Sashe 14
Kwankwason Jimina Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Toh.... Ma... Mi" ya fada a rarrabe yana zare wayar daga kunnen sa.
Tunda ta kira da lambar sunan Nawraah ya bayyana ta Truecaller da tayi saving da 'Nawraah Junaid' Nanata sunan yayi a saman labbansa yana murmushi. Kafin ya Kai hannun sa yana shafa rubutun dake dauke da sunanta ta a jikin screen din wayar tasa.
Nan da nan yayi saving lambar tata da N ya kara emoji na zuciya da kwado❣️🔐. Ya langabar da kansa ajikin sitiyarin yana murmushi. Ji yake tamkar an amsa dukkanin bukatin sa da burikan sa, wai yau number Nawraah ce awayar sa? Kuma gashi Nawraah Zata shiga motars sa ya Kai su gidah?
Wani murmushi mai taushi ya sake kufce masa. Ya murmusa kawai yana ajiye wayar akan saitin zuciyar sa. Daga kansa da zeyi kenan yaga futowar su
Itace agaba itada Amnah kanwarta. Ta zare facemask din hannunta tana tafiya tana gyara zaman mayafin jikinta.
Dama gashi akwai haske sosai awajen duk kuwa da dare ne Amman wasu irin fitulu ne suka dallare ko'ina da-dal da-dal tamkar rana mai tsananin kwalewa.
Tundaga kan dan karamin bakinta dake dauke da labba jajaye. Zuwa siririn hancin ta dake da hujin hancj da barimar hancib agefen dama. Har ya zuwa manyan idanunta tubarkAllah dake dauke da kwalli. Zuwa girarta da ke cike da gashi tamkar zasu hade da juna.
"Tsarki ya tabbtata ga Allah Wanda ya halarci wannan halitta tubarKAllah" ya karasa fada yana sake kurawa Nawraah idanu
A haka suka karasa gaban motar rasa. Yayi hanzarin zare lock , wasila da Raudah da faty sukayi shigewar su baya suna mata daria.
Takaici ne ya isheta ganin itada suka bari da shiga gaban gashi Raudah ta ja hannun Amnah sun shige baya duka.
A kufule ta bude gidan gaba ta zauna tana waiwayawa baya ta dankara musu harara. Anees na hankalce da ita ta wutsiyar idanun sa. Dariya ta taho masa ya danne Kai yana zura mukullin motar hadi da tashinta bakinsa dauke da addua.
"Sannu ku....." Ya fada a hankali yana karya kan motar.
Suka dube shi dukan su. Kafin su fara gayshe da shi. Sai da Nawraah ta mula ta sha iska tukun sannan ciki ciki tache da shi,
"Ina wuni?"
Ya nemi magana a fatar bakinsa ya rasa ya kasa amsa mata. Gashi zuciyar sa na wani irin rawa tamkar Zata fado kasa. Muryarta kadai ta saukar masa da wani irin farin ciki daya kasa bayyana adadin sa, Amman haka kawai bakinsa ya masa bakin ciki yayi nauyi wajen mayarwa sahibar ransa amsar gaisuwar ta.
Ta sake juyawa tana duban sa hadi da tabe baki ta hararo shi. Tana Kara kambama mamaki irin na rashin mutincin sa da tsanar da yake mata. Wato kowa ya gayshe shi ya amsa amman da ke ita ya tsaneta shine yayi shiru ya cigaba da tuki..
Anees kuwa kuka ne kawai ya rage baiyi na. Kwata kwata ya kasa mayar mata da gaisuwar da tayi masa, me zata kira hakan idan ba wulakanci ba? Ya sauke ajiyar zuciya yana girgiza Kai kawai. Ba wani abu da zai fada yanzu a yadda dashi.
Jikinsa a sanyaye duk ba dadi haka ya karasa da su har unguwar su dai dai kofar gidan marayun na su ya faka motar. Suka fita dukan su. Banda kofar Nawraah data saka hannu zata bude tajita a rufe.
"Dan ciremun lock" ta fada masa tana mai nuni da murfin dayaki murduwa.
Yana sane ya saka lock din ya rufe. Wai dan ya samu yayi mata magana ya bata hakuri da ba halinsa bane shariya da sauran su. Amman baki daya gangar jikinsa ta hade Kai da fatar bakinsa sa, sum masa butulci sam ya kasa tabuka komai. Sai juyawa da yayi kawai ya zube mata manyan idanunsa tubarkAllah akanta.
Ta kasa jure kallon da yake mata kamar zai cinye ta. Gashi dama wani irin idanu ne dashi tamkar yana bacci Kuma manya tubarkAllah.
"Ka budemun mana." ta sake fada tana juyawa baya ganin su Raudah sun shige ciki sun barta
"Naw.... Raaah" ya fada ararrabe yana jan kasan lebensa.
Duban sa tayi da sauri Daman yasan sunanta? Ko da yake ai ko awajen mahaifiyar sa zaiji tunda tana temaka musu sosai wani abun ma shi ake aikawa ya kowa musu gidan marayun
"Dan Allah ka budemun" ta sake marairaicewa tana kokarin bude kofar.
"Bani minti biyu please" ya fada a wahale yana jinginar da kansa jikin sitiyarin motar.
Zuciyar sa na harbawa cikin wani irin fizga da takeyi. Gumi na kokarin keto masa dukkuwa da na'urar ac dake bazawa a motar.
Tarin kalamai ne na love confessions akansa da zuciyar sa, Amman ya kasa samun kwarin gwiwar gaya mata. Nawraah ganin abun nasa bana kare bane ta sake cewa
"Zan fita malam"
Bai ce komai ba. Ya Saka hannu ya danna wani button take kofar ta bude. Ta futa da sauri tana buga murfin motar da karfi hadi da hararo motar ta shige cikin gidan marayun da sauri.
Ya dade a zaune amotar kansa akan sitiyarin har sai da ya tabbatar ya samu nutsuwa sukun sannan ya daga kansa. Saitin kirjinsa ne kawai yake masa nauyi mai wani irin radadi marar dadi
A daddafe ya karasa gidah yaga akwai motoci biyu da direbobi. Nan take ya sanar musu sakon Mamin su. Daga baya shima ganin ba zai iya komawa can wajen bikin ba ya sauka daga motar ya bawa wani direba ya hau tasa suka koma can wajen bikin dan cigaba da jigila da mutane..
Yayinda shi Kuma ya karasa shiga gidah ya shige dakin sa direct bandaki ya fada yayi wanka ya dauro alwala ya zube akan gado yana sauke numfashi. Hannunsa dafe da saitin zuciyar sa dake masa zugi...
=====
Koda ta shiga dakinsu sai data tabbatar ta bankawa daya bayan dayan su harara tukun sannan ta fara mita
Suka fashe da dariya suna bata hakuri. Dakyar ta yadda ta sakkoo take gaya musu yadda akayi. Sunata cewa kila bashida lafiya ne waye waye.
Ita kuwa Nawraah bandaki ta shiga ta sakeyin wanka. Tab sauyawa Amnah kaya zuwa na bacci tayi bacci..
Sannan itama ta koma nata gadon ta kwanta ba dadewa marwaan ya kirata suka sha hirar su take gaya masa yadda akayi. Yake sheda mata itama wajen mahaifan sa zashi yayi maganar ta azo a saka rana ayi auren su.
Bayan ta katse wayar ne take gayawa su Raudah yadda sukayi da marwaan. Nan sukaita tayata murna suna tsallen ihu.
Ranar duka dai baccin dadi sukayi baki dayan su musanman Anees daya samu kansa daga baya. Sai murmushi yake idan ya tuno yau yadau Nawraah amotar ya dawo da ita gida har sunyi magana ta fatar baki ma gashi har yanada number ta. Ranar dai har mafarkin ta sai da yayi da ita saboda tsabar zancen ta daya kasa curewa a zuciya da ran sa
:::
Tana Kai Amnah makaranta ta shige library din makarantar su. Kasancewar akwai wani elective course da suke atare da Layla Kuma an basu assignment zasuyi presentation. Don haka tanata sauri ta karasa library din
Sai dai Kash students sun cika shi ba masaka tsinke an hana shiga. Haka ta hakura ta koma wajen wasu kujeru tana jiran Layla.
Wayarta ta janyo tanata dannawa. Can dai ta shiga cikin files din wayar tana sauraron wakokin ta na baya datayi recording.
Wasu tayi dariya dan ta tuno yadda tayi recoding din wasu su sakata hawaye inta jiyo muryar yan gian su haka. Da haka har tazo kan wani recoding din wakar Maher Zain datayi agidan su dr bintu. Tana cikin jine ta fara jiyo zancen da sukeyi. Komai da komai da sanda ummyn su tabarar da plate din tana basu hakuri.
Idanuwanta suka kawo ruwa. Ta mike da sauri tamkar an tsikareta tana tafiya hanyar gate. Ta samu waata kujera ta daban daga gate ta zauna tana cigaba da kunna abubuwa. Har ya zuwa videos gasunan Wanda Alhaji sambaso ke maganar komai da komai da sanda ya tura mahaifin su a baranda ya mutu.
Hannunta ta saka akan bakinta jikinta sai rawa yake. Ta mike tsaye tana kyarma. Idanuwanta na futar da ambaliyar hawaye.
"Innalillahi Wa inna ilaihi rajiun.... Su suka kashe ummy... Suka kashe abbiey... Kuma suka kashe Hamma..."
Juyawa tayi da sauri tana tafiya tana goge hawayen fuskar ta. Ta nufi gidan marayun da suke ta shige daki ta saka mukulli.
Filla filla tayiwa wayar ta saurari komai taga komai. Fargaba, tsoto, karfin gwiwar atare lokaci daya taji sun kamata.
Tashiga zagayen dakin tana nazari sosai kan yadda zata bullowa lamarin. Sai girgiza Kai take. Hawaye daya nabin daya...
"Ni Nawraah... Nayi alkawari da yardar Allah sai karashen mugayen nan yazo inshaa Allahu.... "
"I count all my hopes n you Nawraah... Kefin KWANKWASON JIMINA ce Nawraah, MAI WUYAR SHAFAWA" ta tuno kalaman da mahaifiyar ta da hamman ta ke yawan gaya mata.
Tabbas inshaa Allah ba zata tankwaru ba sai taga karashen mugayen azzaluman da suka kashe mata iyaye da dan uwa...
Littafi ta dakko da biro ta ajiye akan cinyar ta tana daga kanta sama,
"Alhaji sambaso.... Dr abubuakhar dollars, Dr. Bintu... Hajia Qibdiyya... Alhaji ateeks... Waye shi?" Ta tanbayi kanta tana jijjuya shi..
::::
Zaune yake yayi zaman gurfane agaban su. Gabansa na dukan uku uku gefe daya kuma yanada babbar hujjar da zai bayar idan an hanashi yace,
"Na samu matar aure ne... Anan cikin Alharamein university."
Dr bintu tayi murmushi tana duban mai gidan nata tache,
"Lalle mashaa Allah. Finally marwaan ana maganar manya"
Alhaji sambaso shima murmushin yayi yana sakaace hakoran sa da toothpick yace,
"Yar waye? Mulki suke takama dashi ko sarauta?"
"Ba yar kowan kowa bace ... Cuz iyayenta ma sun rasu"
"What?"
"Nawraah mana.. daya daga cikin yaran da kika bawa scholarship ."
Dr bintu na zaune sai ta mike. Alhaji sambaso ya dubeta ya dubi marwaan don baki daya ma ya manta wacece wata Nawraah.
"Wacece Nawraah?" Alhaji sambaso ya tambaye shi yana duban Dr bintu mai dakin sa.
"Alhaji Nawraah fa... Diyar Hindu mai aikin nan ta shekarun baya"
Tana karasa fada Alhaji sambaso ya mike tsaye yana hade rai kamar tsohon zaki ya saka dan yatsa yayi nuni da marwaan cike da bacin rai kololuwa yace,
Tunda ta kira da lambar sunan Nawraah ya bayyana ta Truecaller da tayi saving da 'Nawraah Junaid' Nanata sunan yayi a saman labbansa yana murmushi. Kafin ya Kai hannun sa yana shafa rubutun dake dauke da sunanta ta a jikin screen din wayar tasa.
Nan da nan yayi saving lambar tata da N ya kara emoji na zuciya da kwado❣️🔐. Ya langabar da kansa ajikin sitiyarin yana murmushi. Ji yake tamkar an amsa dukkanin bukatin sa da burikan sa, wai yau number Nawraah ce awayar sa? Kuma gashi Nawraah Zata shiga motars sa ya Kai su gidah?
Wani murmushi mai taushi ya sake kufce masa. Ya murmusa kawai yana ajiye wayar akan saitin zuciyar sa. Daga kansa da zeyi kenan yaga futowar su
Itace agaba itada Amnah kanwarta. Ta zare facemask din hannunta tana tafiya tana gyara zaman mayafin jikinta.
Dama gashi akwai haske sosai awajen duk kuwa da dare ne Amman wasu irin fitulu ne suka dallare ko'ina da-dal da-dal tamkar rana mai tsananin kwalewa.
Tundaga kan dan karamin bakinta dake dauke da labba jajaye. Zuwa siririn hancin ta dake da hujin hancj da barimar hancib agefen dama. Har ya zuwa manyan idanunta tubarkAllah dake dauke da kwalli. Zuwa girarta da ke cike da gashi tamkar zasu hade da juna.
"Tsarki ya tabbtata ga Allah Wanda ya halarci wannan halitta tubarKAllah" ya karasa fada yana sake kurawa Nawraah idanu
A haka suka karasa gaban motar rasa. Yayi hanzarin zare lock , wasila da Raudah da faty sukayi shigewar su baya suna mata daria.
Takaici ne ya isheta ganin itada suka bari da shiga gaban gashi Raudah ta ja hannun Amnah sun shige baya duka.
A kufule ta bude gidan gaba ta zauna tana waiwayawa baya ta dankara musu harara. Anees na hankalce da ita ta wutsiyar idanun sa. Dariya ta taho masa ya danne Kai yana zura mukullin motar hadi da tashinta bakinsa dauke da addua.
"Sannu ku....." Ya fada a hankali yana karya kan motar.
Suka dube shi dukan su. Kafin su fara gayshe da shi. Sai da Nawraah ta mula ta sha iska tukun sannan ciki ciki tache da shi,
"Ina wuni?"
Ya nemi magana a fatar bakinsa ya rasa ya kasa amsa mata. Gashi zuciyar sa na wani irin rawa tamkar Zata fado kasa. Muryarta kadai ta saukar masa da wani irin farin ciki daya kasa bayyana adadin sa, Amman haka kawai bakinsa ya masa bakin ciki yayi nauyi wajen mayarwa sahibar ransa amsar gaisuwar ta.
Ta sake juyawa tana duban sa hadi da tabe baki ta hararo shi. Tana Kara kambama mamaki irin na rashin mutincin sa da tsanar da yake mata. Wato kowa ya gayshe shi ya amsa amman da ke ita ya tsaneta shine yayi shiru ya cigaba da tuki..
Anees kuwa kuka ne kawai ya rage baiyi na. Kwata kwata ya kasa mayar mata da gaisuwar da tayi masa, me zata kira hakan idan ba wulakanci ba? Ya sauke ajiyar zuciya yana girgiza Kai kawai. Ba wani abu da zai fada yanzu a yadda dashi.
Jikinsa a sanyaye duk ba dadi haka ya karasa da su har unguwar su dai dai kofar gidan marayun na su ya faka motar. Suka fita dukan su. Banda kofar Nawraah data saka hannu zata bude tajita a rufe.
"Dan ciremun lock" ta fada masa tana mai nuni da murfin dayaki murduwa.
Yana sane ya saka lock din ya rufe. Wai dan ya samu yayi mata magana ya bata hakuri da ba halinsa bane shariya da sauran su. Amman baki daya gangar jikinsa ta hade Kai da fatar bakinsa sa, sum masa butulci sam ya kasa tabuka komai. Sai juyawa da yayi kawai ya zube mata manyan idanunsa tubarkAllah akanta.
Ta kasa jure kallon da yake mata kamar zai cinye ta. Gashi dama wani irin idanu ne dashi tamkar yana bacci Kuma manya tubarkAllah.
"Ka budemun mana." ta sake fada tana juyawa baya ganin su Raudah sun shige ciki sun barta
"Naw.... Raaah" ya fada ararrabe yana jan kasan lebensa.
Duban sa tayi da sauri Daman yasan sunanta? Ko da yake ai ko awajen mahaifiyar sa zaiji tunda tana temaka musu sosai wani abun ma shi ake aikawa ya kowa musu gidan marayun
"Dan Allah ka budemun" ta sake marairaicewa tana kokarin bude kofar.
"Bani minti biyu please" ya fada a wahale yana jinginar da kansa jikin sitiyarin motar.
Zuciyar sa na harbawa cikin wani irin fizga da takeyi. Gumi na kokarin keto masa dukkuwa da na'urar ac dake bazawa a motar.
Tarin kalamai ne na love confessions akansa da zuciyar sa, Amman ya kasa samun kwarin gwiwar gaya mata. Nawraah ganin abun nasa bana kare bane ta sake cewa
"Zan fita malam"
Bai ce komai ba. Ya Saka hannu ya danna wani button take kofar ta bude. Ta futa da sauri tana buga murfin motar da karfi hadi da hararo motar ta shige cikin gidan marayun da sauri.
Ya dade a zaune amotar kansa akan sitiyarin har sai da ya tabbatar ya samu nutsuwa sukun sannan ya daga kansa. Saitin kirjinsa ne kawai yake masa nauyi mai wani irin radadi marar dadi
A daddafe ya karasa gidah yaga akwai motoci biyu da direbobi. Nan take ya sanar musu sakon Mamin su. Daga baya shima ganin ba zai iya komawa can wajen bikin ba ya sauka daga motar ya bawa wani direba ya hau tasa suka koma can wajen bikin dan cigaba da jigila da mutane..
Yayinda shi Kuma ya karasa shiga gidah ya shige dakin sa direct bandaki ya fada yayi wanka ya dauro alwala ya zube akan gado yana sauke numfashi. Hannunsa dafe da saitin zuciyar sa dake masa zugi...
=====
Koda ta shiga dakinsu sai data tabbatar ta bankawa daya bayan dayan su harara tukun sannan ta fara mita
Suka fashe da dariya suna bata hakuri. Dakyar ta yadda ta sakkoo take gaya musu yadda akayi. Sunata cewa kila bashida lafiya ne waye waye.
Ita kuwa Nawraah bandaki ta shiga ta sakeyin wanka. Tab sauyawa Amnah kaya zuwa na bacci tayi bacci..
Sannan itama ta koma nata gadon ta kwanta ba dadewa marwaan ya kirata suka sha hirar su take gaya masa yadda akayi. Yake sheda mata itama wajen mahaifan sa zashi yayi maganar ta azo a saka rana ayi auren su.
Bayan ta katse wayar ne take gayawa su Raudah yadda sukayi da marwaan. Nan sukaita tayata murna suna tsallen ihu.
Ranar duka dai baccin dadi sukayi baki dayan su musanman Anees daya samu kansa daga baya. Sai murmushi yake idan ya tuno yau yadau Nawraah amotar ya dawo da ita gida har sunyi magana ta fatar baki ma gashi har yanada number ta. Ranar dai har mafarkin ta sai da yayi da ita saboda tsabar zancen ta daya kasa curewa a zuciya da ran sa
:::
Tana Kai Amnah makaranta ta shige library din makarantar su. Kasancewar akwai wani elective course da suke atare da Layla Kuma an basu assignment zasuyi presentation. Don haka tanata sauri ta karasa library din
Sai dai Kash students sun cika shi ba masaka tsinke an hana shiga. Haka ta hakura ta koma wajen wasu kujeru tana jiran Layla.
Wayarta ta janyo tanata dannawa. Can dai ta shiga cikin files din wayar tana sauraron wakokin ta na baya datayi recording.
Wasu tayi dariya dan ta tuno yadda tayi recoding din wasu su sakata hawaye inta jiyo muryar yan gian su haka. Da haka har tazo kan wani recoding din wakar Maher Zain datayi agidan su dr bintu. Tana cikin jine ta fara jiyo zancen da sukeyi. Komai da komai da sanda ummyn su tabarar da plate din tana basu hakuri.
Idanuwanta suka kawo ruwa. Ta mike da sauri tamkar an tsikareta tana tafiya hanyar gate. Ta samu waata kujera ta daban daga gate ta zauna tana cigaba da kunna abubuwa. Har ya zuwa videos gasunan Wanda Alhaji sambaso ke maganar komai da komai da sanda ya tura mahaifin su a baranda ya mutu.
Hannunta ta saka akan bakinta jikinta sai rawa yake. Ta mike tsaye tana kyarma. Idanuwanta na futar da ambaliyar hawaye.
"Innalillahi Wa inna ilaihi rajiun.... Su suka kashe ummy... Suka kashe abbiey... Kuma suka kashe Hamma..."
Juyawa tayi da sauri tana tafiya tana goge hawayen fuskar ta. Ta nufi gidan marayun da suke ta shige daki ta saka mukulli.
Filla filla tayiwa wayar ta saurari komai taga komai. Fargaba, tsoto, karfin gwiwar atare lokaci daya taji sun kamata.
Tashiga zagayen dakin tana nazari sosai kan yadda zata bullowa lamarin. Sai girgiza Kai take. Hawaye daya nabin daya...
"Ni Nawraah... Nayi alkawari da yardar Allah sai karashen mugayen nan yazo inshaa Allahu.... "
"I count all my hopes n you Nawraah... Kefin KWANKWASON JIMINA ce Nawraah, MAI WUYAR SHAFAWA" ta tuno kalaman da mahaifiyar ta da hamman ta ke yawan gaya mata.
Tabbas inshaa Allah ba zata tankwaru ba sai taga karashen mugayen azzaluman da suka kashe mata iyaye da dan uwa...
Littafi ta dakko da biro ta ajiye akan cinyar ta tana daga kanta sama,
"Alhaji sambaso.... Dr abubuakhar dollars, Dr. Bintu... Hajia Qibdiyya... Alhaji ateeks... Waye shi?" Ta tanbayi kanta tana jijjuya shi..
::::
Zaune yake yayi zaman gurfane agaban su. Gabansa na dukan uku uku gefe daya kuma yanada babbar hujjar da zai bayar idan an hanashi yace,
"Na samu matar aure ne... Anan cikin Alharamein university."
Dr bintu tayi murmushi tana duban mai gidan nata tache,
"Lalle mashaa Allah. Finally marwaan ana maganar manya"
Alhaji sambaso shima murmushin yayi yana sakaace hakoran sa da toothpick yace,
"Yar waye? Mulki suke takama dashi ko sarauta?"
"Ba yar kowan kowa bace ... Cuz iyayenta ma sun rasu"
"What?"
"Nawraah mana.. daya daga cikin yaran da kika bawa scholarship ."
Dr bintu na zaune sai ta mike. Alhaji sambaso ya dubeta ya dubi marwaan don baki daya ma ya manta wacece wata Nawraah.
"Wacece Nawraah?" Alhaji sambaso ya tambaye shi yana duban Dr bintu mai dakin sa.
"Alhaji Nawraah fa... Diyar Hindu mai aikin nan ta shekarun baya"
Tana karasa fada Alhaji sambaso ya mike tsaye yana hade rai kamar tsohon zaki ya saka dan yatsa yayi nuni da marwaan cike da bacin rai kololuwa yace,