← Book details Kwankwason Jimina Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 44

Sashe 9

Kwankwason Jimina Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Daidai lokacin da marwaan ya karasa waiensa da sauri ya janyo shi ta cikin glass ya rufe littafin.

Marwaan ya dube shi yana tabe baki,

"Uban yan boko, karfe nawa kazo?"

"Ban wani dade ba"

"Ka fara sanaar karatun kenan. Guy ka dinga hutaawa fa. Kullum kanka na kan littafi kana karatu ne oho. Shegen littafin da baa ganin cikinsa" marwaan ya daga hannu ya kaiwa littafin duka

Anees ya janye da sauri yana murmushi. Yana juyawa ya hango Nawraah sun futo daga kofar garden din. Da sauri ya juya ya dubi Anees ya banka masa harara,

"Baka gayamun ga lover ta can aciki ba. Ka barni a tsaye ni dakai, Gardin banza, Uban me zan maka?."

"Wetin man do man? Haba honey"

"Uwar ka, Allah ya isa shege. Na honey wa uban ka. " marwaan ya amsa shi yana kai masa bugu.

Anees ya yi daria ya cigaba da cewa,

"Wa kake nufi kenan?"

"Dalla can aunty zaka dinga Kiran ta Muna yin aure. Kuma ka kusa fara gayshe ta don kaji. Wannan girman kan naka ba zaka ma iyali na ba wallahi"

Anees ya mike daga zaune da yake yana kakaro murmushi hadi da girgiza Kai yace,

"Zaka tsaya kana zubar maganar ko wajenta zaka. Ka takura mun?"

Marwaan ya Kai masa duka a kafadar sa ya juya da sauri ya nufi wajen su Nawraah. Ya yinda Anees ya wuce cikin theatre din da zasu je class

Gaisawa sukayi da marwaan. Nawraah nata saye fuska. Marwaan ya sunkuyar da Kai yana hango fuskar tata,

"Kyawunki kamar daren goma sha hudu... Kullum kyau kike karawa by Allah."

Ta Saka tafukan hannuwanta tana rufe fuskar ta, ya daga kai yana duban Layla yace,

"Dear sis... Mun kwana lafiya?"

"Alhamxulillaj inlaw..."

"Masha Allah. A'ina zakuyi classes yau?"

"A auditorium ne"

"Okay muje ko?"

Ya basu hanya yana nuna musu da yatsa. Suka wuce sannan yabi bayan Nawraah da sauri.

Suna tafe a hanya yana ta zubar magana kamar yayan kanya. Wani abunma idan ya fada Nawraah murmushi kawai take.

Duk inda suka gitta a school din, sai anyi zunden su. Yammata da yawa na bakin cikin kasancewar Nawraah budurwa agun marwaan, Dan masu kudi. Ita kuwa ba yar kowan kowa bace ya dillalin kashi agidan marayu ma take tsabar rashin gata itada yan uwanta...

_HGL CHARITY FOUNDATION_

_ASSALAMU ALAIKUM WA RAHAMATULLAH!_
JAMA'A BARKANKU DA _WARHAKA... ALLAH YA SAKA MUKU DA ALKHAIRI YA BADA LADA HADI DA BIYA MUKU DUKKANIN BUKATIN KU DA KUKE FATAN SAMU AAMIN_

GODIA DUBU GA TALLAFIN DA KUKA SAKA NA CIYARWAR AZUMI
INSHAA ALLAHU WANNAN GIDAUNIYAR MAI SUNA A SAMA NA KIRAN MUTANE AL'UMMA MASU SON SAMUN LADAN WANNAN MANYAN AIKI DA MUKE SAKA RAN FARA SHI KAMAR
НАКА

1• DAFA ABINCI A RABA GA MABUKATA RANAR JUMU'AH KO A KAI RUWAN SHA GA MASALLATAI RANAR JUMU'AH

2• HAQA RIJIYOYI ACIKIN KAUYUKA DA UNGUWANNIN DA BASUDA RUWA

3• RABA KAYAN ABINCI KO KUDI GA MABUKATA
MARASA HALI

4•KAI ZIYARA GIDAN MARAYU DA KAI MUSU
ABUBUWAN AMFANI DA SUTURA IDAN DA ME BAYARWA

5• KAI TALLAFI KO ABINCI GA ASIBITOCI WAJEN
MASU JINYA MARASA KARFI..

6•KOKARIN KARASA MASALLACI KO YIN MASALLACI
AWAJEN DA BASUDA SHI...

MAI NERA BIYAR MAI GOMA DiK
YADDA HALI YA KAMA ALLAH YA HADA MU A LADAN DUKA..
JAZAKUM ALLAH BiL JANNAH..
DOMIN SAKA TALLAFI GA ASUSU

9044191709
OPAY
JAZAKUM ALLAH BİL JANNAH💜

[5/3, 2:00 PM] Hafsaat🧕💞: _K'K'J_
_(M/W/S)_

_BOOK TWO_

_✍️:MX_

_13_

:::::::::

*Yana* tafe yana ta sake sake akan hanyar sa ta komawa gidah. Ya kan tsaya ya nisa yayi magana shi kadai kamar zaucacce sannan kuma ya cigaba da tafiya a haka har ya karasa gidah cikin sa na ta murdawa tsananin yunwar dake yasar yan hanjin cikin sa ..

Bakin sa dauke da sallama ya shiga parlorn na su. An kawo wuta TV dinsu yar karama tanata nuna faifon bidiyon wani dadaddan tsohon shirin film din hausa.

Yaran basa parlorn. Sai ita kadai tana kallo tana murmushi. Gabanta kuwa wata tasa ce dauke da ragowar fura tasha ta isheta ne da alama...

Ta daga kai jin tamkar an tsaya akanta ta sauke idanunta akan sa yana tsaye shima duban ta yake yi,

"Ya akai ne Auwalu?"

"Ya akai kuwa? Yanzu saboda Allah shikenan ke kinfi kaunar wannan rayuwar da muke cikinta mai tsananin sarqaqiya da wahala? "

"Ah kaji ka da wani zance can daya . To ni me zanyi akan rayuwar da muke ciki? Ba Allah ne ya Kadarta mana hakan ba? Kawai dai saboda ka kwaso fushi da bacin rai shine kake son ka zazzage shi akai na? Gaskia karka sake mun irin wadannan abubuwan ka Kai ni karshe"

"Lalle ma Nusaiba. Wallahi wannan rayuwar da muke ciki har da tagomashin kason lefin ki aciki "

Dogon tsaki taja, Ta dube shi shakeke tana watsa masa harara hadi da saka hannu ta tura masa kwanon furar gaban sa,

"Bismillah dauki kasha, Na tabbatar yunwa ce take dawainiya da Kai wannan zubar zancen da kakeyi wanda bashida Kai"

Ya dubi kwanon furar ya dubeta ya saka kafa ya hambare kwanon sauran kadan ya zube tayi saurin rike kwanon tana duban mijin nata,

"Menene haka auwalu? Nace menene haka?"

"Ni kike mayarwa karamin mutum? Tamkar wani Wanda bashida ishasshen hankali. Ina miki magana ta gaskiya zaki wani kawo kwanon gaba na nayi meye dashi? An gaya miki zakara ne ni sai da tsaba? To ki bude kunnuwan ki dakyau kiji abunda zan gaya miki. Ni ba mutumin banza bane. Kuma ke a matsayin ki na matata wallahi tamkar riga ce zan zare na saka wata. Amman 'yaya fa? 'ya'yana ne wannan alakar ba zata taba goguwa ba. Yadda su Layla suke awaje na hakan matsayina iyalan kanina junaidu suke awaje na."

"Okay yanzu na gano sigar inda zancen ka ya dosa auwalu ah yanzu na gano. Kawai so kake Kaci mitinci na Kaci zarafina. Su 'ya'yan da kake tunkaho na Kane. Kai ka dau cikin su ka haife su ne? Sai ka dinga baje hanci kana wani bubbudawa 'yaya na ne ya ya na ne. Akwai Wanda yace ba yayan ka bane? Allah yabani hakuri ni da na tsugunna na haife su ai bakai ka haifa mun su ba. Haka zalika naka yayan yan uwan ma dai da kaketa fada ba dagaa tsatson kaba bane, komai abunka wannan jalli biyun da Allah yabamu sune yayan ka na gaskia. Don haka banason naji wata magana ta daban auwalu Kai bakasan zaman hakuri nake ba zaman 'yaya nake da Kai ba? Wallahi ba dan yarana ba da tuni na dade da bar maka wannan kangon gidan naka, tunda Kai har abada bazan taba burgeka ba dukkanin abunda zanyi. Wannan tsana da kake mun ina sane da ita a burnin zuciya ta . Na fada na Kara fada yara ne dai bazan rike ba wallahi. Mu kanmu gidan bai ishemu ba Bare wasu a waje, yau da ace Kai me hali ne sosai ka rika tutiya haka. Amman muna zaune Muna rufawa juna asiri kullum banida kima a idanunka sai kawo suka sukaa. Kai Allah ya kyauta. Kowa dai ka nemi ka rabu dashi. Haka yan uwan ka da kuka fito ciki daya wadanda suke rage baki daya ka yanke huldar zumunci da su. Kana fushi da su akan wadanda basa duniyar ma gaba daya. Kaki naka duniya ta so shine dama ai. Su 'yayan cikin naka da baka ta tasu. Da yardar Allah sune zasu rufa maka asiri da yardar Allah , wadanda ka dauka ka fifitaa fiye da yaran da ka haifa da yardar Allah ba zasu zama wasu ba. Tunda kowa kansa yasani ,aikin kawai, Dan Allah daga yau ka sauya musu suna su koma Nawraah auwalu, Amnah Auwalu da ashfeef Auwalu. Aikin kawai"

Ta karasa fada hadi da mikewa ta sauke masa harara da dogon tsaki ta juya ta shige daki da sauri.

Wunin ranar baki daya bappah Auwalu a tunanin Ina ya nufa ya dosa baki daya hankalinsa yanzu kacokam ya koma kan yadda zai karbo su Nawraah daga gidan marayun su dawo gabansa

Tunda sauran yan uwan nasu suma sunyi fatali dashi saboda yana goyan bayan iyalan marigayi junaidu. Shikenan sika daina shiga harkar sa shima ya dena shiga tasu. Da sukan aikowa da yaran nasa hatsin abinci ya hana yace kar a sake kawo masa ko da dai da kwayar zarra ne. Allahn daya basu bai manta dasu ba, Kuma inshaa Allah 'yayan junaidu ba zasu tagayyara ba inde yana da saurin numfashi a kasa.

Ranar a parlor ya kwana yanata Kai adduar gurin Allah kan ya zabar masa dukkanin abunda yafu alkhairi akan kankin kansa da iyalan sa da Kuma iyalan dan uwansa junaidu dama sauran musalmai da ke cikin jalin qaqanikayi....

*********

Kasancewar karashen sati ne na weekends ba makaranta. Zaune suke dukkanin su a dakin su, sun kammala wankin su sun shanya sauran kwasa kawai

Hira suke baki dayan su akan tabarmar dake malale a tsakiyar dakin na su. dakin su. Yayinda Amnah ke tsakiyar su akwance akan pillow. Wasila na yarfa mata kananun kalba style din bob Marley..

_ADVERT👇👇_

_YERWA INCENSE AND MORE_
_(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_

_INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_
_TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_

_MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_

_*YERWA INCENSE AND MORE*_
_DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._

_AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_

_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._

_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_

_NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_

_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_
[5/3, 2:53 PM] Hafsaat🧕💞: _K'K'J_
_(M/W/S)_

_BOOK TWO_

_✍️:MX_

_14_

:::::::::
Chapter 9 · 0% Book details