← Book details Jawaheer Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 45

Sashe 24

Jawaheer Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Washe gari tunda jawaheer tayi sallah asuba take ta kallon wayanta tana tunanin kota kira m samir ne, amma tana tunanin kaman bai dace ta kirashi yanzu ba, dan safiya ne, haka ta zauna akan dadduma harta fara bacci, bata farka ba sai wajan 9 ta ganta akan gado, murmushi tayi dan tasan mum ce ta kawota gadon, fita tayi ta nufi toilet, tana fitowa taga adda tace ga ruwan wanka nan dama yanzu zan kiraki, jawaheer tace toh yar tsohuwa, ansan ruwan tayi ta shiga toilet din, wanka tayi sannan ta fito ta shirya cikin atamfa riga da skirt ya mata bala'in kyau kaman ba itaba, adda tace kai jawaheer atamfan nan ta miki kyau amma na lura dake kaman ke bakya son irin wannan kayan kin fison kiyi ta shiga kaman ba musulma ba, dariya jawaheer tayi tace lah nice ba musulma ba? To a kunnen mai gidan, dai2 lokacin mlm ya fito yace kyaleta amarya ta kishi takeyi dariya adda tayi tace ni na yafe mata kai, jawaheer tace kaji kishin koh kaman dagaske take, dariya duka sukayi mlm yace yaushe zaku gidan? Mum tace anjima kadan abubakar muke jir..... Bata rufe baki ba saiga sallaman abubakar da m samir sun shigo, gaban jawaheer ne ya fadi kallo daya ya mata ya kawar da kanshi, gaida su mum yayi, itama jawaheer ta gaida uncle dinta, ya amsa sannan ta gaida m samir wanda ya amsa a dakile ba tare daya ko kalleta ba, mum tace ma m samir yaci abinci kuwa? Yace a'a tace ai naga alama murmushi yayi mum ta kalli jawaheer tace kema kije kici abinci kafin mu tafi, sannan ki dauko m samir kayan tea tace to, kitchen din adda ta nufa ta hada mishi kayan tea tare da soya mai akwai, falo takai mai shi daya ne a falon su mum na waje suna fira, ajiye mai tayi tare da fara kokarin hada mishi yace no leave it zanyi da kaina, sororo tayi tare da ajiye spoon din jiki a sanyaye, tana son yin magana taji yana fadin gobe zamu tafi abuja, da sauri ta dago tana kallonshi amma shi ba ita yake kallo ba, tace da wuri haka, bana tunanin zan biku gaskiya wani irin kallo ya mata da yasa tayi saurin yin qasa da kai, adda ce ta shigo tace jawaheer kuyi sauri mana, fada mishi dan Allah tunda baji nama yake ba, cikin sanyin murya tace ance kayi sauri muje, kai ya daga alaman yaji, tashi tayi itama ta fita waje da ido ya bita harta bace mai sannan ya lumshe ido, tana tafiya yaji abincin ya isheshi dan haka tashi yayi ya fita shima, uncle abubakar yace zaije kasuwa bada shi zasu ba, mum da adda suka shiga mota daya jawaheer da m samir kuma mota daya, sai security din dake mara musu baya, sai sharara gudu mota takeyi amma babu mai cewa komai, wayan jawaheer ne ya fara kara dan haka ta duba taga number ne, mamaki tayi toh wa yasan number dinta ita dai tasan bata kira kowa ba, har kiran ya tsinke wani kiran ya kara shigowa ta kalli m samir taga ba ita yake kallo ba dan haka ta dauka, tana dauka taji anyi mata sallama ta amsa yace nasan baki ganeni ba koh? Tace eh, yace dr ne, harga Allah ta manta ta bashi number dinta, tace eyya yaka koma gida? Yace lafiya qalau sai dai na tafi da tunaninki, tayi dan murmushi wanda a dai2 lokacin m samir ya waigo suka hada ido, wani irin kallo ya mata wanda yasa tayi saurin juyar sa kanta gefe, ci gaba tayi da wayan taji an fisge, da sauri ta waigo taga yana watsa mata wani irin kallo, yace dawa kike waya? Tace friend dina, yace ok daka yanzu in zakiyi waya a gabana karki karayin wani yare sai english, bata ce mai komai ba ya jefa mata wayan tare dayin tsaki kadan, bai kara ko kallonta ba balle ya mata magana wayanta ne ya fara kara, ganin number din dr yasa ta kashe wayan gaba daya, tafiya suke har suka karasa wani dangareren gida sukai horn mai gadi ya bude, suka shiga ciki bayan an faka suka fito, m samir yana fita baiko bi takan jawaheer ba ya nufi wajan su mum, jawaheer kam canjin da yake nuna mata ya fara damunta domin taga yana nuna halin ko in kula da ita tun jiya, amma koma dai miye yau sai taji miye dalili, shiga gidan sukayi wani dangareren falo suka shiga wanda yaji kayan more rayuwa, adda salati ta fara tana fadin ina zamu kai wannan gida? Dariya su mum suke ta mata suna fadin adda an zama yan gayu, gidan yayi bala'in haduwa gashi gidan sama, falo biyu ne a 'kasa sai daki daya a kasan, sama kuma falo daya ne sai daki uku a saman, fadin tsaruwan gidan bata bakine, adda harda hawaye tana ta sama m samir albarka tare dasu mum, tace jiba abunda muke ta kyama gashi yazo duniya ya bamu babban kyauta, haja taita mai godiya shidai murmushi yake tayi dan bai san mai take fada ba, adda tace babu abunda za'a sa a gidan hakan ya isa, mum tace shikenan dan itama taga babu abunda gidan yake bukata, haka suka fito da fadin zasu sa ranan dawowa, shiga mota sukayi dan tafiya gida, suna cikin tafiya jawaheer ta kalli m samir tace Allah ya biyaka gidan yayi kyau sosai, banza da ita yayi, ji tayi kaman tayi ihu dan takaici, ta bude baki zata kara magana taji yace mai adda take fada dazu? Dadi taji koba komai ya mata magana, tace godiya take maka tare da addu'a, dan murmushi yayi sannan yace ok, ya ciro wayanshi ya danna wasu numbers jim kadan yace dad yakake, shuru yayi sannan yace dad komai normal nan ya fara bashi labari dad din yaji dadi sosai tare da fadin ina jawaheer baice komai ba taga ya mika mata waya, amsa tayi tare da fadin hello dad yace yarinya ta yakike? Amsawa tayi tare da gaidashi nan suka taba fira tana ta dariya daka karshe sukai sallama, ta mika mai wayan sawa yayi a kunne ban san mai dad din ke fada mishi ba naji yace ok dad ba damuwa gobe zamu koma abuja muma, yana fadin haka sukai sallama, kallon jawaheer yayi suka hada ido murmushi ta sakar mai tare da fadin wai mai nayi maka kake shareni? Dan tsaki yayi tare da fadin babu komai, tace toh mai yasa kake shareni? Yace haka kawai bana son damuwa, sakan baki tayi tana kallonshi wato nice damuwa ma, dan tsaki tayi wanda bata san ya fito ba jin hannunshi tayi a bakinta yaja tare da fadin wa kike ma tsaki? Kasa magana tayi dan ya riqe mata lebe, ganin yanda tayi da ido kaman zatai kuka yasa ya sakan mata bakin tare da fadin karki kara min tsaki i hate it, bata ko kalleshi ba balle yasa ran zata bashi amsa, yau ce rana ta farko daya taba bata haushi, danme zai dinga wani shareta ba tare da tamai komai ba, inda yasan yanda ta shiga cikin damuwa aida bai mata haka ba, ido ta lumshe kaman mai bacci, bini bini ya kalleta ganin kaman tayi bacci yasa ya kura mata ido tare da fadin slp beauty, tafiya mota keyi tana sharara gudu, jin tsayuwar motar ne yasa ta bude ido mai yakon ta ganta a gidan adda saita ganta a hotel din da yake kwana, kallonshi tayi suka hada ido, kawar da kanshi yayi tare da fadin muje, kaman ba zata fita ba, komai ta tuna kuma ta fito suka shiga tana biye dashi a baya, dakin da ta sauka tai niyan nufa taji ya janyota sukai dakinshi akan gadon dakin ya ajiyeta, toilet ya nufa yayi wanka jim kadan sai gashi daka shi sai towel ga kuma wani karami yana goge kanshi dashi, kallonshi tayi, tayi saurin kawar da kai, murmushi yayi tare da matsawa kusa da ita ya mika mata karamin towel din yace gashi ki gogemin, kin amsa tayi ganin haka ya kamo hannunta ya mika mata towel din, yace tashi kimin, bata tashi ba sannan bata mai komai ba, yace saboda niba saurayinki bane? Da sauri ta dago kai ganin yanda ya kafeta da ido yasa tayi saurin tashi tare da fadin zan wuce gida, kafada ya daga alaman ke kika sani, ganin yanda ya mata yasa ta fara kokarin fita har takai bakin kofa taji ya riqota tare da fadin wa yace ki tafi? Tace na gaji da zama a nan ne, yace ok to babu inda zaki yau tare zamu kwana ni dake cikin wannan dakin.......

*maryam obam*

*JAWAHEER*

*STORY AND WRITEEN BY......*

*MARYAM ALHASSAN DAN'IYA*
*(maryam Obam)*

*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*

*wattpad @maryam-obam*

*WWW.Maryamobamnovels.com*

https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/

*DEDICATED TO.....*

*Nafisa mrs dan malikin kawo*

Page 35-36
Chapter 24 · 0% Book details