Sashe 24
Kwankwason Jimina Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zama tayi akan kujera ta dau wayarta ta danno Kiran Anees. Ringing biyu ya dauka. Alokacin wayar na hannunsa ya shiga gallery yana kallon fuskar hotunan Nawraah.
"Anees kaci abincin da aka kawo? Akwai abunda kake bukata na daban?"
"No komai yayi Mami. Nagode sosai" ya karasa fada yana daga kansa saboda yadda ya dau ciwo da zafi lokaci daya"
"to shikenan... Sai da safe?"
"Eh sai da safe Mami..."
"To Allah ya tashe mu lafiya"
"Aameen Mami" ya katse kiran bayan sunyi sallama..
Tashi yayi dakyar daga kan gadon nasa. Ya nufi inda aka ajiye masa abincin. Warmers ya bubbude baki daya, kwata kwata bashida appetite din abincin.
Tsattsakura yayi a plate kadan yaci ya shanye juice din, sai daya bada rata sosai sannan ya sha tea din ya balla pain killer ya sha.
Wayar sa ya dauka yakira mai kula da sashen da yake, wanda ya kawo masa abincin dazu,
"Ka dauka ka cinye su dika please sai a mayarwa Mami"
"To ranka ya dade. Allah ya saka da Khairan"
"Aameen Wa iyyakum"
Komawa yayi kan gadon ya zauna. So yake abincin yayi digesting sannan ya kwanta, ya so ya dan fita yayi atisaye (exercise) Amman jikin sa ya hanashi saboda weakness ga kuma kansa dake tsananin ciwo.
Counter ya dauka yana istigfari ya jima yana yi har dare yaja sosai. Bacci ya kauracewa idanun sa. Ya dauro tsarki da alwala ya tada sallar tahajjud da niyyyar Allah ya kawo musu sauki acikin dukkanin lamurana su. Ya Kuma magance musu dukkanin damuwar su. Ya Kuma biya musu dukkanin bukatin su na alkhairi, ya kare su da dukkanin kariyar sa. Kuka yake sosai yana rokon Allah ya kawo masa dauki a rayuwar sa. Tun yanayi a zuci har ya fara fitowa fili yanayi,
"Yaa Allah... Nawraah idan har da alkhairi a tarayyar su da marwaan Allah ka shiga cikin lamuran su, ka saukaka musu kasa auren ya zamanto babbar albarka atare dasu da mu baki daya. Yaa Allah idan ba alkhairi bane agare su. Rabbi kayiwa kowannen su zabin abokin zama na gari Aameen.. "
Ya sake daga hannu sama cikin rokan Allah. Wannan karon muryar tasa har rawa ta fara yi,
"Yaa Allah Nawraah, kaunar Nawraah ta mun illa a zuciya ta da gangar jikina baki daya. Yaa Allah ina rokon ka da tsarkakkun kyawawan sunayen ka cassa'in da Tara. Ya Allah kai ka iya kai zakayi, Yaa Allah nayi tawassali da kai, kai na a duqe, ni bawa ne agare ka domin kai din mubuwayi ne gagara misali, Rabbi ka dubeni ka zare mun kaunar Nawraah a zuciyata. Yaa Allah ina cikin damuwa Yaa Rabbi banida tsimi banda dabara. Yaa Allah ka iya mun Allah ka ciremun tunanin Nawraah, Yaa Allah ka dubeni . Yaa Allah na kamu da kaunar Nawraah. Kaunar da ta gauraye ilahirin jikina da kewaye. Yaa Allah ka kawo mun sauki. Ka zabar mun abunda yafu dacewa da ni, na daga mafificin alkhairi agare ni. Komai nawa Yaa Allah I entrust all my affairs to you..." Yana kaiwa karshe ya kifa kansa, don ji yayi baki dayan gabobin sa tamkar ana sassara su. Dakyar ya iya komawa kan gado ya kwanta bayan yayi addu'oin bacci.
Sai kuma Allah ya temaka ya na kwanciyar ba dadewa bacci yayi awun gaba da shi...
Bayan dawowar Dr abubakhar dollars. Hajiya Qibdiyya mai dakinsa ta temaka masa yayi wanka ya sauya kaya zuwa na bacci. Yaci abinci da drinks. Bayan ya bada rata kuma ya sha tea. Daga nan suka shiga hira da mai dakin nasa. Sai data tabbatar ya samu nutsuwa sannan ta sanar masa dukkanin komai tundaga farko zuwa karshe. Yayi matukar mamaki matuka gaya. Don abun ya girgiza shi sosai fiye da yadda alkalami zai bayyana.
A daren kuma suka shirya yadda komai zai kasance sannu ahankali har su cimma burikan su.... A ranar dai Kam zukatan mutane da yawa basu samu nutsuwa ba. Idanuwa suka kafe. Bacci ya kauracewa idanuwan su. Wasun su sukayi sallar dare wajen neman zabin alkhairin Allah a dukkanin lamuran su...
***
ALHAJI SAMBASO AVENUE....
Tun tuni take jiran dawowar sa shiru shiru bai waiwayo gidah ba, dare ya ja sosai ainun. Ta sake duban agogon dake like ajikin bango. Ta sake sakin wani tsakin a karo na ba adadi....
_ADVERT👇👇_
_YERWA INCENSE AND MORE_
_(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_
_INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_
_TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_
_MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_
_*YERWA INCENSE AND MORE*_
_DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._
_AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_
_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._
_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_
_NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_
_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_
_K'K'J_
_(M/W/S)_
_BOOK TWO_
_✍️:MX_
_29_
:::::::::
*Daga* Kai tayi ta dubi agogon dake like a jikin parlorn da take a zaune. Shiru har yanzu bai dawo ba.
Whatsapp ta shiga kan sunan kawar tata ta rubuta mata,
"Kinsan Allah har yanzu bai shigo ba. Nagaji, gashi bakiji idanu na ba bacci nake ji. Ga maganar da bamu Kai karshe ba." Ta tura mata
"Kema na gaya miki ki turo wannan kudin a buga sammako aje miki . Aikinsa tamkar yankan wuka yake Allah." Ta turo Mata reply.
Murmushi tayi tana girgiza Kai ta mayar mata da,
"Ba damuwa. Ina tunanin yau da daddare ko zuwa da safe zan turo miki. Maybe ma ta account din baban su"
"To shikenan mu kwan lafiya"
"To shikenan kawata. Sai kin ji ni"
Kashe data din tayi ta ajiye wayar a gefe. Tana ta zaune tana sakin tsaki duk bayan yan mintina.
Can tajiyo karar horn din mota da budewar gate. Shine ya dawo ta daga kai ta dubi lokaci a agogo tana sakin kwafa.
Mikewa tayi ta bude kofar parlorn ta zauna..Ba dadewa sai ga shi nan ya shiga bakinsa dauke da sallama
Ta amsa.sallaamr tana kauda Kai. Murmushi yayi yana karasawa inda take ya zauna a gefe yana Saka hannu hadi da karkatar da fuskar ta zuwa gare shi. Domin kauda Kai tayi tana duban gefe tayi masa banza daga amsa sallamar datayi bata kara cewa komai ba
Sarai ya gano fushi tayi. Don haka ya murmusa kawai yana cire hular kansa ya ajiye a gefe. Hadi da daukar remote din ac ya kara sanyin yana sauke numfashi.
"Hajjaju ayi hakuri mana"
"Haba Alhaji tun dazu sai jiran ka nake saboda Allah ga bacci ya isheni, ga maganar da bamu Kai karshe ba. Kawai kaje ka zauna koma inane saboda Allah sai yanzu zaka waiwayo gidah duba karfe nawa fa dan Allah."
Alhaji sambaso ya muskuta ya kamo hannunta tanata turjewa ya zaro ATM card dinsa ya dora akan cinyar ta.
"Da farko dai kafin na fara baki hakuri ga atm card nan kinsan pin din ki sayi dukkanin abunda kike so. Idan transfer kike so ga wayata ki shiga mobile app ki tura.. kinji?"
San murmushi tayi. Dama kuwa tana son ta tura wa kawarta kudi amata aikin data sakata. Ta karbi wayar tasa ta shiga mobile app ta danna code ta Saka adadin kudin da take so tayi transfer zuwa asusun bankin ta.
"A kawo abinci?" Ta tambaye shi tana mikewa tsaye.
Kamo hannunta yayi yakomar da ita ta zauna yana duban fuskar ta yace,
"Gidan mutanen ki naje. Har take cemun na miko miki gaisuwar ta. Nache ai dama kince mun na mika gaisuwar ki kwando kwando na manta.. "
Dan tsaki tayi tana yamutsa fuska tace,
"Nagan ta ai tanata wani feleke a group chat dinmu. Ko sunanta bansan a kira"
"Mu dai cigaba da daurewa dai ... Muna tafiya kasar waje ai shikenan sai sanda muka waiwayo kuma. "
"Meya kai ka can din? "
"Hmm kinsan sai ana sara ana duban bakin gatari. Na dan je wajen Abubakhar ne a site, da fari na je asibitin su baya nan. Sai na biya site anan na same shi. Nake dan bugar cikin sa. Yana nan dai akan bakan sa. Shi ya hakura da kadarorin nan waye waye abar ma maaganar. "
Dr bintu ta fadada murmushin ta tana sake matsawa kusa da shi tache,
"Mashaa Allah. Abu yayi. Toh ita kuma uwar feleken fa? Allah izzarta ta isheni"
"Mutuniyar ki uhm. Ni kinga sunan nata ma ya bace abaki na"
"Qibdiyya. "
"Yauwa Mariya Qibdiyya. Itama ta cemun abar zancen nan kawai sun hakura. Waye waye ai da basusan zasu mallake su ba. shima Abubakhar din yana cewa rayuwar baya data yanzun agidan sa ba ta canza ba, komai da suke ci suke sawa suke bayarwa yana nan baa abunda ya sauya. "
"Yan renin hankali, banzaye... Ayi dai mu gani. Ai dan ragowar kadarorin nasu ma da sannu sai sun wayi gari babu. "
"To kinga dai case dinnan ma an rufe shi. Babu babun sa a agabanmu yanzu. Dan har nake ce masa idan yanaso sai ayiwa shareholders magana abashi wasu wuraren ya biya 20 percent ya nuna a'a"
"Kai ma meye na ka na cewa haka? yanzu da sun amince fa?"
"Bintu tawa kenan. Yo ai idan baka iya taka sahun barawo ba shi zai ya batar dakai.. ai duk cikin shiri ne. Banda abinki daya amince ma 20 percent din da zaa ce ya kawo ma manyan wasu kudade zaa kirawo masa dabazai iya saya ba kingane? "
"Oh yanzu naji batu...nagane"
" Hmm ai kadan ma ya fara gani. Kawai dai for now zamu kyale shi haka. "
"Ina Alhaji ateeks kuwa ya sake maganar kudaden ?"
"Anees kaci abincin da aka kawo? Akwai abunda kake bukata na daban?"
"No komai yayi Mami. Nagode sosai" ya karasa fada yana daga kansa saboda yadda ya dau ciwo da zafi lokaci daya"
"to shikenan... Sai da safe?"
"Eh sai da safe Mami..."
"To Allah ya tashe mu lafiya"
"Aameen Mami" ya katse kiran bayan sunyi sallama..
Tashi yayi dakyar daga kan gadon nasa. Ya nufi inda aka ajiye masa abincin. Warmers ya bubbude baki daya, kwata kwata bashida appetite din abincin.
Tsattsakura yayi a plate kadan yaci ya shanye juice din, sai daya bada rata sosai sannan ya sha tea din ya balla pain killer ya sha.
Wayar sa ya dauka yakira mai kula da sashen da yake, wanda ya kawo masa abincin dazu,
"Ka dauka ka cinye su dika please sai a mayarwa Mami"
"To ranka ya dade. Allah ya saka da Khairan"
"Aameen Wa iyyakum"
Komawa yayi kan gadon ya zauna. So yake abincin yayi digesting sannan ya kwanta, ya so ya dan fita yayi atisaye (exercise) Amman jikin sa ya hanashi saboda weakness ga kuma kansa dake tsananin ciwo.
Counter ya dauka yana istigfari ya jima yana yi har dare yaja sosai. Bacci ya kauracewa idanun sa. Ya dauro tsarki da alwala ya tada sallar tahajjud da niyyyar Allah ya kawo musu sauki acikin dukkanin lamurana su. Ya Kuma magance musu dukkanin damuwar su. Ya Kuma biya musu dukkanin bukatin su na alkhairi, ya kare su da dukkanin kariyar sa. Kuka yake sosai yana rokon Allah ya kawo masa dauki a rayuwar sa. Tun yanayi a zuci har ya fara fitowa fili yanayi,
"Yaa Allah... Nawraah idan har da alkhairi a tarayyar su da marwaan Allah ka shiga cikin lamuran su, ka saukaka musu kasa auren ya zamanto babbar albarka atare dasu da mu baki daya. Yaa Allah idan ba alkhairi bane agare su. Rabbi kayiwa kowannen su zabin abokin zama na gari Aameen.. "
Ya sake daga hannu sama cikin rokan Allah. Wannan karon muryar tasa har rawa ta fara yi,
"Yaa Allah Nawraah, kaunar Nawraah ta mun illa a zuciya ta da gangar jikina baki daya. Yaa Allah ina rokon ka da tsarkakkun kyawawan sunayen ka cassa'in da Tara. Ya Allah kai ka iya kai zakayi, Yaa Allah nayi tawassali da kai, kai na a duqe, ni bawa ne agare ka domin kai din mubuwayi ne gagara misali, Rabbi ka dubeni ka zare mun kaunar Nawraah a zuciyata. Yaa Allah ina cikin damuwa Yaa Rabbi banida tsimi banda dabara. Yaa Allah ka iya mun Allah ka ciremun tunanin Nawraah, Yaa Allah ka dubeni . Yaa Allah na kamu da kaunar Nawraah. Kaunar da ta gauraye ilahirin jikina da kewaye. Yaa Allah ka kawo mun sauki. Ka zabar mun abunda yafu dacewa da ni, na daga mafificin alkhairi agare ni. Komai nawa Yaa Allah I entrust all my affairs to you..." Yana kaiwa karshe ya kifa kansa, don ji yayi baki dayan gabobin sa tamkar ana sassara su. Dakyar ya iya komawa kan gado ya kwanta bayan yayi addu'oin bacci.
Sai kuma Allah ya temaka ya na kwanciyar ba dadewa bacci yayi awun gaba da shi...
Bayan dawowar Dr abubakhar dollars. Hajiya Qibdiyya mai dakinsa ta temaka masa yayi wanka ya sauya kaya zuwa na bacci. Yaci abinci da drinks. Bayan ya bada rata kuma ya sha tea. Daga nan suka shiga hira da mai dakin nasa. Sai data tabbatar ya samu nutsuwa sannan ta sanar masa dukkanin komai tundaga farko zuwa karshe. Yayi matukar mamaki matuka gaya. Don abun ya girgiza shi sosai fiye da yadda alkalami zai bayyana.
A daren kuma suka shirya yadda komai zai kasance sannu ahankali har su cimma burikan su.... A ranar dai Kam zukatan mutane da yawa basu samu nutsuwa ba. Idanuwa suka kafe. Bacci ya kauracewa idanuwan su. Wasun su sukayi sallar dare wajen neman zabin alkhairin Allah a dukkanin lamuran su...
***
ALHAJI SAMBASO AVENUE....
Tun tuni take jiran dawowar sa shiru shiru bai waiwayo gidah ba, dare ya ja sosai ainun. Ta sake duban agogon dake like ajikin bango. Ta sake sakin wani tsakin a karo na ba adadi....
_ADVERT👇👇_
_YERWA INCENSE AND MORE_
_(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_
_INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_
_TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_
_MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_
_*YERWA INCENSE AND MORE*_
_DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._
_AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_
_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._
_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_
_NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_
_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_
_K'K'J_
_(M/W/S)_
_BOOK TWO_
_✍️:MX_
_29_
:::::::::
*Daga* Kai tayi ta dubi agogon dake like a jikin parlorn da take a zaune. Shiru har yanzu bai dawo ba.
Whatsapp ta shiga kan sunan kawar tata ta rubuta mata,
"Kinsan Allah har yanzu bai shigo ba. Nagaji, gashi bakiji idanu na ba bacci nake ji. Ga maganar da bamu Kai karshe ba." Ta tura mata
"Kema na gaya miki ki turo wannan kudin a buga sammako aje miki . Aikinsa tamkar yankan wuka yake Allah." Ta turo Mata reply.
Murmushi tayi tana girgiza Kai ta mayar mata da,
"Ba damuwa. Ina tunanin yau da daddare ko zuwa da safe zan turo miki. Maybe ma ta account din baban su"
"To shikenan mu kwan lafiya"
"To shikenan kawata. Sai kin ji ni"
Kashe data din tayi ta ajiye wayar a gefe. Tana ta zaune tana sakin tsaki duk bayan yan mintina.
Can tajiyo karar horn din mota da budewar gate. Shine ya dawo ta daga kai ta dubi lokaci a agogo tana sakin kwafa.
Mikewa tayi ta bude kofar parlorn ta zauna..Ba dadewa sai ga shi nan ya shiga bakinsa dauke da sallama
Ta amsa.sallaamr tana kauda Kai. Murmushi yayi yana karasawa inda take ya zauna a gefe yana Saka hannu hadi da karkatar da fuskar ta zuwa gare shi. Domin kauda Kai tayi tana duban gefe tayi masa banza daga amsa sallamar datayi bata kara cewa komai ba
Sarai ya gano fushi tayi. Don haka ya murmusa kawai yana cire hular kansa ya ajiye a gefe. Hadi da daukar remote din ac ya kara sanyin yana sauke numfashi.
"Hajjaju ayi hakuri mana"
"Haba Alhaji tun dazu sai jiran ka nake saboda Allah ga bacci ya isheni, ga maganar da bamu Kai karshe ba. Kawai kaje ka zauna koma inane saboda Allah sai yanzu zaka waiwayo gidah duba karfe nawa fa dan Allah."
Alhaji sambaso ya muskuta ya kamo hannunta tanata turjewa ya zaro ATM card dinsa ya dora akan cinyar ta.
"Da farko dai kafin na fara baki hakuri ga atm card nan kinsan pin din ki sayi dukkanin abunda kike so. Idan transfer kike so ga wayata ki shiga mobile app ki tura.. kinji?"
San murmushi tayi. Dama kuwa tana son ta tura wa kawarta kudi amata aikin data sakata. Ta karbi wayar tasa ta shiga mobile app ta danna code ta Saka adadin kudin da take so tayi transfer zuwa asusun bankin ta.
"A kawo abinci?" Ta tambaye shi tana mikewa tsaye.
Kamo hannunta yayi yakomar da ita ta zauna yana duban fuskar ta yace,
"Gidan mutanen ki naje. Har take cemun na miko miki gaisuwar ta. Nache ai dama kince mun na mika gaisuwar ki kwando kwando na manta.. "
Dan tsaki tayi tana yamutsa fuska tace,
"Nagan ta ai tanata wani feleke a group chat dinmu. Ko sunanta bansan a kira"
"Mu dai cigaba da daurewa dai ... Muna tafiya kasar waje ai shikenan sai sanda muka waiwayo kuma. "
"Meya kai ka can din? "
"Hmm kinsan sai ana sara ana duban bakin gatari. Na dan je wajen Abubakhar ne a site, da fari na je asibitin su baya nan. Sai na biya site anan na same shi. Nake dan bugar cikin sa. Yana nan dai akan bakan sa. Shi ya hakura da kadarorin nan waye waye abar ma maaganar. "
Dr bintu ta fadada murmushin ta tana sake matsawa kusa da shi tache,
"Mashaa Allah. Abu yayi. Toh ita kuma uwar feleken fa? Allah izzarta ta isheni"
"Mutuniyar ki uhm. Ni kinga sunan nata ma ya bace abaki na"
"Qibdiyya. "
"Yauwa Mariya Qibdiyya. Itama ta cemun abar zancen nan kawai sun hakura. Waye waye ai da basusan zasu mallake su ba. shima Abubakhar din yana cewa rayuwar baya data yanzun agidan sa ba ta canza ba, komai da suke ci suke sawa suke bayarwa yana nan baa abunda ya sauya. "
"Yan renin hankali, banzaye... Ayi dai mu gani. Ai dan ragowar kadarorin nasu ma da sannu sai sun wayi gari babu. "
"To kinga dai case dinnan ma an rufe shi. Babu babun sa a agabanmu yanzu. Dan har nake ce masa idan yanaso sai ayiwa shareholders magana abashi wasu wuraren ya biya 20 percent ya nuna a'a"
"Kai ma meye na ka na cewa haka? yanzu da sun amince fa?"
"Bintu tawa kenan. Yo ai idan baka iya taka sahun barawo ba shi zai ya batar dakai.. ai duk cikin shiri ne. Banda abinki daya amince ma 20 percent din da zaa ce ya kawo ma manyan wasu kudade zaa kirawo masa dabazai iya saya ba kingane? "
"Oh yanzu naji batu...nagane"
" Hmm ai kadan ma ya fara gani. Kawai dai for now zamu kyale shi haka. "
"Ina Alhaji ateeks kuwa ya sake maganar kudaden ?"