a futa dasu hadiza tace ''banyi asara ba kona mutu na aje maku tabon da har ku mutu bazaku manta dashi ba,''ta karaashe tana kallon gaba dayansu ,yanda fa hadiza ke maganganu kwata kwata babu any remorse ko regret
jamila dataga da gaske harda ita za a hada a tafi, tuni yayanta suka zo ranta, tace
''hajiya hardani za a hada? nifa yar rakiyace? itace ta shirya kuma ta gudanar da komai''
hadiza ta dubeta da fashesehn lebe tace ''au bakisan da haka ba sai yanxu? ay tunda kika tonan asiri nima saina tona naki wallahi, sai duniya tasan da hannunki kika kashe tsohon mijinki tsinanniya''
''akwai tsinanniya data wuce ke? shi uban wacchar yarinyar da kike ikirarin kunyi aure kema ay kasheshi kikayi, au nama tuna ashefa bata da uba ko yar taki?'' jamila ta bata amsa, filin saiya zama kamar na bankade bankade.

suna kallo aka fita da ita da hadiza, yanda ma dss dinnan ke jansu kamar dabbobi.


MATAR TAJ (destined with you)
   Written by 
          Queenmarh

Book2 
PAID
Chapter 54 · 0% Book details